Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
anan mutane suka haushi da duka har gidanshi, seda sukayi mashi raga raga sannan abokanan Cacarshi sukace sutashi subar gidan dasuke ciki zasu sayar sudau kudinsu. Uwani da Nafeesa bakaramin shiga tashin hankali sukayi ba, suna zaune suka farajin hargowar mutane, Mal. Audu yana kwance ko tashi be iyayi yaji mutane sun shigo sunfara yimasu wurgi da kaya, nan take zuciyarshi ta buga ya mutu, koda mutanen suka zo gurinshi se suka samu ya mutu, anan suka fadama Uwani sukayi tafiyarsu, kuka suka saka Uwani tana fadin shikenan katafi kabarmu da tashin hankali. Da kyar suka samu wasu daga cikin abokananshi suka yimashi wanka da sallah suka kaishi makabarta, duka basufi mutum 10 ba wadanda suka kaishi. Bayan kwana biyu da rasuwarshi Uwani tafara rashin lafiya, gashi basuda abinci bare kudin magani, haka Nafeesa tayita jinyarta, koda taje gurin saurayinta yabata kudi tasiyo mata magani korarta yayi dan alokacin ma tare da wata tagansu, haka tadawo tana ta kuka. Lokacin da akayi 7 da mutuwar mal. Audu masu siyan gida sukazo, anan suka koresu, duk inda sukaje neman temako babu me temakonsu dan babu wanda besan halin Nafeesa da uwani ba. Daga karshe suka baro garin har suka hadu da Sarki. ×××××××××× Bayan kwana 7 da rasuwar Maman Nafeesa aka daura aurenta da sarki, mutanen garin sunyi matukar mamakin aurensu, sede wasu suna cewa auren tausayi ne Sarki yayi. Duk wasu kayan aure Sarki ne yayi mata, aka gyara mata bangarenta aka hadata da bayin dazasu rika yimata hidima. Haka Sarki yasa Jakadiya takoya mata duk wasu al'adu na masarautar. Seda Nafeesa tayi wata 1 agidan sarki Jakadiya tana gyarata sannan takaima Sarki ita, bakaramin kyau tayi ba, dan gyara akayi mata bana wasa ba, fatar jikinta kanta seda ta canza. Abubuwa da dama Jakadiya takoya mata, wanda aciki harda biyayya ga gimbiya dan tafada mata ko ita wacece kowa binta yakeyi. Haka kuma ta bata Gimbiya Suhailat agurin Nafeesa. Aranar da Sarki ya kwana da Gimbiya Nafeesa yasameta bata da budurci ajikinta, yayi mamaki sosai, bayan sunyi sallar asuba yadawo yasameta tana kuka, zama yayi yafara tambayarta lafiya, cike da kissa tace kayi hakuri rankai dade dama nasan tunda Mama tarasu bata ida baka labarina ba, nasan dole zaka fahimci wani abu, nasan kagane banzo da budurcina ba, hakan yasamo asaline ta dalilin barayin dasuka shigo mana gida ana gobe za'a koremu daga garinmu, sune suka yimani fyde wanda shine dalilin ciwon Mamana dan Allah kayi hakuri, naso ace tunkafin adaura auren mun samu dama nayi maka bayani dako daya daga cikin bayinka kahadani dashi. Tausayinta yakara kama Sarki yace bakomai Nafeesa, kada insake inji wannan maganar abakin kowa, kibarta tsakaninmu nayafe maki kinji, tace tonagode. Haka zamansu yacigaba da tafiya, Sarki da kyar yasamu yashawo kan Qaseem dan tunda yayi aure yake fushi dashi. Gimbiya Shuwa da Gimbiyar Baban Gida da Gimbiya medaki kwata kwata basa shiri, shiyasa babu me shiga harkar wani, Su biyu sunware Gimbiya shuwa, basa sata acikin harkarsu, sede itama Gimbiya madaki wato Nafeesa awulakance take agurin Gimbiya babba, se abinda tace takeyi, ita kuma tana kaskantar da kanta ne, kawai dan tasamu fada agurinta, dan Gimbiya Shuwa bata kulata, sbd akidarta na tsanar wanda ba dan sarauta ba. Sarkin Fada ne, da jakadiya zaune alambu. Sarkin Fada yace waini Jakadiya haryanzu acikin matan Sarki babu me ciki ne? Yamutsa Fuska tayi tace inaji fa Sarki beda rabon samun da aduniya, bare aje ga maganar magaji, kaga ko mutuwa yayi ai sede abama Kaninshi. Sarkin Fada yace kinko san banason Qaseem ya anshi mulki kinsan yafi Sarki mugun hali, towai meze hana muyi masu kullalla. Jakadiya tayi dariya tace lallai Sarkin fada baka da dama, aini nafison ace sunbata shida kaninshi, shiyasa lokacin dayayi fushi dashi dan zeyi aure naji dadi, sede dayake akwai kauna atsakaninsu kaga basu wani dade ba, suka shirya. Sarkin fada yace amma Jakadiya babu wata hanya dazakibi kishiga jikin Gimbiya Shuwa? Zaro ido tayi tace ni? Rufamun asiri, kana ganin sbd tsabar jinkai irin nata haryanzu bata yarda da kowa ba, sede mijinta. kai de kawai ayi sha'ani amma ina nan ina shirya masu gadar zare kaide kawai ka tsaya kayi kallo. Matso kaji wata magana. Ko kasan cewa nice nan na hana Gimbiya Zakiyya haihuwa agidannan? Sarkin Fada yace lallai Jakadiya nasara maki. Tace uhm kawai ka kalleni kabarni akwai sauran abubuwan bam mamaki atattare dani. Kaide muje zuwa, da sannu sena tarwatsa farin cikin masarautar nan, haka nake bani da kyau, banki kowa yarasa ba, tunda har Allah yasa nazo a Jakadiya. Muje zuwa danjin sauran labarin. Nagode da kulawarku. Ur's NABILA RABI'U ZANGO ( Nabeelert Lady) 08028525263 [23/08, 1:48 p.m.] Nabeelert Lady: ..🛤🛤🏕🏕🏕🛤🛤🛤 AMAKABARTA AKA HAIFENI 🛤🛤🏕🏕🏕🛤🛤🛤 (The story of hard kingdom) Nah Marubuciyar Zamani NABILA RABI'U ZANGO (Nabeelert Lady) @House of Novella Association (H,O,N,A) www.NabilaLady5@gmail.com Season 25⚜30 Masarautar BUBAYERO, babbar masarauta ce mecike da tarihi, ashekaru 18 dasuka wuce Sarki HASHEEM shine Sarki amasarautar, yana da Kani wanda suke Uwa daya Uba daya, su 2 iyayensu suka haifa, kafin iyayensu surasu mahaifinsu shine Sarkin agarin. Sakamakon hatsarin jirgi dasukayi shida mahaifiyarsu wadda ita kadai ce matarshi kuma uwar yaranshi, shine yayi sanadiyar mutuwarsu. Bayan kwana biyu da rasuwarsu .Waziri wanda shine mahaifin wazirin sarki Qaseem, shine yatara jama,a domin anada sabon sarki, ananne aka zabi Hasheem yayan Qaseem aka nadashi Sarkin masarautar Bubayero. Kuma shima Waziri yasauka daga mukaminshi yamika ma babban danshi wato Wazirin Sarki Qaseem. Alokacin Sarki Hasheem yanada Matarshi 1 mesuna Zakiyyah, diyace ga Sarkin Yobe, kuma abokine ga mahaifin su Qaseem, shiyasa suka hadasu auren zumunci, duk da Sarki Hasheem baya sonta haka yayi biyayya ya aureta. Mahaifiyar Zakiyya takasance su 3 ne agurin mijinsu Sarkin Yobe, amma dayake macece wadda tasan kissa da iya tuggu hakan yasa tazamo yar gaban goshi agurin mijinsu, baruwanta dabin boka ko malam, tayarda da kanta. Hakan yasa Zakiyyah tadauki duk wasu halaye nata. Kuma da wannan halinne tajawo hankalin Sarki Hasheem har yabata babban matsayi azuciyarshi. Alokacin da aka nada mijinta Sarki bakaramin dadi taji ba, sede babbar matsalar datake damunsu haryanzu basu sami haihuwa ba, ko batan wata bata tabayiba. Sede yanda takeyima Sarki yasa baya nuna damuwarshi akan haka. Jakadiya itace babbar baiwa datakema Sarki Hasheem hidima tunkafin yazama sarki, ita kadai yabama amana aduka bayin gidan, hakanne yasa lokacin dayahau kujerar mulki yanadata Jakadiyarshi, ko Matarshi batasan wasu sirrinkanshi ba kamar yanda Jakadiya tasani, shiyasa kwata kwata basa shiri. Bayan kaninshi yagama karatunshi akasar misrah yadawo gida, alokacin Sarki yasa aka gyara mashi part dinshi anan cikin gidan, kuma alokacin yazo mashi da maganar matar dayakeso ya aura, Yayanshi bakaramin dadi yaji ba, dan yana son kanin nashi kamar yanda shima yakesonshi. Daya tambayeshi wacece yace mashi diyar Sarkin Misra ce, atare sukayi karatu. Babu bata lokaci yasa waziri yashirya masu tafi sukaje neman auranta, koda sukaje sunsami tarba me kyau, kuma anan take aka bama Qaseem auran Gimbiya Suhailat, Bayan sundawo aka fara shirin biki. Sati 1 akasa yanazuwa akaje akadaura aurensu, suka taho Gombe, sede Sarki Hasheem yace base anbasu bayi ba suna da isassun bayi, haka aka kawo amarya akasata part dinta. Tunda suka hadu da Gimbiya Zakiyya taji ta tsaneta, hakan yasa bata sakan mata fuska, kowa yanaji da kanshi, ita Zakiyyah tana ganin ita diyar Sarki ce, kuma matar Sarki, hakan yasa mulkin yayi mata yawa. Ita kuma Suhailat tana ganin masarautarsu tafi tasu Zakiyyah. Bayan kwana 2 Sarki yasa Jakadiya tadebi bayi masu yawa takaima Gimbiya Suhailat tazabi wanda takeso, bayan tazaba Jakadiya tace tazabi amintattar baiwa acikinsu, wani kallo tamata tace aini bana zabar amintattiyar baiwa alokaci guda, dan haka ki kama gabanki idan ina bukatar hakan basekin fadamun ba. Jakadiya taji zafin maganar haka tajuya tawuce ranta abace, sede dayake ta iya duniyanci bata nuna mata afuska ba. Tsaki Gimbya taja, dan ita duk wanda befito daga gidan sarauta ba gani take beda wani matsayi, shiyasa ra'ayinsu da mijinta yazo daya, dan shima sarauta tashiga jikinshi dayawa yana bata muhimmanci. Sarki Hasheem yakasance mutum ne mesaukin kai sosai, sede shima yana daraja sarautarsu sosai, kuma baya son kai acikin masarautarshi, duk wanda ya aikata laifi ana yanke mashi hukunci dede dashi. Dalilin aurenshi da matarshi ta 2 kuwa yasamo asaline, wata rana yafita rangadi shida Waziri da Kaninshi da fadawa, sunzo wajen gari nesa da cikin gari, se suka hadu dawasu bayin Allah agefen hanya uwa da diyarta, yarinyar bazata wuce shekaru 17 ba, tana zaune kusa da uwar tana ta kuka. Tsayawa sarki yasa akayi yasa aka kirawosu, sede yarinyarce kawai tazo dan matar tana cikin halin rashin lafiya bazata iya tashi ba. Tanazuwa tafadi kasa, Waziri yatambayeta meyasa suke zaune anan haka?. Tana kuka bata basu amsa ba, Qaseem ya daka mata tsawa yace waike ba magana ake makiba kin tsaida mutane, Kallonshi Sarki yayi dan yasan abinda kaninnashi ya tsana kenan, murmushi yayi yamaida kallonshi kan yarinyar. Ihun matar dasukajine yasa babu shiri Sarki da Waziri da sauran fadawa suka sauka daga dokinsu suka nufi gurinta, yarinyar tarigasu zuwa gurinta. Jinine yake fita daga hancinta da bakinta, haka tarike hannun yarta hawaye suna fita daga idonta, akusa da ita Sarki ya tsugunna, fuskarshi cike da damuwa, yayi bakin cikin dabasu fito da mota ba, kallon Waziri yayi yace yazamuyi da ita, yakamata akaita asibiti. Hannun matar yaji takamo babbar rigarshi, dasauri fadawa suka matso dansu cire, amma yadakatar dasu. Kara dukawa yayi yace baiwar Allah kibari mukaiki asibiti kina zubar da jini. Kai tashiga girgizawa, ahankali tafara magana, babu inda zanje dannasan rayuwata tazo karshe, sede ina neman wata alfarma agurinka. Sarki yace inajinki, kadubi girman Allah, kamar yanda Allah yadauka kaka, yafifitaka sama da sauran bayinshi badan yafisonka ba, nasan matsayinka ya girmi alfarmar dazan fada maka, sede inason kayi jahadi domin ka ceci marainiyar Allah daga fadawa wata rayuwa. Sarki yace inajinki, kifadi koma menene nikuma namaki alkawarin zanzamo mecika makishi. Waziri, Qaseem sukayi saurin kallon Sarki jin abinda yafada batare dayasan me matar zata fada ba. Ur's NABILA RABI'U ZANGO (Nabeelert Lady) 08028525263 [23/08, 1:48 p.m.] Nabeelert Lady: ..🛤🛤🏕🏕🏕🛤🛤🛤 AMAKABARTA AKA HAIFENI 🛤🛤🏕🏕🏕🛤🛤🛤 (The story of hard kingdom) Nah Marubuciyar Zamani NABILA RABI'U ZANGO (Nabeelert Lady) @House of Novella Association (H,O,N,A) www.NabilaLady5@gmail.com Season 35⚜40 Zaune suke a falon Malam Bello na Darazo, Sarki ne, se Qaseem da Waziri. Malam Bello babban malami ne, kuma attajiri, duk da yamanyanta amma sbd ilimin dayake dashi idan kaganshi zaka dauka shekarunsa basu kai nashi ba. Shine babban malamin garin Darazo malamin sosai, yana temakon mutane dayawa agarinsu, mutanen garin suna matukar sonshi da girmamashi. Hakan yasa yagina katon gida me bangarori dayawa, ko yaranshi maza 2 dasukayi aure acikin gidan suke zaune da matansu, da yaransu, dama kuma beda yara dayawa yaranshi 4, maza 3 mace 1, itama tayi aure acikin garin bauchi. Matarshi daya uwar yaranshi, se kanwarshi kuma autar gidansu, tunda mijinta yarasu bata kara aure ba, dama kuma bata taba haihuwa ba, hakan yasa tace bazata kara aure ba, itama ta manyanta akalla zatayi shekara 35. Mutane dayawa idan sukazo garin basuda masauki yana basu guri acikin gidanshi, ko idan ya musuluntar da wasu yana basu gurin zama, yana da dalibai dayawa dayake karantarwa. Haka kuma baya aiki da aljanu, sede yana fitar dasu kuma suma sunajin tsoronshi, kuma duk wanda aka kawo marar lafiya yana temaka mashi, hakan yasa mutanen garin dana wajen gari suke girmamashi. Yadade yana yima masarautar Bubayero hidima tun lokacin mahaifansu Qaseem, dan masarautar bata yarda da malamin duba ko boka ba, hakan yasa koda iyayensu suka rasu basu yarda shiba, duk wani temako kowata shawara sukan zogurinshi, kuma Sarki baya aiko kowa gurinshi kode yazo tare dasu Qaseem da Waziri ko kuma ya aikosu su 2, yauma sunzo domin neman wani temako. Bayan sungama gaisawa, Malam yasa ankawo masu kayan motsa baki, dan sunyi waya da Qaseem tun jiya yafada mashi suna hanya. Qaseem ne, yafara magana cike da ladabi. Allah gafarta malam, kamar yanda muka fara magana dakai jiya awaya. Dama bawani abu bane akan matsalar rashin haihuwar Yaya, tun tuni naso muzo shine yake hanawa, shine nace ai koma menene yanada magani, shine mukazo muji daga gareka. Gyara zama malam yayi yacire glass din dayake idonshi yace, hakika nima nadade ina tausaya ma, memartaba, kuma dama tun kwanakin baya damukayi magana dakai, nafarayin istahara akan al'amarin. Kuma alhamdulillahi dama kobakuzo ba nayi niyar kiranka, infada maka abinda nagani. Sede inaso kusani bakomai ne, ake fada ba dan kayi istahara, amma tabbas akwai abinda nagani amma nabarma kaina, kuma insha Allahu abinda ake so ahana za,a sameshi, sede muyita rokon Allah, babu abinda yagagareshi. Kamar kullum abinda nake fada maku kuyi hankali da mutanen da kuke tare dasu bance kuyi bincike ba, amma kada kayarda dakowa kuyarda da kanku, shine zaku zauna lafiya. Abinda nakeso kusani insha Allahu memartaba yanada rabon samun haihuwa, sede abinda zan fada maku agsky ayanzude rabon dana gani zesamu ba'a agurin matanshi yake ba. Amma koma menene nasan zesamu haihuwa insha Allahu, sede adage da addu'a inafatan kunfahimci bayanina? Waziri yace munfahimceka malam, kuma mungode Allah yasaka da alkhairi, muzamuzo mukoma. Malam yace tonima inada wata alfarma danakeso kuyi mani, Qaseem yace haba malam ai kawuce komai agurinmu kafadi koma menene. To kamar yanda kuka sani akwai kanwata kuma autarmu, kunsan mijinta yadade da rasuwa kuma taki yarda tayi wani auren, shine nakeso dan Allah kozaku tafi da ita can tarika temaka ma matan sarki dawasu aiyuka inaganin yafi zamandatakeyi anan tunda can akwai jama,a dayawa. Sarki zeyi magana Qaseem yayi saurin fadin agaskya malam naji dadin wannan magana taka, kuma inaso abani ita inkaima Suhailat, dan mundade muna neman wadda zata zama mekusanci agurinmu, kasan ni bakowa nake yarda dashi ba, itama haka, amma tunda daga gareka tafito, kuma jininkace nayarda da ita sosai. Kuma dama tana da tsohon ciki inata tunanin wadda zata zauna mata. Mungode Allah yabamu zaman lafiya. Ya sunanta? Malam yace sunanta Safeeya. Murmushi Waziri yayi yace mungode malam Allah yasaka da alkhairi. Sarki yace mungode malam, kuma insha Allahu zamu riketa amana. Malam yace nikeda godiya, bari inje infada mata tashirya. Daki yakira Safeeya, sundade suna tattaunawa banji abinda suke fada ba, haka tafito tashirya tayima Matar malam sallama da sauran matan gidan, hada kukansu, haka suka shiga mota suka dauki hanya. Gimbiya Suhailat taji dadin zuwan Safeeya, dan tanajin labarin malam agurin Qaseem, shiyasa tajata ajikinta sosai, dan har karatu take kara mata, hakan yasa suka saba dawuri, duk wata shawara Gimbiya Suhailat tanayi da Safeeya, haka kuma baruwanta dashiga part dinsu Gimbiya Zakiyyah, asalima basu san dazuwanta ba, kamar yanda babu wanda yasan tana da ciki harya tsufa, shiyasa taji dadin zuwan Safeeya. Dan Waziri yahana anuna Safeeya acikin gidan, har seda Sarki yace meyasa Waziri yace yallabai dan Allah abarta, Qaseem yace shikenan yanda kace Waziri. Haka rayuwar gidan tacigaba da tafiya, Cikin Gimbiya Suhailat harya shiga watan haihuwarshi, Qaseem da Sarki suna farin ciki da cikin, dan kamar Sarki yafi Qaseem farin ciki da Cikin, kuma betaba fadama matanshi ba, dan gani yake kamar sun sani kuma beso suga kamar shima yadamu darashin haihuwar. Jakadiya dasu Gimbiya sun hada kansu, Gimbiya Zakiyya babu abinda takeso kamar haihuwa, ayanzu bata da abokiyar shawara se Jakadiya, duk wani sirrinta Jakadiya tasani, sede haryanzu bata karbi gurguwar shawarar Jakadiya ba. Ita ko Gimbiya Nafeesa dama tasan bazata kara haihuwa ba, dan tunzubar da cikin datayi har so 3, likita yace mahaifarta tasamu matsala. Shiyasa bata da damuwa agidan, itade burinta kawai tasamu ta tara abin duniyarta, shiyasa takebin Gimbiya Zakiyya soda kafa, sede tabangare guda kuma sun hade kansu ita da Jakadiyya. Zaune Jakadiya take afalon Gimbiyar Babbar Gida, kallonta tayi tace inajinki Jakadiya wace shawara kika kawo? Gyara zamanta tayi takara rage murya tace Gimbiya bawata shawara bace dama wata dabara nakawo, nace meze hana kicema Memartaba kina da ciki. Saurin tashi Gimbiya tayi tace bangane mekike nufi ba. Wace irin magana kikeyi haka, dama ana cikin karya ne? Murmushi Jakadiya tayi tace Allah yahuci zuciyarki, bahaka nake nufiba. Kinga yanzu ku 2ne matan Sarki, kuma kece Babba taya za,ayi muyarda wata tashigo daga baya ace ta haihu ke baki samu naki ba. Jiya mukayi magana da Sarkin Fada kinsan mutumina ne, agurinshi nasamu labarin Sarki yace daya samu da namiji tofa lallai shine zegajeshi, shine nace meze hana kawai kice mashi kinada ciki, idan yaso sekirika saka tsummuna idan lokacin girman cikin yayi, kinga semuje gidan marayu mudauko yaro namiji kinga kema kinyi na..... marin da aka dauketa dashine yasata tayi shiru. Dasauri tamaida kallonta gurin Gimbiya datake ta huci sbd tsananin bacin rai, cike da tsawa tace kitashi kibacemun daga nan. Kuma ina me tabbatar maki da duk ranar dana kara ganin kafarki acikin part dina wlh sekinbar masarautar nan. Cike da bacin rai Jakadiya tafito, hanyar lambu tanufa inda suka saba haduwa da Sarkin Fada, wata baiwace tafito dagudu zata wuce, dasauri Jakadiya ta tareta dan tagane baiwar Gimbiya suhailat ce. Ke lafiya kike gudu haka? Wlh dama sauri nakeyi inje inyima Sarki Albishir Gimbiya tasauka lafiya tasamu da na miji. Kara goge kunnanta Jakadiya tayi tace bangane mekike fada ba. Dama Gimbiya ciki gareta? Kwarai ma kuwa, aiko Sarki yasan tana dashi. Wani mugun murmushi Jakadiya tayi, tace ki koma za'a isar mashi da sako. Dasauri Jakadiya tanufi gurin Sarkin Fada, sundade suna magana daga baya tafito tana dariya tanufi bangaren Sarki. Bakaramin dadin Sarki yaji ba, nan take yayima Jakadiya kyauta metsoka, Qaseem ma seda yabata kyauta, dan yana gurin aka fadi haihuwar. Kafin wani lokaci gidan Sarki ya sheda haihuwar Gimbiya Suhailat, Qaseem boye farin cikinshi yarikayi, dan bayason Yayanshi yashiga damuwa. Bakaramin tashin hankali Gimbiya Zakiyya tashiga ba lokacin da labari yazo mata. Har kuka seda tayi, gashi takori Jakadiya, haka tasa aka kira Gimbiya Nafeesa ita tarika bata hkr, dan ita ko akanta. Duk wata hidima Safeeya ce take mata, yaronta me kyau sosai, tun yana jariri dayayi kuka se dimple dinshi ya fito. Bayan kwana 7 akayi suna, Sarki da kanshi yasama yaron suna, dan Qaseem yaso yasaka sunan Yayanshi amma Sarki yace yabari zesa mashi suna, shikuwa yayi haka ne, dan yabama matar kaninshi hakkinta ko akwai sunan datakeson tasama yaron. Lokacin dayasa Safeeya ta tambayeta sunan datakeso asama yaron tace tanason asamashi Areef, dan sunan kaninta ne, daya rasu. Sarki yaji dadin tambayr dayasa akayi mata, koba komai yasan ba,a shiga hakkinta ba. Qaseem yayi mamakin sunan da Sarki yasama yaron, koda yabincika yagane shine yasa atambayi matarshi, bakaramin jin tausayin Yayanshi yayi ba, kuma yakara jinjina adalci irin nashi. Bakaramin taro akayi ba, hatta da yan uwanta seda sukazo suna, su gimbiya Zakiyya sunga yanda ake mulki da kuma dukiya, haka suka saki jiki kamar bakomai akayi suna lafiya, se alokacin suka san da zaman Safeeya, dan sunga komenene Gimbiya zata sa sede takirata, gashi kuma ita batada uniform bare suce baiwace, alokacin sunan ne Gimbiya Zakiyya tashirya da Jakadiya, dan tasan koba komai tana mata amfani sosai. Haka rayuwa tacigaba da tafiya, duk yanda suka so susamu wata hanya dazasu kunta tama Gimbiya suhailat babu dama. Jakadiya da sarkin Fada kuwa kansu ahade yake, dan sarkin fada seda yasan yanda yayi yarika shiga bangaren Qaseem, yanuna yana matukar son Areef hakan yasa yashiga jikin Qaseem sosai, duk lokacin da aka kawo Areef Fada, Sarkin Fada shine yake karbarshi yayita renonshi harseyayi kuka sannan amaidashi. Bayan shekara 1 Areef yakara wayau sosai, kullum afada yake wuni tare dasu Sarki, kowa yasan irin son da Sarkin fada yakema Areef, hakan yasa itama Gimbiya suhailat take mashi kyauta akai akai. Lokacin da Areef ya cika shekara 1 da rabi aka yayeshi, dan baya zama agurin Gimbiya yafi zma afada shiyasa kawai ta yayeshi. Duk wani makircin Jkadiya da Sarkin Fada babu wanda yasani, wata rana suna cikin lambu suna makircinsu, Sarkin fada Yace wlh Jakadiya idan har muka bari wannan yaron yagirma kashinmu yabushe, Jakadiya tace meze hana mukawar dashi kowa yahuta. Murmushi sarkin fada yayi yace shawararki tana kan hanya. Shiru yayi jin motsi akusa dasu, saurin juyawa yayi yanufi inda motsin yake, caraf yariko hannun wata baiwa wadda tazo wucewa taji suna magana ta labe tana jinsu. Kuka tafarayi tana fadin wlh, banji komai ba, kuyi hkr, dankwalinta yacire yashaketa dashi harseda ta mutu sannan, Jakadiya tace kaga shegiya, muzaki tonama asiri. Yo da asirinmu yatonu ai gara kowa yamutu. Sarkin fada yazamuyi da gawar, kasande idan aka duba ba,a ganta ba dole ashiga nemanta. Murmushi yayi yace kada kidamu mubarta anan ko anzo anganta babu wanda zece kasheta akayi, daukarta yayi yajefata cikin swimming pool din gurin suka tafi. Da gudu Jakadiya tashiga bangaren sarki tana kuka, Waziri yace lafiya ke kuma zakishigo mana haka? Tana kuka tace wlh nazo wucewa naga kamar mutum acikin ruwa shine nazo infada maku, ai dasauri suka mike suka nufi gurin, fadawa waziri yasa suka cirota, koda suka duba suka iske tamutu. Sarki da Qaseem sun shiga damuwar abinda yafaru, haka akayi mata wanka aka rufeta, koda akayi bincike wata kawarta baiwa take fadin dama tana tsoron ruwa lokacin da aka aiketa lambu daga lokacin bata kara ganinta ba, sese akace ta mutu. Sarki yace kila zamewa tayi tafada kuma babu wanda yaganta. Da haka akarufe maganar, hankalinsu Jakadiya ya kwanta. Wasu mutanene guda 2, tare da wani Dattijo daka ganshi zakaga beyi kama da hausawa ba, yafi kama da larabawa, gefenshi. Kuma wata kyakkyawar matace, fara tasss da ita, itama babbar macece, gefenta wata santaleliyar budurwace kyawunta yawuce afadeshi, daka gansu kaga larabawan asali, yarinyar bazata wuce shekara 19 ba, tare suke da kayansu suna tsaye ajikin wani dankaramin gida me kyau. Mutane 2 dasuke tare dasu daya daga ciki yace to Baba yakaga gidan yayi maka? Cikin hausarshi wadda bata goge ba, yace e gida yayi tunda akwai dakuna 3 aciki kuma kowane da bandaki nashi aciki ai yayi dede. Dayan yace yauwa Baba kamar yanda muka fada maka zaka rika bamu dubu 50 ashekara sune kudin hayar gidan. Baban yace shikenan babu damuwa, amma akwai wutan nefa ko? E Baba akwai komai har ruwa bamuda matsalarshi. Baban yace toyanzu kaine zakazo kadaukemu anjima muje cikin kasuwa muyi siyayyar kayan amfani ko? E Baba kome kakeso zanyi maka, kuma zan kaika inda zaka samu kaya masu kyau. Yace toshikenan yaro nagode bari mushiga daga ciki mu huta. Wadan nan mutanen bawasu bane kamar yanda kukaji ankira dattijon da Baba. Asalin sunanshi ABRAHAM ne, kuma shi mutumin saudiya ne, yatabayin zaman Nigeria har so 2, yayi aiki da hausawa agarin Bauchi, bayan yakoma saudiya ne, ya yanke shawarar dauko iyalinshi yadawo dasu Nigeria, kasancewar yaji dadin zamanshi ABauchi gurin wani mutumin kirki, bayan yatafi seda yayi wata 2 bedawo ba, se wannan dawowar dayayi tare da iyalinshi, sede yayi rashin sa,a yana zuwa Bauchi yasamu labarin rasuwar mutumin. Yayi kuka sosai, dayake akwai Babban yaron Alhajin atare sukayi aiki, kuma shi dan Gombe ne, hakan yasa yanemi address dinshi yazo nan yasameshi, kuma shine yayi mashi hanyar samun gidan dazasu zauna, dan yace tund yariga da yabaro garinsu baze koma ba, shiyasa yace zezauna agurinshi sucigaba da kasuwancin tare. Matarshi daya da yarsu daya, mesuna Rayhana, suna matukar sonta sosai, tana da ilimin boko dana addini, gata da natsuwa baruwanta da hayaniya, tanason iyayenta sosai. Bayan sun huta, dayamma akazo akadaukesu suduka suka tafi kasuwa. Jerin motocin Sarki ne suka shigo cikin gari suna jiniya sundawo daga Yobe, tacikin gari suka shigo dansu gaisa da jama'a mutane se daga masu hannu sukeyi, dan mutanan Gombe suna son Sarki Hasheem sbd yana masu adalci. Rayhana ce da Umminta suka fito daga wani store na kayan kitchen, Mahifinta kuma yana daga dayan bangaren tare da wanda sukazo suna siyan wasu kaya, Rayhana takamo hannunn Umminta dansu tsallaka titi, yaran dasuka dauko masu kayan suna binsu abaya. Wata irin kara da Baba yaji ne, tasashi saurin juyowa dashi da mutanen dake gurin. Innalillahi Wainna ilaihirrajiun, shine abinda mutane suke fadi da gudu Baba yarugo dan ganin abinda yake faruwa. Dasauri sauran motocin suka samu guri sukayi parking suka fito domin ganin abinda yake faruwa. To jama'a muje zuwa anext page danmuji meyafaru. Tnx alot for ur concern to me, my luvly friends. Ur's NABILA RABI'U ZANGO (Nabeelert Lady) 08028525263 [23/08, 1:48 p.m.] Nabeelert Lady: ..🛤🛤🏕🏕🏕🛤🛤🛤 AMAKABARTA AKA HAIFENI 🛤🛤🏕🏕🏕🛤🛤🛤 (The story of hard kingdom) Nah Marubuciyar Zamani NABILA RABI'U ZANGO (Nabeelert Lady) @House of Novella Association (H,O,N,A) www.NabilaLady5@gmail.com Season 40⚜45 Rayhanace rike da Umminta akasa ta rungumeta tana wani irin kuka yayinda jini duk yabata mata jiki. Babanta ne, yakaraso gurin ganin abinda yake faruwa shima yaduka ya rungumo matarshi yana kuka, babu alamun rai ajikinta, dan tunda motar tabigeta nan take tacika. Driver daya kadeta ne, ya iso gurin, abayanshi kuma su Sarki ne da tawagarshi suka nufo gurin dan yana daya daga cikin motocin gidan sarki. Isowarsu tayi dede da Rayhana tamike tana kuka tanufi drivern motar tashakeshi tana kaimashi duka tana kuka. Dasauri Waziri dasu sarki suka karaso gurin, Waziri ne yayi kokarin cireta daga jikinshi yana bata hakuri, komawa tayi gurin Umminta tazube tana kuka gwanin bantausai. Qaseem da Wazirine suka isa gurin, shikuwa Sarki tunda yadora idonshi akan Rayhana yaji wani abu ya soki zuciyarshi, da kyar yasamu ya dedeta kanshi ya karasa gurin, amma duk da haka yakasa dauke idonshi akanta. Waziri yaduka kusa da Baba yakamoshi yana fadin kayi hakuri Baba muje akaita asibiti. Dago kai Baba yayi yana kallonshi yace wane asibiti kuma, bayan tarasu. Cak numfashi Rayhana ya tsaya jin abinda Babanta yafada, nan take tasume. Mamaki ne, yakama mutanen gurin lokacin dasuka ga Sarki yadauki Rayhana yayi hanyar mota da ita, ganin haka Waziri yace ma Baba yatashi sutafi asibitin, Waziri da kanshi yadauketa suka nufi mota, Qaseem dayake bin Yayanshi da kallon mamaki shima yanufi mota suka nufi asibiti. Suna zuwa aka karbesu, dan danan aka fara bama Rayhana temakon gaggawa, Umminta kuwa koda suka aunata anan suka gano ta jima da rasuwa, anan sukayi masu bayani, Seda Su Waziri suka rike Baba lokacin dayaji bayanin likita, abisa kujera suka zaunar dashi, anan Waziri da Qaseem suka shiga bashi hakuri. Baba yace ashede kasarki anan take, jiya mukazo garin nan ashe bazaki rayu damuba. Haka yayita sambatu, suna bashi hakuri. Sarki kam hankalinshi yana kan Rayhana, yakasa tsaye ya kasa zaune, Qaseem ya maida kallonshi gurin Yayanshi, tausayinshi ne, yakama shi, dan tunda yake betaba ganin Yayanshi cikin wannan yanayin ba, tashi yayi yanufi gurinshi. Kafadarshi yadafa, juyowa yayi, yana kallonshi, hannunshi yakama suka nufi wata kujera suka zauna. Qaseem yace Yaya kanutsu Fadawa da mutanen gari suna kallonka, kuma kowa yasan bamuda alaka dasu kada suyi tunanin wani abu. Sarki yace Matar tarasu ko? Kai Qaseem yadaga mashi, Sarki yace Allah kaceci baiwarka kada itama ta tafi. Qaseem yayita bashi baki. Mintuna 30 Rayhana tadauka kafin tafarfado, alokcin har antafi da Umminta gidan Sarki, dan Sarki dayaji cewar bakine agarin shine yaroki Baba akan suje masarautarsu ashiryata ayi mata sallah acan se arufeta. Baba yaji dadin yanda yasamu mutanen kirkin dazasuyi jana'izar matarshi. Suna zuwa gidan Qaseem yawuce part dinshi yacema Safeeya tafito akaita asibiti zata zauna da wata kafin sudawo, haka yasa driver ya kaita yarakata har dakinta shi kuma yakoma. Koda Rayhana tafarka wata mata tagani akusa da ita, cikin Hausarta marar

Chapter 3 of 13