Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
suke samu. Tarasa cikakken Ilimin addini dana Boko, batasan kowa acikin yan uwanta ba, batasan yaya mutane suke ba, har seda Allah yakawota cikin gidan nan. Kalli Umminta, tasamu kanta acikin hauka harna tsawon shekaru 18. Agaskiya mutane basa kyautawa. Nayi alkawarin zan jiyama beauty rayuwa medadi, wadda batayi irinta abaya ba. Zan sama mata makaranta me kyau wadda zata samu cikakken ilimin addini dana boko. Fatana Allah yabani tsawon rai in cika wannan burin dana dauka. Kamar yanda Sarkin fada yake ikirarin yasa anciremun son sarauta azuciyata, to be cuceni ba. Kanshi ya cuta, kuma naji dadin hakan, zanyi amfani da damar dana samu dan insamu lokacin beauty na, nasan inda inason sarauta bazan iya samun lokacinta ba, bare incika mata burin dana dauka, dan haka zan rokisu Abba ayi bikinmu akusa dan bana tunanin zama da beauty akasar nan. Zantafi da ita wata kasa harseta samu ilimi me kyau sannan mudawo. Haisam yace gaskiya ka kyauta, sede kasan da kyar idan su Abba zasu yarda, yanda beauty bata taso agidan nan ba zasu so ace sun sami lokacin zama da ita. Areef yace katayani addu,a insamu shawo kansu. Washe gari da misalin karfe 10 na safe tawagar Sarkin Yobe wato mahaifin Zakiyyah da mahaifiyarta suka iso masarautar BUBAYERO. Dan tun ajiya Sarki Hasheem yasa Sarki Qaseem yafada masu halin da ake ciki. Ba karamin tashin hankali suka shiga dajin wannan labari, ba kamar mahaifiyarta datasan ta dalilin haka zata zama abin tsangwama acikin kishiyoyinta. Zaune suke afalo, sede Familyn gidan ne, kawai aciki, tare dasu Mahaifan Zakiyyah, se kuma Waziri, malam da Jakadiya Safeeya. Agefe guda kuma Zakiyyah ce zaune atakure guri guda se kuka takeyi. Mahaifinta ne yayi gyaran murya yafara magana. Hakika Zakiyyah kinbani mamaki da irin abinda kikayi, saboda kawai kishi irin naku na mata, yanzu inda Allah yabaku sa,a kunsamu damar kashe Fulani da shikenan kema kinza me kisan kai ko?. Ko agidanku dakika taso acikin kishiyoyi kika samu mahaifiyarki, kintaba ganin ance ta harari wani acikinsu? Duk da takasance karama acikinsu amma hakan besa ta rainasu ba. Agaskiya banji dadin abinda kikayima kishiyarki ba. Kuma naji dadin hukuncin da aka yanke maki, wannan shine dede ga duk mutumin da yace Son zuciya zerika bi arayuwarshi, koyanzu da kikaga munzo bawai munzo bane dan ke, munzo ne, kawai dan inbada hakuri agurin mutanen da kika zalunta, babu ruwana da hukuncin da aka maki, haka zaki zauna tare da sauran masu laifi har shekaru 5, idan Allah yasa har lokacin ina raye nibazan hanaki zama gida na ba, amma kisani kina dawowa zan aurar dake ga duk wanda naga dama. Dayake Sarki Hasheem yace kada wanda yafada masu abinda suka aikata da Sarkin Fada hakan yasa basusan maganar ba. Dan Sarki yace yanajin kunyar mahaifinta shiyasa yahana afada masu abinda tayi, duk da ba laifinta bane. Kuka sosai Zakiyyah takeyi ta matso kusa da Babanta takama. Kafarshi tace dan girman Allah Baba kayafemun, wlh nikaina nayi nadamar abinda na aikata, babu irin shawarar da Umma bata bani ba, amma nabiyema hudubar shedan na aikata abinda yazubar da kimar masarautarmu, dan Allah kuyafe mani koda mutuwa zata riskeni acikin kurkutu. Seda kwalla tacikama mahaifinta ido, damma bakin glass ne a idonshi, juyawa tayi kusa da Ummanta takifa kanta bisa cinyarta tasaka kuka, tarasa bakin magana, itama Ummar kuka takeyi sosai, seda suka bama mutanen falon tausayi. Mahaifin Zakiyyah ya kalli Sarki Hasheem da Fulani, yace iname neman gafara agurinku, tabbas Zakiyya ta aikata kuskure dan Allah kuyi hakuri, muzamu koma seku aiwatar da duk hukuncin da kuka yanke ma kowa, kada tausayi ko wani kusanci ya hanaku cika umarnin Allah da Manzonsa. Tashi yayi yana goge kwallar data zubo mashi, yanufi kofa yana fadin Zakiyyah nayafe maki duniya da lahira, Allah yasa wannan abu daya faru yazama kaffara agareki, idan munkara haduwa zanyi farin ciki da haka idan kuma ta Allah takasance se ince Allah yasadamu da alkhairi, haryanzu kinada lokacin tuba, kada kiga anyanke maki hukunci ki kasa cigaba da neman gafara agurin Allah. Yana kai nan kuka yaci karfinshi yayi waje, fadawanshi dake bakin kofa suka mara mashi baya. Tashi Umman Zakiyyah tayi itama zata tafi, Zakiyyah tariketa tana kuka, tace Umma bakice komai ba, dan Allah kimun magana kada in mutu da fushinki. Jawota tayi ta rungumeta tace. Nayafe maki Zakiyyah Allah ya yafe maki, insha Allah zanrika kawo maki ziyara harkifito, idan kuma na mutu, addu,ar ki nake nema, idan kinrigani mutuwa, addu,a ta zata sameki har kabarinki. Sakinta tayi tanufi waje dasauri tana kuka. Da gudu Zakiyyah tabita, sede kafin ta isa harsun tada mota sun nufi gate, haka taruga da gudu, tana binsu, suna fita aka kulle kofar, anan tazube tana kuka, duk mutanen gidan suna kallonta. Acikin mota kuwa Umman Zakiyyah se kuka takeyi, haka Sarki yajawota yana lallashinta. Tace shikenan yanzu kowa seyasan abinda Zakiyya tayi, shikenan yanzu banida sauran kima agurin mutane. Sarki yace namaki alkawarin babu wanda zesan abinda Zakiyyah tayi, sede idan tadawo gida, zamusan abinda zamu fada. Kwanciya tayi tana fadin nagode. Tunda suka fita Sarki Hasheem yake kuka, yakasa denawa,gaba daya tausayin Zakiyyah da iyayenta yakamashi, kuka yakeyi kamar karamin yaro, gaba daya jijiyoyin kanshi sunfito, ganin haka Waziri yayima Likitansu waya, yazo. Bayan yagama dubashi yayi mashi wasu allurai kuma aka bashi magani, ko minti 5 bekara ba yayi bacci. Likita yace jininshi ya hau sosai, kuma zuciyarshi tana bugawa dasauri, saboda tashin hankalin daya shiga, zeyi bacci na tsawon awa 8 kafin ya farka, idan yatashi ayi kokarin mantar dashi duk wata damuwa dazata kara dawo mashi. Sallama yayi masu yafita. Anan suka kulle mashi dakin suka fita. Sarki Qaseem yace Malam muje agama abinda za,ayi kozamu dena kallon fuskokin wadancan munafukan. Waziri ya kalli Areef yace kaja beautyn taka kubar gurin nan banaso taga komai, idan zaka dawo kayi kallo to ita de kabarota acan. Haisam ya kalli Ayman yace kema wuce mutafi banason kirika mun kuka, murmushi tayi tace aini babbace kuma nafi Beauty sanin matsalolin rayuwa. Dan haka kabarni in kalla, hakan ze karamun imani dajin tsoron aikata kowane irin zunubi. Murmushi yayi dan yaji dadin kalamanta. Gaba daya mutanen masarautar harma da mutanen waje seda suka cika babban filin da ake wasan dokuna na Masarautar BUBAYERO, dan kowa yanason yaga yanda za,a aiwatar da wannan hukunci. Hada manyan malaman masarautar suma sun halacci gurin, haka aka fito da masu laifi kowa yasaka kayan yari ajikinshi, gaba daya kunyar mutanen gurin sukeji, gani sukeyi kamar duka mutanen duniya ne, aka tara agurin ganin irin yawan da mutanen suke dashi. Kowa neman boyewa yakeyi bayan dan uwanshi, Zakiyyah duk tafi kowa jin kunyar jama'an gurin, jitake kamar kasa ta tsage tashige. Duk abinda takeyi Malam yana kallonta, besan lokacin da kwalla tazubo mashi ba. Bawai tausayinta yasa shi kuka ba, kawai daya kalli yanda take boyewa dan kawai taga yan tsirarrun mutane, wadan da ko rabin garin Gombe basu kai ba, amma shine take jima kunya. To inda ranar lahira ce Allah ya tadata agaban biliyoyin mutane yazataji? Wannan tunanin shine abinda yasaka Malam kuka. Bayan sun tsaya agurin da aka tanadar masu, kowa yasamu nutsuwa, sannan Malam yahau kan wani guri medan tudu shida Sarki Qaseem da limamin masallacin masarautar, tayanda kowa ze iya ganinsu. Seda Malam yasa liman yabude masu taron da addu'a sannan yafara magana. Har yanzu hawaye basu dena fitowa daga idonshi ba, musamman daya hau sama yaga mutane sun nutsu gefe guda kuma ga masu laifi suma sun tsaya suna kuka. Kyalle yasa ya goge idonshi sannan yafara magana. Alhamdulillahi, kamar yanda kowa yasan dalilin taruwar mu agurin nan, kuma naji dadi matuka da Allah yasa naga Mata da Maza, Yara da Tsofaffi, sun halacci gurin nan. Saboda kowa ze kalli yanda kowa ze amshi hukuncinsa. Nasan yawancin mutanen gurin nan masu hankali, wannan taron kadai ya isa ya tunatar da kowa tashin kiyama, da kuma tsayuwar hisabi. Da farko inaso indanyi amfani da wannan dama inyima jama'a tunatarwa akan rayuwar duniya data lahira, hakika wannan abu da mutanen gidan nan suka aikata yasa mutane dayawa zasu koyi darasi. Zanyi magana akan abu 2. AMANA, da ZINA. Wa iyazubillah. Hakika mutane dayawa sun shagala azamanin nan gurin Cin AMANA. Basajin kunyar ha'intar makusantansu. Dama Manzon Allah (s.a.w), yace idan karshen duniya yazo amana zatayi karanci, bawa ze iya cin amanar Uban gidanshi, kamar yanda Da ze iya cin amanar mahaifanshi. Ayanzu halin damuke ciki kenan mutane basu dauki cin amana abakin komai ba. (1) Kamar yanda yazo acikin hadisin Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata agareshi. Inda Abdullahi bn Abbas (RA) yace. Lallai kyawawan aiyuka suna sanya mutum hasken fuska da na zuciya da yalwar arziki da karfin jiki da soyayya daga bayin Allah. Kamar yanda sabon Allah yake sa fuska da zuciya duhu da raunin jiki da tawayan arziki da kiyayya daga mutane. Rawahul Muslim. (2). Allah ta'ala yana cewa. Kuma wadanda sukayi kokari ga nemar yardarmu. Lallai muna shiryar dasu ga hanyoyinmu, kuma lallai tabbas Allah yana tare da masu kyautatawa. (Suratul Ankabut, Aya ta 69). (3) Allah ta'ala yana cewa. Babu wata musiba dazata sameku, face sai sakamakon abinda hannuwanku suka aikata. (Suratul Al shuura Aya ta 30). Sadakallahul Azim. Kai jama,a, ina zamu kai wannan girman zunubi damuke daukar ma kanmu? Hakika Allah baya yafe laifin wani akan wani. Baka tunanin idan kaci amanar wani Allah yadauki ranshi ko ranka batare daka nemi yafiyarshi ba? Jama'a yakamata mutuba zuwa ga Allah, wlh duniyar nan tafiya takeyi. Kada muyarda wasu subamu amana mu ci masu, ayanzu wanda ka yarda dashi shine wanda yake cutarka. Allah yasa mufi karfin zuciyarmu. Kowa da anyi magana seya ce Shedan. Kada kumanta shifa Shedan seyasamu kofar shiga jikin dan Adam yake iya shiga har yasamu damar yimasa mummunar huduba. Idan har mukayi riko da gaskiya da Amana, muka koma ga Allah, tabbas ze cecemu daga sharrin shaidan. Idan baku manta ba, duk yanda shedan yakai ga hallakar da bayin Allah baze taba samun nasara agurin wadan da Allah ya tsare ba. Ba kuma tsayawa zakayi harse kasamu tabbacin lallai Allah ya tsareka sannan zaka rika addu,a ba. Manzon Allah dakanshi yana neman tsari daga sharrin shaidan, wanda kowa yasani yafi karfin shedan, Allah yariga da ya haramta ma shedan kusantar manzonsa. Amma duk da haka Annabi be kwanta ba yace Allah yatsa reshi baze nemi wani tsari daga gareshi ba. To kai waye dabazaka nemi tsari daga sharrin shaidan ba? Yakamata kowa yadage da yaki da zuciyarshi, ita kadaice hanyar dazata tseratar damu. Allah yasa mudace. Magana ta biyu akan ZINA. Innalillahi Wa inna ilaihirraji'un. Wannan abu itace abinda yake damun mutane dayawa, babu yara, ba manya, marasa aure, har masu aure. ZINA wata musiba ce acikin al'umma. Allah ya haramta zina, shiyasa ma yace kada ku kusanceta. ZINA tana tarwatsa duk wani mutunci na dan Adama, tana sa talauci. Shiyasa Allah yakawo hukuncin ZINA acikin alkur'ani me girma. Dan haka ayau kowa zega irin hukuncin daya kamata ayima duk wanda ya aikata ZINA. Allah yashiryar damu da iyalanmu, baki daya. Kafin afara akwai jawabin da Sarki zeyi maku. Komawa baya Malam yayi yana share kwallan idonshi, Jama,a da dama agurin seda suka zubar da hawaye akan jawabin da Malam yayi. Sarki Qaseem yafara magana, shima daka kalli idonshi zaka gane kuka yayi. Alhamdulillahi, kamar yanda Malam yayi mana jawabi, nasan mutane dayawa sun kara sanin me ake ciki arayuwa. Kamar yanda zamu fara aiwatar da wannan hukunci, ina me fada da babbar murya, daga yau, duk wanda aka kara kamawa acikin kasata, dumu dumu da laifin aikata ZINA , kowani laifi, tabbas se hukunci yahau kanshi. Ko wanene, kuma ko wacece, kowane irin matsayi mutum yake dashi, zamu buga tambari wannan doka zata fara ayau. Kuma naji dadi sosai da dokar zata fara daga cikin Masarautar mu, acikinta ma hada masu sarauta aciki. Karewa ma, hada matan Sarki Hasheem guda 2. Tunda har muka iya aiwatar da hukunci akansu. Babu wanda za,a kara daga ma kafa idan ya aikata zina, watakila hakan yakawo mana sauki acikin kasarmu. Daga karshe ina yima Allah godiya daya nuna mana wannan rana. Sauka yayi idanunshi suna fitar da kwalla. Anan Waziri yasa aka cire Zakiyya da Jakadiya Karima, dasu Mati da Lado gefe guda, kuma aka fadama mutane irin hukuncin da aka yanke masu. Medaki se Kuka takeyi. Tanufo gurin su Gimbiya Suhailat da Fulani, wadanda suma kukan sukeyi. Har kasa ta duka sede takasa yin magana saboda kukan datakeyi, hannuwanta biyu kawai tahada alamun neman yafiya tacigaba da kuka. Kamota sukayi suka rungumeta suna kuka. Seda suka saka kowa kuka agurin, wasu mata sukazo suka kamata, seda tayi addu,a sannan aka sata cikin ramin aka rufe jikinta akabar fuskarta. Tunda su Fulani sukaga haka suka bar gurin suna kuka, mata dayawa seda suka bar gurin, hatta da Sarki Qaseem fada yakoma yana kuka, kasa tsayawa yayi agurin. Bayan anyi mata addu,a akasa yara suka fara jifarta, ahaka harseda ta mut . u😭. Wa iyazubillah. Allah ka tsaremu Wa iyazubillah. Allah ka tsaremu daga aikata ZINA. Amin. Zakiyyah agurin tazube asume saboda tsabar kaduwa, Jakadiya kam kuka kawai takeyi. Haka wasu suka dauketa aka shiga da ita ciki. Boka da Sarkin Fada aka kira. Idanun Sarkin Fada sunyi jajur saboda kuka, haka shima yaje gurin Waziri, da Sauran mutane, yana kuka yana neman yafiyarsu. Bayan anyi masu addu'a aka dorasu saman wani table, aka samasu bakar hula afuskarsu sannan aka ture su daga kan table din. Haka sukayita lilo har suka mut . u😭. Wa iyazubillah. Allah ka tsaremu Sannan aka tasa keyar sauran masu laifi zuwa kurkutu, alokacin Zakiyyah ta farfado itama aka hada da ita. Gaba daya mutanen dake gurin babu wanda bezubar da hawaye ba, jikin kowa yayi sanyi, tsoro yashiga zukatansu. Haka aka taru akayi masu sallah aka wuce dasu makabarta. INNALILLAHI WA INNAILAIHIRRAJI'UN😭. Wa iyazubillah. Allah ka tsaremu . A 😭. Wa iyazubillah. Allah ka tsaremu llah kasa mufi karfin zuciyarmu. Bazan iya cigaba. Da typing ba se zuwa gobe idan Allah ya kaimu. Abinda nafada da kuskure Allah yayafe mani. Nagode da kulawarku, sekunjini anext page insha Allah. Ur's. NABILA RABI'U ZANGO (Nabeelert Lady) 08028525263 [23/08, 1:48 p.m.] Nabeelert Lady: ..🛤🛤🏕🏕🏕🛤🛤🛤 AMAKABARTA AKA HAIFENI 🛤🛤🏕🏕🏕🛤🛤🛤 (The story of hard kingdom) Nah Marubuciyar Zamani NABILA RABI'U ZANGO (Nabeelert Lady) @House of Novella Association (H,O,N,A) www.NabilaLady5@gmail.com Season 115⚜120 LAST PAGE Washe gari Sarki Hasheem yasamu karfin jikinshi, da misalin karfe 10, gaba dayansu suka taru a babban falo, bayan anbude taro da addu,a anan aka fada ma Sarki Hasheem duk abinda yafaru jiya, sosai ya tausaya ma Medaki. Malam yace to Alhamdulillahi, muna godiya ga Allah daya nuna mana wannan rana, inafatan wannan abu da yafaru agidan nan ze zame ma kowa darasi, abinda yarage mana shine mucigaba da neman tsari daga sharrin masu sharri, kuma kowa yadage da addu,a, kada kuyi la'akari dacewar wani yana maku addu'a. Idan har zaka iya saka wani yamaka addu'a to kai meyasa bazaka iya rage wani abu daga cikin darenka katashi karoki mahaliccinka ba? Allah da kanshi yake fada akwai wani lokaci acikin dare wanda yake sakkowa daga sama yazo ya karbi addu'ar bayin da sukayi awannan lokacin. Da aka tambayi manzon Allah wane lokacine wannan? Yace daga karfe hudu zuwa asuba. Duk wanda yatashi awannan lokacin yayi sallah tabbas Allah ze karbi addua'arsa. Ina me maku nasiha da ku daure kurage jindadin duniya kusami lokacin ganawa da ubangijinku acikin dare, ibadar rana kadai bazata isheka ba, saboda duk yanda kaso kebewa da rana kace zakayi ibada ta tsawon minti 30 kadai, dole se wani abu yashigo maka katashi. Amma idan akace maka da dare ne, kana da lokaci me yawa. Kuduba manzon Allah, shifa yariga dayasan anyi mashi albishir da aljanna, amma duk da haka yakan tashi cikin dare yayi ta ibada. To kai waye dabazakayi koyi dashi ba? Wanda aduk cikinmu babu wanda yakeda tabbacin shiga aljanna. Dan manzon Allah yace akwai wadan da zasu dade suna aikata aikin alkhairi, amma karshen wuta ce makomarsu. Kamar yanda wasu zasu dade suna aikata zunubi amma aljannace mako marsu. Dan haka aduk lokacin da kukaga wasu suna aikata alfasha, kada kabata lokacinka gurin aibantasu, kai zaka cinye ladar daka tarama kanka, amai makon haka kayi masu wa'azi idan har kaga zasu dauka, idan kuma abin yafi karfinka to kabisu da addu'a. Manzon Allah yace aduk lokacin da wani bawa ze rokama wani dan uwanshi abu agurin Allah, batare da sanin wancan ba. Mala'iku zasuyi rika yimashi addu'ar duk abinda yarokama wancan shima. Daga karshe, ina kara maku nasiha dakuji tsoron Allah, kuma kucire son zuciya a zukatanku, Allah ze temakeku aduk inda kuke, kuma kuzauna da kowa da zuciya daya, idan shi bahaka yake zaune daku ba, wata rana Allah zetonashi kowa yaganshi, kamar yanda yayi ma wadan da suka wuce. Ina fatan kowa zerike duk abinda nafada maku. Gyaran murya Sarki Qaseem yayi yace, hakika munji dadin irin fadakarwar da malam kayi mana, akwai abubuwa da dama daka tunatar damu, wadanda munshagala dasu abaya, hakika mutum yatashi yaroki Allah da kanshi shine abinda yafi, domin idan kadogara da wani, wata rana Allah yana uya daukeshi, shiyasa akace daka bama mutum kudi yasayi abinci. Gara ka bashi gona yayi noma, haka kuma daka bashi kudi gara ka sakashi makaranta. Wata rana seya temaki kanshi da al'umma. Mungode kwarai da kulawarka agaremu, Allah yabar zumunci, kuma insha Allahu zamu kawo gyara sosai amasarautar nan, ta yanda zamu temaki sauran bayin dasuke cikin masarautar nan, suma susami ilimin addini kada rayuwarsu takare abauta. Malam yace idan kukayi haka tabbas zaku kawo cigaba a masarautarku, kuma yin hakan zesa wannan masarauta ta daukaka, harma wasu masarautun suyi koyi daku. Ni kuma nayi alkawarin turo manyan yarana suzo suma subada tasu gudunmuwar, kaga ahakane, suma bayi zasu gane cewa suma mutanene, kamar kowa. Ina rokon Allah ya amshi wannan niya taku, kuma yasama abun albarka. Ina ganin ayau zanzo in koma. Waziri yace mungode sosai Malam, Allah yasaka da alkahairi, kuma ina ganin kafin kawuce, zamu zabeka amatsayin wanda ze daura mana sabon Sarkin Fada. Malam yayi murmushi yace, to inaganin yakamata abama wanda yakamata abama sarautar tun farko, kafin aci amanarshi. Koba komai, zeji dadin hakan, kuma sauran mutane zasu kara yarda dacewa duk zakaran da Allah yanufa da cara, to ko ana muzuru ana shaho seyayi, yasha wahala ta dalilin sarauta, ya kwashe shekaru dayawa acikin kurkutu. Tabbas babu wanda ya dace da wannan sarauta se shi. Kallon Sarki Hasheem yayi yace, inaso inji wane suna kasama diyar tawa, kafin inkoma? Murmushi yayi yakara kallon Fulani sannan yace agaskiya tunkafin a haifeta dama nazaba mata suna, badan komai nazaba mata sunan ba, sedan inyi godiya ga Allah abisa kyautar da yayi mani nasamun karuwa. AMATULLAHI, shine sunan dana zaba mata. Lumshe ido Areef yayi jin yanda sunan ya burgeshi. Malam yace Alhamdulillahi wannan suna yayi dadi, AMINTATTAR ALLAH kenan, to Allah yasa albarka acikin sunanki da rayuwarki gaba daya. Kowa yace amin. Waziri yace Malam inaganin zaka kara dawowa nan kusa domin kadaura mana aure amasarautar nan, Murmushi yayi yace lallai kam nima naga alama, dan tunkafin inzo nasan da wannan labari, zuwana kuma yakara tabbatar mani da hakan, dan Yarima yafi kowa kaffa kaffa da diyar tawa, yanda kasan ance za'a kwace mashi ita. Dariya suka saka gaba daya. Anan Baban Fulani shima yayima Malam godiya sannan yakara yima Baba na Darazo godiya. Sarki Qaseem yace ai basu kadai ba, gawasu masoyan nan agefe, dan haka tare za,a yi muhuta gaba daya. Kowa dariya yayi. Malam yace to Allah ya nuna mana, amma banaso asaka danisa, gara tazauna da mijinta, hakan ze sa tasamu kwanciyar hankali. Anan aka rufe taro da addu'a. Kwana 3 aka dauka a masarauatar ana zaman jimami, jikin Sarki Hasheem yayi sauki, sede haryanzu yana cikin damuwa, kuma befara takawa da kanshi ba, dole seda sanda, hakan yasa Sarki Qaseem da Waziri suka nemi shawarar likita, shine yace idan ze yarda afitar dashi waje. Zasuyi mashi wani gashi, insha Allah ze dawo dede. Bayan sun sameshi da maganar babu musu ya amince, hakan yasa Waziri yace dashi za,a tafi. Sarki Hasheem yace amma da Fulani zamu tafi ko? Murmushi sukayi sukace ai badamuwa. Lokacin da Sarki Qaseem yasamu Gimbiya Suhailat da maganar cewa tayi suyi hakuri abarta akwai abinda zatayi mata kafin sudawo angma. Yace a,a kinsan Yaya baze yarda ba, kawai kibashi matar shi. Da to kawai ta amsa mashi. Amma azuciyarta tayi alkawarin bazata bari sutafi tare ba, dan Fulani tana bukatar gyara sosai, shekaru 18 acikin hauka, kuma har haihuwa tayi. Dole ma tayi duk yanda zatayi tahana atafi da ita. Zaune suke afalo ana tashirin tafiyarsu, dan anjima kadan zasu tafi,Fulani datake zaune agefen Sarki, tayi saurin rike cikinta. Dasauri Gimbiya Suhailat tace lafiya de Fulani? Nana hankalin kowa yadawo kanta, Sarki Hasheem yace adauketa muje asibiti mana. Gimbiya tace a,a inajin baciwon asibiti bane,birin ciwonmu ne, na mata bari muje cikin gida. Sarki Hasheem yace ina ganin za,a daga tafiyar nan kafin tasamu lafiya. Waziri yace a'a Memartaba, kada wannan yadameka, tafiyarmu bazata wuce kwana 10 ba, inaganin kayi hakuri tunda har angama komai kuma agobe za,a fara gashin nan, kaga likitan yace akwai inda zeje, saboda kaine yadaga tafiyar. Kayi hakuri muje domin neman lafiyarka, nasan ayanzu kanajin babu dadi kowa yana hidimarshi amma kana zaune, guri guda, idan zajayi tafi seda sanda. Sarki Qaseem ya matso kusa dashi yace dan Allah Yaya kada kaki yarda ayi tafiyar nan, wlh Allah kadai yasan halin damuke ciki akan rashin lafiyarka. Shiru yayi, hawaye suna zuba daga idonshi. Hannunshi Sarki Hasheem yakama shima idanunshi sunyi ja, yace karka damu dan uwa na, acigaba da shiri,Allah yasa ayi asa'a. Murmushin jindadi yayi yarungume Yayanshi yace nagode Yaya. Sarki Hasheem yakalli Beauty yace zo Amatullah mu gaisa mana. Murmushi tayi ta tashi tanufi gurinshi tana zuwa tazauna kusa dashi ta dora kanta saman kafarshi. Hannu yasa yashafi fuskarta tace yauwa Amatullahi, Allah yabaki lafiya kema kirika magana kamar kowa. Areef yace Amma Baffa tayi magana so daya a asibiti. Waziri yace insha Allahu wata rana zata yi magana, dan likita yace matsalarta ne sauki ce, kuma base an kaita asibiti ba, zata iya yin magana akowane,lokaci, yace idan har taga wani abu daya tsora tata bakinta ze iya budewa. Sarki Hasheem yace insha Allahu zata samu lafiya. Kuma da mun dawo za,ayi maganar bikunku, Yarima seka fadama abokinka dan ahada tare, ko Ayman? Murmushi tayi ta tashi tafita. Lokaci yana cika suka fito domin tafiya, seda aka kai Sarki Hasheem gurin Fulani sukayi Sallama, sannan suka nufi air pot. Suna zuwa aka fara kiran sunaye, haka suka rungume juna shida Kaninshi, har kua seda sukayi. Yana kallonsu har jirginsu yadaga sannan suka dawo. Dariya Gimbiya Suhailat da jakadiya Safeeya sukayi, Gimbiya tace ai nadauka Fulani bazakiyi yanda nace maki, ba, dan kina tausayin mijinki. Fulani tayi murmushi tace, duk yanda nake tausayinshi ai gara inzauna indawo da martabata ni kaina wani lokacin kyan kyamin kaina nakeji, kiduba fa kigani duk wata kazanta damuke fitarwa haka zanyita ingama babu wani wanka. Kai gaskiya mutanen nan sun cutar dani. Jakadiya Safeeya tace wai ahaka ma kinsamu bakar da ba, kuma kinga acikin kwana goma zaki samu gyara sosai, wanda Sarki zeyi farin ciki da haka. Gimbiya tace ai wannan gyaran na musamman zakisha, suma Yarana nasu nadabanne. Kallon Jakadiya Safeeya tayi tace akwai wani abu danake so inhada, amma anjima idan hubby yadawo zamuyi maganar, kema yakamata, ai ko? Jakadiya tace bangane ba? Murmushi Gimbiya tayi tace a'a bakomai dama gani nayi Waziri tunda matarshi ta mutu be kara aure ba, kuma dama diyarshi daya sunyi mata aure. Shine naga kema mijinki yarasu ai. Dariya Fulani tayi tace kai amma wlh Aunty kin iya hangen nesa. Tashi Jakadiya tayi tana murmushi, Gimbiya tace, ina kuma zakije? Fita tayi bata cemata komai ba. Gimbiya tace Allah da gaske nakeyi, kuma insha Allahu wannan abu seya tabbata, zansa Hubby yafadama Malam, kinga se ayi tare dana su Amatu. Fulani tace Allah yasa. Zaune suke acikin lambu, beauty Amatullah tana zaune agefen Areef yana koyamata karatu, su Haisam suma suna gefe guda suna firarsu. Areef ya kalli Haisam yace wai abokina ya kukayi da Dady akan maganar Ayman?. Murmushi yayi yace yafi kowa mafarin ciki shida Momy dasukaji maganar, yace idan Baffa yadawo zasuzo. Areef yace ai gara azo a aurar damu kowama yahuta ko Beauty na? Kai tadaga mashi tana murmshi. Haisam yace Beauty bahaka zakice ba, a,a zakice. Hararshi Areef yayi yace todan bukulu ai seka hanata, kuma wlh wannan sunan yafita abakinka, tunda de ansamata suna kawai ka kirata da Amatullahin ta. Haisam yace bazan kiraba, ni nariga dana saba. Murmushi Areef yayi yace shikenan, nina zanrika kuran Ayman da Angel. Apple din dayake kusa da Haisam yadauka ya jefeshi dashi, dasauri ya cabeshi yana dariya, Haisam yace wlh baka isa ba. Areef yace tokaima kadena fada mata beauty. Haisam yace nayarda, dannaga alama nizakafi kwara. Dariya suka saka Areef yace dade yafi maka, amma ni inkirata. Beauty kaima haka, ai bazeyuba. Haisam yace towai kai yamaganar fitarku waje bayan aure? Areef yace wlh har yanzu banyi maganar dasu Abba ba, amma yau zanje insamesu. Idan har sukaki zan hadasu da Malam. Haisam yace insha Allah ma zasu amince, duk da nima bazanso kamun nisa ba, amma saboda cigaban Amatu kawai zan hakura, nima inaso inga tadawo kamar kowa. Gimbiya Suhailat tana kwance ajikin Sarki Qaseem suna fira, tace Hubby, dama wata shawara ce, nace bara infada maka kafinsu Yaya su dawo se afada masu aji mezasu ce. Kara yawota yayi yace fada inajinki. Anan tafada mashi abinda takeso. Murmushi yayi yace wlh kamar kinshiga zuciyata, na dade ina wannan tunanin, kawai ciwon Yaya ne, yahanani fada amma tabbas idan suka dawo zansamu Waziri da Yaya da maganar. Wannan abu ne me kyau. Kema Allah yabiyaki da kika kawo wannan shawarar. Sallamar Areef ce ta katsesu, abakin kofa ya tsaya, dan dama al'adarshi ce duk inda yaje baya shiga se anbashi izini kida gidansu ne. Murmushi Sarki yayi yace Allah yayi maka albarka Yarima, hakika ina farin ciki da irin halayenka da kuma tarbiyarka, ace mutum yaje kasar waje yayi karatu amma duk da haka tarbiyarshi bata lalace ba, asalima karuwa tayi. Babu abinda zanma Alkah se godiya, domin nasani shine ya tsare bawansa. Bayan sun gyara zamansu ya amsa Sallamar yace shigo Yarima, shigowa yayi yazauna kusa da Abbanshi tare da dora kanshi saman kafarshi yace sannunku da hutawa Abba. Shafa kanshi Gimbiya tayi tace yauwa sannu Yarima. Sarki yace zanga ranar dazaka girma Areef, ace haryanzu kana hawa cinya. Dariya yayi yace ai babu rana Abba, yace akwai mana, nan da wata daya kam ai zaka zama megida. Kafin kaima kasamu naka dan, kaga saka barmashi ko. Gimbiya tace ai anan zasu zauna ko? Abba yace emana, ai bama son muyi nisa da juna, zamansu cikin masarautar nan zefi. Tashi Areef yayi yana sosa kai yace Abba dama wata alfarma nazo nema, yace fadi duk wata alfarmarka, ni kuma zanyi maka. Anan yafada masu abinda yakeso. Shiru sukayi, yace dan Allah Abba. Sarki yace bawai naki bane, ina duba yanda Yaya zeji, kasan yanada bukatar ganin Amatu akusa dashi, amma se

Chapter 11 of 13