Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
tace zan gani....... kamar daga sama Sarkin fada yace nine shedar akwai ta acikin wannan aiki. Kusan ma itace shugabarmu domin ita tasamu yin wannan aiki, kuma ni inada shedar dazata nunama kowa abinda ma bakusani ba, dama na ajeta sbd irin wannan rana. Ai Gimbiya Zakiyyah batasan lokacin data sauko kasa daga kan kujerar datake ba. Anan Sarkin Fada yatashi yace tabbas ni nasan ayau asirina yagama tonuwa, dan haka banga dalilin bata maku lokaci ba, nasan Allah ya dade yana aramun rana, sede inaso kuyi hakuri da duk abinda zakuji, bakomai bane yasani aikata haka se SON ZUCIYA. Wadda azamanin nayanzu shine abinda yake dawainiya da mutane da dama, wanda kuma bakowa bane yake saka mana son zuciya se shedan, da kuma mu kammu idan muka kasa tsarkake zuciyarmu. Ban kasance mutum nagari ba a masarautar nan, na dade ina aikata abubuwa da dama, sede babu wanda yasani, harzuwa yanzu. Alokacin da aka haifi Yarima Areef, babban dalilin dayasa najawoshi jikina shine dan insalwantar da rayuwarshi, yazamana beda amfani arayuwa gaba daya. Ada nayi niyar kasheshi sede shakuwar damukayi tahana ni, duk da Jakadiya Karima taso akasheshi, nine na hana. Babu irin maganin da ban bashi ba dan kawai inga yazamo dolo agidan nan amma hakan beyuwu ba, abu daya nasan yayi tasiri ajikinshi shine yanda bedamu da sarauta ba. Alokacin daya girma se abun yadawo kaina, tunda yadawo daga karatu na lura bayason ganina, hakan yasa naja baya dashi. Amma sanin naci ribar cire mashi sarauta aranshi hankali na ya kwanta. Wannan kenan. Bayan Jakadiya Karima tazo tasameni akan Gimbiya Zakiyyah tana nemana, bayan naje ita da Medaki suna zaune tafadamun abinda takeso inyi, sunaso insan yanda zanyi inhallaka Fulani da abinda ke cikinta. Aranar da dare itace agurin Sarki, hakan yabamu damar shiga dakin Fulani mu biyu, nina fesa mata abinda yake sa mutum bacci, sede ban fesa mata ba sebayan muntasheta, alokacin taganni seta fara kokarin yimana ihu, hartaji mani ciwo afuska, ganin za,a jimu ne yasani fesa mata maganin, nan take tayi bacci. Kamata mukayi muka fita da ita, muka sata mota, dama munhada baki da masu gadin gate su 2, wato Lado da Mati, hakan yasa suka bude mana kofa muka fita. Munyi tafiya menisa dan seda mukaje wani daji dayake bayan garin Darazo kusa da wata Mabarta, anan muka wurgata cikin wani rami. Sede wanda muka aikata laifin dashi banganshi anan ba, amma inaso ashigomun da amintaccen bawan Sarki Hasheem me kula da komai nashi nacikin gida, shine wanda yatemaka mun mukayi wannan abun. Sarki Hasheem runtse idonshi kawai yayi yana karanto addu,a dan zuciyarshi zafi takeyi, jiyake kamar zata fito. Ganin haka Malam yasa aka miko mashi ruwa yayi addu,a aciki yabama Sarki Qaseem wanda shima kukan yakeyi, yace yabashi. Dakin yayi shiru sautin kukan mutane kawai akeji, jisukeyi kamar almara ce ake fada masu. Bayan anshigo da bawan, anan yaxube yana kuka, yace dan Allah kumun rai wlh Son Zuciya ne da kwadayin abun duniya suka kaini da aikata wannan abu. Waziri yace haka kowa yake fada Son Zuciya, Ai kowa yasan son Zuciya bacinta. Sarkin fada yafiddo wata karamar waya daga aljihunshi yamika ma Waziri yace wannan shine shedar dazata nuna maku akwai sa hannun Zakiyyah acikin duk wani munafunci da akayi, bazan kirata Gimbiya ba sbd tazama tamkar mata agurina. Saurin dafe kai Sarki Hasheem yayi dajin abinda Sarkin fada yafada. Wata waya waxiri yaciro yajona ajikin wayar yahada da T. V ya kunna kowa yamaida hankalinshi akan t,v. Tun daga lokacin dasuke zaune afalon Gimbiya Zakiyyah tana fada masu yanda za,a kawar da Fulani, da duk wani munafunci dasukayi, harzuwa lokacin daya fara neman Medaki, tunda Sarki yaga sunfara aikata masha,a yarufe idonshi, aranshi yana fadin wato dama karya medaki tamashi babu wani fyaden da akayi mata, dama can yar iska ce. Areef kuwa yahana beauty ma ta kalli abinda akeyi, ya kwantar da ita akan cinyarshi yana shafa mata kai, daga haka tayi bacci. Babban abinda ya dagama kowa hankali lokacin da aka nuno sanda suka fara aikata masha,a da Gimbiyyah Zakiyyah. Salati kowa yafarayi, hakan yasa Sarki yabude idonshi, sede yayi dana sanin ganin abinda matarshi da bafadenshi suke aikatawa. Waziri yasa hannu yakashe wayar. Shiru kowa yayi se kukan Gimbiya Zakiyyah dana medaki kawai akeji. Jakadiya Karima ta tashi tace wlh shima akwai abinda befada maku ba, idan bazaku manta ba, alokacin da za,a nada Sarkin fada bashi bane aka zaba ko? Waziri yadaga kai. Nan Jakadiya tashiga basu labarin da Sarkin fada yabata. Mamaki yakama kowa jin irin abinda sarkin fada ya aikata. Hayanice tacika falon. Bayan kowa yanutsu, Waziri yace lallai babu abinda zamuce sede muyi godiya ga Allah wanda shine yake tsaremu aduk inda muke. Tabbas akace dazama da makiyi gara zama da barawo, kuma dama ance makusan cinka shine makashinka. Tabbas kunso kashe abinda Allah yaso yafito duniya, sede babu wanda ya isa ya aikata wani abu seda izinin Allah. Matar da kukaso kashewa da diyarta gasunan araye. Kallon Areef yayi yace daga matar taka kowa yaganta. Murmushi yayi dan seyanzu yafara fita daga duhun dayake ciki, tashin beauty zeyi Malam yace abarta, zata tashi da kanta. Kowa mamakin ganin beauty yakeyi wai itace diyar Fulani, Sarki kam wani irin sanyi yaji yana ratsashi duk da damuwar datake ranshi. Waziri yace akwai bayanin da Malam zeyi mana kafin afadi irin hukuncin daza,ayi ma kowa. Amma zamuje hutu daga nan zuwa bayan azahar dan sallah tagabato, wasu fadawa yasa suka tasa keyar su Gimbiya Zakiyyah, Medaki dasu Jakadiya yace atsaresu. Kuma yasa suhada da mati da Lado. Kuka kawai sukeyi. Sarkin fada kuwa murmushi kawai yakeyi. Matsawa yayi kusa da Gimbiya Zakiyyah yace kinsan akullum tunanin yan sarauta akullum iya karshi harshe, dan basa amfani da tunaninsu sede na bayinsu. Kinga koyanzu ya isa kigane banbanci tsakanin Bawa da me mulki. Kuka tasaka, aka turasu zuwa kurkutu. Nima yakamata inhuta haka kafin sudawo. Ur's. NABILA RABI'U ZANGO (Nabeelert Lady). 08028525263 [23/08, 1:48 p.m.] Nabeelert Lady: ..πŸ›€πŸ›€πŸ•πŸ•πŸ•πŸ›€πŸ›€πŸ›€ AMAKABARTA AKA HAIFENI πŸ›€πŸ›€πŸ•πŸ•πŸ•πŸ›€πŸ›€πŸ›€ (The story of hard kingdom) Nah Marubuciyar Zamani NABILA RABI'U ZANGO (Nabeelert Lady) @House of Novella Association (H,O,N,A) www.NabilaLady5@gmail.com Season 105⚜110 Zaune suke gaba daya harda masu laifi, zuwa wannan lokacin idanunsu haryagaji da zubar hawaye. Sarki Hasheem ya kalli Gimbiya Zakiyya, duk tafita hayyacinta, har seda tabashi tausayi dan yasan halin mahaifiyarta idan hartaji abinda tayi tabbas zata saba mata. Kawar da kanshi yayi ya kalli beauty wadda take haryanzu ajikin Areef, tunda Fulani ta tureta haryanzu taki kara kallonta kuma koda aka dawo sallah agurin Areef ta tsaya, shikam dama haka yakeso, yariketa kamar ance za,a kwaceta. Dan bemanta da halin data shiga ba lokacin da Momynshi tayi mashi fada. Malam yayi gyaran murya yace Alhamdulillahi Allah yakawomu abinda na dade ina fatar Allah yakawomana karshen shi, tabbas masarautar nan tashiga tashin hankali da rudani, wanda zance bacewar Fulani agidan nan tamkar saukowar wani haske ne wanda yazo ya haske duk wani duhu dayake gidan nan. Kuma ya haska duk wasu munafukai dasuke tare da mutanen gidan. Abin mamaki wai ace wanda kayarda dashi yanzu aduniya shine yake cutarka. Gaskiya nayi matukar girgiza dajin wadanda suka aikata wannan ta,asa wai makusantan Sarki ne, acikinsu kaf babu wani bare. Dama haka duniya take, duk wanda zakayima hassada tamkar kana kara kusan tashi da ubangiji ne, domin tunda annabi yasamu makiya to babu wani dan adam din daze iya kubuta daga sharrinsu. Sede abinda nakeso inkara tunatar daku, shine addu,a domin itace makamin mumini, duk da ake cewa bawa baya iya kaucema kaddararshi, amma idan muka rike addu,a babu abinda bazata yimana ba. Addu,a takan canza sharri yazama khairi, kuma tanasa tsanani yazama sauki, dan haka koda Allah ya kaddaro maka wata kaddara marar kyau, idan har karike addu,a abun ze iya zo maka dasauki. Arayuwa baka taba gane makiyinka, harse ranar da asirinshi yatonu. Agskiya Sarkin Fada kabamu mamaki sosai, da irin abubuwan damukaji ka aikata, ba kowane me imani bane ze iya aikata abinda ka aikata. Kaci amanar kanka, addininka, iyayenka, matarka, da kuma Ubangidanka. Duk irin halaccin dayayi maka arayuwa, seda ka ha'inceshi, kashiga gonarshi har 2, duk da haka bata isheka ba seda kayi sanadiyar rugujewar farin cikinshi, tahanyar kauda abinda yake matukar so, kaso ka halakar dasu amma Allah be baka iko ba. Ko kasan ta dalilinka irin ukubar da Fulani da diyarta suka shiga? Mezaka cema Allah aranar gobe kiyama idan yatambayeka akan amana? Ko kasan kalar abincin dasukaci atsawon shekaru 18 acikin MAKABARTA? Ta dalilinka matar da babu ruwanta, bata yima kowa komai ba, amma saboda SON ZUCIYA irin taku kaida mabiyanka kunsa baiwar Allah tahaihu a MAKABARTA. Yarinya ta tashi a MAKABARTA. Bata san kowa ba se Mamanta da kaburbura, da bishiyoyi. Wancen bawan Allah da kuke ganinshi agidan nan badan kowa yake zaune ba sedan farin cikin yarinyar da kukaso ku hanata zuwa duniya. Shine mutum na 2 daya temakeso, wanda badanshi ba haka Yarinya zata girma har shekaru 18 amma batasan komai ba, kuma ita ba hauka ba, barashin lafiya ba. Kawai saboda tsabar SON ZUCIYA irin taku, bara infada maku abinda bakusani ba, kuma zakusan cewar duk zakaran da Allah yanufa da tsara to ko ana muzuru ana shaho se yayi. Idan bakusani ba aranar da kuka wurgar da Fulani acikin dare kuka wurgata cikin rami, to aranar ta haihu, kunsan suwa Allah yaturo mata kawai dan yanason yanuna maku baya bacci? Wasu bayinsa ne, kuma yan uwa musulmai, wadan da suka fito daga jinsin aljanu. Akusa da fadarsu kuka wurgata, kuma cikin ikon Allah alokacin suka temaka mata harta haifi diyarta acikin koshin lafiya. Zakusha mamaki idan nabaku labarin da daya daga cikin aljanun, wanda yakasance shugaba agurinsu, shine yabani labarin abinda yafaru. Bara kuji.... Kaf duk abinda Malam yasani seda yafada masu, gaba daya falon babu wanda beyi kuka ba saboda tausayin Fulani da beauty, kowa ya tausaya masu yanda sukayi rayuwarsu acikin MAKABARTA. Fulani da Beauty sunfi kowa kuka, dan ita beauty tade taso taganta a MAKABARTA. Atunaninta nanne muhallinsu, kuma Fulani ita kadaice wadda tasani, mace, se kuma Baba wanda shima shikadai tasani namiji. Kuka takeyi sosai ayau dataji labarinta, ashe inda take tunanin muhallinsu ne, take cewa acan aka haifeta, ashe muhallin matattune, segashi yanzu ana fadin AMAKABARTA AKA HAIFETA. Malam yace ga Baba nan, shine megadin MAKABARTAR da suke zaune, kuma shine mutumin daya zauna dasu bisa gaskiya da amana, kuma ko matarshi betaba fada mawa ba, harseda yaga lokaci yayi daya kamata yafada mawani, alokacinne yazo yasameni yafadamun......... Duk abinda Baba yafada mashi seda yafada masu, da irin dawainiyar da yayi dasu. Hakanne yasa alokacin da yagama bani labari, mukaje muka daukosu duk da seda wannan aljanu suka rokemu akan mukula dasu idan har wani yakara yunkurin cutar dasu bazasu kyaleshi ba. Tundaga ranar damuka daukosu, nafara tunanin tabbas abinda nagani acikin istaharata yana shige da wadannan bayin Allah, idan baku manta ba Waziri, azuwan da kukayi nafada maku naga Fulani akusa dani, kuma tana raye, sede bansan awane waje take ba. Hakan yasa nafara zargin wannan mata da diyarta zasu iya kasancewa matar Sarki da diyarshi. Amma gudun kada inyi saurin fadar abinda zuciyata take fada mun hakan yasa lokacin da Safeeya tazo mani da alfarmar abata wannan yarinya ta taho da ita nan gidan yasa nayi tunanin barinsu suzo, sena cemata dole sutaho su duka. Hakan yasa naroki alfarma gurin Baba nayabar aikinshi yataho tare dasu. Adaren dazasu tafi nakira Safeeya daki nake cemata ina zargin wani abu akan mutanen nan, itama tace mun zuciyarta tafara saka mata irin abinda nake zargi, dan ita tasan Fulani sosai, amma tacemun bazata iya cewa ita bace dan alokacin ko Sarki yaganta baze iya ganeta ba, tsawon shekaru 18, gashi bacikin hankalinta take ba, kuma bagurin jin dadi ba, babu wankan kirki, babu sallah, ba lallai bane a iya ganeta. Shiyasa nace ma Safeeya sutafi tare, ta ajesu agurinta kuma kada tabari kowa yasan dazamansu idan har tasamu nutsuwa da tsafta zata dawo cikin kamanninta, idan kuma ba ita bace shikenan nace munyi temako. Alokacin nakira Waziri mukayi maganar, dan aduk fadin masarautar nan mutum 3 nafi yarda dasu, kuma yana daya daga cikinsu, Sarki Qaseem, da Sarki Hasheem. Babban dalilin dayasa banyi maganar da Sarki Qaseem ba, nasan yanda halinshi yake, baze taba iya hakura abi abun asannu ba, kamar yanda nashirya, shiyasa ban fada mashi ba. Bayan Safeeya takirani tafadamun tagano wannan mahaukaciyar bakowa bace se Fulani da diyarta, alokacinma nace mata taboye abun harse angano wadanda suka aikata mata haka. Nakira Waziri nafada mashi, kuma alokacin yake fadamun yafara zargin Sarkin Fada. Ni nace mashi yacigaba da bibiyarshi harse ansamu cikakkiyar shedar dazata bada damar kamashi sannan, kuma nafada mashi bashi kadai bane dole akwai wata ko wani makusancin Sarki. Alokacin seyake cemun shifa yana zargin Jakadiya Karima. Nima nayarda da abinda yafada, hakan yasa nace mashi ya zuba masu ido su duka biyun. To Alhamdulillahi yau gashi damukayi hakuri Allah yanuna mana makiyanmu afili. Sede kuma akwai abu daya danakeso intambaya Waziri. Ina wannan bafaden da Sarkin fada yajama sharrin kisa, ina fatan ba,a yanke mashi hukuncin kisa alokacin ba? Gyara zama Waziri yayi yace, alokacin kam Sarki ya yanke mashi hukuncin kisa. Sede ni ajikina bansan meyasa banyarda da hukuncin da Sarki ya yanke ba, kuma zuciyata takasa yarda da cewar shine yayi kisan, amma alokacin kuma zuciyata bata zargin Sarkin fada, sede kawai taki yarda da wanda akace yayi kisan. Hakan yasa naja Sarki falo tafada mashi da kada ya yanke hukuncin dazezo yadameshi daga baya, nine nabashi shawarar daya yanke mashi hukuncin daurin rai da rai. Kuma haka akayi, haryanzu yana nan akurkutun gidan nan. Sede tun lokacin dana fara zargin Sarkin fada da rashin gaskiya acikin gidan nan, tun daga ranar nafara kaimashi ziyara, mukan zauna muyi fira,acikin zaman damukayi ne, nakara yarda dabashine yayi kisan ba, kuma akwanakin baya ne nasa aka canza mashi gurin aiki, harda gurin zama. Kuma tunjiya nasa aka fiddoshi yanzu haka yana masauki. Malam yace kasa akirashi yazo nan. Waziri ya aiki daya daga cikin fadawan gurin. Malam yace wannan shine iyakar abinda nasani agame da rayuwar Fulani da diyarta. Wadda haryanzu babu wanda yasan sunanta. Abinda Baba yake kiranta dashi shine Yar Baba, wanda yacemun ada yaji Fulani tana kiranta da Baby, jin sunan zeyi mashi wahala ne, yake kiranta da diyarshi. Amma ayanzu tunda gashi sundawo gida, za,a iya saka mata sun kuma Waziri se muji daga gareku wane irin hukunci zaku yankema wadannan maciya amanar. Sallamar bafaden da aka aika ne tasasu kallon kofa, tare suke da wanda aka likama kisan da Sarkin Fada yayi, zama yayi yana kwasar gaisuwa, daka ganshi kasan yajigata, atsawon zaman dayayi akurkutu shekaru dayawa. Kallon Sarki Qaseem da Sarki Hasheem Waziri yayi, domin jin abinda zasu fada. Sarki Qaseem yayi gyaran murya yace, ni babu abinda zance, sede kawai inma Allah godiya daya kawomu karshen wannan matsala damuke ciki. Tabbas wadan nan mutane, kunsamu cikin tashin hankali, babu abinda zance maku se Allah ya isa. Sede abu daya nakeso kusani, hakan da kukayi bashine ze samurika tsoron mutane ba,ko kuma mudena jawo su zuwa jikinmu ba, ai ba,a taba taruwa azama daya, idan wani yazo daniyar cutarka, Allah ze aiko maka dana gari, wanda ze zauna da kai badan komai naka ba, sedan son dayake maka domin Allah. Idan kuka kalli Jakadiya Safeeya da Malam,da Matata da kuma matar Yaya wato Fulani, daga baya muka kara samun Baban Darazo da abokin Yarima wato Haisam. Duka wadan nan dana lissafo babu wanda muka hada jini dashi, kuma babu wanda muka tashi dashi acikin gidan nan. Asalima bamu taba tunanin zasu shigo cikin rayuwarmu ba, sedaga baya muka sansu, kuma duk da basu kasance yan uwa agare mu ba, sun zauna damu tsakani da Allah, babu wanda yakeda niyar cutar damu. Idan muka kalli Malam da kanwarshi, bawai dan sun rasa abinda zasuci bane yasa suka shigo jikinmu. Jakadiya Safeeya tazo gidan nan badan kowa ba sedan bin umarnin yayanta, kuma duk da haka tarika kaskantar da kanta agaremu, wanda inda dan kudine zatazo, ninasan babu abinda ze kawota, dan aduk fadin garin Bauchi, darazo, Gombe, harma da makotanmu mutane dayawa sunsan Malam, kuma kowa yasan babban mutum ne. Idan har kudine, bayada damuwa dasu, asalima yakan dauko wasu suci akarkashin shi. Amma duk da haka suke zama tare damu abisa gaskiya da amana. Wannan kadai ya isa yanuna ma kowa cewa wanda baku hada komai dashi ba, ze iya yimaka abinda makusancinka baze maka ba. Yanzu ku kalli irin cin amanar da akayima Yaya, Gimbiya Zakiyya kinci amanar sarauta, kuma kinci amanar iyayenki, amatsayinki na Uwar gidan yaya amma aka hada baki dake, aka cuceshi, koba komai, mahaifinki da Abbanmu abokan junane sosai, kuma dama sune suka hada aurenku, alokacin Yaya bayasonki amma nayi imani da Allah haryanzu betaba fada maki keba ra,ayinshi bace. Haka yakarbi zabin iyayenmu kuma yazauna dake da gaskiya da amana, segashi daga karshe kinzama butulu, bayan butulci ma harseda kika hada da cin amanar aurenku. Wa iyazubillah, kina matar aure amma kika aikata wannan babban zunubi agidanki. Amma kanki kikai mawa, kuma wlh. Kowace irin alaka ketsakinmu bazata hana ayanke maki hukunci dede da laifinki ba. Kuka tasaka tana fadin natuba, dan Allah kumun rai, wlh duk abinda kuka fada gaskiya ne, amma niban aikata abinda kukagani da son rai na ba. Nide nasan babu abinda na tsana kamar zama guri daya da talaka, kuma ni tunda nake wlh wannan aikin da Sarkin fada yamun shikadai ne, yataba hadani dashi harmukayi magana. Akwai sanda jakadiya Karima tazo tacemun wai Sarkin Fada yana gaisheni. Wlh ku tambayeta idan har zata fadi gaskiya zata fada maku irin cin mutuncin dana mata akan abinda tazo mun dashi, wlh babu wata alaka datake tsakanina dashi, ko aranar danasan munfara aikata sabo dashi, yana shigowa da masifa narufeshi, amma bansan ya akayi daga baya harna bashi hadin kai ba. Dan Allah Sarkin fada kafada masu ba laifina bane. Wani malalacin murmushi Sarkin Fada yayi yadauke idonshi daga kallonta. Sarki Qaseem yace wannan kuma yarage naki, kinsan masarautar nan bata yanke hukunci seta tabbatar da sheda tazahiri, kuma ba mutum daya ba, kowa gurin nan yaga abinda kuka aikata, dan haka ki adana kalamanki. Kallon Medaki yayi, yace kenarasa ma mezance maki, kinfi kowa zama cikakkiyar butulu, kinfi kowa sanin dayanda aka aureki da irin halaccin da Yaya yayi maki, duk da nibanyarda da labarin da mamanki tabada ba, amma sbd sanin girman alkawarin da yaya yadaukar mata, haka mukayi hakuri ya aureki. Amma kirasa da abinda zaki saka mashi se irin wannan cin amanar, kema zakiga sakamakonki. Kuma abinda nakeso dake inaso kifada mana wacece ke? Da kuma asalin garinku. Cikin sheshshekar kuka Medaki tace wlh nima bansan inane asalin garinmu ba, nadesan ayawon damukeyi daga wannan kauyen zuwa wani iyayena suka haifeni. Kuma sanin dana yima iyayena basu bani tarbiya tagari ba, babu ilimin addini bare na boko, to sukansu ma basu damu danasu addininba. Nikaina nafara sanin Sallah ne alokacin dana ke bin wata kawata islamiyarsu, anan nafara sanin addini na, harna fara fahimta sosai, sekawai innata tafara doramun talla, domin ita macece meson kudi. Aduk lokacin dana saida tana siyamun duk abinda nakeso, nima tundaga ranar son kudi,yashiga raina. alokacin kuma na hadu da wani saurayi shine yakara huremun kunne, haryayi nasarar ciremun budurcina, seda muka zubar da ciki har 2, kuma Innata bata tabamun fada ba, wannan shine sanadiyar lalacewar mahaifata. Mahaifina dan caca ne, bedamu da ya rayuwata takeba, shiyasa nakasance tamkar dabbar daji, banida wani takunkumin daze hanani aikata abinda naga dama. Sanadiyar Caca mahaifina yarasa ranshi, mutanen gari suka koremu harmuka hadu daku, Innata tafada maku karya har kuka yarda damu. Tabbas nasan naci amanar mijina, wanda yarufamun asiri, duk da yagane banje da budurcina ba, amma be tsaneni ba, asalima cikin laluma ya tambayani, shima nafada mashi fyade akamun wanda karyane, amma haka ya yarda dani, kuma yacemun beyarda infadama kowaba. Dan Allah kayafe mani, nasan bankasance mace tagari ba, naci amanarka dan Allah kuyafemun. Kuka tasaka wanda seda wasu daga cikin mutanen falon sukaji tausayinta,,,,, hayaniya sukaji awaje, Wazirine da fadawa suka leka. Wani kodaddan mutumi suka gani wanda beda kyan gani, sunata rigima da masu gadi. Waziri yace ku kyaleshi yakaraso, haka yataho yanata zare ido. Yana zuwa yace wani nake nema agidan nan nayi mashi aiki be bani kudina ba. Kuma nafada mashi idan har bebani kudina ba zanzo intona mashi asiri. Murmushi Waziri yayi yace kashigo semuji wa kake nema. Kowa mamakin ganin mutumin daya shigo yakeyi, banda Sarkin Fada wanda yaketa muzurai. Waziri yace munajinka wakake nema?. Yace sunanshi Sarkin Fada, kuma ya kasance daya daga cikin mutanen danake yima aiki, duk wani aikinshi nine nakeyi mashi, anan yarika fadin duk irin asirin dayasashi yayi, harda wanda yayima Areef, dana Jakadiya Karima wanda tazubarma Gimbiya Suhailat ciki kuma aka daure mahaifarta, har yakawo asirin karshe dayayi mashi. Yace aranar yazomun akan yanason inbashi maganin mallakar zuciyar Matar Sarki, Zakiyyah, yacemun yadade yana sha,awarta amma yasan bazata taba bashi kanta ba, hakan yasa yazo inbashi magani, alokacin yacemun beda kudi amma yasan idan yasamu sa,ar kusantarta yamallake zuciyarta zesamu kudi. Tun ranar dana bashi bankara ganinshi ba, shine yanzu nazo inkarbi hakkina. Salati kowa yakeyi, sbd wani abin al,ajabin dasuka karaji yabullo. Murmushi Waziri yayi yace kaima seka samu guri kazauna kajira naka hukuncin tunda Allah yakawoka. Zaro ido boka yayi yana fadin aishikenan kuma wlh nayafe mashi kubarni intafi. Seda yabama kowa dariya, nan fadawa suka zaunar dashi. Se alokacin Sarki Hasheem yayi magana, jikinshi asanyaye yace Malam, kafadi irin hukuncin daya kamata ayima kowa abisa koyarwa ta addinin musulunci, kamar yanda yazo a Qur'ani. Dan nagaji da kallon fuskokin wadannan mutanen. Dan duk acikinsu nafijin haushin mutum daya, bakowa bace se Jakadiya Karima. Allah ya isa tsakanina dake, kin cuceni, wlh zan iya yafema kowa agurin nan amma banda ke, bazan taba iya yafe maki ba. Mundaukeki Uwa asheke makiyarmuce nida dan uwana..... kuka yasaka tamkar karamin yaro. Alokacin hatta da Malam seda yazubar mashi da kwalla sbd yanda yakeyin kuka kowa yasan abun yana cimashi rai sosai. Sarki Qaseem yana kuka yace Malam dan Allah ayanke masu hukunci kada ciwon Yaya yadawo. Malam yace Alhamdulillahi, kamar yanda kuka sani duk wani laifi na duniya babu hukuncin da Alku'ani da hadisi basu kawo ba, dan haka zamu duba muga irin hukuncin da Allah yace ayima masu irin laifinku. Zanfara daga kasa zuwa sama, wato daga masu karamin laifi zuwa babba. Zan fara da masu gadi, mati da Lado, tabbas kun aikata babban kuskure, domin da farko kunci amanar masarauta, sannan kunbada gudummuwa gurin aikata fasadi, dan haka hukuncinku anan shine zakuyi zaman kurkutu natsawon shekaru 2, domin aladabtar daku, sannan baku bakara aiki awata masarauta. Se amintaccen bawan Sarki Hasheem, kaima kaci amanar Uban gidanka, sannan kazamo daya daga cikin wanda yatemaka ma Sarkin fada kuka sace Fulani. Dalili daya ne bazesa ayanke maka hukuncin kisa ba, saboda Fulani bata mutu ba, kuma Qur,ani cewa yayi wanda yakashe akashe shi, sbd haka kaima za,a daureka akurkutu na tsawon shekaru 5, tare da aiki metsanani. Gimbiya Zakiyya, kinkasance matar aure, wadda aka kamaki da laifuka biyu. Nafarko kina da sa hannu abatan Fulani, wanda dakunsami dama kasheta zakuyi. Nabiyu kuma laifin aikata zina. To hukuncin zina anan yakasu kashi 2, akwai na wadda bata tabayin aure ba, wato budurwa, akwai kuma na wadda ta tabayin aure. Idan budurwa tayi zina, kuma aka tabbatar dashedu, za,a yanke mata hukunci bulala 100, idan abokin yinnata shima saurayine, hukuncinsu daya. Matar aure. Duk matar datayi zina kuma tanada aure, ko ta taba yin aure. Hukuncinta kisane, tahanyar jefewa da duwatsu, wanda yara ne zasu jefeta harta mutu, za,a rufe duka jikinta cikin rami abar kanta shine za,ayita jifa harta mutu. Idan abokin zinarta yataba aure, hukuncinsu daya, idan kuma shi beda aure, to nata daban nashi daban. Abisa shedar da muka samu daga gurin wanda yayi maki asirin da kika fada wannan alfasha. Kamar yanda yazo a arba'una hadith, mazon Allah yace INNALLAHA TAJAWAZILI AN UMMATI➑➑ Lallai Allah yagafarta ma al'ummata, AL,,KADAHA... abinda sukayi da KUSKURE. WANNISIYANA... abinda sukayi da MANTUWA. WAMASTUKURUHU ALAIHI... da abinda AKA TURSASASU AKANSHI. Rawahul bukhari wa muslim. Abisa duba da wannan hadisi, sarkin Fada yayi amfani da karfin asiri ta hanayar mallakeki har kika biye mashi kuka aikata alfasha. Abisa wannan hadisi, anan bakida laifi agurin aikata wannan zina. Dan haka bazaki dauki hukuncin zina ba anan. Sede hukuncin dazaki dauka na aikata laifin cin amana gurin niyar salwantar da rayuwar Fulani, dan haka zakiyi zaman kurkutu shekara 5. Saura hukunci kuma yarage ga mijinki. Tunkafin yacigaba Sarki Hasheem yace Malam da ita da Medaki duk nayanke igiyara aurena akansu, dan haka kacigaba da yanke hukuncinka. Hannu Zakiyyah ta dora akai tana kuka. Malam yace Medaki, kema hukuncinki biyu ne. Amma tunda nakarshen megaba daya ne, to hukunci daya zamu yanke maki, naki hukuncin kisa ne, tahanyar jefewa, tunda ke kin amsa kece kika bama sarkin Fada hadin kai da kanki. Dan haka hukuncin kisa zaki dauka. Jakadiya Karima kema hukuncin kisa ne akanki, sbd kin aikata kisan kai domin kinsa anzubar da cikin Gimbiya Suhailat. Anyanke maki hukuncin kisa daurin rai da rai akurkutu, tare da horo metsanani. Boka, kaima hukuncin kisa ne, ta hanyar rataya, tunda ka amsa laifinka, kuma Allah kadai yasan iyakar ta,asar dakayi. Hukuncinmu na karshe akan Sarkin fada, kai kam da ana mutuwa adawo to da seka karbi duka hukuncinka. Amma hukuncinka anan shine kisa ta hanyar rataya. Anan muka kawo karshen wannan hukunci na MASARAUTAR BUBAYERO. Inafatan hukunci yayi maku, idan kuma akwai wani abu kuna iya fada, yajuya yana kallon Sarki. Sarki Qaseem yakalli Yayanshi. Kai yadaga alamun hukunci yayi, sannan yace kuma agobe za,a aiwatar da wannan hukunci. Ihu Gimbiya Zakiyyah tasaka kamar meshirin shiga hauka, Medaki da Jakadiya ma kuka kawai sukeyi kamar ransu zefita. Haka aka kara tasasu zuwa kurkutu kafin gobe. Nima nace Allah yakaimu goben da rai da lafiya. Ur's. NABILA RABI'U ZANGO (Nabeelert Lady) 08028525263 [23/08, 1:48 p.m.] Nabeelert Lady: ..πŸ›€πŸ›€πŸ•πŸ•πŸ•πŸ›€πŸ›€πŸ›€ AMAKABARTA AKA HAIFENI πŸ›€πŸ›€πŸ•πŸ•πŸ•πŸ›€πŸ›€πŸ›€ (The story of hard kingdom) Nah Marubuciyar Zamani NABILA RABI'U ZANGO (Nabeelert Lady) @House of Novella Association (H,O,N,A) www.NabilaLady5@gmail.com Season 110⚜115 Kusa da Baban Darazo Fulani ta matsa, idanunta haryanzu basu dena zubar da kwalla ba, dukawa tayi har kasa tace, Baba hakika banida bakin dazanyi maka godiya, kayimun abinda bakowa ne dan Adam bane ze iya yimani shi. Tabbas kazamo daya daga cikin mutane masu muhimmanci arayuwata, kuma daga yau inaso kadaukeni tamkar diyarka ta cikinka, inaso kadauko duka iyalanka kudawo nan dazama dan suma sunzama yan uwana. Baba yace babu komai Fulani, duk abinda nayi maki nayi shine dan Allah, banyi dan wani abu naku ba, asalima bansan wane irin matsayi gareki ba. Hakika naji dadin yanda kika dauke ni, kuma nagode Allah yasaka da alkhairi. Haka kowa yatashi yanufi bangarenshi kafin gobe da safe. Haisam ya kalli Areef yace abokina nizan tafi gida, amma dole gobe indawo in kalli wasan daza,ayi agidan nan. Tabbas nakara daukar darasi agidanku. Allah yakara mana karfin imani kuma yacire mana SON ZUCIYA. Areef yace amin, nima kaina abubuwan gidan nan sun gama daga mun hankali, naji tausayin beauty na sosai, ta dalilin masu SON ZUCIYA tarasa ingantatacciyar rayuwa da kowane dan Adam masu galihu

Chapter 10 of 13