so ta furta ko A a wajen nan domin ba a ko'ina take son raba hali ba
Ummukulsum ta ce" Alhamdulilah, haka ne, na sani na kuma yarda uwata haka take, ke fa ubanki kafin ya zama malami meye bai yi? Ta fada muryarta a dan dage
Fuskarta da Anmy ta tsinke da mari ne ya saka du suka firgice sunna kallonta
Sai a lokacin Anmy ta buda bakinta a hankali ba a tashe ba ta ce" ashe lalacewar tarbiyar naku har ta kai ina zaune a waje kuna tozarta kanku ta hanyar sakarwa harshenku linzami?
Kun san ikon harshe a tare da mutun kuwa? Harshe kan saka bawa ya zama sakarai a cikin al'uma,
Idan baka iya rike harshenka ba zai fada maka maganar da zata saka ka da na sani a cikin duniya baki daya!
Ku shikenan a wajen da ya dace a ji muryarku da wajen da bai dace bama sai ku saki baki ku furta kalma daya?
Ummu a gabana kike rashin kunyar nan? Ummu ni zaki tozartawa iyali? Wuyanki ya yi kwarin da ya isa yankan da zai jazawa mahaifiyarki zagi daga bakin mai nemanki da fitina?
Abih da kansa ke sade yana cike da mamakin rayuwa irin yanda yau shine mace, matarsa take budar baki tana zagin y'ayansa a gabansa aman ya kasa furta mata komai
Sunnayen Allah ya ringa kira ido rufe domin baya so rashin kunyar Mardiya ya kaishi wajen da zai kuma aikata kaifin rabuwa da mace, irin yanda ya rabu da matansa ya yiwa kansa alkawarin ita wannan ta birne shi ko ya birneta, sai dai kash ya yo hakan a lokacin da yake aure da matar da bata san darajar kanta ba, ya yi zama da mata kala daban daban, har yar bariki da ustaziya, bai tashi daukan wannan niyar ba sai a kan wace zata tarwatsa masa nutsuwar zuciya
Tun da Anmy ta fara magana sauranma suka kara sada kansu
Ummukulsum kuwa sai ta fashe da kukan nadamar sakin bakinta da ta yi har haka ta faru
Kanta ta dora a gefen kafadar Najeeba tana kukan inda Najeeba ta rintse idannuwanta tana jin kukan yar uwar tata har cikin zuciyarta
Bata taba jin tsanar matar abih irin na yau ba, tabas bata zo wajen nan dan furta kalma daya ba aman ta rantse a yau b sai gobae ba sai ta tardata du gidan ubanda ta shiga ta ci uwarta!
Sanarwar shigowarsa ya saka Anmy sada kanta tana jin kamar ta fashe da kukan itama, kai ina, dole ne ya bara mata yaren nan dan walahi ba zata yarda ya kara tafia da su ba ya kaisu tarbiyarsu na kara shiga hatsari! A haka zaa aurar da mace a kaita gidan miji a kai me? Ta tabata irin yanda ummu ta kasa dane bacin ranta ta nuna shirme ko miji ya fada zata fada ne!
Ya kai minti ashirin kafin yake karasa shigowa cikin shigarsa ta kamala
Da hannayensa ya dakatar da amintacensa kan ya tsaya a kofa domin shara'ar ta cikin gidansu ce
Direct wajen kujerar ya karasa yana tsaye yana bin kowa da kallo
Yarinyar dake sheka kuka kamar zata sike ya bi da kallo, mahaifiyarta da ta riketa gam ya kuma bi da kallo kafin ya maida dubansa inda yarinyar ke nunawa tana son a saketa ta karasa wajen Najeeba aman an hana
Murmushi ya yi a kasan zuciyarsa domin nan take ya gama fahimtar matsalarsu baki daya sai dai kamar yanda ya kasance sai ya saurara to fa zai sauraran ne dole
A hankali murya a tausashe ya ce" *KI SAKE TA TA JE WAJEN YAN UWANTA*
A hankali ya yi maganar, sai dai kasancewarsa mai cike da kwarjini da bulaliyar dukan magana ya sakata tunkudo yarinyar a biye wanda ita a boye ta yi aman du an gani
Yarinyar kuwa da gudu ta karasa jikin Najeeba
Tana zuwa ta ringa dora kanta a jikinta tana rukunkumeta, sai dai Najeebar bata riketa a jikinta ba itama
Zuciyarta na mata tsale, so take ta riketa ta rungumeta aman ba hali a hankali ta saci kallon yayansu wanda komai a kan idannuwan sarki, shima duban nasa ya kai wajen DAYABU sai ya ga idannuwansa a rintse suke, ya gama hawa stage din da ba zai iya furta kalma daya ba tare da ya yi maganin matar nan ba!
Murmushi ya yi ya idasa gani kan matsalar kafin a hankali ya kai zaune
Sai da ya zauna ya gyara zamansa sannan ya yi sakama a hankali
Baki daya suka dago kawunnansu daga sadawar da suka yi,
Dubansa ya kara kaiwa wajen yarinyar dake ta wawuwar Najeeba dan bata yi shirun ba so take ta kulata ta yi mata wasa ta rarasheta aman ta ki yi mata hakan
A tausashe ya ce" Abu hauraira Allah ya yarda da shi yana cewa" ka so masoyinka daidai gwargwado domin zai iya zamowa makiyinka, haka kuma ka ki makiyinka daidai gwargwado domin zai iya zama masoyinka wata rana
Numfasawa ya yi ya shiga binsu da kallo tun daga kan Abih har zu w a m a h a i f i y a r s a
A h a n k a l i y a k u m a f u r t a " * M E K E D A M U N A H A L I N A N E ? M E K E D A M U N S H U G A B A N C I K I N G I D A N B I Y U N E ? * * Y A Y A A K A Y I Y A Y A R D A K I Y A Y A T A Y I Z A F I H A K A A C I K I N G I D A N S A B A Y A N Y A N A D A I K O N K A T S E T A K O D A K U W A T A H A N Y A R K A W A R D A M A I H A D A S A T A N E A W A J E ? * >?????>?????>?????>?????>?????>?????>?????>?????>?????>?????
* M A G E *
_ ( M a i k w a n c i y a r d ' a u k a r r a i ) _
>?????>?????>?????>?????>?????>?????>?????>?????>?????>?????
* N a *
* S A J I D A *
=ث?(' * T A U R A R I N M A R U B U T A N N I G E R ( A S S O . ) * ?
_ ( T s i n t s i y a m a d ' a u r i n k i d ' a y a ) _ >??
& * [ T . M . N . A ] * & =???=؊??
h t t p s : / / w w w . f a c e b o o k . c o m / T a u r a r i - m a r u b u t a n - n i g e r - 1 1 1 7 7 3 5 6 0 6 7 7 0 0 3 /
_ B i s m i l l a h i r r a h a m a n i r r a h i m _
2 3
B a k i d a y a w a j e n n e y a d a u k i s h i r u , k a w u n n a n s u d u a s a d e a k a s a h a k a kuma NUSAIBA bata daina kukan da take ba
Sarki ya kuma buda bakinsa ya ce" mazon Allah tsira da amincin Allah su tabata a gareshi yana son yin alfahari da mu a gobe kiyama
Aman ta yaya?
Shirun dai ne ya kara tabata a wajen hakan ya saka ya dago yar yatsarsa ya yi nuni da Zahrau a tausashen dai ya furta" Bismillah
Zahrau ta kara sada kanta a hankali ta ce" Allah ya kara girma, ya umarcemu da mu hayayafa dan gobe ya yi alfahari da mu
Kansa ya gyada a hankali kasa kasa ya furta" barakalahu fihk,
Kansa tsaye ya nuna Najeeba dake dan janye Nusaiba daga jikinta ya furta" meye ilar gaba a musulunci?
Dungurar da Anmy ta yi mata ya sakata dagowa domin ta so ta yi kamar bata gane da it ake ba , sai dai ba hali domin a irin yanda Anmy kanta ta nutsu a gabansa abin sai wanda ya gani,
A sanyaye ta furta" *Allah yana yiwa mutane afuwa, aman banda masu gaba da junna*
Dubansa ya maida wajen DAYABU da kansa ke kasa shima kafin ya ce" shin me ya dace shugaba ya koyar tsakanin hakuri da rashinsa?
Yaya DAYABU ya dago yana dubansa kafin ya furta" Hakuri, Hakuri shine ya dace da kowani bawa, mai hakuri zai ci riba
Sarki ya gyada kansa ya furta" Mai hakuri zai kai ga ci
Dubansa ya maida kan iyayensa daga Abih har Anmy
A sanyaye ya furta" shugaba, ya dace ya kasance mai matsanancin hakuri, ya ringa shanye abinda da yawa ba zasu iya shanyewa ba
Shugaba koda na wasan yara ne, ya dace ya zama mai yanke hukunci cikin aminci, da kawar da kai
Dubansa ya maida wajen Mardiya, sunna hada ido ta yi gagawar sada kanta, a hankali ya furta" ka karfafa zumunci, ka yada zumunci, kar ka zamo wanda zai yi silar yanke zumunci
Shiru ya kuma yi kafin ya furta" mai magana bismillah
Anmy ta sauke ajiyar zuciya tana dubansa kafin ta maida dubanta wajen yayanta, a hankali itama ta furta" burina, bai fi zumunci ya dore ba Allah ya ja da ran sarkin damagaram
Shaheed ya lumshe idannuwansa ya maida dubansa wajen Abih
Abih ya buda idannuwansa da sukai masa jajajir , a hankali ya furta" Allah ke bada girma, koda kuwa yaranmu sun zamo shuwagabaninmu mu masu biyaya ne, Allah ya kara datako Mai damagaram
Kuma lumshe idannuwansa ya yi sannan ya maida dubansa wajen DAYABU
Kansa ya sada , a hankali ya furta" na yi kuskure, baki daya ni na ja ragamar wanzuwar wannan fitina,Allah ya ja da rai daga yanzu daga kan DAYABU MUTALAB, har zuwa NUSAIBA MUTALAB bamu da wariya, Allah ya huci zuciyar sarkin garina
Da sauri Najeeba ta kankame NUSAIBA a hankali a jikinta sannan ta sakar mata dan murmushi tana shafa kitson kanta wanda tun wanda ta mata ne ba'a tsefe shi ba kusan sati uku a kan ko wankin kirki ba'a masa ba hakan ya sa ya tsufa duba da sunna da izgar gashi nan da nan gashi ke tohowa a kansu shi ya da du sati sauran ke yawan kunce kansu domin kitso ko saloon a gida ba wani wahala shi ya sa kawunnan nasu ke kara albarka
Murmushi ya yi wanda iya zuciyarsa ne sam bai bayanna a fili ba
A hankali ya kuma furta" Allah ya yi mana jagora
Baki dayansu suka amsa amen banda Najeeba dake kara buda bakin Nusaiba tana kallon hakoranta da suka yi dan duhu hakan na shaida mata bata wanke mata baki har gashi ya kama hakoran yar yarinyar
Shirun da ya dauki wajen ne ya sakata dago kanta dan gannin har ya gama maganar ne?
Idannuwansu ne suka sarke da na junna a lokacin da ya kusan karasowa inda take zaune , da sauri ta mayar da kanta kasa ta sada sakamakon faduwar da gabanta ya yi da kuma irin kallon tsanar da ta ga ya yi mata
A ranta kuwa fadi take" azalumi, ashe harfa fuska biyu ne da kai? Gaka yanzu ka gama maganar wa'azi da masalaha ni kuwa ka tsane ni? Ba damuwa, zaka gane ne dan yanda ka tsane ni ni naka fi ka tsanarka!
Sai da ya fice a fallon da kamar minti goma sannan du suka mike
Irin yanda ta karaso ta warci yarta ta juya buguzum buguzum ya saka baki daya suka zaro idannuwansu
Da sauri Abih ya daga kafarsa zai bita sai dai maganar da Anmih ta yi cewar" idan ka bita yaya zaka rarasheta ne ta maido y'ar?
Ya saka shi dawowa da sauri inda take tsaye da yarensa
Muryarsa har tana hadewa da junna ya ce" yanzu domin Allah Bilkissu ba zaki yi min adalci ba kema? Kema a yanzun ganni kike ni ke daure mata tana haka? Ko so kike na yanke igiyoyin da sukai saura a tsakaninmu ne na jara dauko wata? Ita watar idan na daukota kin san meye halayanta? Wani sabon zama ne za'a kara dorawa da y'ayana shin da me zata shigo?
DAYABU ya yatsina bakinsa yana girgiza kansa, lale ta samu damar da take tunanin har zata iya taka sawun kafarta ta fita da y'ar da sarki ya gama nasiha a kanta
Fitarta kawai suka ganni, hakan ya saka Zahrau kallon Anmy, sanyaya muryarta ta yi ta ce" Eyah, Anmy Najeeba ta fice da sauri Anmy
Anmy ta kallota da sauri, sai kuma ta kalli Ummulkhair ta ce" maza ku bita
Sai da suka fita ta kuma kallon DAYABU ta ce" wai Ummulkhair na tura ta bita, ko ta je ta tayata ba, bi min su ka maido min su ka ji?
Irin yanda take sauri ya yi daidai da Mardiya ta buda gaban motar Abih ta shiga kennan zata rufe ita kuwa ta karaso da wani irin mahaukacin sauri ta tare marfin kofar ta hannata rufewa
Hannunta daya ta saka ta finciko yarinyar ta direta kasa cen gefe sannan ta maida hannayenta ta finciko uwar waje
Da ihu ihu uwar ke fadin" ke baki da hankali ne? Ke wata irin karamar yar iska ce?
Dauke fuskarta ta yi da mari, ta maimaita mata wani sannan ta saka hannayenta ta hankadata jikin motar nan ta rike mata wuya
A masifance ta ce" ke wawuya ce Mardiya, kin so ki ci darajar uwa koda kuwa shekarunmu daya da ke, sai kika bata rawarki da tsale!
Tanas gaskiya kika fada babu wace ta zauna ta yi hakurin zama da shi har zuwa wannan lokacin kamar ke gashi yarki har zata ryfe shekara hudu nan da sati uku da kwana biyu,
Kin san me? Dalilin wannan ni kaina na so na ga mutuncinki, domin a duniya du macen da ta iya jure zaman waje domin y'ayanta nakan bata wani waje mai daraja a cikin mata wanda ba kowa nake ba shi ba
Sai dai ke din kin kasance wawuya a lokacin da kike anfani da kadarar wani ko dama da kika samu na zama matar MUTALAB kina taka mu son ranki!
Warto hijab dinta da Dayabu ya yi da murya a dan dage yana fadin" Najeeba me kike haka? Sakar mata hijab kin san da labari na iya iske sarki har yanzu a cikin gidansa kike fa kin manta a wajen ajiye mitoci kike
Fuzge hijab dinta ta yi, Ummulkhair kuwa na gefe rike da yar ta juyar da ita gefe guda tana dan jijigata har ta yi shiru daga kukan da take na rabota da su ta kwonta a kirjin Ummulkhair duda ita Najeeba take so ta dauketa aman ko a Ummulkhair din aka tsaya da dama domin mamanta ta cika duka da fada da zagi abu ga yaro inda ta fi jin dadi nan ta fi zuwa
Gannin sai kakari Mardiya take ya saka wannan karron ya fardota baki dayanta daga jikin Mardiyar da ta yiwa shakar mutuwa
Yana rike da ita tana tirjewa sai da ya matsar da ita gefe ya riketa a hannunsa da karfi karfi ya ce" zaki dawo hayacinki ko ba zaki dawo ba?
Wata tirjewar ta so yi ta hanyar kuma ridar Mardiya dake tsugune tana rike da wuyanta sai dai bai bata dama ba ta hanyar dauke fuskarta da marin da ya sakata saurin ja ta tsaya tana mai dafe kuncin nata da hannayenta bibiyu dan walahi bata son mari, kai ina dalili za'a maren mata fuska? Ita bata son mari ko kadan
Randa bace ya ce" ke baki isa na tankwasa ki bane ko ke idan ranki ya baci mahaukaciya kike zama?
Na fada maki ki daina, na maido ki da laluma , na nuna maki hanya sai tirje min kike kinai min tijara? Wani irin iskanci ne wannan? Sarki sa'ankine da zai tasheki daga magana yanzu yanzu ki fito ki aikata? Ke din banza ke din wofi?
Da kakausar murya ya ce" ki kiyayi haye a wajen da wargi bai samu wajen zama ba!
Yana gama fada ya hade su da Ummulkhair ya ha su da Nusaibar suka yi ciki
Tana nan tsugune har Abih ya karaso
Yana kallonta ya san an yi ba dadi da y'ayansa, gannin yannayin da take ciki ga kuma ba y'ar a tatare da ita
Shima da nasu da yake jira da ita dan haka a kausashe ya ce" tashi mu je
Mikewa ta yi ta je kusa da motar zata shiga
Waigowa ta yi ta kalli baban filin wajen
Zata nemi gannin sarki, zata labarta masa irin marin da Najeeba ta yi mata komai dadewa, sannan ta daukarwa kanta Alwashin yanda Najeeba ta kasance mai tara samari sai dai ta mutu a haka, domin kuwa ta rantse da Allah sai ta wulakanta rayuwarta
Ba ta taka dokar layar da aka saka masu ta kai hannunta kanta na biyu kennan ba ? Itama zata dawo daga zagon kasar ta bi ta hanyar kasa! Abih kuwa yanzu ta fara zama da shi bata ga ubanda zai rabata da mijinta ba, zumunci ne tsakanin mararsa kunyar y'ayansa da y'arta ta haramta!
Har yanzu hannunta dafe da kuncinta suka shigo Fallon Anmy
Sai da suka shigo ta ja ta tsaya sannan ta waiga dubanta kan yayanta wanda shima yake jin zafin marinta da ya yi
A hankali ta ce" yaya, aman ka san ba dadi marin fuska ko?
Yayanta ya ce" ke kuwa kika mari matar ubanki? Marar kunya?
Kanta ta sada sai ga hawaye masu zafi sun fara fita daga cikin idannuwanta a hankali ta kuma furta" yaya, ka ga irin rashin kunyar da ta aikata a gaban sarkin da kake cewa kar ni na yi ya ji labari? Yaya ka ga yanda take son rabamu da Nusaiba bayan ni ina sonta?
Hannunsa ya saka ya kama hannunta suka karasa ciki, a lokacin kuma Anmy ta fito daga dakin yan matan da ta kai ta shinfide tana kallonsu ta karaso
Zaunar da ita ya yi ya zauna , shima sanyaya muryarsa ya yi ya ce" koma me ta yi, baki ji abinda ya maimaira cewar shi shugaba shine wanda zai iya shanye komai ba? Najeeba ba dan bashi da zuciya ba
Sannan ke da ita idan nace da ke ba faya bane zaki fahimci bambancinku?
Ke kanwarsa ce, wace ya isa ya saka belt ya yi maki dukan tsiya koda kuwa babu rawani a kansa
Ita kuwa matar Abihnsa ce, wace koda da rawani a kansa zai iya daga mata kafa ya kawar da kai ya bita da nasiha yau da gobe har ta fahimta
Najeeba kamar yanda kika fada cewar tana anfani da damarta hakan ne,
Kwarai Mardiya ta taki sa'a a rayuwarmu, ta yi nasarar auren ubanmu dan haka uwa take a wajenmu koda kuwa bata dauki girman hakan ba
Anmy ta yi murmushi a ranta kuwa tana mamakin irin yanda yaron ya kasance tamkar mahaifiya, zai hukunta kannen nasa ya kasa samun nutsuwa
Bambancinsa da mahaifiya daya ne, du irin karfin soyayar uwa tana iya cire kanta ta nuna maka laifinka ta kawar da kanta ta labe ta yi jinyar zuciyarta, aman shi sun gano lagonsa koda ya daga hannu a kansu shi ke dawowa ya zauna ya yi ta rarashi
Sarai ta ga anfanin hakan a yau, sannan ta gane dalilin da ya sa maganarsa take da karfin tasiri a wajensu
Shi din uba ne kuma uwa ne a wajen kannen nasa
Irin yanda yake shanye duka dominsu ya saka shi zamowa shugaba a cikinsu
Hannunsa ya kai wajen fuskar nata da take rike da wajen idannuwansa ya rintse kadan a hankali ya dubi Anmy ya ce" Anmy, ki yi hakuri ki yafe mata bin bayanta da ta yi ta aikawatar da fada a cikin gidan sarki, dan Allah ki yi hakuri
Murmushi ta yi masa tana gannin girman yaron a idannuwanta, ta tabata zai iya zama adali koda a cikin gidansa ne
Shima murmushin ya yi ya mike ya kara tsugunawa ya furta" Allah ya kara girma uwata
Anmy ta ji wani yamyam da wani dadi ya ratsa zuciyarta, a sanyaye ta furta" Allah ya yi maka albarka yarona
Hannun Najeeba ya kuma rikewa kadan kafin ya saketa ya juya ya nufi wajen Ummulkhair dake goye da Nusaiba
Tsayawa ya yi yana kallon yarinyar har ta yi baci
Murmushi ya yi ya dan duka ya mana mata kiss a goshinta sannan ya kalli Ummulkhair a hankali ya ce" Khairiya, kar ki bari khulsum ta yi kukan maganar da ta fada mata kin ji? Sannan kar ki yarda bacin ran mamanta ya saka khulsum tsanar Nusaiba
Ummulkhair ta gyada kanta itama tana rike da hannun yayan nata ta ce" yaya auntu Zahra na tare da ita a dakinmu, tama ce na goya Nusaiba idan ta yi baci a wajen khulsumbdin zata kwana
Kansa ya gyada yana mai jin nutsuwa ta shige shi, dan baya so laifin mahaifiyar yarinyar ya saka kannen nasa gannin bakinta
Yaya, wayar tawa fa?
Gaban goshinsa ya dafe ya ce" ke ba na manta ba, aman kin san meye yayarki ne tace ita zata siya shi yasa na manta zan tambayo maki ita yayane an siyan ne ko yaya?
Murmushi ta yi tana jin dadi a ranta, tap, idan aka ce auren yayansu ne bata san irin abinda zasu yi ba, fatansu Allah ya sa yanda yarinyar ke nuna masu kauna a waje har cikin gidan haka ne, Allah ya sa matar yayansu ta zamo uwa a garesu baki daya
Sai da ya kara shafa bayan yarinyar ya furta" kaita ki shinfideta ki yi mata adu'a sannan ki ajiye wani dan abin ci a kusa dan kar aje ko tana tashin tsakiyar dare neman abinci
Amsa masa ta yi ta nufi ciki
Kanta sade yake a kasa tana tsoron dagowa sakamakon irin kakausan kallon da Anmy ke binta da shi
A hankali ta furta" Anmy ki yi hakuri
Anmy ta yi dan murmushi ta ce" wani abin kikai min ne NAJEEBA Mutalab?
Najeeba ta kara sada kanta a hankali ta ce" Anmy, a gabanku fa take wannan rashin mutuncin
Anmy ta dan daga kafadunta ta ce" eh na gani, ke kuwa sai kika zaneta a bayan idannuwanmu aman a wajen da duniya zata iya gani ba, ai haka ne danka dama ka zane shi kawai
Najeeba ta kara sada kanta dan ta san yaufa tana hannu
A hankali ta budi bakinta zata yi magana Anmy ta ce" ai ban yarda cewar, bayan rashin kunya, rashin sannin ciwon kai, rashin kawar da kai yanzun harta da darajar kanki baki sani ba?
Da sauri ta ringa girgiza kanta ta ce" Anmy
Anmy ta ce" ki yi min shiru malama!
Idan ita ta nuna halayen tarbiyarta ta marar kunya da rashin sannin girman na gaba da ita da raini ke sai kika nuna taki tarbiyar wace kika gada ta masifa?
Kanta ta kara sadawa kasa
Anmy ta ce" ina sannin ciwon kai ga macen da zata yi anfani da karfin damatsunnanta ba dan ta yi ibada ba? Ina hankali ga macen da zata kai hannunta jikin wata da niyar zu gwada karfi bayan ta san wani abu na iya faruwa a wajen ko ita a ga tsiraicinta ko a ga na abokiyar fadan nata ta hanyar yage mata hijab ko zannin dake daure a jikinta ko rigarta haka kawai ta jazawa kansu abin kunya domin na tabata du wace ta san kanta zata ji kunyar a ga tsiraicin yar uwarta mace bale nata! Yaushe kika raina gida mai daraja irin gidan nan da zaki yi dambe a cikinsa bayan wanda bai san irin darajarsa bama ya kiyaye ya girmama shi bake ke da kike cikinsa kika san meye shi?
Yaushe kika raina haduwarki da yayanki wanda nake iya yina dan rufe izgilinki?
Ina kika zubar da class dinki da har zaki mike ki tarbi mutun da fada bayan kin san ance shiruma amsa ce ga mai hankali?
Allah ya huci zuciyarki....Najeeba ta fada tana kara sada kanta
Anmy ta dago dan yatsarta guda ta ce" zaki nutsu ko bakya so ne Najeeba Mutalab!
Tashi ki je dakinki ki yi nafila ki shirya yin baci
Sai da ta kara dukawa ta yi godiya tana kallon fuskar Anmy din da ata daure mata sannan ta shige ciki
Washe garima sun wuni ne sunna gyare gyaren fata, sai dia har zuwa lokacin ba wani sake masu baki dayansu Anmy ta yi ba, idannuwanta a kansu, tana ta daukan dukan abinda bai mata ba tana rubutawa a litafi da byro sannan tana dora question mark a sama, kan neman yanda zata biyo da su
Sai irin dabi'un da ta shiga koya masu na rayuwar gidan sarauta, wace da yawa sun iya sai dai kuma da yawa basu iya ba dole sai an zauna dan ba karamin aiki bane
Irin magana da ido, magana da kai, sasauta kallo ga sarki , irin kallon da zaka masa a cikin jama'a a matsayinsa na sarki, irin wanda zaka iya masa idan daga kai sai shi ne, irin yanda zaka ringa kiran sunnansa a waje da kuma idan dqga kai sai shi ne
Murmushi Najeeba ta yi tana lumshe ido da anmy ta furta" MAI GARINA, a daka kuwa tana iya yi masa special sunna kamar MAI NI
Bayan salolin su magariba da isha ta fito dauke da Nusaiba
Sai da ta duka har kasa ta ce" Anmy, ina son zuwa saloon na dauko abin kitsonta
Anmy ta dubeta, a hankali ta ce" ki dauki kys din motana, ku je ku dawo
Najeeba ta kara yin godiya ta dauki kys din
Tana cikin tuki mesage din Anmy ya shigo
Sai da ta tsaya a saloon ta dauko abubuwan bukatarta sannan ta dawo motar ta duba mesage din
*ki kula*
Murmushi ta yi tana kallon Nusaiba ta ce" wa ke son ice cream?
Ai kuwa Nusaiba ta ringa daga hannunta
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 32
Chapter 33
Chapter 34
Chapter 35
Chapter 36
Chapter 37
Chapter 38
Chapter 39
Chapter 40
Chapter 41
Chapter 42
Chapter 43
Chapter 44
Chapter 45
Chapter 46
Chapter 47
Chapter 48
Chapter 49
Chapter 50
Chapter 51
Chapter 52
Chapter 53
Chapter 54
Chapter 55
Chapter 56
Chapter 57
Chapter 58
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 17 Chapter of 58