tana ihun ni ni ni
Daria ta yi ta karkata ta nufi wajen mai Ice cream
Siya ta yi sannan ta sayan masu kilishi ta nufi wajen hutunta dan bata son komawa yanzu yanzu
Tun da suka tsaya daga inda yake tsaye yana hangen motar gidansa mitar Anmynsa har suka fito ta fitar da darduma ta kawo wajen da take zama ta shinfida
Wayarta ta kunna wakar hausa ta breaker ta ajiye a gefe sannan ta zaunar da Nusaiba dake dan rawa rawa ta buda mata takardar naman tana kallonta ta ce " sai kin ci wannan sannan ki sha ice cream
Ai kuwa yarinyar ta maida hankalinta ta fara ci din domin ice cream din shi ta fi so a bata
Kara gyara tsayuwarsa ya yi ya dan matso kadan dan jin abinda suke fada
Ta dauka ta saka a bakinta tana dan taunawa sai kuma ta ja tsaki a hankali ta furta" idan ya san wa'azin zumunci ko ya san na zalinci?
Sai ta yatsina fuskarta ta mayar da muryarta tamkar tasa wato ta sanyayar da ita ainun ta furta" meye ilar gaba a musulunci?
Ta murguda bakinta a hankali ta furta" yana magana tamkar mace, yanzu haka sarautar samunsa dai ta yi aman sarki ai zaki ne!
Idannuwansa ya zaro da mamakin wai ashe wannan abin du shi ake yiwa?
Kansa ya girgiza a hankali ya karaso ya zagaya ya zauna yana masu salama
Tun da ta gansa sai ta hadiye na bakin nata da sauri sannan ta cire hannunta daga cikin takardar tana mai binsa da kallon mamaki
Hannunsa ya saka ya dauki naman nan duda yana tunanin da wahala ya iya ci domin a rayuwarsa baya son dabi'ar cin abu a titi sam bai iya ba bai saba ba ya daure ya kai bakinsa bayan ya yi bisimillah
Yana ayanna idan ba shaidaniya ba me zai hada ki da kunna waka da dare a wajen nan duda da haske da kuma mutane aman ai ka kiyaye kawai!
Ita kuwa hannun nasa ta bi da kallo irin yanda ya dan jujuya naman sannan ya saka a bakinsa
Da mamakin rashin yi mata salama, da haye mata darduma uwa uba ya kamo kanwarta ya rike a jikinsa sannan ya ci mata namanta take kallonsa
Dagowa ya yi ya kai hannunsa ya danna wajen kashe wakar sannan ya hada idannuwansa da ita
Ido daya ya kashe mata ya dage mata gira daya hakan ya saka ta yi gagawar cire dubanta a kansa tana furta" meye wannan kuma kamar wani dan iska kana kashewa mutun ido, ko dau a yar iska ya daukeni?
Shi bai san ko kawance bana yi da mace farar fata ba shine zai ringa damuna shi wani garjejen fari, yo farin mutun ai sangarta ta kare a wajen, kayan tsantsane kawai
Dubansa ta kuma yi ta ga yana son bude ice cream din, hakan ya saka Nusaiba yin dare dare a saman kafarsa har tana masa daria tana nuna masa
Kai yaro, yaro, bashi da hankali, ta fada a kasan zuciyarta
A fili sai ta tsinci kanta da furta" Me ya sa kake saka kwali a idannuwanka sai kace wani dan daudu ko boka?
Kansa ya dago jin yanda ta yi tambayarta kai tsaye , abin sai ya zame masa wani banbarakwai, sai yake jinsa normal mutun kamar kowa
Tambayar baba ce, sannan ta rashin kunya ce
Aman sai ya ga ai tambaya ce dan haka sai ya mayar da dubansa wajen Nusaiba ya ce"
B o n j u r n o >?????>?????>?????>?????>?????>?????>?????>?????>?????>?????
* M A G E *
_ ( M a i k w a n c i y a r d ' a u k a r r a i ) _
>?????>?????>?????>?????>?????>?????>?????>?????>?????>?????
* N a *
* S A J I D A *
=ث?(' * T A U R A R I N M A R U B U T A N N I G E R ( A S S O . ) * ?
_ ( T s i n t s i y a m a d ' a u r i n k i d ' a y a ) _ >??
& * [ T . M . N . A ] * & =???=؊??
h t t p s : / / w w w . f a c e b o o k . c o m / T a u r a r i - m a r u b u t a n - n i g e r - 1 1 1 7 7 3 5 6 0 6 7 7 0 0 3 /
_ B i s m i l l a h i r r a h a m a n i r r a h i m _
2 4
M a y a r d a d u b a n s a y a y i w a j e n N u s a i b a w a ce ya hudawa Ice cream ya saka dan cokali ya dan dibo ya kai bakinta,
A hankali ya furta" kennan ba bambanci tsakanin abinda Allah ya zana da kansa da wanda mutun ke iya sakawa?
Da sauri ta kuro ido ta yi gagawar furta" astaghrullah
Shima yana kallonta ya ce" sabo na yi? Nifa tambaya na yi
Sai a lokacin ta yi kokarin tsurawa idannuwan nasa ido, sai da ta ji har tsigar jikinta na tashi domin wannan kwalin wani kwali ne mai matukar tasiri, kwali ne mai kayar da gaba da saka mutun sada kansa koda kuwa bai so ba, kwali ne dake matsayin fatar mutun ba wai saka shi aka yi ba , hakan ya sa wajen ke daukan du yannayin da cikin kwayar idannuwan ke da shi
Kwalin a yanzu kyalkyali yake duda hasken duhunsa ya dan risina sakamakon gajiyar dake tatare da shi
Da sauri ta kawar da kanta tana jin wata boyayiyar ajiyar zuciya na kwace mata har ta dan sosa gaban goshinta
Cikin nutsuwa ya kawar da dubansa shima a ransa yana fadin" marar kunya na so na ga shin ke bashi da karfin saka ki kasa kallonsa ne ko me?
Nusaiba dake wasa da ice cream din ta lakato ta nufi wajen bakinsa
Shi kansa bai yi jiran zuwan hakan ba domin ya kuma ciran kilishin nan da ya yi masa dadi a bakinsa yana dan taunawa a hankali
Kawo abin ta yi wajen sajensa tana son lakata masa a bakinsa sai ta lakata masa shi a wajen gemunsa
Idannuwansa ya dan zaro yana gannin abin ya bata daria, dan haka sai ya kalli Najeeba
Gani ya yi kanta na wajen wayarta tana dadanawa
Lakuta ya yi itama ya kai mata bakinta hakan ya sa yarinya ta ringa kaucewa ita wasa ne yake mata
A hankali ya ji zuciyarsa na tunzura shi kan ya yiwa yarinyar wasa, dan haka sai ya bada hankalinsa a hankali ya shiga yi mata cakulkuli
Ihun dariyar da take ne ya saka Najeeba dagowa da sauri tana kallonsu
Ido ta zaro gannin yanda Nusaiba ke zaune dare dare saman cinyar bakon mutumen da bata sani ba sai faman wangala masa daria take
Fuskarta ta hade ta ce" Nusaiba
Da sauri yar ta juyo tana kallonta
Najeeba ta ce" meye haka? Me na ce da ke? Bakya jin magana ko?
Da sauro ta sauka daga saman cinyarsa ta koma jikin Najeebar ta zauna tana kallonta ta ce" aunty ba zan kara wasa da namijin da ban sani ba, ki yi hakuri kar ki fasa yawo da ni
Bata kuma yi mata magana ba sai kokarin mikewa da take ta kama hannun kanwar tata
Bata bi ta kan Ice cream din, da naman da kuma dardumarta ba ta nufi motarta
Sai da ya dan bi su da kallo kafin ya mike cikin izarsa ya dan duka ya dauke kayan harda dardumar aman bai ninke ba domin shi dai zai iya rantsewa yau ya fara yiwa wani aiki bayan mahaifiyarsa, ko mahaifiyar tasa aikin ba wani bane sai irin idan sunna zaune yakan dan masaging din hannayenta, ko ya miko mata abinsha ko abin ci, ko ya gyara mata zaman takalmanta dai haka
Sai gashi ya dauko ledar nama, da su ice cream ya bi bayan yarinyar da yake dakon kamata da abinda yake sane da tana aikatawa haza yake son ganni dan hukuntata a fili ba a boye ba ya bita da kayanta
Bayan motar ya saka hannunsa ya bude ya zuba kayan a ciki yana gannin yanda ta juyo tana kallonsa da mamaki
Bata ce da shi komai ba saima jan motar da ta yi bayan ya rufe ta yi gana tana kara yiwa Nusaiba fadan wasa da maza ko waye
Bayan motar ya bi da kallo har suka bacewa ganninsa
Kansa ya girgiza yana dan murmushi, wato da ake cewa wanzam baka so a jikinka haka ne ko? Ita tana yawonta aman tana yiwa kanwarta fadan kar ta ga tana wasa da maza
Fuskarsa ya kara hadewa ya juya ya nufi wajen zaman domin bai gama hutawar da ya fito yi ba,
Zama ya yi ya dora kafa daya kan daya
Dan gishiri gishirin da ya ji a lebensa ya saka shi dan kallon hannunsa
Da san abin mai a jiki irin maikon kilishin kadan sannan ashe abin ice cream din har a rigarsa
Mikewa ya yi ya nufi motarsa
Hannunsa ya mika ya janyo abin goge baki da goran ruwa ya matsa gefe ya ringa goge du inda ya san zai samu abin
Sai da ya gama gogewa tas tas sannan ya mika hannunsa ya amshi kayansa da amintacensa ke miko masa ya koma gefe ya shiga kimtsawa
Yana gyara rawanin kansa ya kuma girgiza kansa a ransa yana ayanna" ita ga salihar mace mai tarbiya? Lale da bakone ni a rayuwarki da hakan ya birge ni, sai dai Zan iya rubuta labarinki a tafin hannunki harda wanda ke baki sani ba! NAJEEBA zaki zamo aya a garina, a kanki zan yi maganin kananun yan tsageran garina!
Ya kasance a wannan dare cikin nishadi da dan sanyi a zuciyarsa wanda ya jima bai ji ba a kala tun rasuwar yaronsa
Tabas wasa da Nusaiba da ya yi ya saka shi jin sanyi a zuciyarsa dan yarinyar sosai ta rukunkumeshi sai da ta saka shi yi mata murmushi mai sauti sannan ya bita da cakulkuli duda sakaryar yayarta ta rabata da shi dan iyayi nata
Adu'a ya yiwa kansa da sauran musulmai baki daya na Allah ya basu masu albarka baki daya
Sai a lokacin ya tuna da cikin jikin Zinaria, cikin na nan ko ta barar da shi? Duda da irin zubde zubden jinnin da ta ringa yi shi kuwa rabonsa da ita an jima, bai san me ke dauke hankalin yarinyar nan ba kamar itace sarkin ba shi ba,
Uzuririkanta sun yi mata yawa, uzururikanta kamar wace keda nauyin talakawa a kanta? Har ya zama uzururikanta sun fi shi mahainmanci
Shi kennan haka zai yi ta rayuwa ne? Sunna kusa da macen da suka fi nisa da junna
Sunna karkashin innuwa daya aman tafiarsu nada tsayi
Bai san me yasa ta dauki wasu lamura da zafi ba
Ya dace ya ringa samun kulawa ta miji da matarsa wace ta amsa sunnanta a cikon dakansa
Takan saka shi jin nauyinta idan tana masa kirarin nan
Wani sa'in har sai ya dubeta da sauri da mamakin shin mata ya aura ko baiwa?
Sam mace bata da lamari irin na tafiar da soyaya yanda ya dace?
Shi dai ba mai kallon film ko sauraron labarun soyaya bane
Yana anfani ne da ilimin da ya karanta na islamiya
Kwarai adininsa ya koyar da yanda zaka gudanar da rayuwar aurenka koda kiwa kai din shugaba ne
Annabi Muhammad Sallalahu alaihi wa salam , shugaba ne na duniya baki daya, aman irin yanda tsarin tsaftataciyar soyayarsa da matayensa ta kasance dole mutun ya yi sha'awar gudanar da irinta
Idannuwansa ya mayar ya lumshe yana jin wani takaici guda gefe guda dake yawan zo masa
Ko tunani take yanda na iya dane tarin rigingimun talakawana zan iya dane rigimar dake jikina? Ko ni din bana tare da sha'awa ne?
Gannin kamar tunanin ya sako shi gaba ya saka shi mikewa ya shiga nafila, zai fi kyau ya samu ladan nafilar tunda dayan ladan ba zai samu ba, ba zai fita ya je bangarenta ya lalabota ba, idan har ba'a nuna mata mahinmancinsa a islamiyarsu ko a gidansu ba ba damuwa, zai kuma kwatanta wani auren!
Dinkuna masu rai da lafia ke shigowa daga wajen telan Anmy na yaran baki daya
Sai dinkunnan da aka ware tela biyu aka kilace suke zuba aiki na gimbiya Zahrau
Aure har ya zama saura kwana daya tak wanda tun fitar nan ta su Najeeba Anmy bata kuma barinsu fita ba baki dayansu
Abincinsu su ke shiga kicin bisa jagorancinta su girka,
Hirarsu sunna dakanta daidai da masu yi mata hidima ta dakatar, su kuwa basu sako komai a ransu ba domin takan yi haka dama idan y'ayan nata suka zo yi mata yan kwanaki
Bakin da suka zo gidan a daren yau ne suka dan fara daukan hankulan mutane
Sai dai ba wanda ya kawo wannan lamari a ransa
Wayewar garin safiyar juma'a, tun da sasafe ana ta karatu da sadaka a baban masalacin juma'a na gidan sarki
Sosai ake kara gyare gyaren masalacin da zagayensa an saka turaren wuta mai wani irin dadin kamshi ya zagaye ko'ina har cikin anguwanin kusa da gidan sarki
Lokacin sallar juma'a na yi wajen ya gama daukan musulmai
Ko'ina ka duba sune cikin shiga mai tsafta tarin musulman garin damagaram ne sun fito ba yara ba manya ba tsofafi, kowa ya fito cikin tsafta da turare a jikinsa ya zo da karfin gwuiwarsa da tarin son kasancewarsa a wannan waje mai albarka wajen da zai gabatar da sallar juma'a
Dawakai biyu dake tafe da ado irin na sarakuna ya shaida cewa yau zunna da baki bayan sarkin garinsu harda wani sarkin
Sosai aka ringa bada hanya ana miko gaisuwa har suka idasa shiga ciki sannan fogaren dake kakare da dawakansu suka rike dawakan aka rurufe saukarsu
Sallah aka gabatar cike da nutsuwa, kafin a ja doguwar Adu'a sai kuma sanarwar a dakata za'a daura auren SARKIN GARIN AGADEZ
Da yake akan yi daure dauren aure wasu har sun fara tashi sai dai jin daurin auren ya saka su komawa suka zauna
Abih ya saki murmushi a lokacin da yake bayar da auren Zahrau, sai kuma wata nutsuwa da farin ciki ya shiga cikin zuciyarsa a lokacin da ya amshi sadakinta a hannayensa
Daurin aure ya tafi cikin tsarin islama, ya amshi adu'o'in manyan malamai
Lasifikar dake ajiye ce ke sanarwar daurin auren da ya saka zuciyoyi da dama neman tarwatsewa
Daga kwoncen da dake a saman doguwar kujerar falonta daga kasa bayi ne ke yi mata hidima wasu na yi mata tausa wasu na hada mata abin bukatarta ta wuntsilo ta fado daga saman kujerar sannan ta ruruko idannuwanta tana kara kasa kunnayenta dan jin abinda ke fitowa daga spiker masalacin gidan mijinta
Alhamdulilah, Alhamdulilah muryar liman ta furta a lokaci daya ya kuma maimaita kalmar" An daura auren SARKIN GARIN AGADEZ TARE DA GIMBIYA ZAHRAU BISA SADAKIN JAKA HAMSIN TARE DA DOKI MAI KWALIYAR ZINARI WANDA YA ZAMA HALALIYAR GIMBIYA ZAHRAU
wani irin ihu ta saki daga tsayen da take
Bata tsaya ta dauki alkyabarta ba ta juya da gudu ta nufi bangaren Anmy ta biyayiyar hanyarsu
Hanya ce dake boye, wace ba kowa ya san da ita ba aman a yau ta tashi tonata bata tsaya wata wata ba ta bude kofar ta fada falon Anky dake dauke da Anmy da zuga zugan yan matanta da suka fito a gimbiyoyi reras a jere abin ba'a cewa komai
Tana shiga hannayenta saman kanta ta furta" Anmy, me nake ji? An daura auren mahaifina da Zahrau wacece zahrau? A kan me sarki zai yarda a zo garin nan a yiwa mahaifiyata kishiya? Anmy kin san irin yanda Aya ta tsani maganar kishiya shine zai jaza min bakin jinni a wajen mahaifiyata? Walahi ba zai yiwu ba Anmy, Anmy wannan wani irin abu ne bai jima da tozartani ya min kishiya ya bara min abin fade a duniya baki daya ba shine yanzu zai jagoranci tozarcin uwata??
Baki dayansu idannuwansu a kanta suke
Shigar jikinta riga ce diguwa irin ta shan iskar nan domin bata da kauri ko kadan sai malalalen gashin kanta dake daure da dan ribom
Ga cikinta nan ya tasa sosai dan kamar ba cikin watani shida ba sosai ya fito dama alkyaba ke boye shi
Anmy ta cire kanta daga dubanta a hankali ta furta" subahanallah
Zulaihat, auren ne tozarci? Dama auren da mai martaba ya yi tozarci ne a wajenki ke a matsayinki na uwar gidansa? Sannan a yanzu kin ga halin da kike ciki kika fito a haka kina irin magangannun nan muryarki a sama sama tamkar ba ZINARIYAR Sarkin Danagaram ba? Dama haka kuke ko a yau ne abin ya sameki ?
Kallonta Najeeba ta yi ta kuma kalli Anmy ta ga Anmy ta kawar da dubanta wato ita kunyar kallonta take ji a haka ita kuwa ta tsaya kikam sai surfa tambayoyi take da sakin zance haka
Dubanta ne ta kai har wajen cikinta sannan ne ta ga shatin pant din dake cikin jikinta
Itama da sauri ta cire kanta tana kallon Zahrau,
Gani ta yi Zahra'un ta hade hannayenta ta rike da dan karfi
Bata hannata ba, bata kuma yi gigin rarashinta ba, dan bata so tun yanzu ya zamanto ta ringa shiga wani hali bayan bata ga komai ba
Juyawa ta yi ta shige ta bugo kofar da ya saka Anmy dago kanta da sauri ta kai dubanta wajen kofar
Idannuwanta ta lumshe, a hankali take tambayar kanta....shin itane Zulaihat ta bugawa kofa a yau? Lale idan kana raye ba abinda ba zaka gani ba
Yau itane aka bugowa kofa haka
Idannuwanta ta kara rintsewa tana mai taune lebenta na kasa
Aure? Abinda ta kwana da sannin cewa sai an mata shi ita dake auren sarki? Shine zata yi ikirarin an tozartata?
ZULAIHAT kar ki saka ni zarginki mana?
Zaihat kar ki saka zuciyata kin aminta da ke mana bayan hakan bai dace ba zato zunubi ne
Zulaihat a kan auren ne kike aikata haka?
Idannuwanta ta lumshe ta ji zuciyarta na furta mata" *MAI DAMAGARAM ZAI YI AURE, ZAI SAKE WANI AUREN KWANA KUSA KUWA ZULAHAT DOMIN NA IN DAI YARON YA GAJI MAHAIFINSA TO BA ZAI IYA ZAMA DA KWAYA DAYA TAK BA*
Gaba daya hargitsewa gidan ya yi da hayaniya da gude gude da murna domin sai da aka daura auren ne aka shiga shigowa da abubuwan yanka ana yin waje da su dan za'a yi sadaka ne da su
Ba'a jima ba gidan ya kwashi shiru sakamakon dogaren da suka fitar da kowa aka saki hanya aka kara gyara hanya
Cike da nutsuwa da kasauta suke takowa har suka idasa shiga bangaren Anmy
Tunda suka shigo gaba daya yan matan suka zube kasa kawunansu a kasa cike da girmamawa
Waje suka samu suka zazauna kafin suke amsa gaisuwar Anmy
Sai da wajen ya dan dauki shiru kafin cike da muryarsa mai nagarta ya buda bakinsa cikin nutsuwa ya koro adu'a
Ya yi fatan alkhairi kafin ya dora da wata zazafar nasiha wace ta kare a aure bauta ne, zaman raya sunna ta je,
Ya karashe da kausasa muryarsa yana fadin" kar na ji, kar na ga abinda zai saka ni taka kasar garin agadez ba da sunnan zumunci ba ya Zahrau
Kanta dake kasa tana ta hawaye ta kara sadawa tana dan gyadawa
Anmy ta yi musmushi da dan guntun hawaye a gurbin idannuwanta
Najeeba ta kara rike hannunta dan zuwa lokacin hannunta daya a cikin na Najeeba dayan kuwa a cikin na Ummu
Ajiyar zuciya ya sauke a sanyaye ya furta" ANMY, zan kaita da kaina ne
Anmy ta gyada kanta ta sanyaya muryarta ta furta" zan so a je da yan uwanta su yi mata kwana biyu Allah ya ja da kwanakinka
Kai tsaye ya furta" zamu je da UMMULKHAIR da UMMUKULSUM
ANMY ta tsare shi da kallo da mamakin jin abinda ya fada, Abihma dake cen gefe yana amsa waya kasa kasa hankalinsa na kan yaren nasa, sai ya kebance da su sun zanta tare da yayansu, Dayabu kuwa yana zaune dan nesa da su shima a kasa ya tankwashe kafafuwansa
ANMY ta ce" ai su uku ne, akoy NAJEEBA
dubansa ya kara kaiwa wajen Anmy, da duba irin na kar ki min haka, kafin ya zafafa dubansa zuwa ga Najeeba wace tun da ya nuna banda ita ta dago da mamaki tana kallonsa itama cike da jin haushin kalamansa
Irin duban da yake mata na tsananin tsana da wanda ta masa wanda tsaf duba me mai hade da harara kafin ta sada kanta tsaf a idannuwan Anmy
Da mamaki ta kara dubansa ta kuma kalli Najeeba
Murmushi ne ya kubuce mata kafin itama ta maida kanta ta sada tana jin wani tunani na son ta yi shi yanzu yanzu
Muryar sakin Agadez cike da kamala ya furta" Allah ya ja da ran mai Damagaram, zan so a je da kanwata domin na tabata zata debewa Gimbiya kewa
Yana fada ne yana nuna Najeeba hakan kuwa sai ya baiwa kowa mamaki ciki harda ita kanta Najeebar
Yaya aka yi kike da farin jinni a wajen manyan mutane bayan ke din baki dace da samun hakan ba *MAGE?*
Ya ayanna a ransa kafin yake cire dubansa daga kanta ya maida wajen Abih dake dawowa yana dan murmushi, shifa yau wani fayau yake jinsa, yau wani farin ciki yake ji mai girman gaske, yau ya aurar da daya
Tun dazu yake samun kiran mahaifiyarta da kuma Mardiya wace ya ajiyeta gefe ya yi watsi da ita
Yana karasowa shima kansa ya sada a gabansu, domin koda kuwa yana uba a wajen SHAHEED sannan siriki a wajen sark i n A g a d e z t o f a s h i d i n y a n a k a s a d a s u n e d a g a i n d a l a h , A l l a h y a u m a r c e s h i d a y a y i m a s u b i y a y a a m a t s a y i n s u n a s h u w a g a b a n i n k a s a r s a
A h a n k a l i y a b u d a b a k i n s a y a n a k a l l o n A b i h y a c e " " " " " >?????>?????>?????>?????>?????>?????>?????>?????>?????>?????
* M A G E *
_ ( M a i k w a n c i y a r d ' a u k a r r a i ) _
>?????>?????>?????>?????>?????>?????>?????>?????>?????>?????
* N a *
* S A J I D A *
=ث?(' * T A U R A R I N M A R U B U T A N N I G E R ( A S S O . ) * ?
_ ( T s i n t s i y a m a d ' a u r i n k i d ' a y a ) _ >??
& * [ T . M . N . A ] * & =???=؊??
h t t p s : / / w w w . f a c e b o o k.com/Taurari-marubutan-niger-111773560677003/
_Bismillahir rahamanir rahim_
25
Cenxa harshensa ya yi zuwa harshen larabci, ya tausasa muryarsa ya kara sada kansa yana kallon yayan mahaifiyar tasa wanda ke zaune kusa da y'ayan nasa mata shima zuwa lokacin yannayin rashin son rabuwa da su ya bayana a tatare da shi
A hankali ya furta" Allah ya saka da alkhairi Abih, Allah ya biya da dukan bukatu na alkhairi ya kara girma ya kara rufa asiri
Yanda ka bani ragamar komai Allah ya fitar da ni da kai da kowa kunya a lamarin
Kuma dagowa ta yi da mamakin jin irin yanda larabcinsa ke son yi mata wahalar fahimta bayan larabcin yarenta ne, kasancewar larabci ya shiga cikin junna sai ya yi anfani da baban mai wahalar wanda shi Abih din shi ya koya masa shi ya yi magana, a ciki abu kalilan ne ta fahimta
Abih ya yi murmushi shima ya dauki yaren wanda ya tabata ko Anmy bata iya shi ba, shima kasancewar a saudiya ya yi karatu tun yana karami ya kasance yaren larabci kala biyu yake ji, da na wajen mahaifiyarsa da kuma wanda ya zame masa na makaranta ya bashi amsa kamar haka" nagartarka ta shaida kanta, bayan kasancewarka sarki sai kuma kyawawan halayenka suka sayan maka biyaya daga wajenmu iyayenka, Allah ya yi maka albarka, ya baka zuri'a dayiba
A kasan zuciyarsa ya amsa da amen amen amen
Kasa kasa ya yiwa Anmy bayanin ta inda zasu fito su shiga motar da zata sada su da aeroport nan da minti talatin
Mikewa suka yi suka fita ta hanyar da suka shigo
Anmy kuwa ta mike da sauri ta shiga hada hadar harhada mata dukan abubuwan bukata
A lokacin ne Abih ya samu damar kadaicewa da su baki daya
Kansa ya sada kafin ya dago yana dubansu
Sun yi masa wani irin kyau mai birgewa sannan sun yi masa girman da sai yau ya yarda y'ayan nasa masha Allah sun fa girma
Su dukansu sunna cikin wani danyen lesh ne, wanda ya tabata da kudinsa zai tambaya sai ya kalli Anmynsu a firgice hakan ya saka shi kin tambayar kudin domin abinda ya saka ya gansu da shi ya tabata ya kece kudin shada!
Tun daga yan kunnayensu kuwa har zuwa sarkar wuyansu zinari ne da abin hannayensu, ta zahrau ce kawai ta banbanta ta kasance baba sosai da wani irin kira mai ban tsoro domin ba karama bace a girma da tsayi da fadi da kuma kyan fasali
Alkyabobin dake jikinsu kadai abin kallo ne, ta Najeeba ce ta kasance shara shara mai shegen kyau
A hankali ya ce" ban san da wace kalma zan yi anfani dan nuna maku
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 32
Chapter 33
Chapter 34
Chapter 35
Chapter 36
Chapter 37
Chapter 38
Chapter 39
Chapter 40
Chapter 41
Chapter 42
Chapter 43
Chapter 44
Chapter 45
Chapter 46
Chapter 47
Chapter 48
Chapter 49
Chapter 50
Chapter 51
Chapter 52
Chapter 53
Chapter 54
Chapter 55
Chapter 56
Chapter 57
Chapter 58
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 18 Chapter of 58