maciji ba wani jariri ba? Ke ki kiyayi maza walahi bana son fitinar da zata saka ransa ya bace ya batar da ke Najeeba! Ke kin san albarkar anmy kike ci, kin san albarkar su Abih kike ci, aman kina da izgili a abinda ya shafe shi, ke idan ba rigima ba ina ke ina tsayawa kafada da kafada da shi? Ai ko ba sarautar dake yawo a jinnin jikinsa ba shi din yayanki ne, yaya aka yi kike girmama yaya DAYABU ne? Bale ko a cikin mutane akan yi wani halayensa daban!
Najeeba mutumen nan adali ne, aman kuma inaai tabatar maki ya fi macijin nan da ya sumar da ke balaki idan kika tankwalo hakan zaki samu domin mu yan uwanki ba abinfa zamu iya yi maki NAJEEBA!
NAJEEBA dake kallonta ta yi murmushi tana dan girgiza kanta, a hankali ta dan yi atishawa tana dafe daidai kirjinta ta ce" tabas shi din wani ne na yarda, shi din ya girme ni kuma na yarda
Dubansu ta yi ta yi murmushi ta ce" sai dai ni din kamar yanda ya ce ne *MAGE ce ni mai kwonciyar d'aukan rai* zan dauki ransa a lokacin da bai ji ba bai gani ba bai san da zuwan lamarin ba
Tunda ya yi saken na kasance mace......zan nuna masa irin girman karfina a kansa! Shi da takobi take suka, ni kuwa da kalamai nake suka idan na tashi harbi da tawa kibiyar nakan harbi wajen da baya jin magani!
Ummulkhair da ta bude victago ta lakuto ta nufi wajen kirjinta tana shafa mata a hankali ta ce" ki dai bi a hankali, kar kibiyar ta kasance mai zuwa ta dawo ce
Ummukulsum wace itane ta fi su tsoro ta ce" ni dai dan Allah ki yi hakuri, a bar maganar wata ramuwa dan ba wajen bane, ko dan Anmy ai ya isa ya taka ki ki sada kanki, kinafa ji NAJEEBA yanzu yace auren aunty Zahrau karshen watan nan, ke kin ga Anmy kanta sai da ta zabura ta kale shi hakan na nufin ita kanta bata san da maganar ba bale Abih kuma ya zama wajibi su masa biyaya, ke kina kasa zaki wani ce ke aa?
Da yake ta fi rainata dama yan watani ne ta bata ba shekara ba sai ta ce" Ummukulsum ni abin ya fi maki ciwo dan nace zan rama ko? To na fada dan Allah ki dakeni ki huta mana tunda na ta a abokin tagwaitakarki!
Dawowar Anmy da waya a hannunta ya saka su yin shiru
Wayar ta mikawa Najeeba tana mai tsareta da mugun kallon idan bata amsa ba komai na iya faruwa
Wayar ta amsa da hannunta na hagu tana kallon saman screen din
Wauh na ce a lokacin da na ga wace ke zaune itama tana kallonta
Kallon kallo suke yiwa junnansu, har sai da matar ta dan saki murmushi ta lumshe idannuwanta ta bude cike da isa ta ce" ke yar Mutalab sai uwarki ta gaisheki ne?
Ta kasan idannuwanta ta kalli matar aman bata furta ko A ba
Murmushi ta yi tana yi mata kallo mai hade da madaukakiyar soyaya irin ta d'a da mahaifi
Ita kam ta ina zata bi y'ar tata ta dawo mata yanda take so?
Ajiyar zuciya ta sauke ta ce" yaya jikin ki?
Najeeba dai bata ce komai ba, Anky kuwa bata takurata ba ko amsar da ta yi ai ta yi kokari, hakama yan uwanta
Zahrau ce ta leko tana daria ta daga hannunta ta ce" Mama i miss u
Warcewa Ummulkhair ta yi tana ihun cewa" Mama, ni ke missing din ki
Ummukulsum ta amshe ta ce" mama ba ji ce tagwayenki ba?
Daria itama take a hankali ta dan juya idannuwanta wa'inda sukai wani farr da su gasu da girma masha Allah ga gyaran da suke dauke da shi ta ce" an matana, baku san irin yanda nake missing dinku ba, ina kewarku fiye da tunaninku, ina so na zo na ganku, na rungumeku, na ji me kuke ciki, ina son halartar auren Zahra, ina nan ina yi maku tanadin abubuwan da idan kuka saka baki daya damagaram sai ta girgiza
Bakinta ta tabe ta mike kwonciyarta tana lumshe ido, a kasan zuciyarta kuwa tana fadin" abinda kika fi kauri a kai kennan, abinda ya fi maki ni kennan wato abin duniya!
Anmy ta karasa kusa da ita ta ja bargo ta rufa mata, dan zaunawa ta yi gefenta a sanyaye ta ce" NAJEEBA
Kallonta ta yi da kallo irin na wanda take iya yiwa mahaifiyarta
Dukawa Anmy ta yi wajen goshinta ta yi mata kiss a goshin nata a sanyaye ta ce" ki huta kin ji? Dan ina so mu fita da ku duka gobe in sha Allah
Kanta ta dan gyadawa Anmy kafin ta maida idannuwanta ta lumshe
Su kuwa hira suka sha da mahaifiyar Najeeba wace du wasu abubuwa irin su wani lumshe ido, su shan iska, su shagwabe yannayi baki daya nata ne Najeeba ta kwasa, ba wai tana yi dan ta birge namiji bane, abinda dai ta kara a kai shine ta fahimci yana tsuma mazan sai take kara sakar masu shi
Kayan nasa ya tsurawa ido kafin ya watsar da su cikin kwondon kayan wanki
Kasan shower ya tsaya ya dora hannayensa jikin garun wajen yana jin saukar ruwa a jikinsa
Sai da ya gama ya darje jikin nasa da sabulu da soson wankansa kafij ya fito daure da tawul mai tsayi
A hankali ya karasa wajen miror ya tsaya
Turarensa ya dauko ya yiwa jikinsa bari da shi kafin ya jefar da kwalbar dan ya kare sai wani
Idannuwansa ya dan kurawa ido, yar yatsarsa ya kai wajen da bakin abin ya yi yar kwana tamkar wanda yake saka kwali
An haife shi ne da kwali a idannuwansa, shi kansa baya yiwa kansa kallon tsaf domin kwalin nan na tayar masa da tsigar jikinsa shi yasa baya matsewa mutun duba ko yace zai buda girman idannuwansa a kanka domin bai san yaya zaka ga idannuwan nasa ba
Juyawa ya yi ya ciro wata farar jalabiya marar nauyi sosai ya saka a jikinsa sannan ya saka dan gajeran wando
Wajen bed dinsa ya karasa ya kwonta yana mai adu'ar tsari dukan motsinsa
Rmt din Ac ya laluba ya dauka daga kwoncen ya kara masa karfi ya sada shi daidai kansa sannan ya lumshe idannuwansa
Tunanika ne birjik a cikin kwakwaluwarsa shi har ya yi watsi da abinda ya faru tsakaninsa da Najeeba domin ya ajiye hakan a fagen bata da kunya ne zai koya mata hankali a nitse
Baci ne ya sandeshi ya dauke shi , irin bacin nan wanda ke dan fizgarka sama sama
Irin abin nan dake zaburar da mutun a yayin da irin bacin nan ya zo masa ne ya zowa SARKI
Abin sai ya hade da a lokacin da ta kai masa damkar nan ta saka gwuiwar kafarta ta daki wajen da bai dace kafar tata ta kai ba, hakan ya saka shi kara jin wannan balakin da ya ji wanda da ba dan ya rintse idannuwansa ba a lokacin zai iya kurma ihu ne
A zabure ya farka yana mai kai hannunsa wajen ya damka yana mai rints ido domin sak mafarkin kamar a da gaske ne abin zai sake faruwa da shi
Da sauri ya kai dubansa wajen, idannuwansa ya mayar ya lumshe a cikin zuciyarsa ya furta" azaluma, na jikata da ruwa shine ta dakar min wajen da idan ta kasarani na gama wata takama a duniya ko? Ta Allah ba taki ba macuciya da lamarin maza ya gama bude maki ido!
Kuma lumshe idannuwansa ya yi yana tausar kansa
Bai taba nunawa Zinariya ta zo gareshi ba, ta yi kadan ba zinariya ba bai ga macen da zai je ya lalaba ko ya tura mata yar muryar cewa ta dube shi ba! Idan ta kawo kanta ne sannunta idan bata zo ba ko me zai ji yakan taushi kansa ya tirsasa kansa ne ya dane kamar yanda ya iya danne abubuwa da yawa a rayuwa
..........................................
Wajen karfe goma tuni sunna makeken fallonsa,
Fallon da ya saka yan matan daga kawunnansu sunna bi da kallo, falon da ya gama haduwa ya hade ya harhade
Sunna zaune ne saman maka makan kujerun falon na alfarma, kujerun kansu nishi suke sunna murmusmus a ido domin ba kananun kujeru bane baki dayansu irin na gidan sarakai manyan sarakai
Maka makan Ac din ne ke kara huro sanyi a falon wanda sakamakon zaman minti goman da suka yi har jikinsu ya gama daukan sanyin
Fitar da Anmy ne hakan ya sa dole kowace ta bi tsari na saka Alkyaba
NAJEEBA ta saka wata watsetsiyar atampa ja, an yi mata dinkin sket da riga ne , sket din daga baya an yi masa tsaga mai dan tsayi domin ta haye sama kadan sannan sket din ya kamata daga wajen duwawunta tsam sai ya tafi zuwat bai bude din nan ba
Rigar kuwa an yi mata dinkin zamani, an mata baban wuyan nan ne wanda ke saukowa kafada sannan daga gaban an dan yi yar tsaga an fitar da V
Hannayen kuwa an saka masu roba daga sama sun bude sosai daga cen kasa kuwa sun tsuke sakamakon robar da aka saka
Kanta kuwa dauri ne ta kashe na Zahra buhari
Ta rigaya ta saba da rashin zama fuskarta ba a gyare ba hakama ko fita zata yi sai ta tsuke ta gyara fuskarta tas
Hakama yanzun fuskarta a gyare take da simple mak up, idannuwanta kuwa ta yi masu sabo da dora natural gashin ido masu tsayi sukan karawa idon wani sirrin kyau da fuzga ne
A hankali ta sada kanta ta ce"Anmy, me zai hana mu bari gobe mu yi fitar nan? Duba da bai fito da wuri yau ba
Anmy ta buda baki zata yi magana jakadiya ta yi salama
Dukawa ta yi a hankali ta ce" Allah ya kara lafia, Elhaj Mutalab ya karaso
Kanta ta gyada mata dan haka ta mike da sauri ta fita
Tana fita bata jima sosai ba Abih ya shigo da salama
Murmushi ne kwonce saman fuskar Anmy tana amsawa kafin ta mike tsaye ta ce" yaya shigo zauna mana muma jiran fitowarsa ne muke
Karasowa ya yi ya zauna, yaren baki daya suka hadu sunna gaishe shi da yannayin murnar ganninsa
Hannunsa ya dora a gefen fuskar NAJEEBA ya ce" yaya jiki?
Murmushi ta yi ta dan dora gefen fuskar nata a hannun nasa
Ci gaba ya yi da shafa jelar gashinta dake yawo, dayan hannunsa kuwa Ummulkhair na rike da shi tana dan masaging daga kasa kuwa Zahra ta rike kafa daya tana masaging Ummukulsum kuwa tana daidaita masa ruwa daifai misalin shansa
Zamansa ya gyara ya ce" kin san me nake gani kuwa Anmynsu?
Anmy ta girgiza kai bayan ta ajiye masa abinci a plat domin komai a jere yake
Abih ya ce" sarka DAYABU ya saka aka yiwa yaren nan har shi aman banda NUSAIBA
Anmy ta dan yi turus tana kallonsa ta ce" kamar yaya banda Nusaiba? Me ta yi uta Nusaibar da ya wareta?
Abih ya dan yi murmushi ya ce" na tambayi kannen du sun ki fada min abinda aka yi, koma meye na san mai girma ne, aman kuma sun ki fada min abinda ya faru
Dubansu Anmy ta yi daya bayan daya a hankali ta ce" eyah, eyah, ashe zan ga haka da raina tun kasa bata rufe idannuwana ba?
Shigiwarsa da kamshin turarensa da ya shigo du kuwa da irin yanda dakin ke dauke da kamshin turaren wuta ya saka Anmy waigawa wajensa
Fuskarta ta sada, hankalinta ya tashi jin haka,
Yan matan ne du suka mimike aman Najeeba sai ta langwabe a jikin Abih ta lumshe idannuwanta tamkar bata san da fitowarsa ba
Da sauri Zahrau ta saka hannayenta ta mikar da ita inda ta sakar mata harare ita kuwa ta jinginar da ita a jikinta
Ya saka wata shigar ce mai birkita lisafin alhazai
Ya gama kashe shigarsa ne cikin shiga mai daraja
Ya fito a sarkinsa ga rawaninsa mai girma mai kayata sarautarsa
Ja ya yi ya tsaya gaban makeken abin turaran wutar da ake yi ana karawa kafin ya kone ake cirewa a zuba wani yana tashi a hankali domin ba garwashi bane a ciki toka ce mai zafin gaske
Hannunsa ya dora saman dokar wace ke dauke da zafin gaske domin ita ke saka turaren hayaki a hankali a hankali
Da yan yatsunsa ya marmatsa turaren dan ya isa haka sannan ya maida dubansa wajen mahaifiyarsa wace ta fi daukan hankalinsa gannin yannayinta
A hankali ya karaso har kusa da ita kafin ya rage tsayinsa sosai kansa sade ya furta" barka da safiya Anmy
Anmy ta dago ta sauke idannuwanta a saman kansa
Hannunsa ta kamo ta rike tana yi masa duba irin na ido cikin ido, a hankali ta ce" na kawo karar yan uwanka, ina so a mana shara'ar cikin gida , ina so ka zaunar da DAYABU MUTALAB tare da kannensa baki daya ka yi masu tambayar a kan me zasu ware daya daga cikinsu?
Najeeba ta lumshe idannuwanta, tabas itama tana son a hana wannan gaba tsakaninsu da yar kanwarsu, yarinyar zata baka tausayi ne idan ta ga daya daga cikinsu tana rarume rarumen ya dauketa tana kukan ya dauketa sai dai ba hali domin maganar dayabu maganar uba ce a wajensu, sai dai a yanzun fa ta ji azalumin nan ne zai yi maganar sai take jin a kan me?
Idannuwansa ya lumshe wanda hakan ke nufin amsarsa ne na ya karbi bukatar mahaifiyarsa
Agogon hannunsa ya duba a hankali ya furta" karfe tara na dare a falon karatu
Abih ya sauke ajiyar zuciya yana mai jin kanwar tasa a ransa, yana godewa Allah a kulun da ya bara masa ita, ita daya ta rage masa sai y'ayansu
Anmy ta dubi yan matan a hankali ta ce" na san ba zaku fadi laifin yayanku ba, kuma ba zaku fadi abinda kuka yi tsakaninku ba, aman ku sani idan kun ga kun samu wariyar kai to kasa ta birni idannuwana ne
Shi dai yana tsaye ne sai da ta gama ya kama hannayenta ya nufi wajen zama da ita
Yana zaunar da ita ya dawo suka gaisa da Abih kafin ya samu waje ya zauna
Du yan matan uku kasa suka kara zubewa
Aman Najeeba sai ta karasa saman kujerar da Anmy ke zaune ta dane gefen kujerar sannan ta dora kanta a kafadarta
Wannan karron kam komai a kan idannuwansa, mamakin yanda aka yi ta mike kan kafafuwanta da sauri haka da mamakin yanda aka yi ta manta gargadinsa da sauri haka suka saka shi tsaida dubansa a kanta
Lebensa na kasa ya dantse da hakoransa kafin a sanyaye ya buda bakinsa bayan ya gama harhada kalaman da zai yi anfani da su ya c e "
[ 1 / 3 0 , 7 : 1 7 P M ] U m m u S a d e e q : >?????>?????>?????>?????>?????>?????>?????>?????>?????>?????
* M A G E *
_ ( M a i k w a n c i y a r d ' a u k a r r a i ) _
>?????>?????>?????>?????>?????>?????>?????>?????>?????>?????
* N a *
* S A J I D A *
=ث?(' * T A U R A R I N M A R U B U T A N N I G E R ( A S S O . ) * ?
_ ( T s i n t s i y a m a d ' a u r i n k i d ' a y a ) _ >??
& * [ T . M . N . A ] * & =???=؊??
h t t p s : / / w w w . f a c e b o o k . c o m / T a u r a r i - m a r u b u t a n - n i g e r - 1 1 1 7 7 3 5 6 0 6 7 7 0 0 3 /
_ B i s m i l l a h i r r a h a m a n i r r a h i m _
2 2
C i k e d a i z a y a b u d a b a k i n s a y a kai dubansa wajen Abih, a hankali ya ce" Abih, in sha Allah auren Zahrau karshen watan nan na tsayar da shi
Abih ya ringa gyada kansa, tabas ya yarda da abinda ya yanke domin shi din uba ne a wajen yaren baki daya sannan shi da kansa ya isa da shi bale yaren
Sai da ya kara mintunna yana jin sai sanya albarka Abih da Amih suke, yaren kuwa du sun sada kawunansu
Anmy kuwa tana shafa bayan Najeeba, lalabata take domin bata da lafia konda safe da ta farka sai da ta sha maganinta na athsma domin numfashinta ba wai wani daidaituwa ya yi ba
Bakinsa ya buda a karo na biyu ya kaisasa muryarsa ya ce" sai dai ina so hakan ya zamo sirri
Ko da wasa bana so maganar ta fita tsakar gida bale waje domin BINTU kasheta aka yi
Gaba dayansu a zabure suka kale shi
Najeeba kuwa kamar wace aka jefo daga kan Anmy zuwa kasa sai gata ta wuntsilo tana kallonsa a tsorace
Abih ya yi gagawar furta" innalilahi wa ina ilaihi raj'une, wani irin kasheta aka yi? Wa ya kasheta?
Anmih ta kafeshi da ido, subahannalah kasheta? Wani irin kasheta? Gaba daya sai ta ji hankalinta ya tashi da maganar sannan ya sako cewar kar a fitar da maganar Zahrau kennan yana cikin tsantsamin wani ne ya yi hakan a tatare da shi?
Ajiyar zuciya ya sauke yana kallon Abih sannan ya kalli Anmih
A hankali ya ce" Allah masani, sai dai kowa ya yi taka tsantsan sawayen kowa a kirge yake
Gaba daya ta sha jinnin jikinta daga zaunen da take kafin ta maida dubanta wajen yan uwanta
Suma yanzun sarkin suke kallo a tsorace su duka
Yana gama magana ya mike tsaye
Baki dayansu suka sada kawunansu, a hankali suke furta" a huta lafia
Anmih cike da kaunar d'an nata kwaya daya da kuma tsantsar tausayin halin da yake ciki itama ta furta" a huta lafia
Sai da ya shige du suka dago da kawunansu
Rarafawa Zahrau ta yi da sauri ta dora kanta saman cinyar Anmih
Muryarta na dan rawa rawa ta ce" anmy, tsoro nake ji, kamar wanda ya kasheta yana iya kashe ni?
Anmy ta yi sauri girgiza kanta a hankali ta ce" ba zai kashe min ke ba, ba zai kashe min ke ba in sha Allahu
Allah zai hana, itama ki kadara lokacinta ne ya yi
A hankali Najeeba ta kama hannunta ta rike a nata itama cike da tunanin da ya gama hadasa mata zufa daga cikin jikinta
Fitar da suka fasa kennan, domin dama ta yi niyar fita da su ne su je wajen likita a kara duba Najeeba sannan su je wajen batuba wace ta yi niyar damka mata shirin Zahrau dan duka duka auren bai fi sati biyu ba
A dole suka koma bangarenta suka hadu ta saka a kawo mata kayayakin shirya amare a boye
Tun a ranar ta shiga baiwa Zahrau shiri irin na gyaran jiki da hade haden tsumi kala daban daban
Sai take jin dadin yannayin, dan ta tuna da, dan haka ta titino abubuwa irin na da wa'inda ta rike wuta sosai a zamanin mahaifin mai martaba ta ringa kawo dukan abin bukata
Kara kayan gyaran jikin ta yi sosai domin tana darzar fatar Zahrau sauran na darzar nasu da kansu
Tsumin nan ne kawai basa sha, sun rufe a falon Anmy na biyu sun shinfida katuwar tabarma sun dora mata leda du sun saka kannanun kaya sai raha suke, itama Anmy din sai daria takewa shirmensu har tsalen itama sai ta shafa suke hadin madara da kurkum fir ta ce ba zata shafa ba
Turaren wuta mai dadin kamshin ne ta zuba a dan kasko ya ringa ratsa jikin Zahrau,
Tana gamawa Ummulkhair ta dauko masu suma suka hadu a cikin abin rufa su uku suka zuba
Anmy ta bisu da da kallo ta yi murmushi tana girgiza kanta, fatanta Allah ya nuna mata nasu suma haka ta kimtsa su
Da sauri Najeeba ta cire abin rufar tana ta numfarfashi sama sama
Ummukulsum ta warce ta kara rufa su tana fadin" ke ja cen zaki wani bude mana dama mai numfashin kadangaru kawai
Najeeba ta matsa tana sauke numfashi, Anmy ta miko mata sansanyar madarar da ta kadawa Zahrau tana mata dariar itama ta ce" idan ba neman magana ba mai ya kaiki saka kanki ke mai cutar huka?
Amsa ta yi ta kafa kanta ta shanye tas sannan ta kalli anmy ta ce"Anmy ina son na turara jikina nima
Anmy ta ce" to zo nan
Mikewa ta yi ta karasa wajen da aka yiwa Zahrau
Zama ta yi saman kujerar Anmy ta rufa mata bargon aman kanta a waje ta zuba mata turaran mai sanyin kanshi ya shiga bin jikinta
Kafafuwanta ta wara cikin dabara ta kara matsa turaren wajen sosai harda rintse ido dan zafi ta ji na dukan wajen domin da pant a jikinta, tana ji su Nadia na fadin aba turara wajen da turaren wuta ko a yi matsi, to ita me hadinta da matsin? Ama n w a n n a n k a m s a i t a y i ( ( =?2?) )
S u n j i m a a w a j e n k a f i n s u k e f i t o w a s h i m a y a m a t a y i s u k a f i t o d a n a m s a r b a k i
B a y a n s a l a r i s h a ' i y a y a D a y a b u y a s h i g o t a r e d a N A J E E B ,
S u n n a s a n y e d a s h a d a n e a j i k i n s u w a n d o d a r i g a i r i d a y a s u n y i t s a f d a s u
Y a g a i s h e d a A n my yana dan murmushi irin yana neman gyaran nan, sai Anmy ta hade fuskarta ta kawar da kai
Murmushi ya yi a kasan zuciyarsa, bai ce komai ba
Sai da lokacin ya yi du suka nufi bangaren harda kananen
Ta lungun da zai sada su da dakin karatun suka bi suka karasa dakin karatun
A dakin nabar kujera daya tak ce sai shinfidun cafet na alfarma
Sai manyan kur'anai, da alo manya
Maka makan tableau ne dauke da sunnanyen Allah da ayatul kursiyu, da sunnan Muhammad (sallalahu alaihi wa salam), su Alhamdu
Ac hudu ne a dakin sai manyan panka tafka tafka dake kunne suma sunna aikinsu
Tun kafin su Zauna muryar Abih ta shigo da salama
Ba shi daya bane tare yake da matarsa hakan ya sa Anmy kallonsa da kallo irin na me ya sa zai zo da ita?
Kawar da kansa ya yi ya nemi waje ya zauna
Yanda aka yi zaman Abih ya zauna ne tare da Dayabu da Najeeb a bangare guda
Gefen daya kuwa Anmy ce tare da yan matanta kananun du sun dadane mata jiki da yan kananun alkuabarsu sun yi tsaf kamar ka sace su ka gudu
Manyan kuwa kowace na gefe gefenta , su kam yanzun basa sanye da Alkyaba sai zumbula zumbulan hijabai har kasa irin mai habar nan
Mardiya kuwa na zaune gefe guda itama ita daya, ga yarinyarta sai tsala ihun kuka take tana so ta saketa aman ta ki sakin nata
Ta sha wani rantsatsen lesh sai kyalkyali yake yarinyartama ta shiryata cikin wata riga doguwa mai shegen kyau, kyanta zai shaida maka kudinta
Sai ihu take tana kallon Najeeba, dan kaf a cikin yayun nata babu wanda ta shaku da shi irin najeeba dan goyata take ta yi ta mata doki , sannan du idan zata shigo sai ta shigo mata da tsarabar sweet
Wani uban tsaki ta ja ta dangwarar da yarinyar saman cinyarta ta dale keyarta ta ce" zan ci ubanki Nusaiba ki zauna min yau ga jaraba ba inda zaki je
Da sauro Najeeba ya kama bakinsa yana kallon yayansa, a fili ya ce" yaya Mardiya na zagin kanwata bayan ka hanamu zagi walahi
Duban Mardiyar ya yi ya ce" walahi ki bar zagar min kanwa
Mardiya da a cike take irin yanda Abih ya tasota ya tiso keyarta ya kawota a zaunar da su kan laifin da bata san me ta yi ta harareshi ta ce" sai ka hanani zagin nata shege mai katon kai
Da sauri ummulkhair ta dubeta ta ce" aman me yasa kika cika son neman fitina ne ke?
Anmy ta yi mata wani kakausan kallon da ya sakata sada kanta aman kasan zuciyarta a bace yake
Ai kuwa Bilkissu da ba kallon Anmy take ba ta ce" to fa, an tabota
Ranta ya kara baci ta ce" ke bilkisu an taboni ni ga mahaukaciya ko? Yan iska kawai da iyayenku kuke kuma du irin rashin hankalina na fi su domin ni na fi uwar kowa cikinku jimawa da ubanku
Da sauri Anmy ta dago kanta a karo na biyu ta sauke dubanta a kanta
Zahrau ta sada kanta tana jin hawaye na son zubo mata
Ummukulsum ta ce" me yasa idan kin tashi masifarki kike sako iyayenmu? A kan me zaki ringa koya mana muguwar tabi'a ne? Kin dai san uwa ba fin uwa ta yi ba ko? Kuma yai da gobe sai Allah kin san watarana zaki ji kunya? Kar ki manta a damagaram muke idan wannan bai san sirrinki ba wani ya sani balema a tafin hannuna sirrin naki yake
Rufe min baki shashasha, siriin nawa da kika sani meye? A ciki akoy cikin shege ne? Ko akoy yawon ta zubar ne?
Da sauri Dayabu ya dubeta, da yake mahaifiyar Ummukulsum bata zama waje dayan nan ba kennan gori ne ta mata na hakan
NAJEEBA ta kara sada kanta tana jin zuciyarta na yi mata tukuki, sam bata
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 32
Chapter 33
Chapter 34
Chapter 35
Chapter 36
Chapter 37
Chapter 38
Chapter 39
Chapter 40
Chapter 41
Chapter 42
Chapter 43
Chapter 44
Chapter 45
Chapter 46
Chapter 47
Chapter 48
Chapter 49
Chapter 50
Chapter 51
Chapter 52
Chapter 53
Chapter 54
Chapter 55
Chapter 56
Chapter 57
Chapter 58
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 16 Chapter of 58