tace zan gani....... kamar daga sama
Sarkin fada yace nine shedar akwai ta acikin wannan aiki.
Kusan ma itace shugabarmu domin ita tasamu yin
wannan aiki, kuma ni inada shedar dazata nunama kowa
abinda ma bakusani ba, dama na ajeta sbd irin wannan
rana. Ai Gimbiya Zakiyyah batasan lokacin data sauko
kasa daga kan kujerar datake ba.
Anan Sarkin Fada yatashi yace tabbas ni nasan ayau
asirina yagama tonuwa, dan haka banga dalilin bata
maku lokaci ba, nasan Allah ya dade yana aramun rana,
sede inaso kuyi hakuri da duk abinda zakuji, bakomai
bane yasani aikata haka se SON ZUCIYA.
Wadda azamanin nayanzu shine abinda yake dawainiya
da mutane da dama, wanda kuma bakowa bane yake
saka mana son zuciya se shedan, da kuma mu kammu
idan muka kasa tsarkake zuciyarmu.
Ban kasance mutum nagari ba a masarautar nan, na
dade ina aikata abubuwa da dama, sede babu wanda
yasani, harzuwa yanzu. Alokacin da aka haifi Yarima
Areef, babban dalilin dayasa najawoshi jikina shine dan insalwantar da rayuwarshi, yazamana beda amfani
arayuwa gaba daya.
Ada nayi niyar kasheshi sede shakuwar damukayi tahana
ni, duk da Jakadiya Karima taso akasheshi, nine na hana.
Babu irin maganin da ban bashi ba dan kawai inga
yazamo dolo agidan nan amma hakan beyuwu ba, abu
daya nasan yayi tasiri ajikinshi shine yanda bedamu da
sarauta ba.
Alokacin daya girma se abun yadawo kaina, tunda
yadawo daga karatu na lura bayason ganina, hakan yasa
naja baya dashi. Amma sanin naci ribar cire mashi
sarauta aranshi hankali na ya kwanta.
Wannan kenan.
Bayan Jakadiya Karima tazo tasameni akan Gimbiya
Zakiyyah tana nemana, bayan naje ita da Medaki suna
zaune tafadamun abinda takeso inyi, sunaso insan yanda
zanyi inhallaka Fulani da abinda ke cikinta. Aranar da
dare itace agurin Sarki, hakan yabamu damar shiga
dakin Fulani mu biyu, nina fesa mata abinda yake sa
mutum bacci, sede ban fesa mata ba sebayan
muntasheta, alokacin taganni seta fara kokarin yimana ihu, hartaji mani ciwo afuska, ganin za,a jimu ne yasani fesa mata maganin, nan take tayi bacci.
Kamata mukayi muka fita da ita, muka sata mota, dama
munhada baki da masu gadin gate su 2, wato Lado da
Mati, hakan yasa suka bude mana kofa muka fita. Munyi
tafiya menisa dan seda mukaje wani daji dayake bayan
garin Darazo kusa da wata Mabarta, anan muka wurgata
cikin wani rami.
Sede wanda muka aikata laifin dashi banganshi anan ba,
amma inaso ashigomun da amintaccen bawan Sarki
Hasheem me kula da komai nashi nacikin gida, shine
wanda yatemaka mun mukayi wannan abun.
Sarki Hasheem runtse idonshi kawai yayi yana karanto
addu,a dan zuciyarshi zafi takeyi, jiyake kamar zata fito.
Ganin haka Malam yasa aka miko mashi ruwa yayi
addu,a aciki yabama Sarki Qaseem wanda shima kukan
yakeyi, yace yabashi.
Dakin yayi shiru sautin kukan mutane kawai akeji,
jisukeyi kamar almara ce ake fada masu. Bayan anshigo
da bawan, anan yaxube yana kuka, yace dan Allah
kumun rai wlh Son Zuciya ne da kwadayin abun duniya
suka kaini da aikata wannan abu. Waziri yace haka kowa
yake fada Son Zuciya, Ai kowa yasan son Zuciya bacinta.
Sarkin fada yafiddo wata karamar waya daga aljihunshi
yamika ma Waziri yace wannan shine shedar dazata
nuna maku akwai sa hannun Zakiyyah acikin duk wani
munafunci da akayi, bazan kirata Gimbiya ba sbd tazama
tamkar mata agurina. Saurin dafe kai Sarki Hasheem yayi dajin abinda Sarkin fada yafada.
Wata waya waxiri yaciro yajona ajikin wayar yahada da
T. V ya kunna kowa yamaida hankalinshi akan t,v. Tun
daga lokacin dasuke zaune afalon Gimbiya Zakiyyah tana
fada masu yanda za,a kawar da Fulani, da duk wani
munafunci dasukayi, harzuwa lokacin daya fara neman
Medaki, tunda Sarki yaga sunfara aikata masha,a yarufe
idonshi, aranshi yana fadin wato dama karya medaki
tamashi babu wani fyaden da akayi mata, dama can yar
iska ce. Areef kuwa yahana beauty ma ta kalli abinda
akeyi, ya kwantar da ita akan cinyarshi yana shafa mata kai, daga haka tayi bacci.
Babban abinda ya dagama kowa hankali lokacin da aka
nuno sanda suka fara aikata masha,a da Gimbiyyah
Zakiyyah. Salati kowa yafarayi, hakan yasa Sarki yabude idonshi, sede yayi dana sanin ganin abinda matarshi da
bafadenshi suke aikatawa. Waziri yasa hannu yakashe
wayar.
Shiru kowa yayi se kukan Gimbiya Zakiyyah dana medaki
kawai akeji. Jakadiya Karima ta tashi tace wlh shima
akwai abinda befada maku ba, idan bazaku manta ba,
alokacin da za,a nada Sarkin fada bashi bane aka zaba
ko? Waziri yadaga kai. Nan Jakadiya tashiga basu labarin
da Sarkin fada yabata.
Mamaki yakama kowa jin irin abinda sarkin fada ya
aikata. Hayanice tacika falon. Bayan kowa yanutsu,
Waziri yace lallai babu abinda zamuce sede muyi godiya
ga Allah wanda shine yake tsaremu aduk inda muke.
Tabbas akace dazama da makiyi gara zama da barawo,
kuma dama ance makusan cinka shine makashinka.
Tabbas kunso kashe abinda Allah yaso yafito duniya,
sede babu wanda ya isa ya aikata wani abu seda izinin
Allah. Matar da kukaso kashewa da diyarta gasunan
araye. Kallon Areef yayi yace daga matar taka kowa
yaganta.
Murmushi yayi dan seyanzu yafara fita daga duhun
dayake ciki, tashin beauty zeyi Malam yace abarta, zata tashi da kanta. Kowa mamakin ganin beauty yakeyi wai
itace diyar Fulani, Sarki kam wani irin sanyi yaji yana ratsashi duk da damuwar datake ranshi.
Waziri yace akwai bayanin da Malam zeyi mana kafin
afadi irin hukuncin daza,ayi ma kowa. Amma zamuje
hutu daga nan zuwa bayan azahar dan sallah tagabato,
wasu fadawa yasa suka tasa keyar su Gimbiya Zakiyyah,
Medaki dasu Jakadiya yace atsaresu. Kuma yasa suhada
da mati da Lado.
Kuka kawai sukeyi. Sarkin fada kuwa murmushi kawai
yakeyi.
Matsawa yayi kusa da Gimbiya Zakiyyah yace kinsan
akullum tunanin yan sarauta akullum iya karshi harshe,
dan basa amfani da tunaninsu sede na bayinsu. Kinga
koyanzu ya isa kigane banbanci tsakanin Bawa da me
mulki. Kuka tasaka, aka turasu zuwa kurkutu.
Nima yakamata inhuta haka kafin sudawo.
Ur's.
NABILA RABI'U ZANGO
(Nabeelert Lady).
08028525263
[23/08, 1:48 p.m.] Nabeelert Lady: ..π€π€ππππ€π€π€
AMAKABARTA AKA HAIFENI
π€π€ππππ€π€π€
(The story of hard kingdom)
Nah
Marubuciyar Zamani
NABILA RABI'U ZANGO
(Nabeelert Lady)
@House of Novella Association
(H,O,N,A)
www.NabilaLady5@gmail.com
Season 105β110
Zaune suke gaba daya harda masu laifi, zuwa wannan
lokacin idanunsu haryagaji da zubar hawaye. Sarki
Hasheem ya kalli Gimbiya Zakiyya, duk tafita hayyacinta, har seda tabashi tausayi dan yasan halin mahaifiyarta
idan hartaji abinda tayi tabbas zata saba mata.
Kawar da kanshi yayi ya kalli beauty wadda take haryanzu ajikin Areef, tunda Fulani ta tureta haryanzu
taki kara kallonta kuma koda aka dawo sallah agurin
Areef ta tsaya, shikam dama haka yakeso, yariketa kamar ance za,a kwaceta. Dan bemanta da halin data shiga ba
lokacin da Momynshi tayi mashi fada.
Malam yayi gyaran murya yace Alhamdulillahi Allah
yakawomu abinda na dade ina fatar Allah yakawomana
karshen shi, tabbas masarautar nan tashiga tashin
hankali da rudani, wanda zance bacewar Fulani agidan
nan tamkar saukowar wani haske ne wanda yazo ya
haske duk wani duhu dayake gidan nan. Kuma ya haska
duk wasu munafukai dasuke tare da mutanen gidan.
Abin mamaki wai ace wanda kayarda dashi yanzu
aduniya shine yake cutarka. Gaskiya nayi matukar girgiza dajin wadanda suka aikata wannan ta,asa wai
makusantan Sarki ne, acikinsu kaf babu wani bare.
Dama haka duniya take, duk wanda zakayima hassada
tamkar kana kara kusan tashi da ubangiji ne, domin
tunda annabi yasamu makiya to babu wani dan adam
din daze iya kubuta daga sharrinsu.
Sede abinda nakeso inkara tunatar daku, shine addu,a
domin itace makamin mumini, duk da ake cewa bawa
baya iya kaucema kaddararshi, amma idan muka rike
addu,a babu abinda bazata yimana ba.
Addu,a takan canza sharri yazama khairi, kuma tanasa
tsanani yazama sauki, dan haka koda Allah ya kaddaro
maka wata kaddara marar kyau, idan har karike addu,a
abun ze iya zo maka dasauki. Arayuwa baka taba gane
makiyinka, harse ranar da asirinshi yatonu.
Agskiya Sarkin Fada kabamu mamaki sosai, da irin
abubuwan damukaji ka aikata, ba kowane me imani
bane ze iya aikata abinda ka aikata. Kaci amanar kanka, addininka, iyayenka, matarka, da kuma Ubangidanka.
Duk irin halaccin dayayi maka arayuwa, seda ka
ha'inceshi, kashiga gonarshi har 2, duk da haka bata
isheka ba seda kayi sanadiyar rugujewar farin cikinshi, tahanyar kauda abinda yake matukar so, kaso ka halakar
dasu amma Allah be baka iko ba.
Ko kasan ta dalilinka irin ukubar da Fulani da diyarta
suka shiga? Mezaka cema Allah aranar gobe kiyama idan
yatambayeka akan amana? Ko kasan kalar abincin
dasukaci atsawon shekaru 18 acikin MAKABARTA?
Ta dalilinka matar da babu ruwanta, bata yima kowa
komai ba, amma saboda SON ZUCIYA irin taku kaida
mabiyanka kunsa baiwar Allah tahaihu a MAKABARTA.
Yarinya ta tashi a MAKABARTA. Bata san kowa ba se
Mamanta da kaburbura, da bishiyoyi.
Wancen bawan Allah da kuke ganinshi agidan nan badan
kowa yake zaune ba sedan farin cikin yarinyar da kukaso ku hanata zuwa duniya. Shine mutum na 2 daya
temakeso, wanda badanshi ba haka Yarinya zata girma
har shekaru 18 amma batasan komai ba, kuma ita ba hauka ba, barashin lafiya ba.
Kawai saboda tsabar SON ZUCIYA irin taku, bara infada
maku abinda bakusani ba, kuma zakusan cewar duk
zakaran da Allah yanufa da tsara to ko ana muzuru ana
shaho se yayi.
Idan bakusani ba aranar da kuka wurgar da Fulani acikin dare kuka wurgata cikin rami, to aranar ta haihu, kunsan suwa Allah yaturo mata kawai dan yanason yanuna
maku baya bacci? Wasu bayinsa ne, kuma yan uwa
musulmai, wadan da suka fito daga jinsin aljanu.
Akusa da fadarsu kuka wurgata, kuma cikin ikon Allah
alokacin suka temaka mata harta haifi diyarta acikin
koshin lafiya. Zakusha mamaki idan nabaku labarin da
daya daga cikin aljanun, wanda yakasance shugaba
agurinsu, shine yabani labarin abinda yafaru. Bara kuji....
Kaf duk abinda Malam yasani seda yafada masu, gaba
daya falon babu wanda beyi kuka ba saboda tausayin
Fulani da beauty, kowa ya tausaya masu yanda sukayi
rayuwarsu acikin MAKABARTA. Fulani da Beauty sunfi
kowa kuka, dan ita beauty tade taso taganta a
MAKABARTA.
Atunaninta nanne muhallinsu, kuma Fulani ita kadaice
wadda tasani, mace, se kuma Baba wanda shima
shikadai tasani namiji. Kuka takeyi sosai ayau dataji
labarinta, ashe inda take tunanin muhallinsu ne, take
cewa acan aka haifeta, ashe muhallin matattune, segashi yanzu ana fadin AMAKABARTA AKA HAIFETA.
Malam yace ga Baba nan, shine megadin MAKABARTAR
da suke zaune, kuma shine mutumin daya zauna dasu
bisa gaskiya da amana, kuma ko matarshi betaba fada
mawa ba, harseda yaga lokaci yayi daya kamata yafada
mawani, alokacinne yazo yasameni yafadamun.........
Duk abinda Baba yafada mashi seda yafada masu, da irin
dawainiyar da yayi dasu. Hakanne yasa alokacin da
yagama bani labari, mukaje muka daukosu duk da seda
wannan aljanu suka rokemu akan mukula dasu idan har
wani yakara yunkurin cutar dasu bazasu kyaleshi ba.
Tundaga ranar damuka daukosu, nafara tunanin tabbas
abinda nagani acikin istaharata yana shige da wadannan
bayin Allah, idan baku manta ba Waziri, azuwan da
kukayi nafada maku naga Fulani akusa dani, kuma tana
raye, sede bansan awane waje take ba.
Hakan yasa nafara zargin wannan mata da diyarta zasu
iya kasancewa matar Sarki da diyarshi. Amma gudun
kada inyi saurin fadar abinda zuciyata take fada mun
hakan yasa lokacin da Safeeya tazo mani da alfarmar
abata wannan yarinya ta taho da ita nan gidan yasa nayi tunanin barinsu suzo, sena cemata dole sutaho su duka.
Hakan yasa naroki alfarma gurin Baba nayabar aikinshi
yataho tare dasu. Adaren dazasu tafi nakira Safeeya daki nake cemata ina zargin wani abu akan mutanen nan,
itama tace mun zuciyarta tafara saka mata irin abinda nake zargi, dan ita tasan Fulani sosai, amma tacemun
bazata iya cewa ita bace dan alokacin ko Sarki yaganta
baze iya ganeta ba, tsawon shekaru 18, gashi bacikin
hankalinta take ba, kuma bagurin jin dadi ba, babu
wankan kirki, babu sallah, ba lallai bane a iya ganeta.
Shiyasa nace ma Safeeya sutafi tare, ta ajesu agurinta
kuma kada tabari kowa yasan dazamansu idan har
tasamu nutsuwa da tsafta zata dawo cikin kamanninta,
idan kuma ba ita bace shikenan nace munyi temako.
Alokacin nakira Waziri mukayi maganar, dan aduk fadin
masarautar nan mutum 3 nafi yarda dasu, kuma yana
daya daga cikinsu, Sarki Qaseem, da Sarki Hasheem.
Babban dalilin dayasa banyi maganar da Sarki Qaseem
ba, nasan yanda halinshi yake, baze taba iya hakura abi abun asannu ba, kamar yanda nashirya, shiyasa ban fada
mashi ba.
Bayan Safeeya takirani tafadamun tagano wannan
mahaukaciyar bakowa bace se Fulani da diyarta,
alokacinma nace mata taboye abun harse angano
wadanda suka aikata mata haka. Nakira Waziri nafada
mashi, kuma alokacin yake fadamun yafara zargin Sarkin
Fada.
Ni nace mashi yacigaba da bibiyarshi harse ansamu
cikakkiyar shedar dazata bada damar kamashi sannan,
kuma nafada mashi bashi kadai bane dole akwai wata ko
wani makusancin Sarki. Alokacin seyake cemun shifa
yana zargin Jakadiya Karima.
Nima nayarda da abinda yafada, hakan yasa nace mashi
ya zuba masu ido su duka biyun. To Alhamdulillahi yau
gashi damukayi hakuri Allah yanuna mana makiyanmu
afili.
Sede kuma akwai abu daya danakeso intambaya Waziri.
Ina wannan bafaden da Sarkin fada yajama sharrin kisa,
ina fatan ba,a yanke mashi hukuncin kisa alokacin ba?
Gyara zama Waziri yayi yace, alokacin kam Sarki ya
yanke mashi hukuncin kisa.
Sede ni ajikina bansan meyasa banyarda da hukuncin da
Sarki ya yanke ba, kuma zuciyata takasa yarda da cewar
shine yayi kisan, amma alokacin kuma zuciyata bata
zargin Sarkin fada, sede kawai taki yarda da wanda akace yayi kisan.
Hakan yasa naja Sarki falo tafada mashi da kada ya
yanke hukuncin dazezo yadameshi daga baya, nine
nabashi shawarar daya yanke mashi hukuncin daurin rai
da rai. Kuma haka akayi, haryanzu yana nan akurkutun
gidan nan.
Sede tun lokacin dana fara zargin Sarkin fada da rashin gaskiya acikin gidan nan, tun daga ranar nafara kaimashi ziyara, mukan zauna muyi fira,acikin zaman damukayi
ne, nakara yarda dabashine yayi kisan ba, kuma
akwanakin baya ne nasa aka canza mashi gurin aiki,
harda gurin zama.
Kuma tunjiya nasa aka fiddoshi yanzu haka yana
masauki. Malam yace kasa akirashi yazo nan. Waziri ya
aiki daya daga cikin fadawan gurin. Malam yace wannan
shine iyakar abinda nasani agame da rayuwar Fulani da
diyarta. Wadda haryanzu babu wanda yasan sunanta.
Abinda Baba yake kiranta dashi shine Yar Baba, wanda
yacemun ada yaji Fulani tana kiranta da Baby, jin sunan zeyi mashi wahala ne, yake kiranta da diyarshi. Amma
ayanzu tunda gashi sundawo gida, za,a iya saka mata sun kuma Waziri se muji daga gareku wane irin hukunci
zaku yankema wadannan maciya amanar.
Sallamar bafaden da aka aika ne tasasu kallon kofa, tare suke da wanda aka likama kisan da Sarkin Fada yayi,
zama yayi yana kwasar gaisuwa, daka ganshi kasan
yajigata, atsawon zaman dayayi akurkutu shekaru
dayawa.
Kallon Sarki Qaseem da Sarki Hasheem Waziri yayi,
domin jin abinda zasu fada. Sarki Qaseem yayi gyaran
murya yace, ni babu abinda zance, sede kawai inma
Allah godiya daya kawomu karshen wannan matsala
damuke ciki. Tabbas wadan nan mutane, kunsamu cikin
tashin hankali, babu abinda zance maku se Allah ya isa.
Sede abu daya nakeso kusani, hakan da kukayi bashine
ze samurika tsoron mutane ba,ko kuma mudena jawo
su zuwa jikinmu ba, ai ba,a taba taruwa azama daya,
idan wani yazo daniyar cutarka, Allah ze aiko maka dana gari, wanda ze zauna da kai badan komai naka ba, sedan
son dayake maka domin Allah.
Idan kuka kalli Jakadiya Safeeya da Malam,da Matata da
kuma matar Yaya wato Fulani, daga baya muka kara
samun Baban Darazo da abokin Yarima wato Haisam.
Duka wadan nan dana lissafo babu wanda muka hada
jini dashi, kuma babu wanda muka tashi dashi acikin
gidan nan.
Asalima bamu taba tunanin zasu shigo cikin rayuwarmu
ba, sedaga baya muka sansu, kuma duk da basu kasance
yan uwa agare mu ba, sun zauna damu tsakani da Allah,
babu wanda yakeda niyar cutar damu.
Idan muka kalli Malam da kanwarshi, bawai dan sun rasa
abinda zasuci bane yasa suka shigo jikinmu. Jakadiya
Safeeya tazo gidan nan badan kowa ba sedan bin
umarnin yayanta, kuma duk da haka tarika kaskantar da
kanta agaremu, wanda inda dan kudine zatazo, ninasan
babu abinda ze kawota, dan aduk fadin garin Bauchi,
darazo, Gombe, harma da makotanmu mutane dayawa
sunsan Malam, kuma kowa yasan babban mutum ne.
Idan har kudine, bayada damuwa dasu, asalima yakan
dauko wasu suci akarkashin shi. Amma duk da haka suke
zama tare damu abisa gaskiya da amana. Wannan kadai
ya isa yanuna ma kowa cewa wanda baku hada komai
dashi ba, ze iya yimaka abinda makusancinka baze maka
ba.
Yanzu ku kalli irin cin amanar da akayima Yaya, Gimbiya Zakiyya kinci amanar sarauta, kuma kinci amanar
iyayenki, amatsayinki na Uwar gidan yaya amma aka
hada baki dake, aka cuceshi, koba komai, mahaifinki da
Abbanmu abokan junane sosai, kuma dama sune suka
hada aurenku, alokacin Yaya bayasonki amma nayi
imani da Allah haryanzu betaba fada maki keba
ra,ayinshi bace.
Haka yakarbi zabin iyayenmu kuma yazauna dake da
gaskiya da amana, segashi daga karshe kinzama butulu,
bayan butulci ma harseda kika hada da cin amanar
aurenku. Wa iyazubillah, kina matar aure amma kika
aikata wannan babban zunubi agidanki. Amma kanki
kikai mawa, kuma wlh. Kowace irin alaka ketsakinmu
bazata hana ayanke maki hukunci dede da laifinki ba.
Kuka tasaka tana fadin natuba, dan Allah kumun rai, wlh duk abinda kuka fada gaskiya ne, amma niban aikata
abinda kukagani da son rai na ba. Nide nasan babu
abinda na tsana kamar zama guri daya da talaka, kuma
ni tunda nake wlh wannan aikin da Sarkin fada yamun
shikadai ne, yataba hadani dashi harmukayi magana.
Akwai sanda jakadiya Karima tazo tacemun wai Sarkin
Fada yana gaisheni.
Wlh ku tambayeta idan har zata fadi gaskiya zata fada
maku irin cin mutuncin dana mata akan abinda tazo
mun dashi, wlh babu wata alaka datake tsakanina dashi,
ko aranar danasan munfara aikata sabo dashi, yana
shigowa da masifa narufeshi, amma bansan ya akayi
daga baya harna bashi hadin kai ba.
Dan Allah Sarkin fada kafada masu ba laifina bane. Wani malalacin murmushi Sarkin Fada yayi yadauke idonshi
daga kallonta. Sarki Qaseem yace wannan kuma yarage
naki, kinsan masarautar nan bata yanke hukunci seta
tabbatar da sheda tazahiri, kuma ba mutum daya ba,
kowa gurin nan yaga abinda kuka aikata, dan haka ki
adana kalamanki.
Kallon Medaki yayi, yace kenarasa ma mezance maki,
kinfi kowa zama cikakkiyar butulu, kinfi kowa sanin
dayanda aka aureki da irin halaccin da Yaya yayi maki,
duk da nibanyarda da labarin da mamanki tabada ba,
amma sbd sanin girman alkawarin da yaya yadaukar
mata, haka mukayi hakuri ya aureki.
Amma kirasa da abinda zaki saka mashi se irin wannan
cin amanar, kema zakiga sakamakonki. Kuma abinda
nakeso dake inaso kifada mana wacece ke? Da kuma
asalin garinku.
Cikin sheshshekar kuka Medaki tace wlh nima bansan
inane asalin garinmu ba, nadesan ayawon damukeyi
daga wannan kauyen zuwa wani iyayena suka haifeni.
Kuma sanin dana yima iyayena basu bani tarbiya tagari
ba, babu ilimin addini bare na boko, to sukansu ma basu
damu danasu addininba.
Nikaina nafara sanin Sallah ne alokacin dana ke bin wata kawata islamiyarsu, anan nafara sanin addini na, harna
fara fahimta sosai, sekawai innata tafara doramun talla, domin ita macece meson kudi.
Aduk lokacin dana saida tana siyamun duk abinda
nakeso, nima tundaga ranar son kudi,yashiga raina.
alokacin kuma na hadu da wani saurayi shine yakara
huremun kunne, haryayi nasarar ciremun budurcina,
seda muka zubar da ciki har 2, kuma Innata bata
tabamun fada ba, wannan shine sanadiyar lalacewar
mahaifata.
Mahaifina dan caca ne, bedamu da ya rayuwata takeba,
shiyasa nakasance tamkar dabbar daji, banida wani
takunkumin daze hanani aikata abinda naga dama.
Sanadiyar Caca mahaifina yarasa ranshi, mutanen gari
suka koremu harmuka hadu daku, Innata tafada maku
karya har kuka yarda damu.
Tabbas nasan naci amanar mijina, wanda yarufamun
asiri, duk da yagane banje da budurcina ba, amma be
tsaneni ba, asalima cikin laluma ya tambayani, shima
nafada mashi fyade akamun wanda karyane, amma haka
ya yarda dani, kuma yacemun beyarda infadama
kowaba.
Dan Allah kayafe mani, nasan bankasance mace tagari
ba, naci amanarka dan Allah kuyafemun. Kuka tasaka
wanda seda wasu daga cikin mutanen falon sukaji
tausayinta,,,,, hayaniya sukaji awaje, Wazirine da fadawa suka leka.
Wani kodaddan mutumi suka gani wanda beda kyan
gani, sunata rigima da masu gadi. Waziri yace ku kyaleshi yakaraso, haka yataho yanata zare ido. Yana zuwa yace
wani nake nema agidan nan nayi mashi aiki be bani
kudina ba. Kuma nafada mashi idan har bebani kudina
ba zanzo intona mashi asiri.
Murmushi Waziri yayi yace kashigo semuji wa kake
nema. Kowa mamakin ganin mutumin daya shigo
yakeyi, banda Sarkin Fada wanda yaketa muzurai. Waziri
yace munajinka wakake nema?.
Yace sunanshi Sarkin Fada, kuma ya kasance daya daga
cikin mutanen danake yima aiki, duk wani aikinshi nine
nakeyi mashi, anan yarika fadin duk irin asirin dayasashi yayi, harda wanda yayima Areef, dana Jakadiya Karima
wanda tazubarma Gimbiya Suhailat ciki kuma aka daure
mahaifarta, har yakawo asirin karshe dayayi mashi.
Yace aranar yazomun akan yanason inbashi maganin
mallakar zuciyar Matar Sarki, Zakiyyah, yacemun yadade
yana sha,awarta amma yasan bazata taba bashi kanta ba,
hakan yasa yazo inbashi magani, alokacin yacemun beda
kudi amma yasan idan yasamu sa,ar kusantarta
yamallake zuciyarta zesamu kudi.
Tun ranar dana bashi bankara ganinshi ba, shine yanzu
nazo inkarbi hakkina. Salati kowa yakeyi, sbd wani abin al,ajabin dasuka karaji yabullo. Murmushi Waziri yayi
yace kaima seka samu guri kazauna kajira naka
hukuncin tunda Allah yakawoka. Zaro ido boka yayi yana
fadin aishikenan kuma wlh nayafe mashi kubarni intafi.
Seda yabama kowa dariya, nan fadawa suka zaunar
dashi. Se alokacin Sarki Hasheem yayi magana, jikinshi
asanyaye yace Malam, kafadi irin hukuncin daya kamata
ayima kowa abisa koyarwa ta addinin musulunci, kamar
yanda yazo a Qur'ani. Dan nagaji da kallon fuskokin
wadannan mutanen.
Dan duk acikinsu nafijin haushin mutum daya, bakowa
bace se Jakadiya Karima. Allah ya isa tsakanina dake, kin cuceni, wlh zan iya yafema kowa agurin nan amma
banda ke, bazan taba iya yafe maki ba. Mundaukeki Uwa
asheke makiyarmuce nida dan uwana..... kuka yasaka
tamkar karamin yaro.
Alokacin hatta da Malam seda yazubar mashi da kwalla
sbd yanda yakeyin kuka kowa yasan abun yana cimashi
rai sosai. Sarki Qaseem yana kuka yace Malam dan Allah
ayanke masu hukunci kada ciwon Yaya yadawo.
Malam yace Alhamdulillahi, kamar yanda kuka sani duk
wani laifi na duniya babu hukuncin da Alku'ani da hadisi basu kawo ba, dan haka zamu duba muga irin hukuncin
da Allah yace ayima masu irin laifinku. Zanfara daga kasa zuwa sama, wato daga masu karamin laifi zuwa babba.
Zan fara da masu gadi, mati da Lado, tabbas kun aikata
babban kuskure, domin da farko kunci amanar
masarauta, sannan kunbada gudummuwa gurin aikata
fasadi, dan haka hukuncinku anan shine zakuyi zaman
kurkutu natsawon shekaru 2, domin aladabtar daku,
sannan baku bakara aiki awata masarauta.
Se amintaccen bawan Sarki Hasheem, kaima kaci
amanar Uban gidanka, sannan kazamo daya daga cikin
wanda yatemaka ma Sarkin fada kuka sace Fulani. Dalili
daya ne bazesa ayanke maka hukuncin kisa ba, saboda
Fulani bata mutu ba, kuma Qur,ani cewa yayi wanda
yakashe akashe shi, sbd haka kaima za,a daureka
akurkutu na tsawon shekaru 5, tare da aiki metsanani.
Gimbiya Zakiyya, kinkasance matar aure, wadda aka
kamaki da laifuka biyu. Nafarko kina da sa hannu abatan Fulani, wanda dakunsami dama kasheta zakuyi. Nabiyu
kuma laifin aikata zina. To hukuncin zina anan yakasu
kashi 2, akwai na wadda bata tabayin aure ba, wato
budurwa, akwai kuma na wadda ta tabayin aure.
Idan budurwa tayi zina, kuma aka tabbatar dashedu, za,a yanke mata hukunci bulala 100, idan abokin yinnata
shima saurayine, hukuncinsu daya.
Matar aure. Duk matar datayi zina kuma tanada aure, ko
ta taba yin aure. Hukuncinta kisane, tahanyar jefewa da duwatsu, wanda yara ne zasu jefeta harta mutu, za,a
rufe duka jikinta cikin rami abar kanta shine za,ayita jifa
harta mutu.
Idan abokin zinarta yataba aure, hukuncinsu daya, idan
kuma shi beda aure, to nata daban nashi daban. Abisa
shedar da muka samu daga gurin wanda yayi maki asirin
da kika fada wannan alfasha.
Kamar yanda yazo a arba'una hadith, mazon Allah yace
INNALLAHA TAJAWAZILI AN UMMATIβ‘β‘ Lallai Allah
yagafarta ma al'ummata, AL,,KADAHA... abinda sukayi
da KUSKURE. WANNISIYANA... abinda sukayi da
MANTUWA. WAMASTUKURUHU ALAIHI... da abinda AKA
TURSASASU AKANSHI. Rawahul bukhari wa muslim.
Abisa duba da wannan hadisi, sarkin Fada yayi amfani da karfin asiri ta hanayar mallakeki har kika biye mashi
kuka aikata alfasha. Abisa wannan hadisi, anan bakida
laifi agurin aikata wannan zina. Dan haka bazaki dauki
hukuncin zina ba anan.
Sede hukuncin dazaki dauka na aikata laifin cin amana
gurin niyar salwantar da rayuwar Fulani, dan haka zakiyi zaman kurkutu shekara 5. Saura hukunci kuma yarage
ga mijinki.
Tunkafin yacigaba Sarki Hasheem yace Malam da ita da
Medaki duk nayanke igiyara aurena akansu, dan haka
kacigaba da yanke hukuncinka. Hannu Zakiyyah ta dora
akai tana kuka.
Malam yace Medaki, kema hukuncinki biyu ne. Amma
tunda nakarshen megaba daya ne, to hukunci daya
zamu yanke maki, naki hukuncin kisa ne, tahanyar
jefewa, tunda ke kin amsa kece kika bama sarkin Fada
hadin kai da kanki. Dan haka hukuncin kisa zaki dauka.
Jakadiya Karima kema hukuncin kisa ne akanki, sbd
kin aikata kisan kai domin kinsa anzubar da cikin
Gimbiya Suhailat. Anyanke maki hukuncin kisa daurin rai da rai akurkutu, tare da horo metsanani.
Boka, kaima hukuncin kisa ne, ta hanyar rataya, tunda ka amsa laifinka, kuma Allah kadai yasan iyakar ta,asar
dakayi.
Hukuncinmu na karshe akan Sarkin fada, kai kam da ana
mutuwa adawo to da seka karbi duka hukuncinka.
Amma hukuncinka anan shine kisa ta hanyar rataya.
Anan muka kawo karshen wannan hukunci na
MASARAUTAR BUBAYERO. Inafatan hukunci yayi maku,
idan kuma akwai wani abu kuna iya fada, yajuya yana
kallon Sarki. Sarki Qaseem yakalli Yayanshi. Kai yadaga alamun hukunci yayi, sannan yace kuma agobe za,a
aiwatar da wannan hukunci.
Ihu Gimbiya Zakiyyah tasaka kamar meshirin shiga
hauka, Medaki da Jakadiya ma kuka kawai sukeyi kamar
ransu zefita. Haka aka kara tasasu zuwa kurkutu kafin
gobe.
Nima nace Allah yakaimu goben da rai da lafiya.
Ur's.
NABILA RABI'U ZANGO
(Nabeelert Lady)
08028525263
[23/08, 1:48 p.m.] Nabeelert Lady: ..π€π€ππππ€π€π€
AMAKABARTA AKA HAIFENI
π€π€ππππ€π€π€
(The story of hard kingdom)
Nah
Marubuciyar Zamani
NABILA RABI'U ZANGO
(Nabeelert Lady)
@House of Novella Association
(H,O,N,A)
www.NabilaLady5@gmail.com
Season 110β115
Kusa da Baban Darazo Fulani ta matsa, idanunta
haryanzu basu dena zubar da kwalla ba, dukawa tayi har
kasa tace, Baba hakika banida bakin dazanyi maka
godiya, kayimun abinda bakowa ne dan Adam bane ze
iya yimani shi.
Tabbas kazamo daya daga cikin mutane masu
muhimmanci arayuwata, kuma daga yau inaso
kadaukeni tamkar diyarka ta cikinka, inaso kadauko
duka iyalanka kudawo nan dazama dan suma sunzama
yan uwana.
Baba yace babu komai Fulani, duk abinda nayi maki nayi
shine dan Allah, banyi dan wani abu naku ba, asalima
bansan wane irin matsayi gareki ba. Hakika naji dadin
yanda kika dauke ni, kuma nagode Allah yasaka da
alkhairi.
Haka kowa yatashi yanufi bangarenshi kafin gobe da
safe. Haisam ya kalli Areef yace abokina nizan tafi gida, amma dole gobe indawo in kalli wasan daza,ayi agidan
nan. Tabbas nakara daukar darasi agidanku.
Allah yakara mana karfin imani kuma yacire mana SON
ZUCIYA. Areef yace amin, nima kaina abubuwan gidan
nan sun gama daga mun hankali, naji tausayin beauty na
sosai, ta dalilin masu SON ZUCIYA tarasa ingantatacciyar rayuwa da kowane dan Adam masu galihu
All Chapters
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 10 Chapter of 13