2
A h a n k a l i y a c e " * N A J E E B A * ?
i d a n nuwanta ta saka cikin nasa ta ce" Na'am yaya dayabu, na rantse maka karya yake sarkin ba na gaskiya bane suka saka, Aba ya fi karfinka kennan a kasar nan?
Hannunsa ya dago ransa bace ya dafe gaban goshinsa
Bai kuma yi mata magana ba ya juya ya ringa kama kannen nasa masu motarsu yana saka kowa cikin motarsa, baya yi maka magana sai dai ya nuna maka hanya kan ka tafi sha'anin gabanka
Sauran biyun da basu da mota ya janyo hannayensu ya kawo su ya buda bayan motar NAJEEBA ya tura su kafin ya maido hankalinsa kanta
Sai da ya kuma kallonta kafin ya ce" rigarki ta cire, kina kaisu ki tabatar kin koma gida kin saka sutura
Kai ta gyada masa tana kara cije lebenta masu mugun kyau da haske tamkar fatarta bata da wani duhu
Juyawa ta yi ta shiga motarta
Da gangan ta ringa yin kamar motar ta ki tashi har sai da ta ga fitowar mahaifinta ta bi shi da kallo kafin ta yatsina bakinta ta turo bakin ta tada motar gannin yayansu ya karasa kusa da motar mahaifin nasu ta gyada kai ta tabata idan ya gane gaskiya ne ba zai yarda ba sai dai du abinda za'a yi a yi
Gudu take falfalawa da su a baya a zaune sanye da kayan makaranta har ta karasa babar makarantar school mai hade da islamiya
Budewa ta yi suka fito ta buda jakarta ta basu kudin kari suka juya suka tafi cikin makarantar
Motar ta koma ta yiwa kys ta tayar ta kama tafia
Tana tafe tana kara cije lebenta a haka har ta zo wajen danja
Sojan dake cikin motarsa wanda tun ficewarta dazu polisai na tsayar da ita ta ki tsayawa ne ya fito ya zagaya wajen motar nata
Fuskarsa a hade take, sam ba annuri, yana daya daga cikin mutanen da akaiwa sunna dan tsaurinsu da iko da mugun taurinsu a kan aikinsu, sunna kama mai laifi koma waye, sunna da haye basa yarda da raini
Sai dai kamar yanda kowani dan adam yake da point faible hakama na Mala'ila wato sunnan da akai masa shine shagwababiyar mace
Da sauri ta saka hannayenta ta buda gaban motarta
Kayan kwaliya ta janyo da mugun sauri ta buda madubi ta dan duka dan kar a hangota daga gaba ta gyagyara kwalin idannuwanta, ta saka dan jan baki mai tafiya da kalar lebenta ya hadu sosai
Rigarta ta ja ta gyara ya kasance wajen da aka cira matan ya fito hakan ya sa ana gannin dan saman mamanta kadan ba da yawa ba
Zuge gilashin ta yi bayan ta yiwa fuskarta takwaf takwaf
Da wata irin yanga ta dago dara daran idannuwanta ta sauke a kan fuskarsa, lokaci daya kamaninta na salihar mace mai fuzga ya bayanna a tare da ita
Gaban goshinta kuwa kwonce yake da wani irin ni'imtacen gashi wanda ya yi luf luf da shi
Sai da ta kara yin luuuuu da idannuwanta tamkar wace zata sume sannan ta dauki tissu ta ringa goge idannuwanta nan da nan kuma sai kwallah ta taru
Tana kallonsa ta kara rage muryarta, dama mace ce mai karamar murya zazaga hakan ya sa sai da ya kara matsowa ya kashe kunne yana jin abinda take fadi" muryarta a sanyaye, sai dai yannayinta a hargitse ta ce" Allah ya huci zuciyarka sir, hatsari na yi ne cen baya hankalina tashe banma ga sunna tsayar da ni ba, ka gafarceni mai laifi ce ni, idan kuwa na sauka na bada motar bani da ja domin ba wanda ya isa ya ja da ikon da kansa
Wani fadi ya ji kansa ya kara, gilashin idannuwansa ya dan yi kasa da shi hakan ya bayannar da idannuwansa masu jan gaske ,
Murmushi ya yi mata wanda ya bayanar da hakoransa masu tsawarya sannan iskar sigarin da ya zuga ta daki hancinta hakan ya sa da sauri ta kai tissu din nan wajen hancinta ta rufe tana kokarin danne tarin dake son taso mata
Wayarsa ya miko mata yana kallonta da idannuwansa tamkar wanda yake daga maye ya ce" dora min numberki a nan yan mata, zan yi kiranki na fada maki yanda muka yi da su domin na fada masu su barni da ke ne, kin san akoy yan cikan dake son lalata mana gari
Murmushin yake ta saki tana jin cikinta na neman hautsinewa sakamakon shakar warin nan dake fitowa daga bakinsa yana dukan hancinta, a duniya idan akoy abinda ke sakata gudawa to warin baki ne, bata san wani irin rashin lafia ne haka ba wanda idan ta shaki warin baki nan da nan cikinta ke murdawa ta nemi rikicewa harda juwa
Tana faman lumshe ido ta dora masa numbobin da bata san ko na waye bama tana masa dan murmushi ta mika masa wayar
Amsa ya yi ya kashe mata ido daya sannan ya bata hanya ta tayar da motarta ta halba bakin titi
Tana yin nisa ta sauke ajiyar zuciya a fili ta furta" *Wawa kawai!*
Maimakun ta je gidan kamar yanda yayanta ya mata kashedin cenza rigar jikinta, haka ta yi kwana ta je clinik, wato asibiti mai zaman kanta
Tana zuwa bata yiwa kowa magana ba da yar farar jakarta da kuma farin dogon takalminta ta karasa bangaren likitan dake duba mararsa lafia
Gannin yannayinta a wanke ya saka ba wanda ya tsayar da ita, ita kuwa kai tsaye ta karasa ta dan yi knocking
Yana kokarin saka farar rigarsa ta likitoci ya bata damar shigowa domin a tunaninsa nurse din da zata kawo masa liste din mutanen da zai duba ne yau
Kamshin turaranta ya saka shi juyowa da sauri
Lokaci daya fuslarsa ta fadada murmushi yana kallonta
Gannin fuskarta ba murmushi da alamun baci bacin rai ya saka shi saurin kara juyowa yana kallonta ya ce" oh angel, waye ya taba min ke da safe haka na ga fuskar ki a hade kamar wace aka batawa ko baki da lafia ne?
Jakar hannunta ta ajiye saman fararan takardun table din tana kara yatsina fuskarta ta ja dan kwalinta baya gashinta ya kara bayana ta sauke ajiyar zuciya ta kale shi
Sai da ta ja wata yar shasheka sai kawai hawaye ya shiga bin kuncinta
Lokaci daya ya rikice, ya bi ya daburce, ya kai hannunsa da niyar kama hannunta sau uku yana fasawa sannin da ya yi cewa a duniya ta tsani a taba jikinta, du irin yanda take da iya wankar samari kana yin wannan kokarin na kwatanta zaka tabata zaku bata , batawa kuwa wace ba zaku shirya ba
Kansa ya dafe yana jin zuciyarsa na bugawa, a duniya yana son yarinyar nan, idan kuwa ya ga ranta bace yakan fita a hayacinsa, bai san wani irin so ne yake mata mai tsanani haka ba, dalilinta ya sa ya daina fade fade a garin domin tana da kawaye kai bama maganar kawaye ba saloon dinta du wata mai ji da kanta a cen take gyaran kai ne, gyaran jiki ne, ko kunshi, ko mak up shi yasa ya nemi biye biyen matan da yake ya ajiye gefe, matarsa kanta yana kiyayewa kar ta san yanada aure domin shifa a kanta yana iya sakin matar tasa,
Baban burinsa ya sameta, ya cin mata ta aure ko ba aure, sai yana gannin abu ne mai wuya ba auren domin har yanzu baban abinda ya fi bashi mamaki a kanta du irin wayewarta da tarin shagwabarta ko soyayar shan minti ba'a yi da ita, mutane da yawa na mata muguwar fasara, shi dake tare da ita shi ya san wacece ita
Agogon hannunta ta dan kunce tana kallonsa ta ce" kudin jakana sun kare shine hankalina ya tashi domin yau ba zan bude saloon ba kai kuwa ka san inada kashin kudi shine na zo
Kabsa ya dafe cike da kulawa ya ce" Angel, kuma shine sai kin taso? Haba baby idan kika yi kirana ko ina ne sai na zo na kawo maki aman shine zaki taso har ki zubar min da tsadadun hawayenki?
Mikewa ya yi yana maganar ya dauko jakarsa ta laptop ya buda bayanta ya ciro kudi masu kauron gaske ya buda jakarta ya zuba mata
Catin Airtel ya ciro ya buda jakar nata ya kuma saka mata sannan ya dubeta ya ce" kin karya?
Idannuwanta ta juya masa cikin yannayi na lumshe su kafin ta dan cije lebenta na kasa ta kuma sake shi
Jin an kuma buga office din ya saka ta tashi ta dauki jakar nata ta sakar masa murmushin da ya saka saman kuncinta cen sama kamar kusan idannuwanta lotsawa kadan wanda hakan ke kashe masu begenta, ta kara yi masa wani warwar da idannuwanta sannan ta kuma gyara tsayuwarta ta ce" jarumina, ka kula da kanka, sai mun hadu
Bai iya amsawa ba sai wani irin sakai da ya yi da bakinsa ya rakata da kallo tamkar ya janyota ya maidota ya rukunkumeta a jikinsa yake ji har ta fice a office din
Wata wawuyar ajiyar zuciya ya saki a fili ya furta" dole na malaki babyn nan, tawa ce ta ni kadai!
Ita kuwa daga nanma direct shagonta ta nufa, wato saloon dinta
Motarta ta parker ta sauka bayan ta ciro gilas dinta pink coler mai yannayin heart ta dora ta dauki jakarta ta nufi cikin wajen da tun daga kofar take hangen da alama sunna da mutane sosai yau bayan ta hana a dauki mutane da yawa yau sakamakon amaryar da zata shirya
Tana shiga wajen ya dauki ihu, domin kawarta ce bahija da kuma Ramlat suka kawo mata ziyara, kai ziyarar tafe take da son jin abinda ake cicirawa a gari wai sun kai mahaifinsu kara gidan sarki
Itama da murna ta karasa wajensu ta zauna tana kallonsu
Sai da suka gaisa, masu aikinta suka kawo mata jus da ruwa, da sauri dayar ta je ciki dan gyara mata abin kari ita kuwa ta sakarwa Bahija murmushi ta ce" bahija ina zuwa bara na cenza kaya
Bahijarma murmushin ta sakar mata sannan ta dauki Iphone dinta ta danna kira
Shiga ciki ta yi ta cire abayar nata ta dauko wata doguwar riga marar nauyi ta saka mai dan gajeran hannu
Gashin kanta ta hade ta yi sama da shi ta saka masa dan karamin ribom ta daure shi hakan ya sa yake ta reto da cikarsa da kuma tsayinsa ga bakinsa
Tana fitowa gaban madubi ta je ta shiga bin aiyukan da akaiwa mutanen,
Biyu ne atach din da aka saka masu bai yi mata ba domin ya yi tudu da yawa dan haka ta sa a kunce ta shiga hada zare a jikin katuwar allura ta harhada da yawa su kuwa suka shiga sauke masu sai da aka gama na fari ta kama cike da kwarewa da kaunar aikinta ta gyara masu ya yi tsaf tsaf da shi ya kwonta kafin ta caje masu ta masu yanda suke so da shi
Sai da suka gama suka biya kudin da aka yanke masu na aikinsu cike da farin cikin samun biyan bukata suka tafi
Sai da saloon ya rage mace daya ta maida hankali ta saka mata gashin ido ta gyara mata girarta sannan ta saka mata akaifun nan da ake kira natural masu tsadar nan ta gyara mata su sukai wani iri kamar nata domin an rage tsayinsu sosai da sosai sun bada kala
Itama biya ta yi ta tafi cike da farin cikin sakin fuskar NAJEEBA
Sai da suka gama tafia ta je jikin madubin ta juya takardar dake nuna a bude suke zuwa a rufe suke ta dawo wajen ma'aikatan nata
Fuska tamke ta ce" Nadia yaushe kika zama uwar gidana?
Nadia da ta san ta yi laifi ta ce" aunty dan Allah ki yi hakuri, walahi tun jiya suka tambayeni yau zasu zo a masu aiki, kuma ke baki ce min kar na bude ba sai dazu a lokacin tuni sun zo na yi na yi na ce da su su tafi suka kiya, clients dinmu ne aunty ke ke hana mu wulakanta clients dinmu
Wani huci ta sauke ta ce" to maza maza a gyara wajen a tatare komai a tsaftace, minister ya yi amarya nan za'a kawota nan da awa biyu, ku tanadi komai domin tun daga kurkun zamu silleta dan uban mama zata gani ba tace ba za'ai mata kishiya ba?
Daria kawarta ta fashe da shi tana kallonta ta ce" NAJEEBA, wai waye ya taba ki yau du kike hawa uwa fulawa?
Murmushi ta sakar mata kafin ta gyara zama kusa da ita ta dauko gashin idon da zata sakawa kanta bayan natama masu tsayin gaske ne da baki, aman da yake tana da bako yau za'q kara firgita shi
Abin sakawar ta dauka bayan ta saka masa col ta shiga dan hura shi tana kallon yanda Ramlat ta huda hancinta
Murmushi ta yi ta ce" Ramlat idan na kale ki hanci a huje kamar saniya
Ramlat ta hade fuska ta harareta ta ce" bana son wulakanci NAJEEBA
ke dake son a huda maki gwfen lebenki fa, nan har cewa kika yi a huda maki harshenki kina tsoron kanwar dad ne ya sa kika fasa wancen aman ai jira kike a kawo maki dan kunnen zinarin da kika saka a maki a huda maki lebe uwa wata yar hannu
Idannuwanta ta jujuya tana dan rawa da kanta ta kalli madubin ta dago shi sosai a hannunta tana kallo ta kasa kasa ta daidaita ta dora na gefen dama
Dayan ta dago shima ta shiga dan matsa masa kadan a sama ta shiga yarfe shi dan ya sha iska kafin ta dora, kunnayenta ne suka jiyo mata muryar bahija na cewa" wai me kuka je yi fada yau ne?
NAJEEBA ta dan saci kallonta ta daga kafadunta ta ce" matsalar cikin gida ne
Baki ta tabe ta ce" ku dai cikin gidanku kulun matsala, to Allah ya sawaka, aman yaya kuka kwashe da mai damagaram yau?
Sai da ta kuma gyarawa ta dora ta daidaita da kyau, tana dago idannuwan nata sun kara wani irin girma da fuzga ta sauke su samanta ta ce" yau na ji jaraba wai ke ina ruwanki da son sannin abinda ke tafe a gidanmu? Kar ki manta kowa da sirrinsa wanda yake gannin sirri ne haba!
Da sauri ta ce" aa, Allah ya baki hakuri, ni ba wani abin ya sa nake tambayarki ba gani na yi ke ke zaginsa kice ya damu mutane a kasa ya hanna mana rawar gaban hantsi ya tsane ki
Allurar da ta dauko tana kara daidaita kashin idon dan ya yo das kar a ga col din da ta saka da shi ta shiga aiki da shi cikin kwarewa ta ce" ba zaki gane ba, ni ina iya zagin ahalina! Aman ke ya haramta a gareki
Ramlat ce ta yi gagawar cenza zancen ta hanyar sako wani, daidai lokacin kuma yayanta ya yi kiranta cewa gimbiya na nemansu bayan salar isha'i
Sai da gabanta ya fadi, lokaci daya ta shiga aiki cikin rashin kuzari gashi aiki ne jajir a gabanta shirya matar minister guda amarya wace kuma ta yiwa kanta alkawarin sai ta mata kwaliyar da zata firgita uwar gidan domin uwar gidan ce abokiyar gabanta wace suke fada da ita
Ba ita ta bar saloon ba sai da magariba ta shige sosai, bayan ta yi sallah ta kama hanyar gidansu da wani irin gudu
Tana zuwa a kofa ta bar motarta ta yi bangarensu da gudu tana lalubar kys din dakinta
Budewa ta yi ta afka bayi ta shiga wanka da wani irin sauri
Tana fitowa sallah ta yi domin tun tana hanya akai isha
Sai da ta gama ta shiga ciro kayan sif dinta tana ta zubarwa a nan da kyar ta iya daukan wata jar abaya irin na dubai din nan ta zira
Sai da ta zira ta dauki pant ta saka da sauri sauri ta caje gashin kanta ta warci turaranta tana gudu gudu tana fesawa da wayarta a hannunta da wata jakarta baka wace ta dauki takalminta baki a hannu
Ba wanda ta nema dan ta san sun tsufa a gidan Gimbiya da gudu ta fada motarta ta tayar ta warceta ta nufi cikin gida (Gidan sarki)
Ta kofar baya ta bi domin ta san idan ta bi ta gaba zasu kara tsayar da ita ne
Bangare bangare ta ringa ratsawa, gidan dauke yake da gilas wani irin ginni mai haukata bawa
Tana ratsawa har ta karaso bangaren da akan hada su a masu nasiha wanda a nan gimbiya ke hada su
Sai da gabanta ya yanke ya fadi sakamakon hango takalma hakan ya shaida mata kowa na nan ita kadai ce bata zo a kan lokaci ba
Sai da ta dafe zuciyarta a hankali ta furta" woyo Allahna na kara laifi
Da sauri ta saisaita nutsuwarta ta karasa
Hannayenta ta saka ta buda kofar madubin dake rufe mai nauyin gaske wace take goge kal kal duda dare ne kana gannin kanka tar a jiki
Dan dakata ta yi ta ciro jan bakinta ta shafa tana kallon madubin ta saki murmushi, wanda baki daya hakan ya faru ne a kan idannuwanta kanwar mahaifin nasu wato Gimbiya da kuma yan uwanta, sai matar mai martaba da kuma yaronsa prince, dan kuwa madubin irin wanda idan kana gannin kanka daga waje ne kai kuwa ana ganninka daga ciki kuma baka gannin masu ganninka, ita kuwa rashin lafiar dake damunta idan ta ga madubi sai ta amsa tayinsa ta hanyar dan kara gyagyarawa
Hannayenta ta kuma saka ta tura kofar ta shiga da salama kasa kasa
Gabanta ne ya yi tsale ya yi luguden kidi ya fadi , hakan ya sa ta saki jakar hannun nata tana raraba ido jikinta na dan rawa rawa
Yayanta da yayunta da kannenta ta ganni laye a layi daya kowane kansa a kasa kamar sun zo neman gafara
Gefe data matar sarki ce ta sha wata mahaukaciyar kwaliya mai daukan hankali sai walwali take gata fara ce sai haskawa take
Gimbiya ce tsaye a tsakiyar falon itama ta sha wata irin nitsatsiyar kwaliya jikinta sanye da alkyaba
Da sauri ta kara kallon yan uwanta ta ga kowa da alkyaba a jikinsa, ita daya ce bata saka ba, hakan ya kara bata ran maman nasu
Du bata kara firgicewa ba sai da ta sauke dubanta kan MAI DAMAGARAN, SARKI SARKIN SARAKUNA SARKI MAI MULKI CIKIN AMINCI, ZAKI BAYA DAUKAN WARGI, MAI GARI MAI KAUYUKA DAN *ABDUL MALIK ALI BUZU* *SHAHID* yake aban prince *ALI SHAHEED ABDUL MALIK ALI BUZU*
miji a wajen *ZINARIYA ZULAIHAT* yar sarkin agadez, D'A daya kwalin kwal a wajen GIMBIYA *BILKISSU MAI GADON ZINARI*
Kansa ya juyar daga kallon tsanar da ya gama jifanta da shi ya maida kan matarsa dake zaune tana ta sakin isa da takama da sarauta
Yar yatsarsa ya daga ya yi mata nuni da ta fita
Idannuwanta ta lumshe, dama ta san ba zai barta ta ji abinda ya faru ba, baya taba barinta jin ainahin sirrin da ya shafe su, bata san wani irin mutun ne shi mai shegen zurfin ciki da boye laifin yan uwansa
Mikewa ta yi ta kara sakin shigar jikinta alkyabarta ta sauka sosai ta shiga takawa a hankali har ta karaso kusa da NAJEEBA dake tsaye baki daya jikinta ya yi wani kalau kamar ba ita ba
Cikin murya kasa kasa sosai ta kara rabar NAJEEBAR ta ce" kauce min a hanyar yar talakawa!
NAJEEBA ta dago da sauri sannan a hargitse ta sauke kakausan kallo a saman kanta, kafin ta ankara ta.....................
>?????>?????>?????>?????>?????>?????>?????>?????>?????>?????
* M A G E *
_ ( M a i k w a n c i y a r d ' a u k a r r a i ) _
>?????>?????>?????>?????>?????>?????>?????>?????>?????>?????
* N a *
* S A J I D A *
5
A h a n k a l i y a c e " M a r d i y a , a m a n ai y'ayanki ne ina kike so su je su ciyo abinci?
Gannin kamar ta samu dama ya sakata kara juyar da kai gefe ta ce" su je waje mana
Murmushin karfin hali ya yi yana gannin yanda idannuwan NAJEEBA tamkar zasu fado kasa yanda take zaro su tana son gaskata shin Abih dinsa ba zai wanketa sa mari ba? Wai mamansu kan uba yarinyar fa sa'arsu ce, kuma wai abincin me zata hana masu yau kuma?
Murmushi Abih ya yi a hankali ya ce" tashi ki je ki saka a dafa ma y'ayanki abinci Mardiya
Dubansa take, sai dai sam bata gano abinda yake dannewa ba, hakan ua sakata fadin" ai suma sun girma su je waje su ci
Da sauri ya ce" to dauke wannan din, nima yau tunda amaryana zata min rowar abincin ai sai mu hakura mu duka
Wani malulun bakin ciki da mamakin mahaifin nasu ne ya tsaya masu a zuciya
Zahra ce ta sada kanta tana jinjina lale sun bata ran mahaifin nasu da har yau ya nuna halin rashin damuwa a kansu , bayan sun san irin tarin kaunar da yake nuna masu wada dalilin hakan yawancin rabuwarsa da wasu matan nasa su ne sila
Yayansu kuwa kure Aban nasu ya yi da ido yana hango irin yanda yake danne bacin ransa
Bilkisu kamar ta ciji matar mahaifin nasu,
Najeeba a hankali ta kalli mahaifin nasu ta ce" ABIHNA
Wani hararan ya zabga mata kafin ya ce" NAJEEBA MUTALAB, meye?
Idannuwanta lumshe nan da nan suka cika da kwallah a hankali ta ce" kar ka hore mu da fushinka Abih, ba abinda muka yi
Da karfi ya ce" makaryaciya, marar kunyar banza kawai! Ke ba har marin matana kika yi ba??
Da gadara gadara Mardiya ta ce" marina ta yi sannan ta shaki wuyan aunty
Ummulkhair ta ce" ita ba zagin mahaifiyarta kika yi ba?
Ummu kulsum ta ce" zaginta kennan kulun sai tana zagin mana iyaye bayan mun san ciwonsu muna son abinmu
Da haushi Abih ya ce" ai dama na san su ke zuga ku shine zaku mi rashin da'a a nan?
Kai DAYABU ya girgiza ya kalli kannensa ya ce" ku tashi mu je waje mu siya
Du mikewa suka yi , wanda hakan ya saka zuciyarsa tsinkewa sai dai ya ki sakar masu yar karamar da DAYABU ya miko hannu ya bashi
A hankali DAYABU ya ce" saketa mu je na shiryata kar mu yi lati ka ga sai mun sayi abinci kafin mu tafi
Hannunsa ya bige ya ce" da kaniyarka y'arka ce? Na ki na sakin
Hannunsa ya janye yana dan yatsine fuskarsa ya ce" kanwata ce, kuma dole a bani abina domin ni tana gaba da dukan wata katuwa, kuma walahi idan y'a ta kuma cewa ita uwata ce wannan karon ba marin kanwata zata sha ba, zata dauki mari ne daga hannuna!
Yana gama fada ya juya ya shiga tura su du suka fito kowane ransa bace
A hankali ta kamo hannun DAYABU ta sanyaya muryarya ta ce" domin Allah meye laifina a cikin nan yaya?
Ido ya tsura mata da mamakinta, yanzu tambaya take meye laifinta bayan ta wankawa mace biyu mari a jiya matan dake da fada a ji a cikin garin baki daya?
A gaban sarki ta mari matarsa sannan ta tsinkawa matar mahaifinsu mari
Kansa kawai ya girgiza ya ja hannayensu
Sai da ya kaisu bangarensu ya ce" maza ku shirya bara na sa a kawo mana abin kari daga restaurant abusa maza ku shirya kowa ya karya a hanya
Sunna fita Abih ya mike ya ajiye yar saman kujera
Juyowa ya yi rai bace ya nunata da yatsarsa ya ce" ke, aman baki da hankali ko? Yaran a cikin gidan ubansu ki ce ba zaki basu abincin da ba ke ke na ba ba kuma ke ke girkawa ba? Look Mardiya, bana hada y'ayana da kowa , bana iya jure rashin mutunci a kan yarana bayan su kadai malaka duniya
Na rabu da ke ba wani abu bane , lale y'ayana basu kyauta ba aman ki sani ke suka baiwa laya ba ni ba, kuma ke kika tabo har haka ya faru da ke, da baki ringa wulakanci kina jifansu da kalamai kina zagar masu iyaye ba, da ba'a nuna sune masu iya asiri ke aa ba, da du haka bata faru ba
Da kakausar murya, ya jirgice mata tamkar ba shi ba ya ce"
Daga yanzu, daga rana mai kamar ta yau, ki kiyaye hannawa y'ayana abinci, ki kiyaye shiga hurumin da ba naki ba idan ba haka ba Mardiya gorin da
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 32
Chapter 33
Chapter 34
Chapter 35
Chapter 36
Chapter 37
Chapter 38
Chapter 39
Chapter 40
Chapter 41
Chapter 42
Chapter 43
Chapter 44
Chapter 45
Chapter 46
Chapter 47
Chapter 48
Chapter 49
Chapter 50
Chapter 51
Chapter 52
Chapter 53
Chapter 54
Chapter 55
Chapter 56
Chapter 57
Chapter 58
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 3 Chapter of 58