karuwar gida, Kaine d'an iskan gida, tinda har mai aiki kayiwa FYA'DE, Hafeez yafad'amin duk wani abinda kakeyi Wanda babu kyau, sabida kaga ni Makauniya Ce, shiyasa zaka musguna min? Yaya Bilal kasani ni Makauniya Ce ba kurma ba, ganine kawai banayi Amma inajin komai, an fad'a maka nima inason makantar ne? Kuma koda inaso ai Allah ne yayini haka, ko bakasan a cikin Alkur'ani mai girma Allah ya ambaci Makafai ba? Idan kai jahili ne to bari nakoya maka"
"A cikin Alkurni, suratul bak'ara shafi na uku aya ta goma sha takwas Allah ya Ambaci makafai, inda yake cewa (Summun bukmun umyun fahum laa yarji'un)"
✔ote & comment
_Jiddah S Mapi_
*بسم الله الرحمن الرحيم*
🌸🌸🌸🌸🌸🌸
*MAKAUNIYA CE*
🌸🌸🌸🌸🌸🌸
By
Jiddah S Mapi
Page 15....
*___________________________________*
*🌈KAINUWA WRITERS✍🏼 ASSOCIATION*🤝🏻
```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}```
https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation
"Fine! tinda kinsan kur'ani, to Aure zanyi kuma mata biyu rana d'aya, don nalura bakida kunya, wata kila idan nakawo wacce zata baki wahala zaki shiga hankalinki"
"Haba Bilal? Bakasan cewa Allah ya halatta maka ka Auri mata hud'u bane? Ko ka manta da inda yake cewa (fankihu ma d'aba lakum minannisa'i masna wa sulasa warba) Ku Auri abinda yayi muku dad'i daga cikin mata biyu ko uku ko kuma hud'u, ni Asuwa dazan ja da maganar Allah, bugu da k'ari niba sonka nake ba, danasan kai za'a Auramin dabanyi kuskuren yadda ba, Amma duk da haka kai mijina ne kanada hakki akaina, Wanda har sai ranar da Muka rabu kafin ya sauka"
"Ummm dama kinsan Al-kur'ani haka, shine kuma kike aikata zina? Ko kin manta inda Allah yake cewa (wala tukribuzzina) kada Ku kusanci zina, wannan kam kin manta ko?"
Cikin zuciyar Minal kuna yake, tarasa meyasa Bilal ya tsaneta, "me nayi maka kake min sharrin mafi munin Abu aduniya?"
Bilal fita yayi tareda bankad'o mata kofar,
"Yanzu aka fara wasan Malam Bilal, cewar Daddy daya tsaya abakin kofa yaji duk abinda sukayi"
Wucewa Bilal yayi, kamar bega kowa ba, Amma zuciyarshi yasan akwai mutum abakin kofa, b'uya yayi a inda yasan baza'a ganshi ba, tsayawa yayi yana jiran Wanda yashiga d'akin yafito, cikin ikon Allah saiga Daddy yafito daga d'akin, rud'ani Bilal yashiga, to meya kawo Daddy wajen Minal? Kuma saida nafita kafin yashigo, anya bawata akasa?
Astaghfurullah, nasan akwai wata dalilin dayasa yazo, don daddy ko a mafarki bazai cuceni ba, saidai wannan yarinya me kama da Aljanun, nasan zata iya yin komai Dan ba sona takeba"
Wayarshi ce tafara ruri, yana dubawa yaga sunan Abba yana yawo, zuciyarshi ne tayi dumm, da sauri yafurta "Abban Latif?" Mezan fad'a mishi yanzu? Nashiga Uku.
Daurewa yayi yad'auka "Hello Abba ina wuni? Bilal ba gaisuwa ne yasa nakiraka ba, kasani cewa ni Abokin mahaifinka ne tun muna yara, nasan komai nashi, nasan halinshi mutumin kirkine, tun lokacin dayake Raye ina kula da companyn shi da dama, ban cutar dashi ba sai yanzu daya mutu zan cutar dashi? Bilal kaida wannan Daddyn naka kun bani mamaki, shine abinda zaku saka mana dashi? Shikenan Ai akwai Allah, ina rokan Yashiga tsakanina daku, anjima kazo ka karb'i komai na dukiyarka dayake hannuna, kitt yakashe wayar"
Jikin Bilal yayi la'asar a fili yafurta "da wanne zanji? Da Minal datake cin Amana na, koda tunanin meya shigar da Daddy d'akina, ko kuma Abban Latif dayake so na karb'i komai nawa na wajenshi?"
"Da Afrah zakaji yaya Bilal, ka zubar da duk wata damuwa ka Aureni, nayi maka Alkawarin Ranan daka Aureni zan bankad'o maka sirrin dakake son kasani, cewar Afrah wacce hajiya babba ta aikota takira Daddy, da zuwanta taga Bilal yana lab'e itama saita lab'e"
"Juyowa Bilal yayi yana kallon Afrah, wacce tasha Riga da wando, hannun rigan an yanka dogo dogo kamar jelar shanu, Tsaki yaja yaci gaba da tafiyarshi"
Dasauri ta tari gabanshi ta tsunkuya har kasa tarike kafarshi "yaya Bilal nasan nayi maka kaifi a rayuwarka, wallahi na tuba bazan kara ba, idan kace kar in kara sa wando da gyalle wallahi bazan kara ba, nidai kawai ka Amince zaka Aureni koda baka sona, ka dubi girman Allah ka yadda da buk'ata ta, wallahi idan naganka da wannan matsiyaciyar matar taka, sai naji zuciyata kamar zata fashe tsabar kishi, bana son ka rab'e ta ko kad'an, hasalima kwana dakukeyi a d'aki d'aya shiyafi komai d'agamin hankali, yaya Bilal ka taimakawa k'anwarka, please"
"Baiyi mata magana ba kawai ya kwace kafarshi yabar wajen, baisan wani yanayi yake ciki ba, shin tsanarta yakeji ko tausayinta? Baisan meyasa yarinyar take sonshi dayawa ba, son datake yimishi yayi Over, shi yanzu ji yake kamar ya tattara kayanshi yagudu yabar garin Gombe ma gaba d'aya, yaje inda babu Wanda ya sanshi, yayi rayuwa cikin farin ciki ba irin rayuwar dayake ciki ba, wata zuciyar kuma tace " idan ka tafi wa zaiyi maka binceken Abinda yake faruwa? Kamata ace nad'au fansar Ran iyaye na Dana k'anwata kafin nabar duniyar ma baki d'ayanta"
"Hajiya babba ce ta karaso inda Afrah take kwance tana kuka, d'agota tayi tana mata matsifa, " Haba Afrah, ya zaki zubar da Ajin ki na 'ya mace ki sunkuya har kasa kina rokan namiji ya Aureki? Duk abinda kukayi ina jinku, Kinaso ki taunawa mahaifinki Asiri akan Namiji? To ki sani idan kika taunawa mahaifinki Asiri, kika Auri wannan d'an iskan yaron, kinga wannan jikin naki kamar an sawa fulawa yist? To wallahi saikin koma kamar matarshi tsabar ramewa, kai gara itama ai halittar tace haka, kuma ita idan ta rame zatayi kyau, sabida Asalinta Farace, Amma ke idan badan man bilicin ba ai da sai gyaran Allah, ko kallo bazaki ishi mutane ba, kinga ga rama ga bak'antaka saiki dawo kamar An soya kwad'o"
"Haba Hajiya babba wannan ai cin fuskata kike"
Waya fad'a miki?
Ni gaskiya nake fad'a gara ki hakura mushawo kan matsalar a hankali, tinda Allah yarufa mana Asiri kina shafa man dazakiyi haske, gaki da jikinki tab'as b'as, sai mubi komai a hankali ko?"
"Gyad'a kai Afrah tayi nan suka nufi d'akin Hajiya babba suna kullace kullace".
"gidansu Latif Bilal ya nufa, d'akin Abban Latif ya nufa danufin bashi hakuri, yana sallama Abba yamike yace "yawwa ga takaddun gidajenka, da companonin ka, Bilal banason komai yakara shiga tsakaninmu, Wata shari'ar kuma sai a lahira"
Bilal hakuri yarink'a bawa Abba, tareda ce mishi bincike yakeson ayi shiyasa Yace a ajiye Latif, kuma babu abinda 'yan sanda zasuyi mishi, da kyar Abba ya hakura, kafin Bilal yatafi"
"Latif ana kulawa dashi sosai a station, Idan kaganshi baza kayi zaton kamashi akayi ba, har wani haske yakeyi"
_washe gari_
"Minal ce zaune kan d'aya daga cikin kujerun d'akin, muryan Afrah taji tana cewa " Haba yaya Bilal meyasa zakayi shiru, ko kana tsoron kada matarka tajimu ne? Ni gaskiya idan zamuyi soyayyarmu kawai mu fito fili mu nunawa duniya, adaina wani b'oye b'oye, kowa tasan Akwai Aure tsakaninmu dakai, Dan Allah kayi magana yaya Bilal nawa kajiii?"
Zuciyar Minal ce tayi wani kara dummm "soyayya suke yi dama? Haba no wonder Ruwa bata tsami banza, yanda take nuna kishi afili nasan Akwai wani Abu a kasa, Ashe sune manyan karuwan gida, yake kora kunya da hauka?
Allah yashirya al'ummar musulmai"
Murmushin nasara Afrah tayi ganin yanayin fuskar Minal ya sauya, azuciyarta tace "zakiga munafinci yarinya, sai kin bar gidannan da kafarki, bankad'o kofar tayi Alamar ta tafi".
"Bilal ne yafito daga toilet, sabida yana d'an jin surutu kad'an kad'an " wannan yarinyar kodai Aljanu gareta, idan ba Aljanu ba wazaiyi magana shi kad'ai"
Bud'e kofar falo yayi, nan yaganta zaune ita kada'ai "ke? Dawa kike surutu?"
Minal kuma gani tayi ya mugun raina mata wayo, yanzu sugama magana da Budurwarshi kuma yazo yana tambayarta dawa take magana?
Murmushin karfin hali tayi kafin tace "da budurwarka wacce tafito daga d'akin nan yanzu muke magana"
Budurwata? Cewar Bilal "lalle kin tabbata me Aljanu,
To Allah yakawo sauk'i"
✔ote & comment
_Jiddah S Mapi_
*بسم الله الرحمن الرحيم*
🌸🌸🌸🌸🌸🌸
*MAKAUNIYA CE*
🌸🌸🌸🌸🌸🌸
By
Jiddah S Mapi
Page 16...
*___________________________________*
*🌈KAINUWA WRITERS✍🏼 ASSOCIATION*🤝🏻
```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}```
https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation
"Ni banida Aljanu hasalima kora kunya kakeyi da hauka, ina kara tunatar maka niba kurma bace ni MAKAUNIYA CE, naji duk abinda tafad'a, sandarta ta d'auko zata shiga bedroom yayi saurin rikewa, " ke me kike nufi? Dan bakya ganin komai shiyasa zaki min sharri? Ni nahanaki gani? Ko ni na toshe idanunki? Wato kina jin bak'in cikin ina kallon duniya ke bakya gani ko? To indai hassada ne haka zaki kare a Makauniya"
"Na yadda yaya Bilal koda nakare a Makauniya Allah yasani ni Makauniya ce a ido, Amma ba'a zuciya ba irin naka, Kaine ka Makance da duniya, kud'in Ku ya makantar daku, daga kai har kannenka, Amma ni idona ne kad'ai a Makance ba Zuciyata ba, tana gama fad'an haka ta sakar mishi sandar tafara Neman hanya da hannunta har ta iso bedroom"
"Kwankwaso yarike yana kallon ikon Allah, lalle yarinyar nan tana Neman ta rainani dayawa, bata da laifi nida nake kyaleta ne da laifin, yana fad'an haka yawuce d'akin Sabir, Sabir yana kwance yaga Bilal, Aa yaya Bilal Kaine?, eh wallahi Sabir nine ya kake? Lafiya lau Yaya, Amm Sabir dama aika nakeson in baka, Pls idan kaje kasuwa ka siyo min bulala irin dogon nan, Dariya Sabir yayi, yace " yaya Dan Allah me zakayi da bulala?"
"Ina ruwanka, kaide kawai kasiyomin".
Yana fad'a yafita a d'akin.
_washe gari_
Madina ce tazo gaida Minal, tambayarta take ya Umma?
" Umma lafiyarta kalau wallahi, tace in gaisheki sosai, kuma in fad'a miki tana kewarki"
Hmm Umma kenan batasan tafita keya bako? Ai yanzu Madina da ace Umma zatazo ta d'aukeni a cikin gidan nan da nafi kowa farin ciki, Madina wannan gidan k'azamin gidane, babu tsafta a cikin ta, kowa yana cutar da d'an uwanshi, ban tab'a ga Family da basa son junarsu ba irin wannan, kiduba kigani Madina, Daddy yana cutar da Bilal, Bilal yana cutar da ni, Hafeez yana cutar da Daddy, domin Akwai wata rana danaji Hafeez yana waya da abokananshi akan su tari Daddy a hanya zai fita da kud'i yanzu, Hajiya babba tana cutar da jikarta, ta hanyar d'aurata akan turban rashin kunya, Dan Allah Madina wannan Familyn zasu samu Albarka?"
"Gaskiya Minal wannan ba Family bane, to Amma ai ke kinsan gaskiya me ze hana kifad'awa kowa gaskiyar magana ko zasu kintsa Kansu"
Aa Madina babu Wanda ze yadda dani a cikinsu, hasalima duk sun tsane ni, Sabir ne kad'ai nake samun sauk'i a wajenshi, shima yanzu Bilal yace kar in b'ata mishi k'ani, ya zanyi da rayuwata Madina? yaya zanyi? Ni wawiya ce Madina, a lokacin da sukazo tambayar Aurena da nayi bincike da duk haka bata faru ba, Amma babu komai Akwai Allah"
"Gaskiya ne Minal Akwai Allah ki rika yin Addu'o'i safe da yamma, fad'in Alhamdllh da Allahu Akhbar kada yafita a bakinki, sannan Uwa Uba kibi mijinki sahu da k'afa, koba komai Bilal ya Aureki, bai kamata yana fad'a kina fad'a ba, idan kinga ranshi ya b'aci ki bashi hakuri, karki dinga nuna ke ana cutar dake kinji k'awata?"
"Naji Madina kuma na gode, in Allah ya yadda zanyi duk yanda kikace"
"Bilal yafara tausayawa Afrah, koba komai mahaifinta ya rikeni tsakaninshi da Allah, yarinyar tana sona, sannan idan na Aureta zata canja halinta, kuma zan samu lada, na tabba ta da Abbana yana Raye yaga yanda Afrah take sona, to da babu abinda zai hana Auren nan, me ze hana in yadda da buk'atarsu ko sau d'aya ne? Da kuwa Abba na zaiji dad'i"
"Da yamma Daddy yana wajen shakatawa, Bilal yazo ya sameshi, Aa Bilal ya kake? Lafiya lau Daddy, dama wata magana nakeson muyi dakai,
Zuciyat Daddy ne tabada sauti dumm, to Allah yasa ba wata maganar yaji ba"
"Ina...ina jinka Bilal Daddy yafad'a da alamar rashin gaskiya,
" amm Daddy dama ina son in fad'a maka na yadda zan Auri Afrah".
"Da sauri Daddy yad'ago kanshi, Dan gaskata ko Bilal ne yake magana,
Zaka Auri Afrah? Bilal ka yadda har zuciyarka?"
Eh Daddy na yadda zan Aureta koba komai Afrah 'yar uwata ce, kuma da Abba na yana Raye inada tabbacin shi zai had'a Auren nan,
Kuma Daddy dama ina son fad'a maka, ni ban yadda da hatsarin motane kad'ai ya kashe iyayene da k'anwata ba, tabbas Akwai wata kullalliyaa, koma dai menene saina bincika, kuma saina d'au fansa"
"Jikin daddy ne yafara rawa, cikin in ina yafara fad'an hab...hab...haba Bilal meyasa kafiye bincike da zargine?
Bincike fa ba kyau bakaji Allah yace (wala ta jassasuu) ba, kazomin da maganar farin ciki kuma kana kokarin tuno Min da k'anina wanda yafi kowa sona!, Wanda nayi mishi laifi Amma shi yazo wajena yabani hakuri, karka kara wannan maganar Bilal kana jina? To Daddy insha Allahu bazan kara ba,
Yawwa d'an Albarka, yanzu yaushe kakeson ayi bikin naku kaida Afrah?
Daddy ni koda yaushe ma kawai ayi, to to nan da Sati biyu yayi maka?
Eh daddy yayi".
" da dare Minal tana kwance a kasa taji gud'a cikin d'aki, tashi tayi ta shiga Falo, Hajiya babba ce tace "abawa masu gani waje suyi gud'a jikata ta kusa zama Uwar gida agidan Bilal"
"Minal bata gane zancen ba, tadai sake kunne tanajin maganar, kamar Almara"
_To readers Afrah zata Auri Bilal, can you emerging yanda wannan Familyn zata k'aya?_
✔ote & comment
_Jiddah S Mapi_
*بسم الله الرحمن الرحيم*
🌸🌸🌸🌸🌸🌸
*MAKAUNIYA CE*
🌸🌸🌸🌸🌸🌸
By
Jiddah S Mapi
Page 17...
*___________________________________*
*🌈KAINUWA WRITERS✍🏼 ASSOCIATION*🤝🏻
```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}```
https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation
*____________________________________*
"Aure kuma, Bilal zai Auri Afrah? Bayan cin Amana ta da suke awaje baiyi musu ba harsai ya Aureta?, ya Allah wani irin rayuwa na jefa kaina? Minal kin cuci kanki, Allah yasaka miki da alkhairi, tanajin Hajiya babba tana ta habaici bata tanka mata ba tashige bedroom, idonta cike taff da hawaye"
"Bilal ne yadawo gida yaga Minal kwance akan gado tana bacci, tsaki yaja cikin ranshi yace " yarinya karama da ita sai fitina kamar babba, karasawa yayi zuwa kan gadon, yafara bubbugata ke? Tashi, a firgice Minal ta tashi jin muryanshi, tana kokarin sauka akan gadon, jikin Bilal ne yayi sanyi ganin yanda ta tsorata Dan taji muryarshi, "yaya Bilal kayi hakuri zan sauka maka, ban sani bane bacci ya d'auke ni"
Tausayi tabashi sosai, zuciyarshi ta karye, a hankali ya riko hannunta, yace "babu komai kiyi kwanciyarki zan kwanta a gefe"
Lalle yau da idonta yana gani babu abinda zai hana ta waro su da kyau ta kalli Bilal domin ta tabbatar ko shi yayi maganar, a hankali ta koma kan gadon tayi kwanciyarta tare da Jan bargon daidai wuyarta, lumshe ido Bilal yayi ganin yanda take bacci, kamar wata baby,
"Auzu billahi shine abinda yafito daga bakinshi, me kakeyi haka Bilal? Kar ka bada kanka mana, ya zaka fara tausaya mata da wuri haka? Duk laifin datayi maka? Juyawa yayi yatafi toilet, Alwala yayi yazo ya shimfid'a sallaya yayi sallah raka'a biyu tareda Addu'ar Allah ya bayyana mishi duk wani wanda yake munafurtan shi, yana idarwa yaje ya kwanta akan gadon gefen Minal, yajuya yana kallon fuskarta, Idanunta manya me d'auke da Zara zaran eye lashes, hancinta yanada tsayi sosai, sai d'an karamin bakinta, Wanda tad'an tab'ewa sabida shagwab'a, tanayi mishi yanayi da kanwarshi Nabeela, hannu yasa akan fuskarta yana shafawa, haka har bacci ya d'aukeshi"
_Asuba tagari_
"Minal ce ta bud'e idonta a hankali, ganin Bilal tayi ya rungumeta a jikinshi yana bacci, da alama kuma baccin yana mishi dad'i, a hankali ta zame jikinta daga nashi tana Jan tsaki, haka kawai zai sani a gaba ya rungume, sai ya jira Afrah idan ya Aureta ya rungume, amma dai bani ba, " ke? Me kike cewa?" Cewar Bilal da tun tashin ta shima ya farka,
"Turo baki tayi tace Nidai bance komai ba".
"kifad'a ma kiga dukan da zanyi miki, dama nasa Sabir ya siyomin bulala a kasuwa, na lura ke saida bulala"
"Ai ni ba jaka bace da za'a siya bulala don ni"
"Kiyi magana yanda zanji mana kiga dukan dazanyi miki, Amma kina magana a hankali"
"Sai ka bud'e bakinan Tinda kanada karfi, tafad'a daidai lokacin data rufe kofar toilet d'in"
Bilal shi har mamaki abun yake bashi, ace yarinya karama ta tsaya tana rainashi Amma ya kyaleta? Tsaki yaja kad'an kafin yasauka a kan gadon"
"Hajiya babba da Afrah anata rawan kai Bilal ya yadda zai Auri Afrah, waya ta d'auko takira frnds nata tana fad'a musu ta kusa Aure, Hajiya babba ce ta katse wayar tareda cewa " bafa waya yakamata kiyiba yanzu, tashi zakiyi ki dafawa masoyinki abinci da lemon Apple me sanyin dad'i, tin yanzu ki koyi yanda zaki kula dashi, ki kwace shi gaba d'aya daga wajen wancan Aljanar kina jina?"
"To Hajiya babba yanzu ma kuwa" tafad'a tana mekewa"
"Kitchen Afrah tashiga tareda d'aura tukunyar Abinci, jallof na shinkafa ta dafa, tareda yin lemon Apple, jallof d'in yaji manja da gishiri, tareda had'in gwiwar Barkono, da Uban tumatur, juyewa tayi a plate kafin ta nufi d'akin Bilal, tasan bazata sameshi ba saida Azahar, hakan yasa ta jera a dinning table, tanayi tana wak'arta na habaici, Dan taga Minal awajen, cewa take (matarshi makaho, shalugude, shima makaho, shalugude, yaransu makafi, shalugude)
Minal tana jinta Amma bata ce uffan ba, haka harta gama tayi tafiyarta, Minal bata kulata ba"
"Da Azahar Bilal ne yadawo gida, lokacin Afrah tad'au wanka dawata duguwar Riga, Wanda aka bud'e Kasan, babu laifi tayi kyau, tana ganin Bilal ta mike tareda cewa " sannu da dawowa yaya Bilal"
"Bilal kallonta yayi ta cikin glass nashi, sannan ya murtuk'e fuska yace " yawwa"
"Am yaya Bilal dama na gama maka Abinci, muje nazuba maka ko?
Bilal bayason yawan magana, sai kawai yayi gaba ya kyaleta, shiru Afrah tayi Hajiya babba ce ta lek'o tace mata " bishi mana k'atuwar banza, mara wayo"
"Zumb'ura baki Afrah tayi kafin tabi bayan Bilal, tana zuwa ta Ganshi akan dinning, dad'i taji sosai, ta karaso Inda yake tareda d'aukan plate tazuba mishi, "to yaya Bilal nawa aci Abinci lafiya"
"Bai kulata ba yafara laluben plate d'in, Afrah ganin yana Neman inda plate yake yasa Tamika mishi,
Minal tana jin duk abinda suke Amma bata damu ba sabida tasan ko ta damu babu Wanda zai kulata, Babu ruwanta da familynsu yanzu"
"Ta b'angaren Bilal kuma yayi haka ne Dan ya baiwa Minal haushi, Amma sai yaga bata ma damu ba, Abincin ya d'ebo cike da cokali yakai bakinshi, Unty gishiri ne tafara gaida bakinshi, sai kuma wani irin yaji, da kuma tsamin tumatur, shi yama rasa yanda zai fara tufar da abincin tsabar gishiri, rikewa yayi a bakinshi, yakasa ci yakasa tufarwa, Afrah ce tace " yaya ci Abincinka mana Kasan ban tab'a shiga kitchen ba sai yau, kuma Dan kai nayi gajiyar girki please kaci sosai"
"Saurin tufarwa yayi yace, kin d'ana Abin cin kuwa? Girgiza kai Afrah tayi Alamar Aa, yace okay "gashi ki cinye ko kuma in fasa Auren ki"
Haba yaya me yayi zafi dazaka fasa Aurena? Kaga indai Akan Abinci ne miko min in ciye,
'Daukan plate na Abincin tayi ta kara a flask, kafin tad'au cokali tasa abakinta, taji wani irin gishiri, da sauri ta tufar tareda d'auko kofin ruwa ta kuskure bakinta, Bilal ne yace saita cinye abincin tas kafin tafita, hakan kuwa akayi da kyar da kuma da gumi har ta cinye Abincin,. Tana gamawa tafara shek'a Amai, tsakaninta da Allah"
"Minal sai dariya kawai takeyi"
"Bilal ko kulata baiyi ba yatashi ya tafi, Hajiya babba ce tashigo, tarike Afrah suka tafi cikin gida, meya faru Afrah? Keda kika kaiwa yayanki Abinci saiki fara shek'a Amai?"
Hajiya babba wallahi yaya Bilal mugune baya sona, Dan kawai gishiri yayi yawa a abinci saiya ce saina cinye"
"Kiyi hakuri Afrah, duk abinda yayi miki saikin rama indai ina gidan nan, haka ta lallab'a Afrah har tayi shiru"
"Da yammacin ranar Bilal ne zaune a falo yana duba wasu takaddun company, Minal ce tazo cikin falon, tana kiran yaya Bilal? Yaya Bilal?
Bilal yayi mamakin yanda take kiranshi, "ke lafiya?"
"Yawwa tafad'a tareda zama a gefenshi, tace " yaya dama wata magana nakeson muyi da kai"
Ummm hmm ina jinki, shine Abinda yafad'a"
"Yaya dama inason in rokeka ne, Dan Allah Dan Annabi, Dan darajar iyayenka, ka taimaka ka kaini India a gyara min idona, wallahi ko baiwarka kace in zama, wallahi zanyi"
"Tabashi tausayi sosai yanda take rokanshi, saiya tuna da kanwarshi Nabeelah idan tana rokanshi Abu saita had'ashi da Allah da Annabi, to Amma yasan idan wannan yarinyar tafara ganin duniya to ya Shiga uku da raini, koda shike zeyi matane sabida Allah badan halinta ba"
"Sai nayi shawara, shine abinda yafad'a"
"Yaya Dan Allah kayi shawara me kyau, ina son ganin mahaifiyata, ita kad'ai nake da Aduniya, banida kowa Sai ita"
"Ke nace miki Sai nayi shawara koh?"
"To yaya nagode"
"Shi mamaki ma take bashi yanda ta sunkuyar da kanta tana mishi magana.ba raini ba tsiwa"
"Minal kuma a zuciyarta tace Allah yasa ya yadda, sarkin girman kai da d'agawa"
✔ote & comment
_Jiddah S Mapi_
*بسم الله الرحمن الرحيم*
🌸🌸🌸🌸🌸🌸
*MAKAUNIYA CE*
🌸🌸🌸🌸🌸🌸
By
Jiddah S Mapi
Page 18...
*___________________________________*
*🌈KAINUWA WRITERS✍🏼 ASSOCIATION*🤝🏻
```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}```
https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation
"Bilal ne ya yanke shawarar sai bayan Aurensu da Afrah kafin yakaita India"
"Minal datayi sallah Addu'a kawai take Allah yasa ya yadda, da dare ta kara rok'anshi tace " yaya Bilal Dan Allah ka taimakamin"
Bilal yace "naji Amma sai bayan Aurena da Afrah, idan zaki iya jira idan kuma bazaki iya ba sai ki zauna a haka"
Minal tace "Aa yaya Bilal wallahi zan iya hakura"
Yece "dayafi miki"
_washe gari_
Madina ce tazo gidan, ta fad'awa Minal Umma batada lafiya.
"Minal dajin haka yasa ta shirya wai su tafi "
Madina tace "Aa Minal kibari idan Mijinki ya dawo ki tambayeshi idan ya baki izini sai gobe kije ki duba ta"
Minal tace "Haba Madina sai kace bakisan matsayin Umma awajena ba? Umma fa mahaifiyata ce idan banje na dubata ba waye zai dubata? Sabida Bilal bazanki zuwa duba mahaifiyata ba, kinga idan bazaki kaini ba, to bari na tafi da kaina"
Madina tace "Aa Minal kiyi hakuri, muje dama ni ina guje miki fushin mijinki ne, domin yana kawo fushin ubangiji"
Minal tace "okay nasan bakida niyan tafiya, kinga sai Anjima"
"Da sauri Madina ta riko ta tace Aa wane ni? kinga muje"
"Tafiya sukayi zuwa gidan Umma"
Minal tana Shiga tafara kiran Umma!!!
Umma ce taji muryanta sai ta tashi cikin murna ta rungume Minal.
Tace "yata sannu da zuwa"
Minal hawaye ta share jin muryan Umma tana magana a hankali,
Tace "yawwa Umma ya jikin naki?"
"Da sauki Minal"
'Daki suka shiga Umma ta d'ebo mata ruwa tasha kafin ta tambayeta
"Minal ya naga kin rame? Me yake daminki?"
Minal tarasa me zata fad'awa Umma sai kawai tace "Am Umma nayi rashin lafiya ne acikin kwanakin nan ciwon ciki ne ya dameni, har saida aka kaini Asibiti"
"Asibiti kuma Minal? To meyasa shi mijin naki bai fad'a min ba?"
"Mijina kuma Umma?"
Umma tace "Eh kullum ai yana zuwa nan muyita hira har dare kafin ya tafi"
"Zuciyar Minal ne yabada sauti Dummm, "ta yaya Bilal zaizo gidan nan? Anya ba wani bane yake yiwa Umma karya da sunan Mijina?"
Umma tace "tunanin me kike yi Minal? Ko akwai Matsala ne? "
Minal tace "Aa Umma bawani tunani kawai de bai tab'a fad'amin yana zuwa nan ba"
"To ai ba dole bane ya fad'a miki sabida shi mutumin kirki ne yanada mutunci"
Minal tace "to Umma saidai mu godewa Allah"
Haka suka karasa firansu, Minal ta koma gida da yamma.
"Ta b'angaren Bilal kuma yana zaune a falo yana tunanin ta yaya za'ace Hafeez ya yiwa matarshi jagora? Yakaita gidansu? Da karfi ya furta "dawata akasa".
"Minal ce tafi sallama"
Bilal yace "ke? Ban hanaki Alak'a da Hafeez ba?"
A hankali tace "Hafeez kuma? Me yayi?"
"Okay tambayata ma kike?
Wato ke iskanci a jininki yake, Hafeez ne yayi miki jagora, Kun fita tunda safe shine don bakida kunya sai yanzu zaki shigo min d'aki?"
Minal tace "nifa ban gane me kake cewa ba yaya Bilal, ka fahimtar dani"
"Okay to bari in fahimtar dake, Belt ya ciro yafara zabga mata, kota ina, saida yaga tayi lilis kafin ya tsallakata tareda cewa " kuma nafasa Fitar dake kasar india, saidai kije shi Hafeez d'in ya kaiki"
"Hajiya babba da Afrah Wanda suka lab'e a bakin kofa ne sukayi saurin Baron wajen, Dad'i Afrah takeji, don Bilal ya daki Minal"
Hajiya babba tace "Dama na fad'a miki saikin cire tsoro kafin kiyi nasara, yanzu badan munyi wannan plan d'in ba ai bazai dake ta ba"
Afrah tace "wallahi Hajiya babba baki tab'a birgeni irin na yau ba, nagode miki sosai kakata kuma takwarata"
Hajiya babba tace "ba godiya yakamata kiyimin ba, yanzu zamu fara kirkiro wata munafinci, Wanda zai daina yadda da ita kwatakwata, yaji ya tsaneta".
" to
All Chapters
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 6 Chapter of 14