Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
magana me ban al,ajabi, kuma kaima kayi kokari sosai, wanda bakowane ze iya abinda kayi ba, lallai duniya babu gsky, tsoron Allah yayi karanci aduniyarmu da zukatan mutane, yanzu dan Allah ina wanda yakeda alhakin haukatar da wannan mata zesa dumbin zunuban daya dauka nata ita da yarta har na tsawon shekaru 18?. Innalillahi Wainnailaihirraji'un. Yanzu Baba abinda nakeso da kai, ka kwantar da hankalinka, insha Allahu babu abinda ze sameka, kuma zamuje musamesu a inda kabarsu, addu,a zata temakemu akan wadan nan aljanu, kuma zanyi magana dasu, dan suma basuda niyar cutar dasu, asalima suna temakonsu ne. Bara inkira sauran dalibaina su shirya muje musamesu, amma ai bazamu bar bayin Allah acikin daji ba, kuma a MAKABARTA. Kodan lafiyar ita yarinyar. Tashi yayi yakira yaranshi yafada masu su shirya zasuje wani guri, koda yadawo, yasamu Baba yana jiranshi, haka suka dauki mota yasa aka kira Jakadiya da matarshi suka shiga, dan sutemaka masu gurin daukosu. Baba addu,a kawai yakeyi Allah yasa su samesu, agurin. Nima nace amin Baba. Ur's NABILA RABI'U ZANGO (Nabeelert Lady) 08028525263 [23/08, 1:48 p.m.] Nabeelert Lady: ..🛤🛤🏕🏕🏕🛤🛤🛤 AMAKABARTA AKA HAIFENI 🛤🛤🏕🏕🏕🛤🛤🛤 (The story of hard kingdom) Nah Marubuciyar Zamani NABILA RABI'U ZANGO (Nabeelert Lady) @House of Novella Association (H,O,N,A) www.NabilaLady5@gmail.com Season 15⚜20 Hankali tashe Baba yafito daga motar yanufi inda rumfarsu take, amma abun mamaki babu ita babu dalilinta, idan ba wanda yasan da ita ba, babu wanda zece mutane sun taba zama agurin. Wasu irin zafafan hawayene suka fara zarya afuskarshi yan fadin Innalillahi wainna ilaihirraji,un. Zama yayi adede inda rumfar take yana kuka. Malam ne, yakaraso gurin yadafashi yace Baba ba kuka yakamata kayi ba. Insha Allahu nizan dawo dasu duk inda sukaje, dama munsaba da aljanu, masu taurin kaima ina gogawa dasu, har kafiran cikinsu muna fama dasu, bare kuma wadannan da alama musulmai ne. Baba yace wlh malam, da,a ace sun dauke su Yar Baba bansan inda suke ba, gara ace banfada maka ba, muyita zama dasu anan har mutuwa tazo tasamemu. Tsautsayi ne, da kuma tausayi yasani karya dokar dasuka saka mun. Shiru malam yayi, can ya kalli daya daga cikin yaranshi yace daukomun shinfida acikin mota kataho mun da gorar ruwa, bayan yakawo mashi ya amsa yafara alwala, shikuma ya shinfida mashi abin sallah. Kallonshi yayi yace kacemasu Jakadiya sukoma mota suzauna harsenace sufito. Sallah yafara yi, kowa yana kallonshi, seda yayi raka,a 4 sannan yazauna yafara karatu, da yayi seya tsaya yayi adduo,i sannan yacigaba. Seda yadauki tsawon minti talatin, sannan wata kura ta taso kafin wani lokaci sega rumfar su Yar Baba ta bayyana agurin datake. Hamdala malam da Baba sukayi, dasauri Yar Baba ta iso kusa dashi tana dariya. Daya daga cikin yaran malam, wani yace Tsarki ya tabbata ga mahaliccin dayake tsara halittun bayinshi. Anya wannan yarinya mutum ce? Aini tunda nake bantaba ganin yarinya me kyanta ba, damma wai tana cikin rashin galihu, wannan da,a birni take gidan masu kudi ai se anrika boyeta. Dariya nakusa dashi yayi yace kaima kenan dakake iya magana. Baba se shafa kan Yar Baba yakeyi yana murmushi, ita ko tashige jikinshi don da alama tsoron mutanen gurin take, dan atsawon rayuwarta bata taba ganin kowa aduniya ba, daga Mamanta se Baba. Mamanta kuwa kasa fitowa daga runfar tayi, se kuka takeyi. Malam yace Alhamdulillahi, Allah mungode maka, kallon gefenshi yayi yace bayin Allah, meyasa bakuso atemaki wadannan mutanen? Kowa yafara kallon inda malam yake magana, sede babu alamun kowa agurin, maganar mutum daya tafara tashi me cike da alamun ladabi. Allah yagafarta malam, mundauki tsawon shekaru 18 muna tare da wadannan bayin Allah, mune muka temaki wannan mata, alokacin da takusa halaka, wanda babu wani dan adam daze iya temakonta, semu, kuma ga dukkanin alamu munga kamar hadari ne, ya jefota gurin datake, sede koda muka bincika bamuga alamun mota tayi hadari ba, asalima mugunta akaso ayima wannan mata. Shiyasa muka temaketa, sede haryanzu Allah bebamu ikon gano dalilin daya kawota nan ba, kuma babu wani asiri ajikinta, wannan lalurar datake tare da ita da alama kode ajikinta take, ko kuma buguwar datayi ne yakawo mata ita. Malam yace naji, amma me kuka sani game da ita? Tsawon shekaru 18 dasuka wuce wata rana da dare muna zaune afadarmu. Se kawai mukaji fadowar wani abu akusa damu, sede abun mamaki, muna dubawa semukaga mace ce da tsohon ciki, kuma cikin ikon Allah babu abinda yasamu cikin, anan muka kara dubawa semukaga tabbas bil adamace, anan nasa yarana dasu dubamun ko hadari ne akayi, dayake akasan wani rami muke, hakan yasa nayi zaton ko hadari ne, dan wani lokacin idan akayi hadari mutane suna fadowa nan. Bayan yadawo yace mun babu wata mota datayi hadari, kafin mu ankara semukaji wannan mata tana nishi da karfi, nan take nagane haihuwa zatayi, anan nasa akayima me dakina magana. Allah gafarta malam, ita dasauran wasu jinsinmu suka temaka mata harta haihu, sede koda ta haihu bata cikin hayyacinta, haka suka gyarata ita da diyarta, aka samo kaya aka samata, anan nace su kwantar da ita kusa da mahaifiyrta. Dayake safiya takusa, haka muka tashi mukabarta agurin ita da yarinyarta, anufina idan gari yakara haske kila wasu suganta sutemaketa. Bayan dare yakarayi muka sake dawowa fadarmu, abun mamaki kuma bamuga wannan mata ba, senayi tunanin wasu sun daukesu, muna nan zaune sega daya daga cikin yarana yazo yacemun ahanyarshi tazuwa nan yaga anyi wata runfa agefen wata MAKABARTA sede yar karama ce akayi, daya kara matsawa seyaga wata jaririyace kwance acikin rumfar, saman hakukuwa anshinfida mata zani tana bacci, daga waje kuma wata mata ce kwance agaban rumfar, dan tayi masu kadan bazasu iya shiga su 2 ba, asalima rumfar yara ce, abinda yabashi tsoro yaga wata halitta daga cikin jinsinmu sede basa cikin zuri,armu wato musulmai, yaganta tana kokarin daukar yarinyar. Shine yaje gurin dasauri, to dayake sunsan kowaye kuma suna tsorona, yana ganinshi yayi saurin bacewa. Shine yazo yana fadimun, koda nasa adauko munsu senaga wannan matar ce tajiya, nan take tausayinta yakamani, anan nayi alkawarin kareta ita da yarta kuma babban dalilin dayasa nabarsu aMAKABARTA, sbd bazeyiwu nakaisu cikin jinsina ba, haka kuma nagane bil adama basuda tausayi harsuka iya barin wannan mata ita da yarta acikin daji babu metemakonsu, shiyasa nasa yarana suka yimata rumfa babba wadda zata isheta ita da yarta, kuma nasaka yarana suzama masu gadinsu. Kasancewar bata da hankali yasa abubuwa da dama mune muke temakonta dasu, tundaga abinci dakuma ruwa, na hana yarana subarta tafita daga MAKABARATAR, sbd ina gudun kaidin bil adama, ko gawa aka kawo babu wanda yake iya ganinsu, nina zaba masu suyi rayuwarsu ahaka. Aranar da megadi yazo lokacin yarana suna sallah, basuyi tunanin wani zezo ba, hakan yasa shima yayi sa,ar ganinsu. Danaga shima yanada zuciyar imani hakan yasa na kyaleshi yacigaba dazama dasu, sede banyarda yafadama kowa ba, dan nasan zuciyar kowa daban take, kuma yayimun alkawarin baze fada ba, mune muke daukesu aduk lokacin dayayi niyar fadama wani. Koyanzu yaci sa,a kaine yafada mawa, amma daba kai bane, yanda muka daukesu nayi niyar bazan ajesu anan kasar ba gaba daya, gara nakaisu wata kasa inda babu wanda yasansu, nasan zasu temakesu. To malam wannan addu,ar dakayi ita kadai tadawo damu. Kuma nayima Baba hakuri tunda naga alkhairi yakeson su dashi, yanzu Malam kome kayanke zamubi umarninka, amma kasani duk inda zaka kaisu kada karabasu dan yarinyar nan bazata iya zama awani guriba batare dasu ba. Kaima Baba kasan yanda kuka shaku. Malam yace naji dukkan bayaninka, kuma naji dadi sosai daya kasance kaine katsinci wadannan bayin Allah, nasan irin halin temako dakake dashi bazaka taba barin wani abun cutarwa yasamesu ba. Allah yabiyaka kaida yaranka, hakika zakaran da Allah yanufa da cara, to ko ana muzuru ana shaho seyayi. Tabbas wannan yarinya Allah kadai yasan irin alkhairin data debo kuma shine yaraya abunshi. Yanzu abinda nakeso infada maka, gaskiya zaman yan adam agurin nan beyi ba, saboda rayuwar gaba, kaga wannan yarinya tagirma, yakamata ace tashiga cikin mutane, dan kada wata rana tafi haka girma ace zata koma cikin mutane abun ya gagara, kalli yanda take cike da firgici sbd ta ganmu wanda banga laifinta ba, nasan bata taba ganin kowa ba, se mutum 2. Dan haka nayi maka alkawarin zandaukesu zamuje mu sama ma wannan mata magani, duk da kace ciwonta babu asiri ajiki, zamukaita asibiti aduba lafiyarta, kuma nizan rikesu tamkar jinina. Nagode sosai daka fahimcemu. Godiya sosai Malam yayima wannan shugaban aljanu sannan yabace. Malam yace to Baba kajide yanda mukayi dashi, yanzu yakake ganin za'ayi? Baba yace naji dadin abinda kayi, kuma dama abinda nake fata kenan arayuwata inga ranar dasu Yar Baba zasu bar gurin nan, shiru yayi yana goge kwallan idonshi. Malam yace yanzu kutashi muje gida semusan abinyi. Jakadiya da matarshi yasa sukamo maman Yar Baba, tana ganin zasu dauketa tafara kuka sosai, da kyar suka kamata, shima seda Baba yaje yakamota yarike hannunta dana Yar Baba sannan ta bisu, gurin shiga mota kuka Yar Baba tasa masu, tsayawa tayi takishiga motar, duk tarike Baba, dakyar yasamu tashiga, haka suka nufi cikin gari. Zaune suke afadar Sarki Qaseem, Waziri yamika gaisuwa tare dafadin Allah yatemakeka, munje kuma mun isar da sakonka, malam yace afada maka sunanan suna addu,a insha Allahu za,a dace, kuma yace afada maku Fulani tana nan araye, sede haryanzu Allah be gwada mashi inda take ba. Ga wannan ruwan addu,a ne yace akawo na me martaba. Areef ne ya amshi addu,ar ya ajeta agefen Sarki. Gyaran murya Sarki yayi yace to Alhmdullh, inaganin muma semucigaba da addu,a nasan wata rana Allah ze bayyana mana Fulani da kuma abinda tahaifa, addu,ar mu Allah yasa kome ta haifa ace shima yana raye. Waziri yace maganar gashin jikin memartaba, meze hana a maidashi yazamana duk bayan kwana 2 sbd inaganin hakan zefi temaka mashi. Sarki yace hakan ma yana da kyau, muje abashi maganin. Areef yatashi yadauki maganin suka nufi gurinshi. Gimbiyar Babbar Gida suka samu agurinshi tana bashi kayan marmari, sallama Waziri yayi, daya daga cikin fadawan yaje ya sanar da ita zuwan me martaba. Komawa yayi yamasu iso sannan suka shiga, bayan sungaisa yatambayeta mejiki tace dasauki, tashi tayi tafita, jakadiya ta mara mata baya. Duka sauran bayin suka fita, se Babban Hadiminshi ne, kuma wanda sarki ya aminta dashi ne kadai yarage, karbar robar Sarki yayi yazauna kusa da Yayanshi, yace sannu yaya, Malam yace yana gaisheka, kuma yace abinciken dayayi yagano Fulani tana raye bata mutu ba, insha Allahu zecigaba da addu,a za,a ganta. Kokarin dago kanshi yafarayi jin anyi maganar Fulaninshi, cike da farin ciki Sarki da Waziri suka temaka mashi yajingina, wani murmushin farin ciki ne, ya bayyana afuskarshi. Shima Sarki dasauran mutanen dakin kowa farin ciki ne, yacika fuskarshi. Sarki yace hakane Yaya bata mutu ba, ga wannan maganin yace abaka kasha, dan Allah kada kaki karba, kaga yau shekara nawa ana kawo magani baka sha, ayau naga farin cikin dana dade bangani afuskarka ba, inaso kasha maganin nan, kaga kaima zaka samu karfin yimata addu,a. Babu bata lokaci yabude baki, Sarki dakanshi yabude robar yayi bismillah yafara bashi maganin, tas yashanye, aka dauko dayar robar Sarki yace wannan ajiki za,a shafa maka, kallon Waziri yayi, babu bata lokaci yakama keken yaturashi suka nufi daki. Cike da farin ciki Areef yafita yanufi bangaren Momynshi. Dede zewuce alambu yahadu da sarkin Fada, kara hade fuska yayi, sarkin fada yamatso dasauri yana washe baki yace Allah yatemaki mejiran gado. Hannu kawai Areef yadaga mashi yawuce, da harara Sarkin Fada yabi bayanshi, kwafa yayi sannan yayi gaba. Bayan sunje gida dakyar Yar Baba tasaki Baba Jakadiya takamata ita kuma Ladidi matar Malam takama Maman yar Baba suka shiga ciki, haka yaran gidan suka rika sakin baki suna kallon Yar Baba, itam seboyewa take ajikin Jakadiya. Daki takaita tazaunar da ita, haka suka kama Mamanta suka nufi bandaki da ita, da kyar sukayi mata wanka, sun sabata yafi so 5, haka suka fito da ita se kuka takeyi. Dakin Ladidi suka kaita, sannan Jakadiya tariko Yar Baba takaita bandaki, kintsayawa tayi, dan bata taba ganin irin shiba, seda Jakadiya ta tsaya takoya mata yanda zata wanke jikinta da soso haka tasata tayi wanka tawanke mata kanta, sannan suka fito, kallo daya zakayima yar Baba kagane tsanin kyan datake dashi, dan kamatake da larabawa. Bayan sungama shiryasu suka basu abinci anan maman Yar Baba takwanta se bacci, yar Baba kuwa tanajikin Jakadiya takwanta tayi shiru, ita kuma tana gyara mata gashinta, wanda yaji mai se kyalli yakeyi, daga haka itama tayi bacci. Malam ne yaleko yace idan sungama sufito suji abinda ya yanke akan su Yar Baba. Ur's NABILA RABI'U ZANGO (Nabeelert Lady) 08028525263 [23/08, 1:48 p.m.] Nabeelert Lady: ..🛤🛤🏕🏕🏕🛤🛤🛤 AMAKABARTA AKA HAIFENI 🛤🛤🏕🏕🏕🛤🛤🛤 (The story of hard kingdom) Nah Marubuciyar Zamani NABILA RABI'U ZANGO (Nabeelert Lady) @House of Novella Association (H,O,N,A) www.NabilaLady5@gmail.com Season 20⚜25 Malam yayi gyaran murya ya kalli Baba yace nataraku anan dan infada maku abinda nayi tunani akan wadannan bayin Allah, da farko de dakai zanfara Baba, kaga kamar yanda akayi mana bayanin akan 'Yar Baba, bazata iya rabuwa da kai ba, shine nace meze hana idan har kanajin zaka iya zama dasu, kayi hkr da waccan sana'ar taka kadawo nan cikin gari kaida iyalanka nikuma namaka alkawarin gurin zama harma da aikinyi aduk inda kake so. Amma Baba kaduba kagani mekace? Gyara zama yayi yace agskiya Malam, nikaina banajin zan iya hkr da rashin 'Yar Baba akusa dani, nayi sabo da ita sosai wanda basauki bane ace za'a rabamu, kuma kamar yanda nayi alkawari zankula dasu nayarda zanbar aikina da muhallina indawo nan mucigaba dazama. Malam yace gaskiya naji dadi, kuma insha Allahu zaka samu aiki me kyau, duk da acan ma aikin lada kakeyi nan ma wani aikin ladan ne, tunda temakon bayin Allah zakayi. Zamucigaba dazama dasu anan kuma gobe zamuje asibiti mukai ita wannan mata domin a aunata asan wace irin kalar hauka gareta, idan maganin asibiti ne, se adorata akan magani, idan kuma na hausa ne, semudawo acigaba dayi mata addu'a. Jakadiya tace Yaya, dayake kanwarsu ce itace auta, tunda mijinta yamutu bata kara aure ba kuma bata taba haihuwa ba, shine Malam yasama mata aiki agidan Sarki, ta dalilinshi Gimbiya Shuwa tabata Jakadiya dan tace ta aminta da ita. Kallonta yayi yace inajinki meyafaru? Saddar da kanta kasa tayi tacigaba da magana. Dama wata alfarma ce nakeso zannema agurina kaida Baba, amma dan Allah kada kucemun a'a. Wlh tun da muka dauko bayin Allan nan naji 'Yar Baba tashiga raina, musamman dazu datake kwance akan cinyata senake mata kallo kamar 'Ya ta dana haifa da cikina, duk da Allah be bani haihuwa ba, amma ayau naji inada sha'awar samun diya tabbas da za'a bani 'Yar Baba zanfi kowa farin ciki da hakan, kuma zantafi da ita can gidan Sarki mucigaba dazama da ita, amma Yaya mekace?. Shiru yayi yana kallon kanwar tashi, yana ganin lokacin datake goge kwalla afakayce dan tasan yahanata kuka akan rashin haihuwa. Tausayinta yakamashi, kallon Baba yayi yace Baba mekace game da maganarta? Baba yace ai Malam kai muke saurare duk abinda kayanke dede ne, nide fatana kada akawo wani abun dazeyi sanadiyar nisantani da kuma mahaifiyar wannan yarinya daga 'Yar Baba. Allah yasani nidanake cikin hankalina zanshiga damuwa sosai, bare kuma ita wadda ta haifeta. Malam yace shikenan gobe idan mundawo daga asibiti mukaji bayanin likita nikuma zan fada maku abinda nayanke, amma Baba dan Allah kada kacemun a'a aduk abinda zan zartar, kuma kaima insha Allahu babu abinda ze rabaku da Yar ka, duk inda taje kaima zakaje. Bayan kowa yatashi Malam ya kwanta yana kara tuno yanda wannan aljanin yafada mashi yanda suka tsinci wannan mata, rufe idonshi yayi yakara tuno lokacin da Sarki yake fada mashi halinda Fulani take ciki alokacin dasuka nemeta suka rasa. Ajiyar zuciya yayi yatashi cike da tunani aranshi yana addu'ar Allah yasa tunaninshi yazamo gaskiya, amma koma menene yace zeyi istahara da dare. Wai lafiya Yarima naganka cikin farin ciki haka? Murmushi yayi yace wlh momy yau Baffa yayi murmushi, kuma yasha maganin damuka karbo mashi agurin Malam na Darazo, Tashi zaune tayi cike da annashuwa tace lallai ga dukkan alamu kunzo mashi dawani bayani me dadi ko? Nan yafada mata abinda Malam yace, hamdala tayi tace ai insha Allahu Allah zebayyana Fulani da ita da abinda akema bakin ciki agidan nan, kasanni tausayin Baba nakeyi, shiyasa banason haduwa dashi sede nayi mashi aike. Yarima yace Momy niduk lokacin damuka hadu da Sarkin Fada kawai se inji raina yana baci, kawai nide mutumin be kwantamun arai ba, ganinshi nake da siffar munafukai. Momy tace Allah sarki, kaine kake ganinshi haka, amma aduk cikin fadar Sarki ai inaji babu wanda yake maka son da sarkin Fada yake maka tun kana yaro, kama cire wannan abun daga ranka kawai shedanne yake maka wasiwasi azuciyarka. Shiru Areef yayi amma sam zuciyarshi bata yarda da abinda tafada ba. Bayan sungama shafa mashi maganin ajikinshi bacci yadaukeshi, kamashi sukayi suka kwantar dashi bisa gadonshi suka rufo mashi kofar, Sarki yace insha Allahu Allah yakusa kawo mana karshen wannan halin da muke ciki. Waziri yace da alama wannan maganin zeyi aiki ajikinshi dan tunda naga yasha naga wasu alamu. Sarki yace Allah yasa, suna fita sukaci karo da Jakadiya, kara gaishesu tayi, Sarki ya kalleta yadauke kai, Waziri yace zaki iya tafiya dan me martaba baya bukatar wani abu, kuma ma yasamu bacci, Jakadiya tace to ai shikenan Allah yabashi lafiya, juyawa tayi ta tafi tana me hararar Waziri tagefe. Da Sallama tashiga falon Gimbiya ita kadai tasamu se bayin dasuke mata hidima, zama tayi tana fadin Allah yatemakeki, Allah yasa kifi haka, murmushi tayi tadaga mata hannu, Jakadiya ta kalli sauran bayin dasuke falon, lokaci guda sukayi hanyar waje. Gimbiya tace da alama akwai magana abakinki? Tace kwarai ma kuwa Gimbiya, waigawa tayi tace amma rankishidade banga Gimbiya karama ba, ko lafiya? Yamutse fuska tayi tace oho kinsanta da nawa yanzu haka tana can tana shiryawa kinsan yau ita zata karbeni. Gyara zama Jakadiya tayi tace ai me martaba ma yasamu bacci, kuma da alama ya karbi maganin dasuka bashi, dasauri Gimbiya ta tashi zaune, tace haba Jakadiya wane irin labari ne marar dadinji kike fadamun haka? Allah yahuci ranki Gimbiya 'Yar Babbar Gida, kaina bisa wuya, banga amfanina aduniya ba idan har nazamo daya daga cikin masu bata maki rai, agafarceni Gimbiyar Sarki mace daya tamkar da dubu, kedayace me haske agurin me martaba, duk sauran matanshi bayinki ne Gimbiya me mulki gaba da baya. Wani kayataccen murmushi Gimbiya tasaki, ahankali tace inajinki menene shawara? Nagode Gimbiya, amma aganina meze hana mubi shawarar dana fara kawowa daga farko inaganin ita kadaice hanyar dazata bulle mana, dan mutanen nan suntashi tsaye akan wannan al'amari inajin tsoron abinda zedawo. Maganar Gimbiya medaki sukaji tana fadin wannan shawara taki Jakadiya tayi dede, amma ina ganin kamar haryanzu Yaya batayi na'am da ita ba. Zama tayi tare da daukar apple tafaraci. Jakadiya tace Allah yatemakeke Gimbiya, barka da fitowa, hannu tadaga mata tamaida kallonta gurin Gimbiya tace Yaya dan Allah wannan karin kada kice zaki ki karbar shawararmu, wlh ayanzu kissa da tuggu basuci kawai mubama Jakadiya dama kamar yanda tanema daga farko. Wani kallo Gimbiya tabita dashi, sannan tace wai meyasa kuka kasa fahimtata, koda yake ba laifinku bane daga ke har ita babu wanda yakeda jinin sarauta ajikinshi. Tashi tayi ranta abace tashige daki, da kallo Gimbiya medaki tabita, Jakadiya ko cikin sauri tabi bayanta jiki na bari. Karamin tsaki Gimbiya medaki taja ta tashi itama tabi bayan Jakadiya tana Allah wadai da wannan kaskancin datasa kanta ake mata. Washe gari bayan sunje asibiti likitoci suka taru akanta, anyi mata gwaje gwaje kala kala, bayan sungama likitan yakira malam office, seda yayi rubutunshi sannan yakalli malam yace, agsky munyi duk wani bincikenmu kuma sakamako daya yake bamu, wannan mata lalurarta acikin kanta take, kuma mtsalace mesauki, sede kafin asamu abinda zedawo maka da hankalinka shine aiki, abinciken damukayi mungano cewar buguwa tasamu akanta, komade hadari ne, ko kuma akwai abinda yabugar mata kai, wanda shiyayi sanadiyar haukacewarta. Amma abu mafi sauki shine duk ranar data kara samun makamancin abinda yafaru da ita, kota bige ko kuma ace arika nuna mata abubuwan datayi tarayya dasu kafin tasamu matsalar to zata iya dawowa hankalinta. Dan haka yanzu gida zaku koma da ita, akwai magungunan dana rubuta sekuyi mata amfani dasu. Godiya malam yayi mashi yakarbi takardar maganin yafita. Koda sukaje gida ajikin Jakadiya Yar Baba takwanta hartayi bacci, dan yanzu tafara sakin jikinta, sede daga Jakadiya bata yarda da kowa agidan se ita. Adaren ranar bayan sallar isha'i malam yakara tarasu, hada Baba dan yaje yadauko iyalanshi yazo anan malam yabashi daya daga cikin gidajenshi suka sauka aciki kuma yasa aka zuba mashi kayan abinci dana amfani. Malam yace to Baba kajide abinda likita yace agame da ciwon wannan mata ko? Dan haka nayanke shawarar za'a bama Jakadiya su ta tafi dasu can masarautar datake, dan Sarki mutumina ne, dazu munyi waya da waziri, kuma nafada mashi komai sede banfada mashi tarihinsu ba, kuma Baba wannan tafiya hada kai za'ayita, acan zaka samu aikin dazakayi idan yaso daga baya idan komai yadedeta zaka iya zuwa kadauki iyalinka. Sede Baba banaso kafadama kowa labarinsu, kasan mutane akwai son zuciya nafiso kabarshi atsakaninmu wata rana zasuji labarinsu, kuma abangaren Jakadiya Waziri yace zasu zauna, kasan kuwa bangarenta yana daga bayan lambun gidan, bakowane yake zuwa ba, sede kai tunda sunsan kowaye kai zaka iya zuwa aduk lokacin dakakeso. Allah yabaka ikon rike sirrinku, sekayi ahankali da gidan sarauta, ba,a aboki agidan, kowa da halinshi yake zaune, dan haka kazama cikin shiri gobe insha Allahu zakutafi da safe. Allah yakareku daga dukkan sharri. Baba yace amin, kuma naji dadin abinda kamun, ga iyalai na nan, nasan zaka kulamun dasu Allah yabaka ikon zama dasu lafiya, amma taya zamurika magana da kai? Murmushi malam yayi yace kada kasamu damuwa akwai waya ahannun Jakadiya, kuma iyalanka zasu zauna cikin kwanciyar hnkl, fatana Allah yabaku sa'a. Haka kowa yatashi Jakadiya tanacike da murna, harta tashi yace Jakadiya kisameni adaki, Bayan sun shiga naji malam yafara magana, akwai abubuwa da dama da zuciyata take sakamun akan wannan matar, shiyasa ma nace zakutafi tare. Kara rage murya yayi yana mata bayani,akan yanda yakeson abubuwan sutafi, sede duk yanda naso inji abinda suke fada ya gagara, haka nadawo inajiransu sufito, sundauki kusan awa daya suna tattaunawa sannan tafito. Washe gari dasafe Malam yabada mota akadaukesu suka nufi babbar masarautar Gombe. To jama,a bara muji menene asalin labarin wannan masarauta. Tuna baya, Asalin Labarin. MASARAUTAR BUBAYARO. Muhadu a page nagaba. Ur's NABILA RABI'U ZANGO (Nabeelert Lady) 08028525263 [23/08, 1:48 p.m.] Nabeelert Lady: ..🛤🛤🏕🏕🏕🛤🛤🛤 AMAKABARTA AKA HAIFENI 🛤🛤🏕🏕🏕🛤🛤🛤 (The story of hard kingdom) Nah Marubuciyar Zamani NABILA RABI'U ZANGO (Nabeelert Lady) @House of Novella Association (H,O,N,A) www.NabilaLady5@gmail.com Season 30⚜35 Qaseem yayi saurin fadin haba Yaya kasan mekake fada kuwa? Sarki yace koma menene Qaseem nasan baze wuce tace in....... kara kamo rigarshi datayi ne yasashi yin shiru yamai da hankalinshi gareta. Bawan Allah ga 'Yata nan, ita kadai Allah yabani, mahaifinta yarasu nikadai narage mata, kuma nima gashi Allah zerabata dani. Daga cikin wancan kauyen muka fito, mutanen garin suka koromu sbd kawai wani yayi ma mahaifinta kazafi, sakamakon hakan ciwon zuciya yayi ajalinshi. Mu kuma suka koromu komai basu bari mundauka ba. Inarokonka kobayan babu raina kada kabari Nafeesa takoma garinmu, kamar yanda kamun alkawari inason rayuwar Nafeesa tayi albarka dan Allah kadaure ka auri Nafeesa. Qaseem cike da bacin rai yace dalla malama kifadi abu meyuwuwa kinko san dawanda kike magana? Idan baki sani ba, to........ tarin daya taso matane yasashi yinshiru suka maida hankalinsu kanta bakaramin shiga tashin hankali Sarki yashiga ba, ganin tana wani irin aman jini, Nafeesa ko se kuka takeyi, Sarki yatashi yace ma Waziri adauketa ko akan doki ne, mutafi da ita asibitin cikin gari. Wani bafade Waziri yasa yadaukota, Haka Nafeesa ta tashi tana kuka. Cak bafaden daya dauketa ya tsaya jin jikinta yakara nauyi, Waziri yace muje mana katsaya kana bata lokaci, Ranka yadade ade zo aduba wannan baiwar Allah naji jikinta yasaki, dasauri Sarki yadawo dabaya, suna zuwa Waziri yataba hannunta yaji yadawo, yasa hannunshi gurin hancinta yaji ba numfashi, sam yamanta da diyarta agurin yace Rankai dade inaji fa ta mutu. Wani kara da Nafeesa tasaka nan take tafadi kasa sumammiya. Sarki cike da damuwa yasa Fadawa suka dauketa da mahaifiyarta aka dorasu akan doki aka nufi gida dasu, Qaseem kanshi jikinshi yayi sanyi yatausaya ma Nafeesa sosai. Ko kafin sukai gida maman Nafeesa harta saki, dan akwai dan tafiya, suna zuwa sarki yasa aka kira Jakadiya nan Waziri yayi mata bayanin komai aka shiga da gawar cikin gida. Ita kuma Nafeesa aka kira likitansu domin yadubata. Babu bata lokaci aka gama shiryata akayi mata sallah tasamu jama'a sosai, haka aka kaita gidanta na gaskiya, jikin Sarki yayi sanyi sosai dan yasan yariga da yadauki alkawarin da dole yacikashi. Bayan sundawo yakira Waziri dan suyi magana, bebi takan Qaseem ba, dan yasan baze bada goyon baya ba. Sosai Waziri yakara karfafa mashi guiwa kuma yakara tunasar dashi muhimmanci alkawari, da kuma irin jihadin dazeyi, Waziri yace kobaka aureta ba, kasama mata miji acikin gidan nan ko awaje hankalinka baze taba kwanciya ba sbd bakasan irin rikon dazeyi mata ba. Sarki yace bakomai ai itama mutum ce, kamar kowa kuma yin hakan dazanyi baze ragemun wani abuba, sede Allah yasani atsarina banida ra'ayin auren macen da bata fito daga gidan sarauta ba, kuma wannan ra'ayi nane shiyasa Qaseem yakeda irin ra'ayin, segashi nashi haryafi nawa. Nasan zeji haushi na, amma dole incika alkawarin dana dauka dazaran Nafeesa tasamu sauki za adaura auren banason tashiga cikin damuwa. Allah yabani ladar abinda nayi. Bakaramin tashin hankali Gimbiya Zakiyya tashiga ba da Jakadiya takawo mata maganar auren Sarki ba, duk da batason Jakadiya amma daga ranar tafara sakar mata fuska dan tasan zatayi mata amfani. Koda tafada ma mamanta shawara daya tabata, kada tasake tanuna bacin ranta akan auren, kogurin Sarki banyarda ki nuna bacin ranki ba. Da wannan shawarar Gimbiya tasamu sauki aranta. Koda Jakadiya taga tafara samun sakin fuska agurin Gimbiya seta kawo mata shawarar kozata kaita gurin bokanta. Dawani kallo Gimbiya tabita, cike da bacin rai tace waiku meyasa bakuda tunani idan zakuyi magana. Ko anfada maki gidan sarauta gidan hauka ne? To kada kikara zomun da wannan maganar banzar. Jakadiya cike da ladabi tace Allah yahuci zuciyarki, kiyi hkr insha Allahu baza'a karaba, tace tashi kije idan kinsamo wata shawarar wadda tayi dede da tsarina zaki iya dawowa. Wacece NAFEESA? Diyace ga malam Audu da Uwani sunkasance talakawa ne, sosai mal. Audu beda wata sana'a data wuce Caca haka Uwani muguwar masifaffiyar mata ce, dama cirani yakawosu kauyensu alakocin Nafeesa tana da shekara 15, Uwani macece mesan kudi sosai hakan yasa take dorama Nafeesa tallar gyada, duk sanda taje talla acikin tasha dakin wani saurayinta take zuwa yasiya duka yabiya bukatarshi da ita. Seda tayi ciki har so 3 suna zubarwa, kuma Uwani bata cemata komai, shikuwa mal. Audu dama babu ruwanshi dasu. Gaba daya sun dami yan garin, ana haka wata rana mal. Audu yayi Caca aka cinyeshi beda abinda ze bada hakan yasa yaje gidan wani mutum yasato rago, yana fitowa aka kamashi,

Chapter 2 of 13