Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
ace ana daura aure zaku tafi. Areef yace wlh Abba koni dole ce zata sani yin nisa daku, kuma ina me tabbatar maku shekara 3 zamuyi, niba burina beautytayi zurfin karatu ba, kawai inaso tasamu karatu me kyau, dan koda tayi karatun ni bazan barta taje wata University ba, kawai tasamu karatu kodan sbd rayuwarta data yaranta. Gimbiya tace gaskiya kayi magana me kyau, kuma nima nagoy bayanka son dazamu nuna mata kenan mubarta tasamu ilimi me kyau, kuma tunda saudiya zakuje, nasan zata samu ilimi me kyau, kaga daga kai har ita kunje kusa da gida, kafin kudawo zaku zagaya dangi. Sarki yace shikenan, idan Yaya yadawo zamuyi maganar dashi. Areef yarungume Abbanshi yayi yana dariya. Gimbiya tace ammafa zaku rika zuwa bawai zama zakuyi harseta gama ba. Sarki yace dama ai baza,ayi haka ba. Haka suka cigaba da shirye shirye, Amare suna shan gyara, dan masu gyara na musamman daga meduguri aka dauko, Fulani daki guda aka ware mata ita da ne gyaranta, tunda tashiga bata fito ba, akoda yaushe suna cikin gyara, sallah kadai da cin abinci suke tadasu. Bakaramin kyau takarayi ba, tadawo tamakar wata yarinya, komai nata yadawo kamar da. Beauty kuwa masu gyaran har mamakin kyanta sukeyi, gashi dama tunda aka fara gyaransu su Areef suka dena ganinsu, duk ya gama shuga damuwa. Ayaune, masarautar BUBAYERO tacika da mutane, anata gyara da shirin tarbar Sarki Hasheem. Kowa kagani cikin masarautar cikin farin ciki yake. Fulani tasha kwalliya kamar meshirin zuwa zaben sarauniyar kyau, tayi kyau harta gaji, haka suka kaita dakinta dayasha gyara har yafi ranar da aka kaita kyau. Motoci harma da mashina ne, suka je dauko Sarki. Ana bude kofar jirgi mutane suka fara fitowa, sarki Qaseem yazuba id kawai yaga ta yanda yayanshi zefito. Waziri yafara hangowa, daga bayanshi ya hango Yayanshi cikin shiga ta alfarma yayi matukar kyau, kamar bashi bane yayi ciwo abaya ba. Da kafafuwanshi 2 yarika saukowa daga jirgi, ai Sarki Qaseem kasa hakura yayi ya karaso, cike da murna ya isa gurinshi uka rungume juna. Kowa na gurin seda suka burgeshi. Haka suka nufi gida cike da farin ciki. Suna zuwa Sarki Qasee yajashi zuwa part dinshi, yace Yaya kashiga kashirya kada kafito seda dare, Fulani tana daki tana jiranka, nasan kagaji dayawa. Murmshi yayi yace shikenan nagode, sena fito. Har falo yakaishi sannan yafito fuskarshi dauke da annashuwa. Tura kofar dakin Fulani yayi, lumshe ido yayi dan wani da daddan kamshine ya bugar mashi hanci. Da sallama yashiga, ai cak ya tsaya ganin Fulaninshi, da gudu tarugo ta rungumeshi, hannuwanshi 2 yasa ya rungumeta, wani irin farin ciki sukeji dukansu. Sun dade ahaka kafi tajashi zuwa cikin dakin, riketa yayi yana kallonta, yace anya ba masanye akamun da Fulanita dana sani ba? Murmushi tayi tace kila, jawota yayi, yace gaskiya nagodema Allah dayasa bantafi dake ba, gashinan an maidomun da mata kamar yar shekara 18. Murmushi tayi tacire jikinta daga nashi tana fadin sannu da hanya, muje kayi wanka kaci abinci. Murmushi yayi yace nikam bazan iya cin abinci ba, tunda naganki, dariya tayi tace a,a muje de. Haka tajashi zuwa bandaki. Bayan yafito ya shirya takawo mashi abinci, da kanta tarika bashi yana jingine jikinta, kamar karamin yaro, yahanata sakat. Da haka tagama bashi abinci, yaje yayi brush yadawo yana fadin taho kimun tausa, bacci zanyi. Murmushi tayi tanufo gurinshi, yace amma kicire wannan kayan zasu damenim tace amma naga bacci zakayi, ina ruwan kayana da kai, kanne mata ido yayi yace e sonake musami AMINULLAH. Dariya tayi yajawota shima yana dariya. Koda Sarki Qaseem sukaje fada da dare, Sarki Hasheem befito ba, ganin haka Waziri yace abari se gobe, azauna, akwai gajiya atare dashi, Sarki yace a,a amarci kawai yakesha. Waziri yace kaima ai sekaje kasha naka. Murmushi Sarki yayi yace kaima nan da wani lokaci kaza fara shan naka. Dariya Waziri yayi yace seda safe, Sarki yace to Allah yakaimu. Areef ze zaune afalon Jakadiya kamar zeyi kuka ya kalleta yace haba Aunty dan Allah sokukeyi inshiga wani hali, kinfi kowa sanin damuwar danake ciki, shikenan ace kullum so daya zanga beauty gaskiya bazan iya ba. Ina gyaran nan danni akeyishi? To nide abarmun ita haka banaso. Dariya Jakadiya tayi tace yi hakuri bara inturo maka ita karkamun kuka, fita tayi sega beauty tafito. Tsayawa yayi yana kallonta, tana zuwa tazauna kusa dashi tana murmushi, yakamo hannunta yace haba beauty nan shikenan sekirika guduna. Kema bakison ganina ko? Girgiza mashi kai tayi, yace yauwa kokefa beauty na, hannunta yasaki, yace jeki dauko mani abinci yunwa nakeji, tashi tayi tadauko mashi, akasa tadameshi, nan tazauna tazuba mashi. Atare suka fara cin abinci, yana bata tana bashi, har suka gama sannan suka zauna yana mata fira. Washe gari se bayan azahar sannan aka taru afada, atare Sarki Hasheem da Fulani suka fito, daka gansu kasan suna cikin farin ciki. Bayan angama gaisawa, aka bude taro da addu'a. Sarki Qaseem yace Alhamdulillahi, munama Allah godiya daya kawomu wannan rana Yaya yasamu lafiya, komai na masarautar nan yazama dede, ina rokon Allah daya kara tsaremu damu da yaranmu baki daya. Dan haka inaganin zanmika ma Yaya kujerarshi, dama amatsayin rikon kwarya na amsa. Sarki Hasheem yayi murmushi yace, a,a ai kuma nida mulki har abada, wanda nayi abaya ya isa, kaine zaka cigaba da mulkarmu, kafin Yarima yakawo karfi se abashi, amma wannan maganar ma kabarta. Waziri yace wannan magana haka take, munriga da munyanke zaka cigaba da zama Sarkin Gombe, har Allah yakaimu lokacin dazaka sauka. Allah yatayaka riko. Waziri yace magana ta 2 akan maganar bikinsu Yarima ne, munsami labarin mahaifin Haisam zezo gobe da jama'arshi neman auren Ayman, dan haka nan da sati 2 za'ayi bikinsu in Allah yakaimu. Kallon Baffan beauty yayi yace akwai wata magana da Yarima yazo mana da ita, jiya Sarki Qaseem yake fadamun. Anan yafada masu alfarmar da Yarima yake nema. Shiru Baffan beauty yayi bece komai ba. Can yadago kai yace ai hakanma yana da kyau, Se ayi magana acan kasar asama mashi aikinyi kafin itama tagama karatun nata. Allah yasa aje asa'a akuma samu abinda akeso. Sarki Qaseem yace kuma akwai dayar maganar, aure danakeso inyi, dama akan Waziri ne da Jakadiya Safeeya, ina ganin insha Allah nan da sati 2 tare danasu Yarima za,a daura. Dago kai Waziri yayi yasaki baki yana kallon Sarki Qaseem. Baffan beauty yayi murmushi yace lallai kamar kashiga zuciyata. Dan Allah Waziri kada kace komai, kawai kayi fatan alkhairi, kasan baza zaba maka abinda zakayi dana sani ba. Sunkuyar da kai Waziri yayi yana murmushi. Sarki Qaseem yace ai ya amince, Allah yakaimu musha biki. Shirye shirye ya kankama agidan su Yarima, iyayen Haisam sunzo anyi magana, kuma har can misra an fada masu, kuma sunce zasuzo. Baba Fulani ma yakira yan uwanshi yafada masu, wasu daga cikinsu sunce zasuzo. Duk wani shirin tafiyarsu Areef angamashi, anyi masu visa, da takardar shedar zama akasar, kuma an sama ma Areef aiki acan har gudan dazasu zauna ansamu. Dayake abun namasu sarauta ne. Babu wani bidi'a dazasuyi abikin, hakan yasa aka kira me wa'azi yazo yayi masu. Ayau ne dubban jama,a suka halarci daurin auren mutane, 3 nagidan sarautar BUBAYERO. Daurin aure ne daya tara mutane dayawa, daga garuruwa daban daban, harma daga kashashe. Bayan daurin aure akayi babbar walima, anci ansha, kowa seda ya yaba da irin auren wannan Masarauta. Gashide auren yaransu, abin sonsu akeyi amma kuma babu wata bidi'a da akayi. Mutane dayawa abin ya burgesu. Adaren ne kafin azo daukar Ayman, Sarki yatarasu duka domin ayi masu nasiha. Nasiha meratsa zuciya sarki yayi masu, bayan yagama Baffan beauty ma yayi masu. Yace Amatullahi, kiyi hakuri kinga gobe da safe zaku tafi, babu ruwanki da kowa, bakisan kowa ba se mijinki. Kada kiyarda wasu suzo maki dawani abu, yanda baki magana, karkiyarda kibiyema kowa, kuma kimaida hankali akan karatunki, inhar kinaso kidawo kusa damu, amma idan bakiyi kokari ba, acan zakuyi tazama. Ko kinaso kuzauna acan? Kai ta girgiza yace yauwa, Allah yayi maku albarka. Kema Ayman, kindega abinda yafaru azuwanki gidan nan, damma kinci sa,a gidanki daban ne, amma duk da haka bana son kisaki jiki da mutane, dangin mijinki kirikesu da hannu 2, kowa kizauna dashi da zuciya daya, Allah zetemakeki akan makiyanki. Allah yabaku zaman lfy. Anan Waziri shima yayi masu tashi nasihar, se yan uwan Ayman da dangin Fulani dasukazo, kowa seda yayi masu nasiha. Se kuka sukeyi, bayan angama masu Sarki Qaseem yace kuje, yanzu za,azo adaukeki. Bayan suntafi, Sarki yace Waziri kaima yanzu zamu kawo maka taka amaryar. Dariya suka saka, gaba daya. Da misalin karfe 9 aka dauki Ayman, wanda Areef shima yadauki beautynshi amota suka tafi rakasu. Bayan kowa yatafi yarage daga amarya da ango se su Areef. Haisam yace abokina yakamata muje inrakaku. Duka Areef yakai mashi yace wlh kai dan iska ne, wlh se ince ba inda zani, Haisam yace da kyau, ai akwai wani dakin, indarabon asamu dan gidanmu kuma shikenan. Areef yace a,a ni baruwana kaine dan iska nikam nafison dan saudiya. Haisam ya kalleshi yace wlh abokina banason tafiyar nan taku, shiyasama bazan je rakiya ba, amma zamu zo dan acan zamuyi honey moon dinmu, Areef yace bakomai nasan sanda zamu tafi ma baku tashi daga baccin gajiya ba. Dariya Haisam yayi yace ammade ai munyi sallah ko, Areef yace tobara mutafi nasan beauty na tagaji gara muje ta huta, mike wa sukayi, Haisam ya rungume shi idanunshi har yakawo ruwa. Shima Areef seda yazubar da kwalla, sun dade ahaka, kafin suka saki juna. Har bakin mota suka rakasu, Ayman da Beauty se kuka sukeyi,da kyar Areef yacire beauty daga jikin Ayman. Ayman tace Yaya yanzu shikenan gobe zaku tafi? Kallonta yayi zeyi magana kuka yataho mashi, kawai jan beauty yayi suka shiga mota. Amota yayi ta lallashin beauty, da kyar tayi shiru, haka suka nufi gida shima duk bayajin dadin rabuwarsu da Haisam dan bakaramin sabo sukayi ba. Beda wani aboki se shi, dashi kadai yasaba. Har dakinta na bangaren Jakadiya Safeeya ya kaita sannan yatafi. Kwallan data zubo mata ta goge, takalli Jakadiya Karima tace yanzu kalli yanda duniya tajuya mani baya, kamar ni da mulki na da matsayina amma kalli yanda kowa yamanta ni acikin gidan nan, biki akayi ayau amma banida damar fita inje gurin. Jakadiya Karima tace, Zakiyya kenan, idan zakiyi hakuri ki aje wata sarauta ki rungumi kaddara kiyi. Har garama ke, zaki iya kirga kwanakin ki,nifa? Sede afitar da gawata. Saboda haka kinganni nan namaida gurin nan kamar gidana, idan harzaki rika yimani maganar wata sarautarku, ina me tabbatar maki zanbar maki dakin nan, kuma bazaki kara ganina ba, dan kinsan babu wanda zezo yazauna tare dake. Shiru Zakiyya tayi tana jinyanda Jakadiya take fada mata maganganu. Murmushin takaici tayi tace duniya kenan. Washe gari tunda safe aka fito rakiyarsu Areef, idanunshi sunyi ja sosai, dan tunjiya yakema iyayenshi kuka, Abbanshi har cewa yayi kode afasa tafiyar ne, yace a,a Abba, nasan damun tafi komai ze wuce. Haka suka shiga mota aka nufi air pot dasu, ko acan da kyar aka ciresu daga jikin iyayensu, suma seda sukayi hawaye, suna kallo har jirginsu yadaga, sannan suka juya zuwa gida. Acikin jirgi kam lallashin beauty Areef yayi tayi, mutane se kallonsu sukeyi, dan sunga suna kama sosai, gashi dama beauty da kyar tashiga jirgin, shiyasa tashige jikin Areef, ko ido takasa budewa. Shiyasa kukan nata yazama 2. Suna sauka dama mota tana jiransu,daukarsu tayi suka nufi gidansu, gida ne, mekyau, yaji komai, kayansu aka shigo masu dasu. Wanka Areef yace suje suyi, rufe fuska beauty tayi tana murmushi. Cak yadauketa bema tsaya jiran yardarta ba. Haka sukayi wanka suka fito, dakanshi yashiryata aka kawo masu abinci. Da dare ma kawo masu abinci akayi, bayan sungama yadauketa suka nufi toilet, wanka sukayi tare da alwala, sallah sukayi sannan yajawota suka nufi gado. Washe gari da safe dakanshi yashiga kitchen yahada masu break, bayan sungama yajata zuwa daki suka koma bacci, seda azahar suka tashi, wanka sukayi sukaci abinci suka fito falo, takarda da biro yadauko yajawota suka zauna falo, yace beauty yau labari zamuyi fa. Haka yayita rubuta mata yana bata tana rubuta mashi abinda tasani, idan ta manta ya tuna mata. Haka suka cigaba da rayuwarsu acikin gidan gwanin ban sha,awa, akullum suna yin waya da yan gida, satinsu guda sannan suka fara fita, aranar yakaita makaranta shi kuma yawuce gurin aiki, seda yayita lallashinta kafin ta hakura, yace dasun tashi zezo yadauketa. Rayuwar Areef da Amatullah gwanin ban sha,awa, suna matukar son junansu, akullum tare suke fita ya kaita makaranta, shikuma ya wuce aiki, se da yamma suke tashi, dayake makarantar hade take da islamiya, shiyasa sesun kai yamma, kuma Beauty tana gane karatun sosai, babu ruwanta da kowa, karatunta tasa gaba. Haka rayuwa tacigaba da tafiya, suna da wata 3 dayin aure, ciki yafito ajikin beauty, bayan sunje asibiti akayi test aka gano ciki dan wata 2, bakaramin murna Areef yayi ba, haka yakira gida ya fada masu, suma sunyi murna sosai. Tunda suka koma gida yake riritata, damma cikin beda laulayi, Haka yakira Haisam yayi mashi albishir, shima alokacin yake fada mashi Ayman ma tana dauke da ciki itama wata 2, Areef yace amma naji dadi, zamu fara cika ma su Abba gida da jikoki. Haisam yace idan muna da rai muma semu hada zumunci. Areef yace Allah ya kaimu. Amma wai yaushe zaku zo, kasanfa muna son zuwa ziyara gurin yan uwa, gurin dangin su beauty, danasu Momy. Haisam insha Allah zamu shirya muzo. Yace to Allah yakaimu Baffan beauty ya kalli Fulani, datake kwance ajikinshi, dawowarsu daga asibiti kenan, fuskarshi dauke da murmushi, yace babu abinda zance maki Fulanita, sede godiya, tabbas ke haske ce acikin rayuwata. Ashe inada rabon ganin yarana, aduniya. Ina rokon Allah ya saukeki lfy. Murmushi tayi tace amin. Yace ina ganin Gimbiya Suhailat zata rigaki haihuwa ko? Kai tadaga mashi, tace wlh ni kunya nakeji, yace kunyar me kuma?. Tace haba dan Allah, yanzu kana ganin Amatu ciki gareta, Ayman ma haka, ga Aunty, yanzu kuma ace nima haka, kuma suk kusan tare zamu haihu. Dariya yayi yace kin manta dayar ai, tace wa kuma? Yace matar Waziri mana. Tashi tayi fuskarta dauke da mamaki, tace da gske Aunty Safeeya tana da ciki? Yace da gske mana, dazu yake fadamun, nace kinga ikon Allah ko? Tace gaskiya kam, wama yayi zaton Aunty zata haihu, yanda ta dade bata taba haihuwa ba. Yace aishi Allah babu ruwanshi, yana yin abunshi aduk sanda yaso,babu ruwanshi da tsufanka ko yarintarka. Fatanmu Allah yasa mugama da duniya lfy. Tace amin. Amma de ba gida su Yarima zasu dawo ba idan zata haihu ko? Dariya yayi yace wai naga duk kinbi kin damu, ina ruwanki dasu?. Kinsande muna da inda zamu ajesu ko? Kuma zamu sami masu kula dasu, dan haka ki kwantar da hankalinki. Shiru tayi bata ce komai ba. Jawota yayi yace dazu Yarima yake fadamun zasu je ziyarar yan uwa. Murmushi tayi tace kagani ko, Nibanje ba, ga jikarsu nan har zataje, yace karki damu kema zakije, Allah yasaukeki lafiya. Tace Amin. Zaman Haisam da Ayman, zama ne na so da kauna, yana kula da ita sosai, itama haka, kuma tana daraja yan uwanshi. Acikin satin ne, yagama shirya masu visa suka daga zuwa saudiya domin zumunci. Bakaramin dadi su Areef sukaji ba, da ziyarar dasuka kaimasu, kuma agidansu suka sauka, ko abinci basa tsaywa girkawa, sede sufita suci awaje, dagacan suwuce gurin shakatawa. Dayake Beauty suna hutu. Sun zagaya gurare dayawa, sannan suka shirya dukansu suka nufi misra, yan uwansu bakaramin dadi sukaji ba. Kwanansu 3 sannan suka wuce garinsu Fulani, suma sun tarbesu sosai, sun sha gata, kwanan su 3 acan ma, sannan suka dawo gida. Kwana 2 su Haisam suka kara sukace zasu wuce, har kuka sukayi dasuka rakasu, da kyar Areef yacire beauty daga jikin Ayman, haka jirginsu yadaga suka dawo gida yana lallashi. Bayan wasu watanni Gimbiya Suhailat ta haifi diya mace, ansha hidima sosai, sede su Areef basu jeba, dan beauty tana Exams. Yarinya taci sunan mahaifiyarsu Sarki Qaseem Fatima, ana kiranta da NOOR. Bayan wata 2 da haihuwarta Fulani ma tahaihu yan biyu, mace da namiji,gaba daya gidan seda kowa yasan anyi haihuwar yan 2, Sarki Qaseem bakaramin dadi yaji ba, ganin Yayanshi yana samun haihuwa yanzu. Alokacin beauty tagama Exams dinta, shima yadauki hutun shekara. Hakan yasa suka nufo gida, bakaramin farin ciki mutanen gidan sukayi ba, apart dinsu da aka gina masu anan suka sauka, wata dattijuwa aka kawo ma beauty wadda zata rika temaka mata, ana cemata Ladingo. Ranar suna akasama namijin sunan Mahaifinsu Sarki, macen Kuma sunan Mahaifiyar Fulani. Ana kiransu da AMEER DA AMEERA. Anyi shagali sosai, su beauty da Ayman da Jakadiya Safeeya sunata fama da tsohon ciki. Bayan suna da sati daya Ayman da Jakadiya Safeeya suka haihu, Ayman ta haifi Namiji itama Jakadiya Namiji. Beauty kuwa kuka tasaka dataji ance Ayman ta haihu. Areef yatambayeta lafiya awayarta ta rubuta mashi ita fa tsoro takeji, dariya yayi uajawota yace ki kwantar da hankalinki, babu wata wahala kinji ko? Kai tadaga mashi tana murmushi. Adaren itama ta tashi da nakuda, dama beauty ga tsoro, gaba daya taki sakin jikinta se kuka takeyi, tun Ladingo tana kokari harta gaji, Areef kuwa kamar shine yake nakudar, kallonshi Ladingo tayi tace agaskiya Yarima ina ganin sede fa akaita asibiti, idan bahaka ba, za, iya rasa abinda ke cikinta. Cikin rudewa yace to kihada kayan bara infada ma su Momy. Cikin lokaci kankani aka nufi asibiti da ita, hankalin kowa yatashi ganin yanda beauty tafita hayyacinta. Suna zuwa aka nufi labour room da ita. Kowa yakasa zama, Areef kuwa kuka yasaka, Haisam ne yajashi suka fita waje yana lallashinshi. Areef yace kasan Allah daga wannan haihuwar beauty tagama haihuwa. Dariya maganar tabama Haisam sede ya dake ganin halin da akeciki. Haisam yace addu,a zaka rika yimata, yace haba Haisam kalli fa yanda take shan wahala, baiwar Allah wlh da ana karbar haihuwa dana karbar mata. Amma anyi na farko anyi na karshe, banason yaran dayan dazata haifa ya isa. Haisam yace duk wannan ma bata taso ba, kaide muyi Addu,a Allah yasauketa lfy. Areef yace amin. Amma......... sunanshi yaji ankira cikin wata irin murya da Yaya Areef,, cak ya tsaya da magana dazeyi, yajuya yana kallon inda yaji muryar tafito. Ai dasauri yanufi cikin asibitin Haisam yabi bayanshi. Suna zuwa kusa da labour room din suka jiyo kukan jariri, da gudu Areef yanufi dakin, cikin sauri Haisam ya rikeshi, yana fadin maza basu shiga, kajira afito da ita. Areef yana hawaye yace kasakeni, wlh duk da bansan muryar beauty ba amma nasan ita ce ta kirani, kasakeni inje inga beauty na. Da kyar su Waziri suka hanashi shiga, Momynshi ta matso tace haba Yarima kayi hakuri mana, kallifa yanda ake kallonmu. Zonan kazauna kaji, yanzu za,a fito da ita. Wani likita ne yafito fuskarshi dauke da murmushi yanufo gurin. Sarki Qaseem ya tarbeshi yace yaya jikin Amatullah?. Likita yace Alhamdulillah tasauka lafiya, tasamu baby girl, kuma duk suna cikin koshin lafiya. Sarki yace Alhamdulillah. Likita yace yanzu za,a kaisu dakin hutu, idan kungama kusameni office, akwai wani albishir din. Godiya sukayi mashi, yawuce. Areef yariga kowa shiga dakin da suke, kotakan jaririyar be biba, gurin beautynshi yanufa. Hannunta yakama yarike sosai yana sannu beautu na, nine ko? Murmushi tayi mashi, yace sannu bazan karaba kinji? Kamar daga sama yaji tace Yayana ga babynmu. Surin dago kai yayi yana kallonta. Itama shi take kallo, cikin farin ciki yanunta yama kasa magana, kai tadaga mashi. Ai yama manta da mutanen dakin kawai ya rungumeta da karfi, harseda tayi dan kara. Momy tace lfiyarka Yarima? Saurin sakinta yayi yajuyo yana sosa kai yace wlh Momy beauty tayi magana. Suma mamaki ne yakamsu, suka nufi gurinta. Murmushi tayi tace Momy. Cike da farin ciki Momy ta matsa kusa da ita tace da gaske ne, ashe? Ikon Allah, lallai Fulani zatayi farin ciki. Allah mungode maka. Sarki yace Sannu Amatullah, cike da kunya tace yauwa Abbah, yace bari muje gurin likita mudawo. Zaune suke a office din likita, bayan yagama rubutunshi yacire glass dinshi yace albishir din dana ce maku kilama idanunku sungane maku? Sarki yace tabbas yau munga abin farin ciki, sede muyi ma Allah godiya. Likita yace haka ne, dama nafada maku, akowane lokaci maganarta zata iya budewa, sbd akwai irinsu, kasan akwai wani zakaga kurma ne, bayaji baya magana amma sakamakon wani tashin hankali bakinsu yana budewa. To itama Allah yasota gashi ta dalilin haihuwa bakinta yabude. Kuma jikinta babu wata matsala, zuwa anjima idan tahuta zaku iya tafiya, ga magungunan dazatayi amfani dasu anan. Allah yabada lafiya. Godiya sukayi mashi suka fita. Segurin karfe 11 na dare suka koma gida, gaba daya murna tacika gidan, Ayman jitake kamar itama tadawo gida, dan Haisam yace tazauna tunda hidima tayi masu yawa, agidan. Kowa cewa yake yarinyar tana kamada Areef, shiko bakinshi yaki rufuwa, yamaki fita daga dakin, seda Momy tayi mashi da gaske sannan yafita. Haka akayita shirin suna, Momy tace ma, Haisam yamaido Ayman gidan ayi suna gaba daya,daga baya sesu koma. Aranar suna bakaramin taro akayi ba, diyar Beauty aka samata Khairat, dan Areef da kanshi yace babu sunan wanda zesa, shi khairat yajeso. Yaron Ayman shima Haisam be tsaya saka sunan kowa ba,yasa mashi Fahat. Waziri kuwa sunan Baffan beauty yasaka ma yaronshi wato Hasheem, ana kiranshi da Karami. Bakaramin dadi Baffan beauty yaji ba da irin karar da waziri yamashi ba. Sarki Qaseem shine yasayi komai na jariri harda ragunan suna. Gaba daya masu laifin gidan aka fiddo haka aka raba masu aiki, kowa danashi, Zakiyya abangaren masu abinci aka kaita, tanayi tana kuka, ahaka suka gama, aka sallamesu kowa aka bata nata. Bayan kwana biyu mahaifiyar Zakiyyah ta kawo mata ziyara, sunsha kuka sosai, ayanayin data ganta, kallonta tayi tace Zakiyyah kinga irin abinda nake fada maki ko? Yanzu ina sarautarki da mulkinki gashi nan kinkare a gidan kurkutu, acikin talakawa marasa galihu. Cikin kuka tace wlh Umma nayi dana sanin shiga wannan bakar rayuwar dana shiga, kuma insha Allahu na dauki darasi. Umman tace bakomai ai kin kusa fita kema kidawo gida. Allah yayi maki sauyi da miji nagari. Ta dade kafin ta tafi, takawo mata abubuwa dayawa. Zakiyyah se kuka takeyi. Seda suka sami wata 2 kafin sukayi shirin tafiya, visa Sarki yasa akayima Ladingo yace sutafi da ita seta rika temaka mata. Haka beauty tacigaba dazuwa makaranta tare suke tafiya da Ladingo, idan zasu shiga aji seta barmata Khairat. Yanzu karatun yana mata sauki sosai, dan har larabci tanaji tana maidawa. After 2 years. Beauty ce tafito hannunta rike da takardu tana ta farin ciki tanufo gurin Areef da khairat dasuke tsaye jikin mota suna jiranta. Khairat tayi wayo sosai, sede haryanzu ba,ayi mata kanwa ko kani ba. Tana zuwa tafada jikinshi tana murna. Kara rungumeta yayi yace congratulation my beauty na. Allah yanufa yau kingama karatunki. Khairat tace Dady nima kadaukeni, dariya suka saka yace yi hakuri yau ranar Mimie ce, janta yayi suka shiga mota suka nufi gida. Party sosai suka shirya aranar, dan beauty hada qur'ani tasauke, gashi aharkar boko yanzu sede takoyama wani. Bayan kwana 2 suka fara shirye shiryen komawa gida dama tuni yagama hada komai na aje aikinshi. Bayan suje sunyi tsaraba washe gari suka dira a nigeria. Kowa yayi farin ciki da dawowarsu. Haisam kamar ze zuba ruwa akasa dan farin ciki. Beauty ta kalli Ayman wadda cikinta har yafito kadan tana dariya tace Aunty yanaga haka? Hararta tayi tace kema zakiyi ne ai, haka suka nufi gida. Babbar tarba, kowa yana cikin farin ciki. Haka rayuwarsu tacigaba da tafiya acikin masarautar, Areef yakoma aikinshi, suna zuwa cikin wanciyar hakali shida Haisam. Iyalen Baban darazo sunajin dadin zaman gidan sarautar, babu abinda basa samu ta ko ina. Ayanzu cikin masarautar karatu akeyi sosai, dan Malam ya aiko da malaman dasuke koya masu karatu, gaba daya bayin dasuke gidan, harma da masu laifi, ana fidda masu ranar karatu. Sosai suke jin dadin abinda ake masu, gaba daya canji yasamu agarin Gombe, duk wanda ya aikata wani laifi, ana yanke mashi hukunci dede dashi. Bayn shekara 2 beauty takara haihuwar da namiji, ana kiranshi da Faisal, Ayman ma yaranta biyu, mace da namiji, macen sunanta Labiba. Ayau ne Zakiyya tafito daga kurkutu, rungume suke da juna ita da Jakadiya Karima, kuka kawai sukeyi. Zakiyyah tace Allah yada fuskokinmu, da ace ba,a gidan nan kike ba, dazanyi maki alkawarin kawo maki ziyara. Amma yanda zanbar gidan nan bana fatan inkara dawowa. Kiyafemun abinda namaki nima nayafe maki. Jakadiya tace nayafe maki. Allah yabaki miji nagari kema kiyi aurenki. Da kyar suka rabu sunata kuka. Sallama tayima sauran mutanen gurin tafito. Mahaifyarta ce, tazo daukarta, haka suka nufi fada kallo daya zakama Zakiyya kasan tafita hayyacinta, gaba daya tayi baki ta rame. Azaune suka iske iyalan masarautar, kowa fuskarshi cike da annuri. Kallonta sukeyi cike da tausayi. Zama tayi bayan sungama gaisawa, ta kalli Baffan beauty, suna hada ido ykara daure fuska ya dauke idonshi daga kanta. Wasu hawayene suka zubo mata, ahankali tace Nasan banida bakin dazan rokeka gafara, amma duk da haka bazan yi kasa aguiwa ba, dan girman Allah kaya femun abubuwan dana yimak. Hakika naga rayuwa, kuma hakan kadan ya isheni darasi. Banaso in mutu da hakkinka kayafemun. Kuka ne yaci karfinta. Shiru yayi kamar bazeyi magana ba, can yace bakomai nidama nadade da yafe maki. Allah ya shiryeki. Matsawa tayi kusa da Fulani, takamo hannunta, tana kuka tace Fulani dan .... saurin rufe mata baki tayi tana girgiza kai, hawaye suna fita daga idonta tace nayafe maki. Allah ya yafe mana baki daya. Haka tayita rokon mutanen falon tana kuka, har seda tasa wasu kuka. Tashi sukayi auka masu sallama, har bakin mota aka rakasu, amma banda Sarki Qaseem, Waziri da Baffan beauty. Seda suka tafi sannan suka dawo. Bayan kwana biyu da komawar Zakiyyah gida tadan murmure, mahaifinta yakira Ummanta da ita suna zuwa, ya kalleta yace, zakiyya ina tayaki murnar fitowa daga gidan yari. Basena kara tunatar dake rayuwa ba. Nasan azaman da kikayi kin kin koyi darussa da dama. To Alhamdulillahi dama arayuwa ana son idan mutum yayi kuskure yayi kokarin gyarawa. Shiyasa Allah da kanshi ya saukar da hukuncin daza,ayi ma masu laifi, domin yazama darasi agaresu. Mutane dayawa ta dalilin wannan hukuncin suke shiryuwa. Naji dadi sosai danaga kin koyi darasi. Abunda yasa nakiraki dama kinsan nace dakin fito zan aurar dake,somin zamanki agidan nan babu abinda ze amfana maki, se tarin bakin ciki. Dan haka nazaba maki miji, amma idan beyi maki ba, kinada ikon canza wani ba dole zanyi maki ba. Goge hawayen idonta tayi tace, babu wani zabi dazakamun inki binshi, nayarda da duk wanda kazabamun. Murmushi yayi yace naji dadi, kuma bakowa bane se Wazirina. Shikadai

Chapter 12 of 13