ta gyara zamanta ta saka yar cokalinta tana dan diba kadan tana sakawa a bakinta
Wayarta ta dauka ta rubuta message kamar haka" *Na so zuwa dan gannin likitan zuciyana, sai dai na cika da fargabar irin yanda ya kasance mau cike da kwarjini a idannuwana, na yi masa kallon tsaf din da har na lura da irin hararar da matarsa ke jefa min wanda ya sakani jin tsoron zuwa wajensa a wannan rana Shin likitan zuciyana zai yi kin alfarmar fadawa gimbiya cewa na zo ya auna ni? Zai taimaka ya hada ji da wani likitan wanda zai auna ni? Domin ina tsoron tsumamun idannuwansa su sakani tsumewa na lume a cikin kogin da ba zan iya fitowa ba.....sako daga NAJEEBA MUTALAB*
Tura sakon ta yi ta ci gaba da shan ice cream dinta
Ta kuwa harbo a daidai, domin a lokacin ya gama shiryawa tarbanta, matarsa kuwa ta gama shiryawa cin ubanta a kofar clinik din domin zuwan wani bako a cikin bakar mota sidik ya saka baki daya aka fitar da kutanen dake ciki sai majinyata da masu jinyarsu daidaya, hakan ya sakata dakatawa a kofa ita da babar y'arta wace ta rakota su ci uban NAJEEBA! (HOUM)
har tsuma hannunsa yake a lokacin da ya karanta mesage din da sai ya rantse bai taba karanta mesage mai dadinsa ba ya shuga bata amsa kamar haka *bukatunki, ki tabatar da amsasu ne hannu bibiyu a wajen likitan zuciyarki, wa kike so ya duba maki zuciya da ya fi ni? Ni zan kula da ke na ririta zuciyarki na yi mata fadan da ba zata kuma yi maki suka ba, zan sanarwa mamanmu cewa kin zo, aman zan biki bashi ko ki zo na duba ki ko na zo na duba ki, domin bana wasa da zuciyar mai dauke da zuciyata!*
Samun kanta ta yi da sakin murmushin mesage dinsa, lale ba laifi kalamansa zafafa ne da har suka sakata kwafarsu
Lale yana da tsumamun kalamai kuma ta yaba
To yaya fagen aljihunsa?
Ta tambayi kanta tana murmushi
Sosai take jin dadin iskar wajen harma ta cika da mamakin ina mai kwali ne yau? Dan bata gansa ba, ko ya shige wani wajen ne? Ko ya koma abujar?
Lokaci na shige mata bata sani ba domin ta dukufa tana amsa mesage din tarin samarinta kowane daidai da takun tafiyarsa ciki kuwa harda sojanta da likitanta, da ambasador dinta
Sosai take nishadi harma yannayi tsoro da firgici suka barta
Bakinta take tabewa idan ta ga wani mesage din,
Takan girgiza kanta idan ta ga sakon kowani gara sai ya daki kirji ya turo mata sako
Wata yar dariya ta yi a bayane a lokacin d ata tuna maganar yayanta da yake cewa, mace idan ta zama ita kowama saurayinta ne, zata ringa haduwa da samarin kala daban daban, su gajale, su zinataile su wawaye, su mahaukataye da sauransu
Najeeba, ki kula a garin damagaram, domin mai damagaram ba zai hukunta wani dan ya maki laifi ba.....
Wannan maganar ita ta tunatar da ita da maganar dunkum cewar awa biyu ya bata
Wata irin zabura ta yi ta duba agogo
Karfe goma ce ta gota harda minti arba'in
Wato ta dauki awa biyu da minti talatin da bakwai
Wata irin dirowa da ta yi ta mike a guje ta saki ledar naman da ta yi niyar kaiwa yan uwanta da uce cream din ta aniya dankara gudu da alkyabarta a hannunta tana ihun kiran kabu kabu
Tana tsayar da dan acaba ta bashi jaka biyar hakoranta har sunna hadewa ta ce" ka falfala gudun mutuwa da ni ka kaini magama gudun hanyar gidan sarki
Mai yin na banzama bale harda kudi da kuma rokon mai hawan? Ai kuwa ya buga babur ya tayar ya warcu babur a dubub lamba ya nufi wajen da aka bukata
Adu'a kawai take tana saka alkyabarta jikinta na rawa tana fatan Allah ya sa bai zo ba
Na mutu ta fada a dan fili a lokacin da ta ga motarsa tsaye a wajen da suka ajiyeta, sannan daidai kudin nan da ta watsa da yake dare ne Allah bai kawo wanda hankalinsa ya kai wajen ba
Shikenan ta kuma fada tana son dirkowa aman sai da dan acabar nan ya sadata gata ga motar yana washe mata baki irin ya mata abin kirkin nan
Sai kawai ta ji ita kam ta gama yawo,
Dokar Anmy ce kiyaye acaba wace shi ya dora ita kuwa ta dorawa y'ayanta
Yakan fadawa Anmy cewa, bai ga daraja a macen da zata wara kafarta ta hau acaba ta zauna jikin mai mashin ya jata ba
Tuki da ya gaji birki da sauransu komai na iya faruwa a babur din nan
Gaba faya jikinta na rawa ta shiga kiciniyar saukowa
Kyar ita yake kallo, tun da suka karaso kusan minti talatin kennan ya ga kudadensa da ya bata a zubde a kasa
Wato ita bata cin halal shine ta je ta nemo haram dinta?
Sai kuma irin jiran da ta saka shi yi, zai rantse da Allah ko mahaifiyarsa bata saka shi jira daga lokacin da Allah ya kara daga darajarsa ko mamansa ke bashi daraja ta kiyaye lokutansa
Sai gata kuma an kawota a babur har kusa da motarsa
Karasa sauka ta yi tana yiwa mai babur ihun" ka yiwa Allah ka yi tafiyarka na ce ka bani cenji ne?
Sai hajia ya fada yana sara mata sannan ya tayar ya juya abinsa
Ja ta yi ta tsaya a wajen da take ta kasa karasawa wajen motar bale har ta shiga
Gaba daya ta gama yankewa kanta hukuncin id a n d a z u A l l a h y a k u b u t a r d a i t a y a n z u n f a ?
Z a b u r a t a y i a l o k a c i n d a t a g a y a n a . . . . . . . . .
M o r e c m n t m r p a g =??
[ 1 / 2 8 , 1 0 : 5 8 P M ] U m m u S a d e e q : >?????>?????>?????>?????>?????>?????>?????>?????>?????>?????
* M A G E *
_ ( M a i k w a n c i y a r d ' a u k a r r a i ) _
>?????>?????>?????>?????>?????>?????>?????>?????>?????>?????
* N a *
* S A J I D A *
=ث?(' * T A U R A R I N M A R U B U T A N N I G E R ( A S S O . ) * ?
_ ( T s i n t s i y a m a d ' a u r i n k i d ' a y a ) _ >??
& * [ T . M . N . A ] * & =???=؊??
h t t p s : / / w w w . f a c e b o o k . c o m / T a u r a r i - m a r u b u t a n - n i g e r - 1 1 1 7 7 3 5 6 0 6 7 7 0 0 3 /
_Bismillahir rahamanir rahim_
20
Zabura ta yi a lokacin da ta ga ana sauke madubin bayan wanda ta tabata a nan yake zaune
Sosai aka zuge shi sannan ya sauke dubansa kakausan duban nan mai abin tsoro a kanta
Fitsarine ta ji zai zubo mata daga mararta
Da sauri ta juya ta matsa sosai tana dan rawar nan dan ta rike shi kar ya zubo
Haska wajen ta yi ta yi bismillah ta janye wandonta kasa kadan ta duka ta shiga fitsarin nan domin idan bata yi shi ta tabata zata yi shi a motar cen
Kansa ya yi saurin kawarwa daga wajenta, amintacensa kuwa dama kansa a sade yake yana cike da mamakin lalle yarinyar nan ta isa
Su suke tare da sarki SHAHEEd , wato gurnanin zaki
Su suka san waye Sarki SHAHEED
Yaya aka yi ta taka doka haka har haka?
Sai da ta kusan karasa fitsarin ta tuna bata da ruwan kama ruwa
Gaba daya ta ji jikinta ya kwashi wani yamyamyam na kyamar kazanta
Bata wasa da tsaftar wajen nan ko da wasa gashi yau ta yi fitsari a wajen nan sannan a gaban sarki gashi babu ruwa
Sai da ta gama sosai ta cire wandonta dan ba zara iya mayar da shi ba ta mike a hankali jikinta na ci gaba da rawa
Tana tunkaro motar ya kuma dagowa yana yi mata duba irin na mamakin fitsarine ta yi d agaske haka gabansu ? Lalee ta cika rashin kamun kai da rainin hankali
Kara datse lebensa ya yi na kasa yana gannin lokacin da ta karasa isowa ta ja ta tsaya daga nesa gaba daya jikinta na rawa hankalinta a matukar tashe baki daya wani kuzarinta ya bace sai tarin tsoron dake cin ranta
Dubansa ya cire daga kanta ya kalli wajen amintacensa
Sai da ya dauki mintunna kafin ya ce" bani faro
Da sauri ya buda wajen da ake saka ruwan ya dauko ya juyo gaba dayansa ya dan risina ya mikowa sarki
SHAHEED ya mika hannunsa na dama ya amsa yana rike da ruwan
Cen ya saka hannunsa zai bude hakan ya sa amintacensa saurin kokarin budewa dan ya bude masa
Bai bashi damar yin hakan ba ya dakatar da shi da hannunsa
A hankali ya bude kofar
Ziro kafarsa da ya yi ne ya saka NAJEEBA daga hannayenta duka biyu ta dora saman kanta
Gaba daya ta ga wajen ya masu kadan idan tace zata gudu ta rantse ba inda zata je zai kamata
Ruwan nan masu sanyin gaske sannan babar butali ne ya yi tsaye daga jikin motar
Da hannunsa ya yafito ta
Kafafuwanta ta shiga dokawa a hankali tana jin uwa ta ce na ki, sai dai gannin daga ita sai shi fa sai mai shigar masa taraya sai kawai ta ji kafafuwanta na kaita inda yake tsaye
Daga dan nesa ta ja ta tsaya ta sada kanta
Kansa ya kara gyadawa gannun bata zube ta ringa yi masa fadanci ba
Rabonsa da ya ga mutun ya yi tsaye haka kansa da kansa ba tare da ya bashi izinin hakan ba tun barin garin sarkin agadez , sai Anmy wace take mahaifiyarsa
Ko matarsa takan zube ne kafin ta nemi wani lamarin a wajensa
Yatsarsa baba da ta tsakiya ya hada ya dan bada wani sautin da ya sakata dagowa
Kudaden daje zube a kasa ya nuna mata da idannuwansa
Itama kudaden ta bi da kallo domin wutar motar a kunne take
Da sauri ta karasa ta duka tana tsintsincewa
Sai da ta gama dauke dukan wa'inda take ganni ta harhada su ta karaso kusa da shi wannan karron ta miko masa su
Hannayen nata da kudin duka ya bi da kallo,
Wa shi? Take mikowa kudi haka?
Sai abin ya so bashi daria a kasan zuciyarsa
Idab ya fahimta yarinyar banda rashin kunya harda rashin hankali ke damunta
Yau gashi da rigar sarautarsa a tsaye a gaban yar yarinyar nan marar kunya tana miko masa kudi hannu da hannu a tsaye kikam
Baban goran ruwan nan ya saka hannunsa ya bale cikin dakiya ya mika mata muryarsa a kausashe ya ce" *ki tsaftace najasar dake tare da ke*
Najasa? Ta tambayi kanta, ko fitsarin da na yi? Ta kuma tambayar kanta
Amsar gioran ruwan ta yi ta matsa gefe kadan ta duka ba abinda ya dadata da kasa domin ita ai ganni take dare ne yayama aka yi ya gane fitsari na yi? Take tambayar kanta
Ruwan sanyi ne da shi, gata bata saba anfani da ruwa masu sanyi ba sai dai ita kanta yanda take jin jikinta na yi mata kaikayi dole ta yi anfani da ruwan tana kara matse hikinta ta mike tana ajiyar zuciya
Ruwan ta riko ta juyo sai dai ganshi a tsaye a wajen da yake
Dan bakinta ta tabe a ranta tana ayanna wato bayan cin haram ko dai kwarto ne? Yo wannan saka ido har ina?
Karasowa ta yi kanta a sade a kasa dan nesa da shi kadan
Gannin bata yi abinda ya yi jiyar sai ta yi a yau a waje a bakin titi ba ya saka shi juyawa kusa da tagar amintacensa
Murya a kausashe ya ce" bani biyu
Dauko masa biyun ya yi masu sanyin balaki ya miko masa
Amsa ya yi wannan karron ya ringa takawa cike da kasaita da isa har ya karasa inda take tsayen
Buda goran ruwan ya yi cikin dakiyar fuska ya ce" ki dauri niyar yin wankan janaba a zuciyarki
Da sauri ta dago kanta da wani irin tsoro da mamakin jin abinda ya fada
Sai dai kafin ta gama fahimta tuni ya shiga tsiyaya mata wannan ruwa mai sanyin balaki tun daga saman kanta mai dauke da alkyaba da hijab a kasa ruwan na ratsata har cikin jikinta ga yannayi na sanyi ga kuma tana da cutar huka wato athsma
Gaba daya ta rikice jin saukar ruwan nan hakan ya sakata kwala kara tana furta" ANMY
kafarta ta daga da niyar kwatar kanta sai dai abin ya gagara dan wata damka da ya yiwa hannun nata da hannunsa daya ya kuma bale dayan da hakorinsa shima ya daga tun daga kan nata ya shiga bulbule mata shi
Da karfin gaske ta fincike Alkyabar dake saman kanta da dayan hannunta, ido rufe ta yi cikinsa ta rukunkumeshi gaba daya jikinta na rawa tana jin numfashinta na neman fara bugawa
Bakinta ta buda zata bashi hakuri sai dai ta gaza sakamakon jan shedarta da ta fara har numfashin ya fara wani kara sama sama yana hiiiiiiiiik, hiiiiik tamkar wace ta zo fitar rai
Sarai ya san cutarta kuma ya san ta tashi ne aman bai daina ba sai da ya gama bulbule mata yana son bambareta da jikinsa aman ta mane masa tamkar cingan
Yana gamawa ya saka hannunsa ya dago fuskarta
Muryarsa a kausashe yana yi mata duba irin na tsana ya ce" me ya sa kika zabi zubar da mutuncinki? Idan na iyayenki bai dameki ba naki fa? Ke kin kasance sakarya a cikin mata
Ban taba jin kyamar halita irin yanda nake kyamar halayanki ba, na tsani na ji a cikin kanena akoy ki! Ki sani tsakanina da ke ba alfarma ko tausayawa!
Magana ta karshe da zan maki bayan ta idannuwana da nake maki kan ki kiyayi hada hanya da ni, sarkinki nake ba tsaranki ba! Idan ke takamarki *Mage ce* ni kuwa *kaifin wuka ne NAJEEBA MUTALAB!*
gaba daya ta idasa sikewa ta tafi luuuuu ta fada a jikinsa sumamiya
Baya tare da wani damuwa ko firgicin gannin ta summe masa
Hasalima idasa rikota ya yi ya turata motar sannan ya shiga gidan gaba domin ko suturar jikinsa kyamatarta yake bare zama kusa da ita a karo na biyu bayan ta gama wannan wulakancin
Amintacensa kansa a kasa, magangannun sarki tas a kunnayensa sai dai bai san wanka ne ya mata da kayanta a saman titi ba
A hankali ya tashi motar zai nufi cikin gida, muryarsa a cinkushe ya ce" Degza da allura
Yana gama fada ya maida dubansa bakin titin yana mai bale agogon hannunsa
A nan ya yarda agogon , ya kuma bale botiran rigarsa daga ciki
Da gudu ya shiga pharmacy ya amso maganin da allurar
Yana kawo masa ya duka ya mika masa sannan ya juya ya shiga wajen direban
Ruwan Allurar ya fashe kanta ya tsira tsinnin allurar ya zuki ruwan ya saka kwalbar cikin ledar
Sunna karasawa cikin gida hanyar sirrinsa ya fito da kansa cikin takamarsa ya buda bangaren da take
Hijab din nata ya kama ya cire dan samun wajen da zai mata allurar
Rigar dake kasa ta atamfa ce mai damamen hannu
Jikinsa ya laluba ya ciro wata yar siririyar wuka mai kaifin balaki ya kama rigar ya yaga wajen hannun
Allurar nan ya caka ya tsira mata ba tare da ya bi ka'idar a hankali ba domin zafin tsiya ne da ita
Yana gama tsira mata ya dauki ruwa ya dan warwatsa mata
A zabure ta farka daga summar wahalar da ta yi, idannuwanta ne suka sauka a kan macijin da ya cire masa dafinsa suka zuki abubuwan bukata a jikinsa hakan ya sa ya kasa motsawa sai ya ki mayar da shi cikin kwalbar dan bashi da niyar kashe shi, zai mayar da shi wajensa ne
Gefen fuskarta na gogar jikinsa hakan ya sa ta sauke ajiyar zuciya ta koma duniyar summa daga kwoncen da take
Tsaki ya ja a cikin zuciyarsa gannin summan fa ta kuma yi
Dubansa ya kai wajen amintacensa
Ba zai iya tura shi ya kaita bangaren Anmy a irin wannan lokacin ba, idan kuwa shine zai kaita dole ya bi ta hanyar da zata sada shi da fallon Zinariya sannan ya bi ta fallonsa ya bi ta doguwar hanyar da zata kaishi bangaren Anmy din ba tare da ya bi ta hanyar da kowa kan iya ganninsa
Hannunsa daya ya mika ya daukota
Dauka irin na yara ya yi mata a hannayensa bai rufe motar ba bai masa magana ba ya juya ya nufi bangaren Zinariyar
A daidai lokacin tana zaune a fallo ita da yayarta sunna cin abincin da ta saka aka masu wato gasashen naman rago ya ji kayan hadi sai turiri yake sunna ci sunna hirarsu hankali kwonce
Kasancewar hanyar ta sirri ce, ba'ai masa iso ko ta saka ran zai iya zuwa a irin wannan lokacin
Jin karar bude wajen ya sakasu waigawa a tare
Da yake kofar mai dauke da dan haske ne sai suka ga yannayin tsayi da fadinsa hakan ya sa da sauri suka mike yayar nata ta warci hijab dinta ta saka haka itama
Kofar ya turo da kafarsa
Kasancewar tafiar nan tamkar ta giwa a jinninsa ne ko yanzu ba sauri yake ba a hankali yake tafia da uta a hannunsa
Gaba dayansu suka zube kansu a kasa har sunna hada baki wajen furta" barka da war haka mai martaba
Bai iya amsawa ba, da kansa kawai ya dan gyada kai,
Jin kamar zai wuce da kyakyawan takalminsa ne ya saka Zinariya dago kanta a hankali
Gabanta ne ya kwonci kwonci ya yi faduwar da ita kanta ta kusa zubewa daga duken da take
Ya shige ciki hakan ya sa ta kara zabura ta mike
Da sauri yayar tata ta riko hannunta ta ce" ina zaki je?
Warve hannun nata ta yi ta ce" baki ga waye a hannunsa ba? Yarinyar nan da nake fada maki nace da ita yar talakawa ta mari fuskana itace a hannun mijina mai daraja me ya kawota bangarenmu? Me ya hadata da shi? Me ya sa ya dauketa da hannayensa masu matukar daraja da kima a duniya baki daya?
Aman idan kika je me kike son yi bayan kin san sarkinki ne shi kuma kanwarsa ce? Ta fada tana son tareta
Hannayenta ta kuma warcewa tana kallonta ido cikin ido ta ce" shi ya sa kika kasa gagarar kishiya! Koda kare jinni biri jinni ni Zinariya sai na kafa tarihin zama daga ni sai mijina
Babu shegiyar da ta isa ta hau hannunsa haka ya bi ta falona na barta da hankalinta da ranta koda kuwa zan yi yawo tsirara ne!
Tana gama fada ta juya da sauri tana bin bayansa, yayar tata kuwa ta yi gagawar daykar waya dan kiran mamansu
Tun da ya shigo Anky dake zaune da su Zahrau suka zabura sunna kallonsa
Da sauri Anmy ta karasa dan itace kawai zata iya tarbansa
Har hade maganarta take wajen fadin" sususubahannalah, Shaheed me ke damunta kar dai ciwon zuciyar ya yi tsanani
Irin yanda ta rikice yake kallo, da ta san shagalinta ta je ba asibiti ba zata rikice haka?
Anmy ta ce" likitan ya yi kurana yake ce min da sauki aman zata koma ya kara bincikata, wai summa ta yi ne Shaheed?
Ta fada tana rungumota jikinta a lokacin da ya ajiyeta saman kujera
Tsayawa ya yi yana kallonta, yayaunta kuwa du suka duduka kansu sunna faman yi masa barka da warhaka
Bai baiwa Anmy amsa ba ya juya a hankali zai tafi
Har ya kusan fita ya juyo, muryarsa a hade ya ce" ZAHRAU, ki shirya aurenki karshen watan nan idan Allah ya aminta
Yana gama fada ya juya ya fice a dakin
Kicibis dukai da ZINARIYA wace ta labe dan jin abinda ya hada shi da ita har ya rungumota haka, sam bata ji takun fitowarsa ba
Bai kulata ba ya fice ya barta kai sade tana fadin" a huta lafia mai damagaram
Yana fita suka rikice, kan mai dankarawa da gudu ya daukowa Anmy ruwa, sai mai kara rungumarta
Da gudu Anmy ta yi ciki dan kiran likitansu ,
Tana shiga Najeeba ta ja dogon numfashi
Idannuwanta a rintse tana jikin Zagrau bata bude ba ta furta" *BAN TABA TSANAR HALITA IRIN YANDA NA TSANEKA BA! NA RANTSE SAI NA RAMA A KANKA KO A KAN ALADEN MATARKA!*
a tsorace suke kallonta, Zahrau ta dora hannunta gefen fuskarta a hankali ta buda bakinta zata yi magana sai ga Anmy ta fito da wayar a kunnenta tana fadin"
. . . . . . . . . . . . . . . =??[ 1 / 3 0 , 1 1 : 5 8 A M ] U m m u S a d e e q : >?????>?????>?????>?????>?????>?????>?????>?????>?????>?????
* M A G E *
_ ( M a i k w a n c i y a r d ' a u k a r r a i ) _
>?????>?????>?????>?????>?????>?????>?????>?????>?????>?????
* N a *
* S A J I D A *
=ث?(' * T A U R A R I N M A R U B U T A N N I G E R ( A S S O . ) * ?
_ ( T s i n t s i y a m a d ' a u r i n k i d ' a y a ) _ >??
& * [ T . M . N . A ] * & =???=؊??
h t t p s : / / w w w . f a c e b o o k . c o m / T a u r a r i - m a r u b u t a n - n i g e r - 1 1 1 7 7 3 5 6 0 6 7 7 0 0 3 /
_ B i s m i l l a h i r r a h a m a n i r r a h i m _
2 1
A s u m e n e t a k e d octer ki zo yanzun
Da sauri ummulkhair ta ce" Anmy ta farfado
Anmy ta ajiye wayar tana karasowa itama ta duka ta kamo Najeeba ta rungumeta a jikinta tana fadin" Najeena, meye? Jikin ne ya saka kika suma? Likitan ya nuna min da sauki kar na damu kuma yayanku ya shigo da ke a summe meye ne?
Najeeba kam irin yanda zuciyarta ke kunna bata da bukatar komai sai na kadaicewa
Ga jikinta du a jike yake gashi zuciyarta na yi mata zafi tamkar ta ciji babu
Anky, zan kwanta
Tsurawa fuskarta ido Anmy ta yi na dan lokaci kafin ta shiga taba jikar jikinta da cirar hannun rigarta sannan ba alkyaba a tare da ita ba hijab dinta
Tana kallonta ta ce" me ya fari da ke kika dawo min ba a yanda kika fita ba?
Najeeba ta ja numfashinta da kyar ta ce" Anmy, athsmana ne ya tashi,
Anmy ta kara jin tausayin yarinyar fiye da sauran yan uwanta
Kamata suka yi suka nufi dakinsu da ita
Saman bed din suka shinfideta Anmy na ta shafa kanta tana kallonta
A hankali ta ce" Allah ya baki lafia bara na je na fadawa yaya cewar da sauki
Mikewa ta yi ta juya ta fita
Tana fita da sauri Zahrau ta riko hannayenta ta ce" me ya faru da ke? Me ya maki? Waye kika tsana? Me aka yi?
Gaba dayansu hankalinsu a tashe yake su duka
Najeeba ta cije lebenta na kasa tana jin wani irin kunci a zuciyarta
Muryarta a kausashe ta ce" SHAHEED NE, Shaheed ne ya min wankan janaba
Da karfi suka kusan fadi a tare kan me cewa" quoi? (What?), sai me cewa Me?
Idannuwansu a zazare a waje cike da tsoron abinda ta fada din
A hankali ta ja hancinta ta tashi ta dan jingina tana kallonsu, sai da ta kuma lumshe idannuwanta ta bude , a hankali ta kabarta masu abinda ya faru
Kwarai sun ji tausayinta sai dai Zahrau na budar bakinta sai ta ce" Najeeba, rashin jin maganarki ke jaza maki fitina
Ke da ya sauke ki ya ce ki je ku hadu a lokaci me ya hana ki zuwa ki yi jiransa?
Ummulkhair ta ce" bama wannan ba, tsakani da Allah ciwon zuciyar nan dama karya ne Najeeba? Ke kam bakya jin magana ban san me ke kwakwaluwarki ba
Ummukulsum ta ce" NAJEEBA, kudin da ya baki kika watsar? Sannan kika yi fitsari a gabansa a gaban yaronsa? Me kike so ya dauke ki? Najeeba ko bai yi tunanin baki da kamun kai ba ai kema kin san baki da shi ko?
Najeeba ta lumshe idannuwanta a hankali ta ce" eyah, me zai hanna ku taru ku min dukan tsiya dan na taba dan gwal?
Dagowa ta yi ta firfito da idannuwanta ta dauki hannunta ta nuna kanta ta ce" na rantse da wanda raina ke hannunsa bashi da mutunci, kuma bai sani bane irin yanda ya yi ikirarin ya tsane ni na fi shi tsanarsa, zan nunna masa a aikace, ba dai ni Najeeba ba? Nice ya kwontar jikin maciji?
Kallon Ummukulsum ta yi ta ce" ji wani kililin kasau da ita kamar ta Allah ke nan kyankyaso ne ya shiga rigarki kika cire rigar da wasu kannanun nonuwanki kina ihu a gaban kannenki,
Ummukulsum ta ce" ai dai ni ban yi fitsari a gaban mazan da ba maharamaina ba
Ta buda baki zata rama Zahrau ta ce" kun ga ku saurara mu ji da abinda ya sha mana kai mana haba da Allah, ku kawai baku da aiki sai fitina? Maganar zaki rama bata taso ba! Ki rama me? Ta yaya? Ki bari ki mutu maza su kaiki ba mata ba dan walahi da zaki ji tarihin bawan Allahn nan sai jinninki ya hau, baki yi mamakin yanda aka yi yake damkar maciji da hannunsa katon
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 32
Chapter 33
Chapter 34
Chapter 35
Chapter 36
Chapter 37
Chapter 38
Chapter 39
Chapter 40
Chapter 41
Chapter 42
Chapter 43
Chapter 44
Chapter 45
Chapter 46
Chapter 47
Chapter 48
Chapter 49
Chapter 50
Chapter 51
Chapter 52
Chapter 53
Chapter 54
Chapter 55
Chapter 56
Chapter 57
Chapter 58
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 15 Chapter of 58