kimtsa ko'ina
Bayan kin san da Abih ya fada da ihu ya fada a nasiha cewar ba zai taba bari a daukar mana yan aiki ba har sai mun tara y'aya? Ban san nufinsa a kan hakan ba ni sam
Najeeba ta ce" ban ga aibu ba dan mun gyara datin da muka bata tare da kai! Maza da suka amsa sunnayensu na maza
Mazan da suka rayu da adini a jikinsu, sukan taya matayensu aikace aikacen cikin gida
Bana gannin walwala da sabo a wajen namijin da zai gimshe min fuska shi ga mai gida ni ina dauke cen goge cen gyara cen wanke cen shi ko gani baya yi bale ya yaba
Aunty ni zan koya masa sannin zafina, ya kama min mu taru mu rufawa junna asiri
Kina son sannin dalilin Abanki na hanawa a kawo maki yan aiki? Ba komai bane face shi burinsa ki gina gidanki, ki shaku da mijinki, ki san kanki ki san wa kike aure kafin a kawo maku masu sangartar da ku ta hanyar kuna zaune kafa mike ku ringa saka su dauko maku ruwa, kawar da plat din abincinku
Zahrau ta zauna bayan ta jefa mata tsintsiya ta sauke ajiyar zuciya a hankali ta ce" nima na so haka a tare da ni sosai
NAJEEBA ta duka ta shiga share dakin tana dukawa har kasan bed dinta kasancewar kasansa a bude yake tana sharowa sosai ta dago tana dubanta
Murya a sanyaye ta ce" bai zama lale ki amincewa rayuwar gidan sarauta ba! Bai zama lale ki auri mutumen nan ba
Farin cikin ki na gaba da komai
Idan har zuciyarki ta ki amince maki da hakan ba dole bane!
Dan murmushi ta yi tana share dan karamin cafet din wajen ta dan dago ta ce" sannan kina iya mayar da lokacinku naku wanda zaki saka sarkin Agadez shara a daka, a lokacin da ba masu yi maku hidima, babu idannuwan bafadanku
Ta karashe tana kashe mata ido da yannayi na shakiyanci
Daria ta yi tana girgiza kanta , NAJEEBA ta ce" namiji, ya kasance namiji a gaban wasu bakin fuska, aman amini a cikin gidansa
Zahrau ta karkato sosai tana dubanta ta ce" ta yaya? Ta yaya kike tunanin zan iya aiwatar da wani abin da zai zo masa sabo a rayuwarsa?
Ke kin sha gannin vidion gimbiyarsa inda take takun kasaita, wuyanta hannayenta kafarta dauke da zinari
Kin ga irin yanda take zuba kudi
Ke kin ga kalar fatarta kin kuma ga kalar kyawunta
Bayanta akoy wata guda dake taka rawarta itama
Wacece ni da zan iya jerawa da su? Kin ga kalar fatana bak'a ce,
Bani da wani kyan da zan iya dukan kirjina na jera da matan nan
Jikina ke mutuwa NAJEEBA
NAJEEBA ta yi sakalau tana kallonta
A hankali ta ce" da ba dan ke yayata bace, da sai nace ki tashi ki fitar min a dakina domin a duniyata bana son macen dake raina kanta ko wacece!
Muryarta ta dan daga tana kallonta da tsintsiya a hannunta ta ce" shine me dan kina bak'ar mace? Ita bak'a ba zata je gidan sarauta ba kennan sai fara? Kin manta halayan mace ke siyan mata mutunci idan mutuncin ne , soyaya idan soyayar ne?
Meye aibunki a jikinki meye baki da shi?
Meye laifinki a fuskarki me ya gaza na mace?
Kina nufin fatar naki ce ta fara baki haushi a yanzu kuma bayan mun kasance masu takama da kalar fatarmu?
Bakinta ta turo ta ce" kudi kuwa, kudi aunty, kina tunanin sunna da wata matatsa ne ta fi aljihunsa?
Zaki amshi kudin mijinki da dabara ki kashe da hikima ba tare da shi kansa ya gundura da tunanin kina da kashe kudi ba
Wani gwauron numfashi ta sauke tana kallon NAJEEBA , idan Najeeba na fadi sai take jin abin ba wahaka, sai ta shiga aunawa sai ta fara tunanin anya kuwa? Anya hakan zai zo da sauki kamar yanda kanwar nata ke fada?
Wayarta dake saman bed din NAJEEBA NE TA FARA KUKA
duban wayar suka yi a tare
NAJEEBA ta dauko tana kallon number
Zahrau ta ce" waye?
NAJEEBA ta daga kafadunta ta ce" nima ban sani ba ba sunna ai
ZAHRAU ta juyar da kanta ta ce" tun da safe ake kirana da number ko ba mai 00 karshe ba?
NAJEEBA ta gyada kanta tana kara kallon number
A hankali ta ce" aman number nan batai kama da irin number yan cenken numbobi ja
Tana fada ne tana dagawa ta kara a kunnenta
Dan shirun da akai yi ne ya saka Najeeba kuma kallon number ta ga ba'a kashe ba
A handsfree ta saka ta ajiye sannan ta yi mata nuni da su yi shiru
Sharar da take ta ci gaba da yi tana gyarawa da kyau
Sai da ta gama sharar ta kwashe ta zubar ta dawo ta shiga ciciro kayanta tana gyara masu ninkinsu tana mayarwa a muhalinsu
Wata kamilaliyar murya ce ta yi magana kamar haka" Asalamu alaiki gimbiyana
Dan shiru ya yi kafin ya dora da fadin" ki ja ajinki da kyau sarauniya ....aman yaya aka yi baki nemi number mijinki kin ji inda jirgi ya wurga maki shi ba?
A tare suka zazaro ido a lokacin da suka fahimci mai sanyaya maganar nan ba kowa bane face sarki
Wata wuntsilowa Zahrau ta yi tana kara firfitar da idannuwanta
Da gudu NAJEEBA ta warto byro da takarda ta janyo wayar tsakiyarsu
Da wani irin sauri ta yi rubutu sannan ta nuna mata
Sai da ta sauke ajiyar zuciya sannan ta sanyayar da muryarta sosai da sosai kafin ta ce" amincin Allah ya tabata a gareka
Murmushin manyan mutane ya yi jin da kyar dai ya samu jin muryarta a karo na hudu tun bayan nemawa Zinaria afua, da godiyar da suka yi masa
Ya tabata yarinyar ba sai an bata lesson din jan aji kafin magana ba, da alama saraurar a jinninta take ba sai an koya mata wani abin ba
Shima shirun ya yi mata, domin shi dai ai sarki ne abin nan a jinninsa yake ba wai hawa ya yi daga sama ba
Wani rubutun ne ta nuna mata dan haka a hankali ta yi dan murmushi ta ce" yaya hanya? Ya gajiya?
Shima murmushi ya yi kafin ya bata amsar cewa" gajiya ba zata kau ba sai na kilace ZAHRA
ZAHRAU ta kuma zaro ido hakama NAJEEBA
Da gangan Najeeba ta rubuta " to wai shekarunka nawa?
Ta nunawa Zahrau
Allah ya taimaketa sai ta karanta take maimaitawa dan haka bakinta ta cije tana wurgawa Najeebar fillow
Lokaci daya ta ce" NAJEEBA bakya jin magana walahi
Murmushi ya yi jin kamar kokowa suke, shima ya maimaita sunnan Najeeba
Zai iya cenko ko wacece Najeebar nan, yana ga itane wace suka fiya dunguri a boye idan sunna tsaye tare da yan uwansu
Tana mintsinnin Najeeba tanai mata cakulkuli ne tana fadin" baki da kunya Najee mijin nawa zan yiwa wannan tambayar?
Sai kuma ta yi dif ta yi saurin kallon wayar
Da wani irin sauri ta sauka tana fadin" na shiga uku, da sauri ta warci wayar ta kashe tana zaro ido
Shi kadai ya ringa daria a bayane na kuruciyar yaran,
Da yake ya shigo hutun yama ne sai kawai ya rubuta mata message ya tura sannan ya ci gaba da abubuwan da yake
Da mamaki ta ringa bin message din da kallo, hakan da suka yi bai bata masa rai ba, saima magana irin ta tsokana
Dama saraki na da raha haka? Ta kuma tambayar kanta
Da baya baya ta fada saman bed din tana daria, a hankali ta ji dan tsoho na raf da zuciyarta..............
.............................................
Sannin cewa a gobe zai yi zaman fada ya saka shi gama komai nasa da wuri sannan ya kwonta saman bed dinsa ya shiga jan carbi
Ta shiryawa yauma, ta gama sabawa da irin jarabarsa hakan ya sa a yanzu idan bata ji shi a tare da ita ba take jin sam ba dadi
Tana wani irin kishinsa wanda ya zarce misali bale a matsayinsa na sarkin garin ta tabata ko tana so ko bata so wata rana sai wata ta so shiga rayuwarsu
Abinda ba zata iya aminta da shi ba kennan
Irin yanda ko mahaifiyarsa take jimawa bata ga kalar fuskarsa ba bale wata cen yar banza ta gane mata sirrin dake haukata zuciyarta a kansa?
Tana godewa Allah da yake rufe fuskarsa wanda mutane da yawa sai dai su shaida hotonsa aman basu taba ganninsa a fili ba
Wannan na kara daukaka darajarta ko a cikin gidan sarautar cewa itane macen dake gannin fuskarsa a duk lokacin da hakan ya raya mata
Salama ta ringa yi, a hankali ya amsa mata ya maida kansa ya ajiye
A hankali ta ringa takawa dan karasawa wajen da yake sai dai bata kai ga idasawa ba ya dago ya sauke idannuwansa a saman fuskarta wanda hakan ya saka ta ja da sauri ta tsaya tana jin gabanta na faduwa
Me ya bata masa rai? Irin kallon iyakantarta da shi kennan
Gabanta ne ya yi wata irin yankewa ya fadi, tsoro ta ji kan kar dai a je mahaifiyarsa ta fada masa cewa ita ta fada mata ta ji kamshin turaren da ba nasa ba a jikin rigarsa?
Gannin ya koma ya kara kwontawa ya saka jin kafafuwanta sun fara yi mata rawa rawa
A hankali ta juya ta koma falonsa ta zauna hankalinta tashe tana jiran fitowarsa ta ga idan zai amsa gaisuwarta?...................
Kansa kawai ya dan girgiza ya maida ya ci gaba da jan carbinsa
A ranar NAJEEBA bata fita saloon ba, sai washe gari wajen karfe goma
Ta gama shiryawa cikin tsararan shirinta
A yau riga da sket ta saka na atampa
Bata daura dan kwalin atampar ba sai wani dan kwali ja irin takalmin kafarta da jakarta ta dan yafa a gefen kafadarta
Hannunta dauke da agogo dan siriri yatsotsunta kuwa basu da zobe ko daya
Kanshin turare take bazawa mai dadin gaske ga turaran wuta da ta turarawa kanta sosai take baza dadadan kamshi
Ta zo tsakiyar gidansu ta hadu da yar kanwarta wace ita daya ce ta rage a gidan sauran du sun tafi makaranta masu aiki sun tafi aiki, itama dan karama ce
Murmushi ta saki ta karasa wajen yarinyar ta duka ta dagota tanai mata wasa
Yarinyar kuwa sai daria take tana dora kanta saman kirjin Najeebar
Najeeba ta duba kitson kanta ta ce" heyi an mata kitson nan ya tsufa mu je saloon a tsefe shi a sake sabo
Daga nesa da su kadan ta ji muryar matar babansu na fadin" kar ki daukan min y'ata ta saka ta ringa ramewa dan datin dake jin ki! Ajiye min yarinyata malama
Dagowa ta yi tana kallonta
Ta ga tana fadi ne tana nufota wato zata zo ta amshe yar
Mikewa ta yi da sauri ta sungume yarinyar ta karasa wajen motarta wace ta sha wanki dan da sasafe dan saurayin mai gadin ya amshi kys dinta ya wanke mata ita tas domin Najeeba nada kyauta sosai hakan ya sa kowanensu ke son kyautata mata koda bata nema ba
Cikin motar gidan gaba ta saka yarinyar ta rufe ta koma ta zauna itama ta rufe motar
Sai da ta danne horn sannan ta tayar ta yi baya baya da matsiyacin gudu wanda take hango matar baban nasu na ihun ta bata y'arta aman ta tabe baki ta fita a gidan da baya baya
Gashin kanta ta take birki ta nade shi dan ya fara damunta sakinsan da ta yi sannan ta dauki hanyarta tana tukin tana yiwa yarinyar wasa
Cikin nutsuwa ta karasa kofar shagonta
Sai dai irin motocin da ta gani ya sakata dan yin tsam tana bin su da kallo
Tas ta gane motar dake gaba ba motar kowa bane face ta matar Ambasador domin motar tare ya siya masu ita tata ta siyar dan su yaya ba zasu barta hawa motar kato haka kawai ba
Dama sun taba message da junna inda take mata kashedin bin mijinta har tana kiranta cewa" an koro su daga kasarsu sun zo sun samu arziki sunna bibiyar mazan mutane, abin ai gado ne ga kanwar ubanta ta amshe sarki kiri kiri , ga mamanta ta tafi yawon neman kudi ko karuwanci ba!
Hannayenta ta hade ta dan murza su, ta dauko turaranta ta kara fesawa ta kara gyara girarta sannan ta dauko kanwarta tana kara yi mata wasa ta fito daga motar aman bata dauko jakarta ba dan kayan hannunta sun mata yawa
........cikin nutsuwa take takawa har ta karasa kofar shagon.................
Hannunta ta saka ta kwonkwasa dan a bude mata tana kara kallon kofar shagon ta ga tsaftarsa ta yi mata sosai
Sai da ta yi murmushin dama ke nake jira ta kalli kawayenta ta nuna masu da bakinta sannan ta mike bugudum bugudum bugudum ta karaso wajen kofar ta dora hannunta ta............
[1/20, 9:50 A M ] U m m u S u h a n =?
?: >?????>?????>?????>?????>?????>?????>?????>?????>?????>?????
* M A G E *
_ ( M a i k w a n c i y a r d ' a u k a r r a i ) _
>?????>?????>?????>?????>?????>?????>?????>?????>?????>?????
* N a *
* S A J I D A *
=ث?(' * T A U R A R I N M A R U B U T A N N I G E R ( A S S O . ) * ?
_ ( T s i n t s i y a m a d ' a u r i n k i d ' a y a ) _ >??
& * [ T . M . N . A ] * & =???=؊??
h t t p s : / / w w w . f a c e b o o k . c o m / T a u r a r i - m a r u b u t a n - n i g e r - 1 1 1 7 7 3 5 6 0 6 7 7 0 0 3 /
_ B i s m i l l a h i r r a h a m a n i r r a h i m _
1 2
B a k i n s a y a b u d a z a i y i m a g a n a , s a i d a i t a rigaye shi ta hanyar juyawa ta waiwaya ta kuma juyowa wajensa
A rikice take, hankalinta a tashe yake hakan ya sa a hargitse ta nuna masa motar ta ce" zai zai taba min jikina
Idannuwansa ya kausasa yana dubanta,
Sai da ya yi iya yinsa ya kara matse damatsunnan hannayenta dake cikin dafin hannayensa ya ce" ba abinda ya kawo ku nan kennan ba?
Magana ne ya yi mata a kausashe, a kidayance ,
Iskar bakinsa dake kusa da ita sosai ne ta fito ta daki hancinta
A hankali ta lumshe idannuwanta tana jin zafin rikon da ya yiwa hannayenta
Kanta ta ringa girgizawa da sauri ta ce" aa, aa, ni ba yar iska bace
Idannuwansa da sukai ja ya kai dubansa wajen motar, gannin na cikin motar na kokarin fitowa ya saka shi yi mata wani ja tamkar ya ja dan karamin yaro sosai
Sai da ya kara yin cikin duhun da ita ya sasauta mata rikon karshe ya saki hannayen nata
Da yake ya jima cikin wajen, ya fita ganninta sosai duba da ita a rikice take sai abin ya mata yawa take ta neme nemen inda zata saka ranta
Bakinsa ya tabe ya juya da sauri zai tafi
Da wani irin karfi ya ja ya tsaya hakan ya sa ita da ta tarbi gabansa dukan kirjinsa da goshinta
Hannunta ta kai gaban goshin nata tana sosawa a hankali ta ce" aushhhhhh
Tsayawa ya yi kawai yana kallonta
Sai da ta sosai sannan tana dubansa ta ce" dan Allah ka taimaka ka fitar da ni daga wajen nan, walahi ban taba zuwa ba kar wancen mugun ya cin min
Ji yayi gaba daya ta gama raina masa wayo, itane take gudun kar namiji ya cin mata? To ko ta danfaro shi wasu kudade ne take gudun ya kamata ya amshe?
Sai dai irin kallon da yake mata zai iya gannin yar karamar wayarta a jikinta ta cikin rigarta sakamakon rigar a matse take sosai
Bayanta baya gannin kudi ko abin kudi idan dai ba a cikin sket dinta ta saka ba
Shi zata kalla ta rainawa hankali?
Kansa ya girgiza ya ce" ba saurayinki bane?
Najeeba bata taba zuwa wajen nan ba, sannan zata iya rantsewa bata taba samun kusanci da namiji irin yanda Ambasador ya yi mata a yau ba
Hakan ya sa baki daya jikinta ke rawa takaici ya gama rufe mata zuciyarta
Hannunsa ya kai ya damki hannunta ya juya ya shiga janta
Bin bayansa kawai take
Bata san shi, bata taba haduwa da shi, bata san mutun ne ko aljan ba, bata san shima zai cutar da ita ko akasin hakan ba abinda ta sani daya ne tana son ta yi nisa da motar Ambasador
Tana so ta yi nisa da shi baki daya dan tana da muradin kasancewa ita daya
Gani take ko ina ta bi idan ta zo wucewa yana iya ganninta, gani take zai kuma yin yinkurin aikata mumunan aikin nan da ya yi na hada jikinsa da ita
Sai da ya fito bakin titi da ita ya saki hannunta
Juyawa ya yi yana tafia cike da wata irin kasaitar da ta sakata zubawa bayansa ido
Tsalaka titin ya yi wanda har sai da ta rintse idannuwanta sakamakon wani mai mota da ya so kade shi cikin ikon Allah maimakun ya tsere da sauri ko ya yi gudu dan tseratar da rayuwarsa sai ya zama mai motar ne ya take birki har hakan ya yi kara sosai
Tana buda idannuwanta ta ga ya tsalaka, bai kade shi ba mai motar ya leko kansa yana fadin" ka ga malan rai zaka yiwa kwombo? Ka wani hau bakin hanya kana tafe da takama tamkar *mai DAMAGARAM?*
idannuwanta ta yiwa luuuu ta ga ya shige kwanar hakan ya sakata daga kafarta a hankali tana gyara rufar lafayarta
Ta sha cika dare a shago dan takan kai har sha daya idan aiki ya mata yawa
Aman yaya DAYABU ke zuwa ya tarbota su tafi gida
Yau sai ta ringa tafia tana hankalce da mutane cike da tsoron daren
Da haske ko'ina ba wani duhu ya game garin ba
Mai mashin ta tsayar ta hau ta fada masa ya kaita anguwar gidan sarki
Yana kaita ta bashi mai akun nan guda dake bayan wayarta
Ido ya zaro ya ce" haba dai Hajia yaya zan samu cenjin wannan?
Bata yi masa magana ba ta juya ta nufi ciki tana tafe cikin nutsuwa
Baki da hanci ya saki yana kallonta har ta shige babar kwanar gidan sarki
A hankali take tafe tana jin zuciyarta na dokawa dan bata san yanda za'a yi ta samu shiga ba
Motar da ta hasketa ne ta sakata rintse idannuwanta ta rabe waje daya
Kusa da ita aka tsaya tana jin jikinta ya dauki rawa dan sam bata son aikata laifi a wannan waje
Wanda ya fito daga motar ya sakata sauke ajiyar zuciya
Da gudu ta karasa ta fada jikinsa lokaci daya ta saki kuka tana kara dora kanta a jikinsa
Kiransa Anmy ta yi cewa bata ga NAJEEBA ba, maza ya samo mata ita
Gabansa ne ya fadi ya shiga kokarin cireta a jikinsa sai dai ta ki bada dama tana kara shiga jikinsa tana hawaye
Muryarsa a cakule ya ce" NAJEEBA, meye? Me ya faru? Me ya same ki? Ke da wa?
Kukan take tana jin ciwo a ranta , gannin ya bambareta daga jikinsa tana kallonsa ta ce" yaya, me me yasa kowani namiji yake son nuna min shi dan iska ne? Yaya me ya sa suke son nunawa mutun iskanci?
Gabansa ne ya kara faduwa hakan ya saka shi kurewa fuskarta kallo
Muryarsa na rawa rawa ya ce" Najeeba, kar ki fada min abinda zan tsani kaina , kar ki fada min abinda zai sakani yin gaba da ke
Mutuncinki kika zubar?
Da sauri ta rintse idannuwanta dan jin maganar da girma sosai a kunnayenta
Sai kuma ta bude tana girgiza kanta tana kokarin rungume hannayenta a kirjinta
Hannunta ya kamo ya sakata cikin motar ya tayar ya juya cikin gidan
A hankali yake tafe har ya karasa wajen ajiyar motoci
Yana dakatawa ya kashe motar a hankali yana sauke ajiyar zuciya
Sai da ya sanyaya muryarsa sosai sannan ya ce" da me kike jiran ganni bayan kin ce zaki amshi abubuwan hannayensu?
NAJEEBA ke baki yarda sun san gidanku ba, wanda ya san gidanku ya tabata mai naci ne ya kai kansa gidanku
Najeeba ke baki yarda sun san kina da mahaifi tsayaye da kuma yayan da zasu ringa shaku ba
Najeeba, kin mayar da aljihunsu wajen wasanki , kin kware wajen iya juya tunaninsu su fitar da dukiyarsu su kashe maki
Dubanta ya yi ya ce" me kike jira? Me zasu so su kuwa a wajenki? Bayan sun san ba su kadai bane, sun kwana da sannin basa layin wa'inda zaki aura
Me zai hanna su yi tunanin iskancin kike so bara su nuna maki ba?
Kansa ya sada gannin ta kure shi da ido kuma harga Allah du ta fi su magana ga shegen karfi da idannuwanta ke gare su
A hankali ya ce" kin san wani namijin na nuna irin haka dan ya gane shin matar ya kilace ce ko matar a watse ce?
Wanin kuwa da kika gansa dama dan a watse din ne
NAJEEBA, shi irin haka a haka ake rasa na kirkin
Tsorona a haka na kirkin ya sulube maki ke kanki baki ankara
Hannunta ya kamo ya dago yana dubanta ya ce" idan kika kare mutuncin kanki, kon kare mutuncinki ne a farko, kin kare na y'ayanki, sannan kin kare namu
NAJEEBA, kin fito daga tsatson da ya yo sunna, Allah ya daukaka
Abu kankani ake jira karamin abu ya zaga gari
Shi yasa nake maku nasiha cewa ku kama kanku ku rike mutuncin kanku
NAJEEBA ta lumshe idannuwanta a hankali ta ce" ya, kai ka san ni ba yar iska bace ko?
Kansa ya daga yana dubanta
A hankali ta dantse lebenta na kasa tana jin ciwon abin a kasan zuciyarta
Dan kawai na so abin aljihunsu sai su so jikina?
Ta tambayi kanta da kanta
Sai ta girgiza kanta tana mai bawa kanta amsar cewa" da ya kare aikatuwa a duniya, da na gile shi da hakorina na kashe shege! Kudinka sai na ci idan har kana iya saki aman fa ba zaka zo ajiyata ba karya ne!
Hannun yayan nata ta kamo ta ce" zaka raka ni wajen Anmy? Kar ta min fada
Murmushi ya yi ya bude motar suka fita
Sunna tafe tana tsara irin abinda zata yiwa Ambasador, sai na ci ubansa na rantse! A haka har ta dauki alkyabarta da ta ajiye ta dora ta kara gyarawa suka nufi ciki
...........................................
Karfe biyu na dare
Alkyabarsa yake cirewa a hankali
Sai da ya cireta sannan ya shiga warware rawanin kansa
A hankali ya gama warwarewa sannan ya kama babar rigar ya sauketa
Sai wata riga dake ciki baka ta kama jikinsa sosai sai wandon shadar dake kasan rigar
Mikewa ta yi tana karasawa inda yake tsaye ya baiwa wajenta baya
Sai da ta dawo gabansa ta daga kanta tana kallon fuskarsa
A hankali ta kai hannunta wajen sajen fuskarsa ta dora
A hankali ta shafa tana kallon yanda idannuwansa ke lumshe
Hannunta ta saka ta shiga kokarin cire masa rigar sai dai tsayinsa ya saka sai dadafe take ta kasa cirewar
Dan murmushi ya sakar mata ya tayata ta hanyar rage tsayinsa
Rigar ta cire masa sannan ta kai wajen hancinta tana sinsinawa tare da lumshe idannuwanta
A haka har ta kai hancinta wajen bakon turaran da ta ji a hancinta
A hankali ta kara rintse idannuwanta jin yannayin kanshin Princsss a jikin rigar
Tana kallonsa ya shige bayi ita kuwa ta zauna saman lafiyaye tatausan bed dinsa da rigar a hannunta jikinta a mace ranta a bace hankalinta a tashe
Ya jima sosai a bayin kafin ya fito yana tsane ruwan wankan da ya yi
Turarensa yake shafawa yana hangenta ta madubin dake gabansa
Ya so ya yi nafila, sai fai gannin ta zo harka tana zaune har warhaka ya saka shi karasa kimtsa kansa ya saka kayan baci riga da wando mai dogon hannu sannan ya karasa saman bed din
Hawa ya yi ya kwonta yana kallon sama
A hankali ta karasa ta haye saman kansa ta dora kanta saman kirjinsa
Kamar wace take fada ta sada kanta sosai ta ce" Allah ya ja zamanin sarkina, Allah ya karawa mai martaba lafia da jisan kwana, Allah ya tsare mulkinka mai gidana
Idannuwansa kawai ya lumshe, bai san yaya aka yi yake jin kalaman nan a waje sannan ya ji su a dakansa ba, yana son jin wasu kalar kalamai na kulawa ba irin wadinnan ba masu zafi yake son ji wasu kala daban aman sai ya fita waje ya ji kirari ya dawo daka ya kebance da macen da ta fi kowa sannin sirin jikinsa wace suka rigaya suka zama daya itama sai ta bi shi da kirari
Hannayenta ta kai ta kashe wutar dakin, yar karamar dake gefen bedma ta saka hannunta ta kashe
Sannin cewa bai taba mu'amalantar mu'amala da ita da haske ba ya saka ita da kanta ke kashewa a irin wannan lokacin, kwarai ta fi kowa kiyasta sanninsa domin ba idannuwanta suke gane mata ba, jikinta ke daidaita mata irin girmansa
Idannuwansa ya lumshe yana jin kwarai yana da bukatar hakan,
A hankali ta shiga zamewa
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 32
Chapter 33
Chapter 34
Chapter 35
Chapter 36
Chapter 37
Chapter 38
Chapter 39
Chapter 40
Chapter 41
Chapter 42
Chapter 43
Chapter 44
Chapter 45
Chapter 46
Chapter 47
Chapter 48
Chapter 49
Chapter 50
Chapter 51
Chapter 52
Chapter 53
Chapter 54
Chapter 55
Chapter 56
Chapter 57
Chapter 58
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 9 Chapter of 58