Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
dadi wadda suka koya agurin Babanta danshi zaman dayayi anan yasa ya iya hausa, kallonta tayi tace Ina Ummi na? Matsawa Safeeya tayi takamota tace kiyi hakuri tana daki, kai Rayhana tashiga girgizawa tana fadin ance ta mutu ai. Kuka tasaka marar sauti, sede daka jishi zakasan yana ci mata zuciya. Ahaka aka turo kofar dakin, tana daga kanta taga Babanta ne da wasu mutane, shima idonshi yayi ja sosai. Dasauri yakaraso gurinta ya rungumeta shima yasa kuka, tsaya su Sarki sukayi suna kallonsu cike da tausayi. Ganin tasamu sauki likita yasallamesu. Bayan sunfito Rayhana tana jikin Babanta hawayene kawai suke fita daga idonta, Baba yakalli Sarki yace Yallabai inaganin Zamu koma garinmu gobe, banga amfanin zamana anan ba, dama nazo daniyar zama anan, amma tunda narasa matata gara mukoma nida yarinyata. Mungode Allah yasaka da alkhairi, kuma munyafe ma wanda ya banketa, sede yaje yayi azuminshi. Shiru Sarki yayi yanajin wani zafi aranshi, kasa magana ma yayi ya tsaya yana kallon Rayhana. Qaseem ne yayi saurin fadin a,a Baba yanzu kaga dare yafarayi, muje gida koma menene semu tattauna. Part din Gimbiya Suhailat Qaseem yace Safeeya tawuce da Rayhana, shikuma Baba suka nufi bangaren Waziri dashi, Part din Sarki Qaseem yawuce dan tunda suka shigo yawuce part dinshi. Kwance yasameshi abisa gadonshi yana kallon sama. ( Niko nace Kadde ace su Sarki anshiga layi ne ). 😉). Zama Qaseem yayi yadafashi cikin sanyi murya yace Yaya tundazu naga kashiga cikin damuwa, wanda kuma bahaka muka taho da kai ba, damuka dawo Yobe, kafadamun damuwarka, idan baka fadamun ba, wazaka fada mawa? Tashi Sarki yayi yakalli Qaseem yace shikenan yanzu Qaseem tafiya zasuyi? Ai yakamata ace tunda harsunzo daniyar zama garinmu kuma sukayi rashi tadalilinmu yakamata ace mubasu muhalli akusa damu suzauna, wlh Qaseem haka nan araina naji banaso sutafi. Murmushi Qaseem yayi yace kada kadamu Yaya munyi magana da Waziri bazamu bari sutafi ba. Sarki besan lokacin da wani Murmushi ya kwace mashi ba. Tashi Qaseem yayi shima yana murmushi yace Yaya bari inwuce seda safe. Harya kai bakin kofa yajuyo yace Yaya Allah tabbatar da alkhairi. Dasauri yafita yana dariya. Murmushi Sarki yayi ya girgiza kai yanajin wani sanyi yana ratsashi. Rayhana kuwa tana falon Gimbiya Suhailat sunata lallashinta. Cike da tausayi Gimbiya tace kiyi hakuri kinji, daga yau munzama yan uwanki, bazakiyi maraicin Uwa ba, kinga nima ba'a nan kasar nake ba. Daga yau kinga nasamu yar uwa, haka sukayita lallashinta hartasamu taci abinci tayi wanka suka nufi dakin Safeeya suka kwanta. Washe gari Baba yasa aka kira mashi Rayhana tana zuwa suka fara kuka, Waziri yace suje fada Sarki yanason ganinsu. Bayan Sungama gaisawa Sarki yakara yimasu ta'aziya. Anan waziri yafada ma Sarki sunyi magana da Baba yace ya hkra zasu zauna, sede yafiso yakoma gidan daya kama yazauna aciki. Qaseem yace Baba dan Allah kayi hkr kazauna tare damu kaga Rayhana zatafi jin dadin zama anan saboda akwai mutane, amma acan daga kai se ita, kuma daka fita zata zauna ita kadai, kaga kadaici zeyi mata yawa. Baba yace shikenan naji zanbarta anan amma nikam nafiso nazauna acan. Waziri yace shikenan Baba munyarda, amma zakayi hkr kadawo kusa damu, kaga can yayi nisa kuma zakayi nisa da 'yarka, akwai wani gida nesa kadan da masarautar nan za'a gyara makashi se asaka maka wadan da zasu rika yimaka hidima seka zauna, kaga koba komai kana kusa damu. Baba yace to nagode sosai, Allah yakara budi. Kallon Rayhana yayi wadda tayi lamo ajikinshi, cikin larabci yayi mata bayanin komai, shiru tayi tana kuka, kai tashiga girgizawa tace ita bata yarda ba, da kyar yasamu yashawo kanta. Haka yayi masu bayani ta amince, bakaramin dadi Sarki yaji ba, tagefen ido Qaseem yakalleshi shima yayi murmushi ganin farin ciki kwance afuskar Yayanshi. Haka aka gyarama Baba gidan aka zuba komai, yakoma ciki, Qaseem da kanshi yazabi bayi maza da mata dazasu rika yimashi aiki. Rayhana kuwa ankawo mata kayanta, kuma Gimbiya Suhailat da Qaseem sunce agurinsu zata zauna. Gimbiya Zakiyya da Gimbiya me daki bakaramun jin haushin abinda akayi sukai ba, baram ma Gimbiyar Babbar Gida, gani take kamar anmaidata saniyar ware,Jakadiya wadda itace take kawo masu duk wani labari daga fada. Kallon Jakadiya Gimbiya tayi tace agskiya jikina bebani zaman wannan balarabiyar agidan nan akwai alkhairi ba. Kawai ni tunkafin inganta wlh naji na tsaneta, tsana ma ta sosai, dan haka dole musan wane irin kulli zamuyi mata tabar gidan nan. Jakadiya tace Gimbiya da ace Gimbiya suhailat tana daukar zuga kuma tana bani fuskar shiga gurinta danaje mata dawani kaidi wanda na tabbata setayi sanadiyar fitar wannan yarinyar agidan dan sena nuna mata mijinta akwai dalilin dayasa yakawota gidanshi tazauna. Gimbiya medaki tace kai amma Jakadiya kinkawo shawara me kyau, kuma dole sekin san yanda zakiyi kisamu kishiga jikinta. Gimbiya Zakiyya tace ni nasan me za'ayi, ina Sarkin Fada, ai mutuminta ne, dan haka tagurinshi zamu samu damar aikata abinda mukeso. Jakadiya tace angama ranki yadade. Murmushin farin ciki tayi takoma ta kwanta tana fadin seyanzu nafara jindadin aiki dake, dan kinfara kawo shawara irin tamasu tunani, wato yan gidan sarauta. Kallon Gimbiya medaki Jakadiya tayi, suka hada ido, su duka sunji zafin maganar data fada masu, amma haka nan suka hadiye bacin ransu. Kwance Gimbiya Suhailat take ajikin Qaseem yana wasa da gashinta, Gimbiya tace Hubbi kasan mene? Yace sekin fada, wlh naji dadin zuwan Rayhana gidan nan, naji dadi sosai daka kawomun ita part dina, inajinta ajikina sosai. Qaseem yace nasan zakisota, shiyasa nakawo maki ita, kinsan nasan duk wani abu daya dace dake. Kinma san menene? Tace a,a inaso kikara kula da ita sosai, dan inaji ajikina Yaya kikema kiwo. Dariya suka saka tace kai Hubbi da gske? Yace sosai ma, kodazu munyi maganar da waziri, shima ashe yagane abinda Yaya yake ciki. Kai amma naji dadi, aikuwa zankoya ma Rayhana yanda zata kwace Yaya daga gurin wadan can matan nashi. Jinjina ta musamman gareku masoyana. Nagode sosai, sekunjini a next page😘 . Ur's. NABILA RABI'U ZANGO (Nabeelert Lady) 08028525263 [23/08, 1:48 p.m.] Nabeelert Lady: ..🛤🛤🏕🏕🏕🛤🛤🛤 AMAKABARTA AKA HAIFENI 🛤🛤🏕🏕🏕🛤🛤🛤 (The story of hard kingdom) Nah Marubuciyar Zamani NABILA RABI'U ZANGO (Nabeelert Lady) @House of Novella Association (H,O,N,A) www.NabilaLady5@gmail.com Season 45 ⚜50 www.NabilaLady5@gmail.com Season 45 ⚜50 Sarkin Fada ne zaune afalon Gimbiya Suhailat, Areef yana bisa cinyarshi yanata wasa yanacin biscuit, Murmushi Gimbiya tayi tace Sarkin Fada kaida mutumin naka ne? Washe baki yayi yace barka da fitowa ranki yadade uwargidan Yallabai. Zama tayi, bayan sungaisa Areef ya mika hannu alamun tadaukeshi, murmushi tayi tace a,a nibazan dauke ka ba, ai nadauka kamanta dani, kara wangale baki yayi kamar yaji abinda tafada. Hannu tamika mashi segashi yataho. Lafiya de Sarkin fada naganka awannan lokacin? Kanshi yadan sosa ahankali yace lafiya lau, dama wani dan labarine naji awaje shine nace bari inzo inji daga uwar dakina ko haka zancen yake, dan abun yashafeki, nikuma aduniya babu abinda zanji dangane dake ace nabarshi. Inajinka, E to, to dama de akan wannan bakuwar balarabiyar ne datake zaune agurinki, shine naji mutane suna cewa wai yallabai Qaseem ne yakawota, koshima zebi sahun Memartaba ne yabi Sunnah. Kuma da alama itace ze aura ko? Wani murmushi Gimbiya tayi takara kallon Sarkin Fada, gaba daya babu natsuwa atare dashi, kozama yakasayi. Kara murmushi tayi tace tonagode, amma nibani da labari, sede kazauna inaji yakusa shigowa semuji daga gareshi, zaro ido yayi yace haba Gimbiya rufamun asiri, ina ni ina zama inyi irin maganar nan da Yallabai, nifa dama ban tabbatar ba, kawai kinsan bazanso arika maganarki ina guri ba, shiyasa nace gara inzo inji da kunnena. Murmushi tayi tace gaskiya kam ka kyauta, to bahaka maganar take ba. To harnaji dadi, aini bazanso ayima uwar dakina abokiyar zama ba. Tonizan koma, ahuta lafiya. Mikama Areef hannu yayi nan yataho suka fita. Murmushi tayi ta girgiza kai, kallon wata baiwa tayi tace takira mata Safeeya. Bayan tazauna ta fada mata abinda Sarkin Fada yace mata. Shiru Safeeya tayi nadan lokaci, sannan tace nifa Gimbiya dama nafada maki banyarda dashi ba, ina yawan ganinsu tare da Jakadiya, amma kikace kinyarda dashi. Gimbiya tace bakomai Safeeya ki kyaleshi ni haryanzu ina mashi kallon mutumin kirki, kila da gaske yaji maganar, kinsan gidan nan akwaisu da gulma, bare sunga ankawo yarinya mekyau dole surika tsegumi. Safeeya tace amma duk da haka kirika kula sosai Gimbiya, ba'a saurin yarda da mutum, nasan kuma wannan halin kine, amma naga kinyarda dashi. Tace shikenan Allah yashige mana gaba, tace amin. Haka suka cigaba da rayuwa, su Gimbiya Zakiyya duk yanda sukaso su hada tuggu akori Rayhana sunkasa. Sarki kuwa Son Rayhana yayi girma azuciyarshi, gashi baya ganinta dan bata fitowa sede idan zataje gaida Babanta ita da Safeeya, ganin abun zedameshi ya yanke shawarar fadamasu Qaseem. Waziri ne da Qaseem Zaune afalon Sarki, su dukansu cike suke da murnar abinda Sarki yafada masu, dama kuma abinda suke jira suji yafada kenan, dan Waziri yace ma Qaseem yabari shida kanshi yayi masu maganar. Waziri cike da murna yace agskiya naji dadin wannan labari, nima tunda naga yarinyar kawai naji ta kwanta mun arai, duk da bata fito daga gidan sarauta ba, amma inaganin aurenku akwai alkhairi aciki. Amma mekace Qaseem? Murmushi yayi yace aini nakasa magana sbd farin ciki. Duk da inada ra'ayin kin auren wadda bata fito daga gidan sarauta ba, amma nikam nayima Yaya sha'awar auren Rayhana, sbd mune muke tare da ita nasan halinta mekyau gashi babu ruwanta, tana da addini, Allah ya tabbatar da alkhairi. Sosai Sarki yaji dadin maganarsu, kallon Waziri yayi seyayi shiru. Waziri yace to ai ba tsayawa zamuyi ba, zanyi magana da Malam domin yayi mana addu'a akan al'amarin, kome yafada semuyi magana da Baba. Qaseem yace wannan yayi dede, Allah yate maka. Waziri yace amma inaso abar maganar anan, harse komai ya tabbata, kasan halin mutane. Sarki yace wannan yayi dede. Bayan kwana 2, malam yakira Waziri suka yi magana akan istaharan dayayi. Waziri yaji dadin abinda malam yace, sundade suna kara tattaunawa akan masarautar, sannan sukayi sallama. Qaseem yakira yafada mashi komai, sannan suka fadama Sarki. Sosai yaji dadi, waziri yace zasuje suga Baba. Gimbiya Suhailat da Safeeya sunji dadin maganar, sede Rayhana batasan abinda akeyi ba. Da dare Gimbiya Suhailat takirata, bayan tazo Gimbiya ta sheda mata dalilin kiranta. Sunkuyar da kai tayi tana murmushi bata ce komai ba, Safeeya tace Rayhana kiyi magana mana kin amince? Da gudu ta tashi tana dariya tashige daki. Dariya Gimbiya tayi tace Allah mungode maka, gaskiya naji dadi sosai. Allah yashige mana gaba. Safeeya tace amin, amma ina tausaya mata gata karama babu ruwanta zata shiga cikin matan Sarki. Gimbiya tace kinsan yanda Yaya yake sonta kuwa? Betaba auren Soyayya ba seyanzu zeyi, kinsan baze bari wani ya wulakanta taba, kuma akusa dashi za'a ajeta, bakiga ana kara gyara part dinshi ba? Nasan de kawai su Gimbiya Zakiyya zasu sha kayan haushi sede suyi hakuri. Nikam yanzu zan kara koyama Rayhana zama dasu, kuma dole ayi mata gyara na musamman, nasan dawuri za'ayi bikinta amma duk da haka daga gobe zata fara amsar gyara. Bayan su Waziri sunje gurin Baba sukayi mashi bayanin daya kawosu, sosai Baba yaji dadin maganar, nan take ya amince, masu suka bada kudin neman aure dubu dari biyar. Anan aka yanke rana sati 2. Godiya sukayi mashi kuma suka fada mashi basu bukatar komai. Zaune Jakadiya take afalon Sarki, Bayan sungama gaisawa yakalleta cike da girmamawa, danshi yana matukar girmamata, dan sunyi sabo sosai, komatanshi bayajinsu kamar yanda yake jinta, sun share shekaru tare tun farkon zuwanta gidan, take mashi hidima, shiyasa yabata amana sosai. Kallonta yayi yace dama nakiraki ne dan inbaki sako kifada ma su Gimbiya Zakiyya da Nafeesa maganar aurena nan da sati 2. Akwai Yarinyar da take zaune gurin Suhailat wadda mukazo da mahaifiyarta nan akayi mata sutura wadda driver na ya kade harta rasu. To itace nakeso na aura. Washe baki tayi tace amma naji dadi sosai, kallonshi tayi tace Rankai dade da alama naga kana son Rayhana sosai, bantaba ganinka cikin wannan farin cikin ba alokacin da zakayi aure ba, se wannan karon. Ko aurenka na farko banga wannan farin cikin atare da kaiba. Murmushi yayi ya sosa kai, dan yanajin Jakadiya kamar mahaifiyarshi dan tagirmeshi, yace wlh Jakadiya ina mata son daban taba yima wata mace ba. Dariya tayi tace Allah ya shige mana gaba, kuma anan danaga ana gyara za'a ajeta ko? Yace haka ne. Murmushi tayi tace gskiya nafi kowa farin ciki da wannan al'amari, sbd yanzu Uban gidana zesamu abinda ranshi yakeso. Dan haka zan daukota domin akoya mata zama agidan sarauta. Kallonta yayi yace ai inaganin kamar Suhailat tana koya mata, babu damuwa nasan zata kula da ita sosai. Jakadiya tayi murmushin yake tace toshikenan bari inje infada masu Gimbiyar. Check yadauko guda 2 yace takaimasu kowa dai dai. Wasu kudi yadauko yamika mata yace ga wannan kema kirike ahannunki. Godiya tayi mashi tafita. Gurin Sarkin fada tawuce, abinda yafaru tafada mashi, sosai suka shiga tashin hankali. Sarkin Fada yace kina ganin Sarki baze iya samun haihuwa da wannan yarinyar ba kuwa? Kinsan fa ance larabawa albarka garesu. Jakadiya tace kada kadamu nasan abinda zanyi, damma Sarki yace ba,a gurina zata zauna ba da tunkafin tashiga gidanshi zanyi kokarin hanata haihuwa, amma kasan ni amintattar Sarkice dan haka kome nakai zesata taci, dan haka kada kadamu inde ina raye bazan bar Sarki yaga kwanshi aduniya ba. Shekarata nawa ina mashi hidima amma haryanzu nakasa zama wata acikin gidan nan, haka zankare a Jakadiya?. Sede inzama fitila ina haska wasu ni ina kona kaina, ai rashin gata ba hauka bane, dan haka gara kowa yayita zama ahaka, shima wannan yaron dande ka hanani dayanzu na aiwatar mashi. Sarkin fada yace kiyi hakuri wannan yaron yashiga rai na, Allah yasani badan so nafara daukarshi ba, amma daga baya yashiga raina sosai, dan haka kibarshi, ninasan ko Sarki yamutu sede Qaseem yahau kujerarshi bade Areef ba, dan haka mutsaya akan sarki da matanshi. Yanzu kije ki kaima Gimbyar Baban Gida mugun labari, dannasan ita kadai zata shiga damuwa, banda Medaki, itakam ai tamu ce. Dariya Jakadiya tayi tace wlh bakada dama. Yace Allah kuwa kinsan daza,a bani Gimbiya medaki ai dana more, tun lokacin datazo gidan nan miyau na yabiya kawai senaji wai Sarki ze aureta. Jakadiya tace ai naga alamar itama yar hannu ce, amma matso kaji. Wata dariya suka kwashe da ita Sarkin fada yace kina ganin haka za,ayi? Tace sosai ma, amma bayanzu ba senan gaba idan komai ya zama dede. Wani uban gumi ne yake fitowa daga jikin Gimbiya Zakiyya, kara kallon Jakadiya tayi tace yanzu jakadiya har saurin zuwa ki kawomun wannan bakin labarin kikeyi? Jakadiya tayi kasa da kai tace Allah yahuci zuciyarki, shima Sarki ba sonta yake ba, kawai tallarta Babanta yayi mashi, kuma kinsan Sarki dasaukin kai shiyasa ya amsa, amma dakanshi yafadamun ke kadaice macen dayakeso aranshi, duka sauran ya auresu ne abisa lalura. Dan haka ki kwantar da hankalinki. Komawa tayi tazauna, saurin zuba mata ruwa jakadiya tayi tamika mata. Bayan tasha tace yanzu ya za'ayi kenan? Jakadiya tace Ranki yadade kamar yanda kika saba, hakan zakiyi, kinsan Sarki yana yabonki akan halayyarki tarashin tada hankali aduk lokacin dazeyi aure. Yace shiyasa yake kara sonki. Murmushi Gimbiya tayi tace shikenan, amma wannan karon bazan kyale wannan yarinyar ba. Jakadiya tace ai bazamu barita dadeba. Ita kuwa Gimbiya medaki duk da taji haushi kadan amma ana bata magudan kudi tamanta da fushin. Jakadiya tace dama nasan bazaki damu ba, se waccan sarkin kishin, ita tana ganin kamar ita kadai sarki yakeso dan tafito daga gidan sarauta. Medaki tace aisetayi tayi nikam inde da kudi ya auri 10 ina ruwa na, nasan kawai zanrasa kulawar danake samu duk bayan kwana 2 , nasan hakanne kawai zedameni dan Sarki akwai iya shiga rai. Dariya Jakadiya tayi tace ai Gimbiya nasan matsalarki, kuma wannan badamuwa bace kede kawai kirikeni zaki samu yanda kikeso. Sarkin fada ma yanzu yaganni zanshigo nan yace ingaisheki, kinsan ke kadai yake gaidawa aduk matan gidan nan gaskiya yanaji dake. Medaki tayi dariya tace ai yana da kirki damma kada ace wani abu ai daya rika rakoki munashan labarai. Murmushi Jakadiya tayi tace ah, tunda kinaso ai angama. Sati 2 Gimbiya Suhailat tadauka tana gyara Rayhana, takara kyau, sosai kyanta haryaso yayi yawa, tasha gyara sosai. Duk wata kissa Gimbiya ta koya mata, dayanda zata zauna da matanshi, babu abinda bata koya mata ba. Duk wanda yakwana yatashi agarin Gombe babu wanda besan Sarki zeyi aure ba, gaggarumin biki aka shirya gidan kanshi yasha gyara, hankalin Gimbiya Zakiyya bakaramin tashi yayi ba, dan tagano irin son da Sarki yakema Rayhana, tun daga dukiyar dayake kashewa da kuma irin hidimar da taga Qaseem yanayi, wanda tasan shikanshi yana murna da bikin. Taso ta tadama Sarki hankali akan auren, amma mamanta tanaji tahanata, tace bakida hankali Zakiyya? Kina ganin akan abinda yakeso baze iya wulakantaki ba? Tunwuri idanma wasu ne suke zugaki togara kidawo hanya, kina ganin nice karama acikin matan Abbanki amma yanzu nice nazama babba, dan haka banyarda kikara tada hankalinki akan auren nan ba. Kuma banyafe maki ba, idan har kika yarda wata tajaki kukaje gurin wani malami ko boka. Hakuri Gimbiya Zakiyya tayi ta bata kuma tayi mata alkawarin bazata je gurin kowa ba, kuma bazata kara tada hankalinta akan auren ba. Da haka ta kwantar da hankalinta, sede tayi alkawarin idan har tuggu da kissa suna sa mutum yaci riba zatayi amfani dasu takori Rayhana daga gidan Sarki. Ayau ne miliyoyin jama'a daga jahohi daban daban da manyan sarakuna na garu ruwa suka halarci bikin Sarki Hasheem da Rayhana, wanda aka daura akan sadaki million 1, kowa yasheda wannan auren Soyayya ne Sarki yayi, ankashe dukiya sosai, anci ansha maroka da mawaka sun sami kyauta sosai. Adaren ranar Sarki da sauran Sarakuna da manyan masu kudi sukayi kayatattar walima ababban dakin taron masarautar Bubayero. Bayan sungama kowa yanufi masaukinshi, kuma ranar aka kai amarya Rayhana dakinta dayasha dukiya kamar ba,a nigeria ba. Yayin da wasu suka cika da farin ciki alokacin Gimbiya Zakiyya tarasa inda zata sa kanta sbd tsabar bakin ciki. Jakadiya kuwa jan Sarkin Fada tayi suka nufi part din Medaki acan suka zauna suna bikinsu. Nima nace yakamata abar amarya da Ango su sha amarcinsu. Nagode sekunji ni a next page . .😘. Ur's NABILA RABI'U ZANGO (Nabeelert Lady) 08028525263 [23/08, 1:48 p.m.] Nabeelert Lady: ..🛤🛤🏕🏕🏕🛤🛤🛤 AMAKABARTA AKA HAIFENI 🛤🛤🏕🏕🏕🛤🛤🛤 (The story of hard kingdom) Nah Marubuciyar Zamani NABILA RABI'U ZANGO (Nabeelert Lady) @House of Novella Association (H,O,N,A) www.NabilaLady5@gmail.com Season 50⚜55 Washe gari. Basu suka tashi ba, se 8:00, dasauri Sarki yatashi ganin ko sallah basuyi ba, gaba daya kunyar fita yakeyi dan yasan kowa nagidan yasan baya fashin sallah amasallaci, babban abin kunya ma abokananshi sunce zasu biyo sugaisa da Amarya kafin su wuce, gashi nan yamakara. Kallon Rayhana yayi wadda take kwance fuskarta tayi haske ga sahun kwallan datayi jiya nan kwance afuskarta. Murmushi yayi yashafi gashinta wanda ya hargitse, ahankali yace kece farin cikina GIMBIYA FULANI. Kiss yayi ma goshinta yatashi yaje yayi wanka yana fitowa yatada sallah, bayan yagama ya dauko Waya yakira Qaseem, yana dauka yace ai Yaya dayanzu zankiraka ince bakifa suna Falo harsun kusa gama karyawa. Sosa kanshi yayi yakara kallon Fulani yayi murmushi yace Uhm ka aika Safeeya taje takiramun Jakadiya tazo gurin Fulani nizan fita gurin baki. Shiru yayi sannan yace amma Yaya meze hana kamaidata dakinta se inturo Safeeya tazo ta kula da ita, kasan bazata yarda Jakadiya ta kula da ita ba, tunda basu saba ba. Murmushi Sarki yayi yace shikenan to bari in maidata dama dan naga Jakadiya ita kadai keshiga dakina shiyasa nace haka amma yanzu zan maidata dakinta. Kashe wayar yayi kunya duk takamashi yanzu yazecema mutane. Bayan yamaida Fulani dakinta wanda kofa ce kawai tarabasu da falon Sarki, duk abinda yakeyi tana jinshi kunya ce tahanata bude ido. Zama yayi yana kallonta, can kuma yatashi yafita yanufi gurin baki, akofa yahadu da Safeeya, cike da girmamawa ta durkusa tagaisheshi, amsawa yayi yana me mata fara'a. Yace yauwa Safeeya idan tashirya kaya suna nan su zata saka zasu gaisa da baki. Da to ta amsa mashi yayi waje, yana fita fadawa suka mara mashi baya suna kwasar gaisuwa. Duk wanda yaganshi aranar yasan yana cikin farin ciki, dan duk yanda yaso yaboye fara'arshi kasawa yayi. Yana shiga falon baki suka fara yimashi tsiya, sosai yake dariya dayake yashigo cikin abokanshi. Wani Sarki yace gskya Hasheem bantaba ganin wannan farin cikin atare da kai ba, kada muna skul baka wannan fara'ar. Lallai baseka fada ba, kowa yasan yanzu ne kayi auren soyayya. Wani yace aidole yayi farin ciki wlh auren so daban yake, shiyasa banyi aure ba seda nasamu wadda nakeso. Haka sukayita barkwanci suna dariya, wani yace kaga kada muyi rana gara afiddo mana Amaryar data hanaka sallah amasallaci muganta muga wane irin zabe ne kayi haka. Dariya yayi yace a gaskiya sede muje Falona babu wanda ze fitomun da mata tana amarcinta tafito waje. Dariya suka saka yafita. Abakin kofarshi yahadu da Jakadiya, saurin dukawa tayi tana mashi kirari, murmushi yayi yace Jakadiya kina lafiya? Tace lfy lau Rankai dade, dama tundazu naso inzo induba yakuka kwana sekuma naji ance badakai akayi sallah ba, shine nace to kobaku tashi dawuri ba?. Murmushi yayi yace hakane, ai har Safeeya tazo tana gurin Fulani. Fulani? Jakadiya takara maimaita sunan aranta. Murmushi tayi tace to ai shikenan, bara inje ingyara dakin yace to. Dakin Fulani yawuce, tunkafin ya isa wani da daddai kamshi ya dakar mashi hanci wanda yayi sanadiyar saukar kasala ajikinshi. Lumshe ido yayi aranshi yanakara jin son Fulani. Kwankwasa kofar yayi, da sauri Safeeya taje tabude. Dukawa tayi tana fadin ai har angama, murmushi yayi yace nagode, Jakadiya zata kawo maki tukuicinki. Godiya takara yimashi tafita. Yana shiga yayi mutuwar tsaye, ganin irin kyan da fulani tayi kamar ba mutum ba. Tasbihi yafarayi aranshi yana kara yabon irin kyan Fulani. Zaune take tunda taji shigowarshi ta dukar da kanta, hannunshi taji ya zagaye mata kafadu dasu, saurin rufe ido tayi, mikar da ita yayi suna fuskantar juna, murmushi yayi ya matso da fuskarshi dede ta ta harsunajin numfashin juna, ahankali yace Fulanita babu gaisuwa? Saurin kwantar da kanta tayi bisa kirjinshi tana murmushi, kara rungumeta yayi sosai kamar ze maidata ciki, kamshin turaren da Gimbiya Suhailat tabama Safeeya tasa mata duk yafara rikitashi. Sassanyar muryarta ta doki kunnanshi dafadin Ina kwana. Seda ya hadiyi miyau sannan ya amsa tare da lalubo lips dinta yahade danashi. Sun dade ahaka har yana neman wuce gona da iri yaji karar kofa. Dagata yayi yace kinga kinmantar dani mutane suna jiranmu, gaskiya senayi da gaske kada kirika sani jin kunya afada. Kamata yayi suka fito. Akofar falon ya tsaya yakara gyara mata mayafinta, yace gskiya dande kada suce namasu rowa dabazaki fita kowa yakallemun ke ba. Ahaka suka shiga falon tana jikinshi, kallo ne yadawo kansu, kowa seda ya yaba da zaben Sarki, anan suka rika yimashi tsiya, itade sede murmushi, ko fuskarta kasa dagawa tayi, ahaka suka gama gaisawa, kyaututtuka da dama suka bata, daga masu kudi se zinari wasu hada kyautar mota. Tasamu zinarai dayawa da kudi, wasu kayan ma an nadesu bansan ko menene ba. Sallama sukayi mata, Sarki yace bari inmaidata daki kada tayi tuntube. Gabada sukasa dariya. Qaseem da Waziri tare da Sarki dasauran fadawa suka taka masu hargurin motocinsu, kowa yaji dadin haduwar dasukayi haka suka tafi suna cike da farin ciki, dan sundade basuyi irin wannan haduwar ba. Bayan sungaisa dasu Waziri yawuce part dinshi dominsu karya. Da Jakadiya yahadu tagama gyara mashi daki ankawo abinci tashirya masu, yace sannu da kokari Jakadiya, tace sannu da dawowa, Yace yauwa kije falon baki akwai kayayyakin Fulani kyautace da abokanai na sukayi mata, akwasosu ki kawomun su dakina, hannu yasa a aljihu yaciro kudi masu yawa zasu kai 100k, yabata yace yauwa gashi kibama Safeeya tukuicinta ne ayi mani godiya da irin gyaran datayi ma Fulani dazu. Amsawa tayi ta tashi tawuce. Wani irin kululun bakin ciki ne, yarufe Jakadiya, ganin irin kudin da Sarki yabama Safeeya, aranta tace wato mutanan nan so sukeyi sucireni daga jikin Sarki, ayanzunne yakamata insamu dukiya daga gareshi ta dalilin Amaryarshi nasan akanta ze iya yima mutum kyautar mamaki, amma dan bukulu suka turo wata tazo tayi aikin da nice nakeyinshi aduk sanda Sarki yayi aure. Tabbas sena tashi tsaye akan Safeeya naga alama nan gaba Sarki ita zemaida yar gaban goshi. Ninasan mezanyi, anfada maki sona da yakeyi haka nabarshi. Tsaki tayi tawuce falon domin kwaso kayan, mamaki da tsoro ne, suka cikata lokacin datayi arba da irin kayan da tagani afalo. Gaba daya tarikice ganin irin wannan dukiya. Aranta tace badan Sarki yaga kayan nan ba, wlh dasenayi nawa. Wata babbar jaka tajawo tasaka kayan duka aciki tadauka tanufi dakin sarki dasu. Bata samesu afalo ba, da alama abincin ma adakinta suke ci. Tsaki taja tace shikenan kuma za,a maida mana Sarki bita zai zai, yo aduk matanshi akwai wadda yataba shiga dakinta ma? Lallai Gimbiya zankai maki labarin daze tarwatsa zuciyarki, wanda zesa ki karya akidarki ta rashin zuwa gurin boka, ai wlh tunda nabace dole insamu abokan tafiya. Murmushi tayi lokacin data tuna yanda Sarkin fada yafara samun shiga gurin Medaki. Kwafa tayi tajuya tafita. Wasu zafafan kwalla ne, suke fitowa daga idon Gimbiya Zakiyya, duk irin jiji da kanta, yau gashi agaban Jakadiya tana kuka, damma Jakadiya takori sauran Bayin. Lallashinta Jakadiya tacigaba dayi tana kara kwantar mata da hankali. Gimbiya hakuri zakiyi, amma dole sekintashi tsaye, wlh bakiga irin makudan kudin da aka bama Fulani ba, dan sunan danaji Sarki yakirata dashi kenan. Babbar damuwata yanda taki barinshi yafito fada, abinci ma adakinta sukaci. Infada maki...... Marin da taji ya sauka akuncinta ne, yasata saurin hadiye sauran gulmar data kwaso. Cike da tsoro takara dukar da kai tana neman gafara. Ke wace irin dabba ce? Wlh bansan ke dakikiya bace se yau, anfada maki gidan sarauta gidan bayine? Inbanda rashin sanin darajar sarauta taya zakizo kina fadamun irin wadan nan sakarkarun maganganun irin na jahilai irinku. Ina cikin damuwa zakizo kina fadamun abinda bantambayeki ba. Bance kifadamun abinda sukayi ba, kawai na tambayeki ina Me martaba shine zaki wage sakaran bakinki wanda yasaba dashan bakar kuka da daddawa kizo kina fadamun maganarsu. Daga yau kika kuskura kika kara fadamun abinda banice na tambayeki ba, wlh, kinji narantse maki sekinbar masarautar nan. Kara dukawa Jakadiya tayi, tana bata hakuri, tashi tayi ta tureta tashige daki, tana fadin karna kara ganin kafarki anan sena nemeki. Wasu hawayene suka zuboma Jakadiya, diyar cikinta saboda kudi da mulki yau itace take zaginta da cin mutunci har haka. Tashi tayi tana fadin yo idan har nabarki kikaci ribar zaman gidan sarauta ai ba macece ta haifeni ba. Qaseem ya kalli Gimbiya Suhailat yace ni kaina yau ina cikin farin ciki bansan abinda yasa ba, Yayana yana cikin farin ciki dole in kasance acikin farin ciki, inama ace Rayhana itace matar Yaya ta farko, nasan har abada baze kara marmarin kara aure

Chapter 4 of 13