Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
ina ta gudu kar ki fada halakan da wasu matan auren ke fadawa, cikin masifa tace ka yaudareni, i am not perfect but my parent raised me well, ina da tarbiya daidai gwargwado, na san haqain aure bazan ci amanar aure ba duk da ba na sonka, amma kasan zuciya bata da kashi, da a ce na amince fah? Ni zaka ga laifi, yayu saurin cewa i baki amince ba Alhamdulilah, you have a good heart, ki yafe mun ki maido son da kikewa Umar ki dawo dashi kan Suraj, duk da kece ba ki gane ba, Da Suraj da Umar duk suna nane, karki manta Sunana Suraj Umar Z. Bilkisu ta fashe da wani kukan, kaci amanata, ka yaudareni, u were fooling me all dis while, u were-- da sauri ya zura harshensa cikin bakinta, ya shiga bata hot kiss, tayi tayi ta tureshi ta kwaci kanta, amma ta kasa, sai da ya ga tayi laqwas kafin ya saketa dan kanshi ya kalleta idonta a runtse yace Bilkisu I was just testing you nd Alhamdulilah u've passed uo test, zan baki lokaci kiyi tunani, ki gano cewa i mean u no harm, kuma nine Masoyinki na gaskia. Ya fita daga kichin din, a sannan nan ne naurar aiki ya dawo jikinta, abunda ya hadata da YaSuraj ya dawo mata, ta sa yatsarta kan lips dinta tan shafawa, tare da fadin what just happened?? Bauchi Amira look what i bought, ta kauda kai, ya juyo da ita haba Amirah, kalla fa, tickets ne xamuje Makka muyi Umrah ni da wifey na, nd za mu je 2countries of ur choice for our honeymoom, ya qarashe fadin haka tare da daga girarsa, ta tabe bakih ta miqe tace nifa ba inda zani, Ya fincikota ta fado jikinsa, ya matse ta, murya kasakasa me kama da rada yace haba lil sis meerah, nine fa bigbrosamir dinki, ko me namiki ai yaci ace kin yafe mun, Uhm? Ya mata peck a goshi, ya qara wani a kan hancinta, ya sake mata wani a gefen neck dinta, jikin Amira ya hau kyarma, ganin bigbro dinta na neman wuce gona da iri ya sa ta cewa fine, i will come with u, ya sake murmushi, yace dats my lilsis, i love u kinji? Ta kauda kai, yace ko bakiji ba? Da sauri tace naji wlh, yayi daria ya dagata yace me tsoro kawai... Kaduna Fitowar ta wanka kenan Ta tsaya a bakin sif dinta, tana tunanin kayan da zata sa, ita dai yau ba zata sa wani manyan kaya ba, idonta ya kai kan wasu riguna da Mummy bon ta siyo mata da taje dubai, a cewarta wai ta dinga ma Jawad kwalliya, tunda ta jefa rigar cikin wordrob ba ta qara waiwayansa ba sai yau, ta daga rigar chapdijam, daya ta daga, wannan riga haka, rigar ta hadu iya haduwa, saidai kirjin budadde ne, kuma iyakatar guiwa, kawai sai ta ga tana son sa rigar, tunda ba kowa gidan bari kawai ta sa, ta sa rigar nan ta kalli kanta, woooooww, wallahi nayi kyau kamar wata ba indiya, ta gyara gashinta ta yi dan kwalliya, ta fita parlor, Wayarta ta jona a AUX ta qure volume ta sa waqar Falguni, ta shiga rawa a hankali, Thats wat happens wen u are home alone tace a ranta.. Cikin barcinshi yaji Kida na tashi samasama, da sauri ya miqe, kanshi ya shiga sarawa sakamakkon kidan da yakeji, alamu a parlorn gidansa ne, waye ya sa Waqan nan? A gajiye yake, yana son ya samu barcinnan, be dade da shigowa kasar ba, daga Amsterdan inda yaje Workshop, yafi kwana 3 beyi bacci ba, burinshi ya samu hutu, shi yasa yana dawowa gidan da misalin qarfe 7 na safe ya shige dakihnsa don hutawa, amma ga wani kidih na son hanashi bacci, a zucciye ya tashi ya yi hanyar parlorn. Baki bude ya tsaya kallon halitar da ke rawa tsakaninta da Allah, Rawa take cikin kwanciyar hankali, kallo daya za kai mata kasan cewa kyakyawa ce, rigar da ta sa yayi mugun birgeshi, hannayenshi ya nade ya na kallonta, karo na farko kenan da Jawad ya tsaya kallon Fadila, ji yayi wani abu na fizgarsa, wani abu yakeji game da ita, haka kurum jikinta ya bata ana kallonta, da sauri ta waiga suka hada Ido, daskarewa tayi, yaushe ya dawo? Tambayar da ta ma kanta kenan, sai kuna taji kunyar shigarta bayan ta lura da mayataccen kallon da Yajawad ke binta dashi, Jawad ya dawo hayaccinsa, da sauri ya murtuke fuska don kar yarinyan nan ta raina shi, ya shiga borin kunya, yaje ya kashe socket din, ya nufo ta gadan gadan, ya ce keee uban meyasa xakicika min kunne da waqah, baki san ina sonyi bacci bane? Ta murguda bakih tace wa ma ya san ka dawo? Haka kurum yaji murgudenta ya mai kyau, ya kamo ta, tare da matse bakinta wa kike murguda ma baki? Ta saki qara waiyo bakina, yace kika qara sai na cire bakin, ta qara murguda mai baki, haan mutum da bakinsa? Ina ruwanka da ni? Ya qara kamo bakin da hannunsa tare da matsewa, yace kina qaryar rashin kunya ne, ni tsaranki ne? Don kin ga na sa miki ido shine kike min abubuwan da kika ga dama koh? Ya qara matse bakin, Ihu takeyi amma ba aji sbd ya matse mata bakin da qarfih, ya dan sasauto riqon da ya mata sakamakon idonshi da ya sauka kan kirjinta, ya shagala da kallonta, ita ko da sauri ta tureshi tayi cikin dakinta, shiko ya dadi kan kujera yana maida numfashi, haushi kansa ya fara ji, zuciyarsa ke tmbynshi meye haka? What jus happened? Kar ka ba yarinyar nan chance din raina ka. Ya miqe ya yi dakinsa yana me sakin tsakih me qarfih.. _Bibilicious Biebee_ 4⃣6⃣ 🏡GIDAN GANDU🏠by 💕Biebee Isa💕 Gidan Gandu 🏠by 💕Biebee Isa💕by 💕Biebee Isa💕Biebee Isa💕Biebee Isa💕Zubewa tayi kan gado tana maida numfashi, lokaci guda taji ta tsani wannan rigar, ta tuna abun da ya shiga tsakanin ta da Ya Jawad, wayarta ta dauko. Ta latso Amal, ta na dauka ko gaisuwa babu, tace kizo ki amshi yan iskan rigunan da kika kawo mun, bana so wlh, Sai da Amal taci dariarta sosai kana tace me sukayi halan? Ta kwashe komai ta gaya mata, Amal ta ska wani dariar, tace lallai kam jawad ya fara dawowa hanya, karki damu ina nan zuwa da wasu kayan, dole muke qara haukatar da Jawad, Takaici ya sa fadila kashe wayar tana bambamin masifa... Abuja Ringing Uku ya dauki wayar, ya duba Samir ne ke kiran, ya kalli patient din da ke zaune gaban desk dinshi yace just a minute pls, ya dauki wayar tare da fadin Hello Sam, Samir yace hey Zaid, ya ne? Ya iyali? Yace lfy lao ya aiki? Yace wlh fine, had to dump it tho, Zaid yace Meyasa? Samir yace Zamuje honeymoon neh da madam, ya fada tare da kallon Amirar da tayi kanar bata jishi ba, Zaid ya jinjina kai, lallai abun naka azimun, har aiki ka ajiye don Amira? Samir yace har abunda yafi aiki zan ajiye takan Lilsiswifey nah, Zaid yace daniska Sam ka zabure, yace va laifi na bane, So ne, yanzu dai ba wannan ba, Yimin texting adireshin gidanka ga mu a Abuja, don Gobe jirgin mu zai tashi, Gashi lilsis tace ba zata kwana a hotel ba ita dole sai gun Maysah, Zaid yace oryt ni dai ina Asibiti i will be closing by 2, but i will text u d address, ok bro, sukayi Sallama, nan take Zaid ya tura ma Samir Address din gidanshi. Samir ya nufa Gwarinpa basu sha wahalan gane gidan ba, Hannun Samir maqale da na Amira suka nufa cikin gidan bayan Maigadi ya tabbatar mai nan ne gidan Dr Zailani, Knocking sukayi a parlorn, Maysah tafito cikin sanyinta ta bude kofahn ihu suka sake me qarfih tare da qanqame junansu, Samir yace oh ni zaku kashe min kunne, Maysah tace Yasamir sannu da zuwa, lallai u suprised me, ba waya ai da na shirya tarabnku, suka shigo suka zuve a gado, ta gaida Yasamir, ya amsa tace Yazayd din na gurin aiki sai 3yake dawowa, yea dont worry munyi waya, shi ya min kwatance ai, ta miqe tace bari a kawo abinci, ya miqe yace noo nidai ga amanar baby na dai, Idan Zayd ya dawo Qila naxo, idan kuma ba tym sai gobe idan zamu wuce, Maysah tace tohm Ya Samir, tafiya zakuyi halan? Yace Honeymoon zamu ko lilsismeerana? Ta kauda kai, Maysah kuwa ta shiga tafi da kyau yayanah, yace yauwa qanwata, ki lallaba min lilsiswifey nah, tana fushi dani, Maysah tace ai ta yafe maka ma ta gama, yauwa bari na dan shiga garih, ya matso saitin Amira ya bata light peck a kumatu, yana fadin take care, Maysah ce ta rakashi har qofa, kafin ta dawo gun Amirah, kee whatd dat for? Sai shan qamshi kike kina shashare yasamir, me ya mikine?Amira tace ke kyaleshi, sai ynz ya mato kaina, da har kuka fa nake mishi don ya kulani amma ko a jikinshi, ynz kuwa lokacina ne da zan rama ta kwashe komi ta gaya mata, Maysah tace lallai Amira har yau kina da wauta, wallahi garin jan ajin ki zai zo ya tsinke ku koma gidan jiya, Mazan yanzu sai ana lallabasu, tunda har ya gane laifinshi ya kuma bada haquri ai sai ki bada kai bori ya hau, cikin mu 6 wa kika ga mijinshi na mai yanda Yasamir ke miki?Think, this is ur opportunity, Amira ta jinjina kai, tace toh shkn sis, kuma Allah ya karkato zuciyoyin mazajenku kanku, tace Amin, Wayar Maysah tayi qara, ta dauka ta duba Fati tahir ta gani, ta dauka hello guntuwa ya akayi, a bangaren fati tahir tace ke wallahi kizo skul, gashi nan Xaks yayi fixing lectures,nan da 30 mins kinsan halinsa sarai, maysah tace Oh Allah, toh gani nan zuwa, ta kashe tana cewa sis, zuwa skul ya kamani, wani lecturer ne yayi fixing lectures yanzu nd i have to go, Amira tace dont worry ai ina nan, yauwa sis make ur sef at home, akwai Abinci a kichin, tayi hanyar dakih don shiryawa. Maman diyya ce ta turo kofah tana yatsina, ta kalli Amirar da kallo daya ta mata ta watsar, maman diyya tace kee, wacece wannan? Maysah da murmushi tace kanwata ce, maman diyya ta tabe bakih, tace mekika dafa? Maysah tace jollof rice ne, ta yatsina fuska tace ki dafa min doya ki daka min sakwara, ni ba zan ci shinkafan nan ba, Maysab tace Mummy pls, lectures xanih, i need to attend it, Maman diyya ta wurga mata harara tace zakiyi ko ba zakiyi ba? Maysah tace kiyi haquri zanyi, Amira da ta zuba musu ido ta miqe tace yi tafianki Maysah, lemmie handle dis, Maman diyya tace keee, meye haka? Amira tayi murmushi tace Mummy lectures zataje, kar ki damu ni zan miki sakwara, da egusi kikeso ko? Tace eh, karki damu, Maysah muje ki nuna min kayan amfanin, Maysah baki bude take kallon Amira, mamakinta ya rufeta, Amirar ce tayi sannyi haka? Lallai kam aure ya chanza Amira, tace ok sis muje kichin din, maman diyya tace ki min sauri 30 mins na baki, yunwa nakeji, Amira tace karki damu Mummy, 15mins yayi yawa, Suka shiga kichin ta nuna mata komai, a gurguje Maysah ta shige dakih ta fito da jakka ta kalli Amira tace Sisi na tafi, thank u so much u really saved my ass, Amira tace dont mention, jus take care and take ur time kinji, oryt bye.. Amira ta shige dakin da Maysah ta fito, ta rage kayan jinkinta ta dane gado ta bararraje ta shiga sharar bacci. Maman Baddiya ta ji shiru, ta kalli agogo karfe 3:45, har an fara kiraye kirayen sallah laasar, ita da tace a mata sakwara tun kafin qarfe daya, Har ynz shiru takeji, ko alamun daka bata ji ba, ta miqe dai ta fita parlorn, ta kalli Dinning, kulolin dazu ne, ba ta yi qasa a guuwa ba ta qarasa ta bude kular, jollof rice din da Maysah ta girka ne, tayi tsaki ta nufa kicin, ba alamun an fera doya balle an daka, ta gama dube dubenta bata ga wani abu me kama da sakwara ba, ran ta yayi mutuqar baci, ta fita kamar zata tashi sama, ta banka dakin Maysah, Amira ta gani kwance ta na sharar bacci, ta matsa gadon ta daka ma mata duka a baya ke don kutumar ubanki waye tsaranki?ni zakiyi wa bariki, Amira ta tashi a firgice tana mustsutsuka ido, tace lafiya? Nace don ubanki ina sakwarar da kika ce zaki man? Ke bakiyi min ba kin hana a yi min, idon amira ya qeqeshe, ta kalli Maman badiyya tace ke dai banza ce wlh, harbkin yarda xan miki sakwara? Yo uban waye bawanki da zakisa aiki? In ba zaki ci abin da aka girka ba ki barshi, ke in banda abun kunya kinzo ki tare gidan diyarki har kina sa Matar gida aiki, wallahi Maysah kika samu, Ki gode ma Ubangiji da ba nice matar Zaid ba, da sai na shayar dake madarar mamaki. Baki bude maman diyya take kallon Amira, ba ta taba zaton zata iya gaya mata magana haka ba, ta zata itama kamar Maysar take, ta ma tsorata da alamuran Amira, yarinya qarama ta ke gaya mata magana haka? Ai ko yau zataci uban yarinyar nan, sai ta saukar mata da duk abunda ke kanta, tace ke yau sai naci Uban Babanki, amira ta kalleta tace Uban babana? Tsoho kenan? Maman diyya tace shifa shege Maye, ai muna da labarin Musbahu Zailani bokan zaure ne, shege tsohon banza, yau sai naga uban da ya tsaya miki, Don uban-ba ta qarashe ashar din ba Amira ta daddage ta kamtse maman badiyya da mari, bata gama tunanin ko marinta akayi bat ta qara jin wani marin, ta dago kai ta kalli Amira, kika mareni? Ta ko qara mata wanih, ta dafe kuncinta ta sake ihu waiyo na shiga uku tace jamaa ku taimakeni jikan Mayu sun kamani, jikar Zailani, Amira ta daga hannu zata qara mata wani marin Maysah ta shigo da gudu... _Bibilicious Biebee_ 4⃣7⃣ 🏡GIDAN GANDU🏠by 💕Biebee Isa💕Gidan Gandu🏠by 💕Biebee Isa💕by 💕Biebee Isa💕Biebee Isa💕Biebee Isa💕 Ganin Maysah be hana Amira kara ma maman badiyya wani marin ba tare da nuna ta da yatsa, tace ki ka qara cewa tak sai na lakada miki dukan tsiya, da sauri maman Badiyya ta riqe bakinta don ta fi danganta Amira da wadda ke aiki da Aljannu, amma in banda Aljannu wacece zata kalli girmanta ta daga hannu ta mara har kala 5? Maysah da sauri ta janye Amira tace Haba Amira me-- shut d hell up amira ta katseta, tace ba a haifi uban da zai zagih tsoho gabana ban mareshi ba wlh, duk tsufan ka, ko da gemun ka na jan kasa ina iya kamtse ka da marih, ko waye, ni gwara a zage baba da a zage tsohonmu, sum sum maman maysah ta ja tsamin jikinta ta bar dakin kar ta qara jin wasu yatsu biyar a kumatunta, Maysah tace yau na bonu! Amira kin san me kika ja min? Allah kadai ya san me zai faru idan diyarta ta dawo, amma Meerah be kamata ba-- Amira tace Maysah i told u to shutup dint i? Wai ke me ke damunki? Kina gidan mijinki amma baki da maraba da er aiki, ke baiwarsu ce? kin tsaya suna juya ki, toh wlh idan zaki kwatar ma kanki 'yanci ki kwatar, in ko ba haka ba, duk sharar da suka dibo kanki zasu zubar tana kaiwa nan ta shige toilet don watsa ruwa. Tare suke da Alh. Haladu a wani hotel sun gama aikata sabo, qarar wayarta taji, ganin mamarta ne ya sa ta sake tsaki ta dauka, hello mama, ya akayi ne? Ji tayi maman na kuka, Badiyya ba lafiya, yanzu na sha tagwayen mari kala 3, badiyya ta zaburo, wani dan abun uban ya mareh ki? Nidai ki dawo, ko nayi tafiata, Badoyya ta miqe a gurguje tace ma Alhaji haladu zata je gida Emergency ne, be bi baasi ba ya ciro bandir din 1000 yace zasu yi waya. A sittin ta shigo gidan, tayi dakin mamar, Zaune ta sameta zaune kan gado Fuska ya suntume ya kumbura, fuskar tayi jaaa, Mama me ya sameki? Waya miki rauni a fuska? Tace Wata ce ta zo gurin Rumaisah, Badiyya ta shirga uban ashar tare da kwabe dankwalin kanta ta ci dan mara, tayi hanyar fita, tace kul badiyyah, Wlh yarinyar nan ba ita kadai bace, Tare take da Aljannu, mama ba Aljannu ba Allah ya sa Almatsutsai ne sai na ga uban da ya tsaya musu a gari Abuja, ta fita tayi dakin Maysah, Amira na zaune tana shafa, Maysah na Sallah, ta sa kai tana sujjada Badiyya ta fincikota, ta maqureta, Amira tace ke karuwa, bakisan darajar Sallah bane da ba zaki iya bari ta idar ba ki mata ko me zaki mata? Au na manta fa ke jahila ce, Badiyya ta juyo ta kalli Amira da bata fasa shafar hodan da takeyi ba, tsaf ta ganeta, yarinyar da ta taba mata rashin kunya ne wata rana da taje neman Zaid a Maid. Amira ta rufe powdern ta ajiye, tace ni kike nema, ba Maysah ba don kamar nice na mari uwarkih kamae so 5 ne ko 6 i cany remember dai? Ta kalli maman Badiyya da ta labe a bakin kofah ta kasa shigowa tace, Mummy mari nawa ma na miki? Badiyya ta sake Maysah, tace Amira kike ko uban wa? Karon mu na farko na qyaleki, wannan kuwa zan nuna miki ni ba saar ki bace balle kuwa uwata, ta matso gadan gadan ta nufi Amirah, Maysah tayi saurin riketa Aunty Badiyya kiyi haquri, laifina ne, wlh laifina neh, ni zaki hukunta, Amira cikin fushi tace Maysah kinci ubanki, ki kyaleta muga abun da zata yi mana? Da alamu tsautsauyi yake niyyar kawota kusa danih, jin haka yasa maman badiyya zuwa ta kama diyyarta, badiyya ya isa, na gaya miki yarinyar nan ba ita kadai bace, ni wlh na yafe, Allah kadai yasan abun da zata miki, Nan Badiyya ta tirje ta shiga bambami da ihu da masifa, mamar ta riqeta gam. Tunda suka shigo gidan suka san cewa va lafia, da sauri Zayd yayi parking ya fito, Samir din ma parking din yayi suka shiga da sauri, Dakihn Maysah suka nufa, ganin maman Badiyya riqe da ita ta na tirjejen a barta ta bige Amira ya sa Zaid zuwa ya janye Badiyya, Shima Samir ya janye Amira tare da rungumeta, a hankali take sakar da ajiyar zuciya, Maysah kuwa sai kuka take tayi, Zaid ya ce Sam matarka is unstable, ka kwasheta ku tafi, kaga yanda ta maida min gida? Samir ya kalli zayd ya wurga mai Harara, yace ka dai san waye unstable not my wife, ya dago Amira dake kwance a kan kirjinsa yace meerah na me ya faru? Ta dago ta kalli Zaid tace Kalli fuskar sirikar ka, ba gardama ya juya ya kalli fuskan maman Badiyya da ya kumbure, yace subhanAllah Mummy me ya sameki? Badiyya tayi caraf tace marinta fa tayi Zaid, Zaid yace Mari?? Amira tace ba daya ba, marirrika ta sha, kuma ko yanzu ta sake yin abun da tayi zata samu fiye da haka, Ran Zaid ya baci, ya kalli Maysah cikin tsawa yace ke kika sata koh? Kuka ta keyi ta kasa cewa komai, ya kalli Samir yace Sam ka ga abun da nake ce ma ko? Ka hukunta matarka ko ni wlh na hukunta ta, ba zan dauki raini , ba zan yarda a rai na min Iyalina ba, don rashin kunya ki daga hannu ki mari someone that is old enuf to b ur mother? Samir yace Easy mana zaid, ai ba mu ji meye dalilinta ba, ya fuskanci Amira yace lilsis tell me what happened? Cikin rashin tsoro ta warware musu komai tun bayan tafian samir har zuwa yanzu. Ran Zaid yayi mumunan baci, fita yayi daga dakin ya fada dakinshi, Ran Samir ya baci ya kalli Maman Badiyya yace ki gode ma Allah ba a gabana kika zage tsoho ba, wlh da yanzu kina kwance gadon Asibiti ya kalli matarshi yace lets go ya fita shima. Amira ta kalli maman badiyya tace dis is wat happens wen u mess with Musbahu Zailani ta suri jakkarta ba tare da ta kalli Maysah ba tace mun wuce. Badiyya ta fice daga dakin maman ta bita a baya. Maysah ta zuve kan gadi tana kuka a hankali.. ****** Mama me kike tunani da kika zagen musu kaka haka? Kinsan me kikayi kuwa yanzu? Kinsan yanda suke son wannan tsohon? Ai ko mahaifansu ba sa son su kamar yanda sukeson tsohonsu, yanzu shikenan kin ja min, Zaid yayi fushi, Mamar Badiyya ta kalli diyarta tace kiyi haquri, ban ta ba tsammanin abun nan zai juye ya koma haka ba, indai Zaid ne ba matsala yanzun nan ba sai anjima ba zai sauko, ta miqe ta dauko wani turare ta bata tace ta shi ki shafa kije gunsa, ina tabbatar miki da cewa sai yadda kikayi dashi. Badiyya tayi shewa tace woo mummyna shisa nake sonki, ta miqe ta fada toilet don gyara jikinta kafin ta nufa dakin Zaid.. **** Tunda daga kofar dakin ta ke cin karo da kwalba da gwangwanin giya, Hakan ya tabbatar mata da gogan nata ya sha giyarsa yayi tatul, don ta san fushin da ya dauka giya kadai ce zata kwantar mai da hankali, chan kusurwa ta hango shi yana baje, idonshi lumshe amma ba bacci yakeyi ba, tun kan ta qarasa gunsa yaji wani qamshin turare, da sauri ya bude idonsa, Giya ce ta fara gaya mai karya, ganin badiyya yayi ta rikide ta koma mai Maysah, da sauri ya fincikota ta fada jikinshi, ya shiga sarrafata, badiyya abin nema ya samu ta biye mai suka lulu duniyar maaurata. What?? Alhaji Haladu yace cikin kidima, Jawad aka ba contract din da nake expecting? PA dinsa yace eh yallabai, yanzu ma yazo refinery yayi signing contract din, yace zai tafi in 10days time, Zufa ya shiga tsatsafo ma Alhaji Haladu, Yaron nan na so ya shige gaba na? PA yace ai Alhaji daga sama ne abun, ni ya kamata naje Amsterdan, aka ce na barshi ya za a ban contract din Niger-Delta na barshi ya tafi don na san zan fi samu a na Niger Delta din, yanzu kuma sai ace shi zaije to wlh ba zai rayu ya ga wannan ranar tafian nashi ba, wlh ba zan barshi ya dakushe min tauraruwata ba, yaro kankani ya shige gabana ba. Wayar sa ya lalubo Gambo Kisa Gayu, ringing biyu ya dauka hello ya Alhaj, be tsaya sauraron kirarin da ya saba mai ba yace kana ina Kisa Gayu? Wlh gani Damaturu ina wani operation ne, kayi maza ka zo kaduna Gobe Goben nan, kaii Alhaj anya zan iya zuwa? Gaskia ina wani dan aiki ne zuwa jibi ko gata zan diro,Ni ka dawo gobe ko nawa ne zan biya ka, yace Alhaj kayi haquri ka bari har na dawo, idan kuwa emergency ne sai na turo ma yarana, Aa Kisa gayu na fi yarda da aikinka, na baka nan da kwana 3, yace lafia lao lokacin na gama komai anan, me kakeso ayi ne? Yace Akwai wani yaro da ya shige hancina ya qudundune, yaron da ya hanani rawan gaban hantsi, wai shi Jawad Zailani so nake a min maganinshi, Yallabai me kake so a mai me? Yace so nake a kasheshi.. _Bibilicious Biebee_ Gidan Gandu 4⃣8⃣ Gidan Gandu by 💕Biebee Isa💕Biebee Isa💕Biebee Isa💕 tohm zanyi qoqarin dawowa da wuri, idan ban samu damar dawowa ba, zan turo ma yarana, suma kwararru ne, Alhaji Haladu yace banso a samu matsala, yace Kar Ka damu Alhaji, sai dai kaji daga gareni, a haka sukayi Sallama, Alhaji Haladu ya tattara kayanshi ya wuce Kaduna.. Lagos Zuciyarta ta amince da Shawarar da ta ba kanta, inda zuciyar k ce mata, ta manta komai da ya faru a baya, ta rungumi mijinta, tunda be da wani aibu, hasalima shi ke biye da ita, ita kuma na wulaqantashi, ya kamata ta zage damtse wurin kyautata wa mijinta, tunda har ya kai ga shaawar sake wani auren, kuma har ga Allah kyautata mata da yakeyi zuciyarta ta kamu da sonshi, son da ba ta tunanin ta taba ma wani mahaluki irinshi. A yau tayi niyyar faranta Ran Mijinta Zayyad, Yau zata Roke shi gafarar abubuwan da ta mishi a baya, da sauri ta tashi ta shiga kicin don daura abinci, Watanni takwas kenan da zuwanta legas ba ta taba yin abinci don Zayyad ba, yau kuwa gashi ta shiga shirya mai kayan dadi, sai da ta gama fried rice dinta da fried plantain, kafin ta yi pepper chicken dinta, wurin karfe 1:30 ta shirya komai kan dining, da sauri ta fada toilet don yin wanka, ba jimawa ta fito, ta shirya cikin wasu riga da skirt na atamfar hollan da ya yi matuqar yi mata kyau, rabon da ta shafa kwalli a idonta har ta manta, yau ko Hanifa har da kwalliya, ta feshe jikinta da turarruka masu kamshi, ta kashe daurinta, hanifa tayi kyau har ta gaji, kallo daya zaka mata kasan tana cikin nishadi. Karfe 2:30 taji horn din shi, da sauri ta leqa window, shi din ne, sai yanzu ta qare mai kallo, Zayyad kyakyawa ne gashi da kyan zuciya, ita kanta ta san YaZayyad yayi haquri da ita, shisa yau takeson faranta mai, don runtse ido zatayi ta rungumeshi, da sauri ta fita daga dakin, ta zo fitowa kenan santsin tiles ya kwasheta da sulbe ta fadi ta gurde kafa, Azaba ya hana ta sake ihu, amma hawaye tuni ya fara sunturi. Shigowa yayi da Sallama, idonsa ya sauka kan hanifa, da sauri ya qarisa gunta ya na tambayan lafia? Kasa magana tayi, hawaye kawai take iya, fadiwa kikayi? Sannu kinji tashi, ya danyi yunqurin ta da ta, ta saki ihu me qarfi, Yaya kafana, Me ya samu kafan? Ya kalli Kafar ya ga ya dan jirkice, nan ya fara salati ya rude iya rudewa, sabarta yayi kamar wata baby ya kaita daki ya shimfide kan gado, yace sannu, bari najeh na siyo Robb ko Deep heat na shafa miki kinji? Ta kasa cewa komai, da gudu ya fita, ba ayi minti 15 ba sai gashi ya dawo, da Magunguba cikin leda, Ya dibo maganin zafin ya shiga shafa mata a qafa a hankali, ita kuwa sai ihun kuka takeyi don Zafin da takeji, sai da ya shafe mata kafa da robb kafin ya ballo Ibrufen pain killer da wani sleeping pills, ya bata ta sha, sannan ya shiga shafa mata kai yana cewa sannu kinji, try nd have some sleep, cikin kuka take cewa Yaya Abincin kan Dinning, da sauri ya kalleta, mamaki ya rufeshi, amma har a ranshi ya ji dadi, yau shine da abinci?Lallai kam Allah na gode ma, yace karki damu Hanee, zanci but sai kinyi bacci, bata tsaida kukanta ba har bacci ya kwasheta.. Kano Tunda ta gano gaskia game da YaSuraj ta kulle kanta ta shiga tunani, ta fuskanci son da

Chapter 13 of 20