iyayenshi da kanwarshi wanda haryau zuciyarshi tanayi mishi wasi-wasi akan wannan hatsari dasukayi, juyawa yayi ahankali yana kallon wani Agogo dake cikin ɗakinshi wanda Daddynshi yabashi tin lokacin yana primary yana daraja agogon sosai, gani yayi har karfe takwas yayi dasauri yasauka akan gadon yayi hanyar toilet, wanka yayi da sabulanshi me kamshi sannan yafito yashafa mayukanshi me kamshi da sanyaya zuciya, wata jar riga yaɗauko wanda aka rubuta Mad over you ajikin da bakin rubutu, sai wani jins nawando dayasa da picap jaa yasa da baƙin flatshoe namaza yaɗauki makullin motarshi yafice agidan.
"Minal kuwa yau wayarta take dubawa kowani bayan mintuna gani take kamar zaman datakeyi na ɓata lokaci ne gashi Umma zataje unguwa yau tahanata fita ko ina
Kuma tasan zuwa unguwar Umma idan taje bata dawowa dawuri
Gashi yaune su Alhj Umar da Alhj Nura zasu cika kudirinsu akan abokin gabanta wato Bilal, duba agogo kawai take idan karfe biyar yayi zatayi tafiyarta acewarta ko Umma bata dawoba
Karfe 5:50 cif Minal tafita agida babu wanda yasani sabida Umma bata gida Mashin me kafa uku takama tayi hanyar company tana zuwa tawuce wajen me gadi tagaidashi ina wuni baba? Yace lafiya lau ɗiyata meya fito dake yau da goshin mangariba haka?
Minal shiru tayi dan tarasa me zatace sai can wani tunani Yafaɗo mata tace Baba dan Allah yau Bilal yazo aikine?
Be zoba cewar baba megadi amma lafiya kike tambayarshi?
Eh dama baba wallahi sonake nbashi hakuri akan abinda yafaru cewar Minal amma dan Allah kokasan adreshin gidansu?
Eh nasani inji Baba megadi G.R.A house Number 3
Tom nagode baba cewar Minal
Fita tayi dasauri takama mashin tace me mashin Hause Number GRA house number 3 zaka kaini amma inason kajirani sabida sauri nake
To badamuwa Hajiya cewar me mashin ɗin"
Shikuma Bilal yau agidansu Latif ya wuni suna hira sai karfe 5:30 yadawo gida, kwanciya yai yaɗan huta kaɗan kamin yatashi yanason yayi alwalar mangariba,
Masallaci yatafi lokacin daya fito Minal dame mashin sunata hira kamar dama sunsan juna kasancewar Minal akwai saurin sabo da mutum masallaci me mashin ɗin yaje shima yabarta awajen, Minal tana zaune agefen mashin ɗin taga wasu mutane guda biyu sunzo zasu shiga gidan Alhj Umar zuciyarta ne yayi bala'in tsinkewa amma kuma saita tuna mutanen dazasu zo ze kasance 'yan dabane su kuma waɗannan da shadda ajikinsu me zafin gaske sannan da wata 'yar karamar jaka ɗayan yarataya awuyarshi da alama abokan Bilal ne
Kallonsu take har suka shige gidan.
Bayan an idar da mangaribane Bilal yadawo yaga mace zaune akofar gidansu amma tajuya kanta ba'a ganin fuskarta kawar dakanshi yayi yawuce gida ko kara kallonta beyi ba,
Ita kuma Minal ganin yashiga gida yasa ta tashi da sauri zata shiga gidan taɓoye lokacin megadi yana masallaci dasauri tashig ciki tarasa ta ina zata farabi acikin gidan Babban gidane batasan ta inane garden da ake faɗaba tsayawa tayi tana tunani taji ance ke!! Me kijeyi anan? Fitsari ne kawai btayi ba awando tsabar ruɗewa juyowa tayi taga wani tsoho da alama megadi ne yadawo, jikinta yana rawa tace dama Latif ne ya aikeni wajen yaya Bilal dajin haka se megadi yace ok ok jeki dataga tatsira sauke ajiyar zuciya tayi tace Alhmdllh dama Baba yacemin a garden kuma bansan gadmrden ɗin ba
Kibi senta har karshe zakiga garden ɗin nima dan ina sauri ne yasa bazan kaiki ba sabida Alhaji ya aikeni, to baba nagode cewar Minal"
Minal senter tabi kamar yanda Baba megadi yace daidai wajen kwana taga wasu 'ya'yan itatuwa kala kala wajen dasanyi sosai sannan yana kamshin fruits lumshe idonta tayi tana mejin daɗin yanayin wajen,
Tana buɗe idonta ahankali ahankali tayi tozali da Bilal zaune kan plastic chair dawata farar center table agabanshi wanda aka cikata da kayan itatuwa dakuma drinks kasancewar inda yake akwai ɗan haske kaɗan yasa take iya ganinshi
Ɓuya tayi abayan wata bishiyar inab yanda zata iya hango duk abinda ze faru.
"Shikuma Bilal kawai yana zaune ne amma sam yau yanajin wajen baya mishi daɗi, karan takun mutane yafaraji abayanshi daya juya sai yaga ba kowa
Waya yaɗauko yakira Latif yace mishi dan Allah Latif kazo akwai wata magana dazamuyi
Ok cewar Latif"
Yana kashe wayar yaji an ja plastic chair dayake zaune akai yana kokarin tashi yaji ɗayan ya rirrike hannayenshi duka biyu,
Gani yayi ɗayan yaciro wani abu a kwalba yana kokarin watsa mishi kafarshi yaɗaga ya buge abun dasauri meshi ya ɗauko ragowan suna kokarin watsa mishine yajuya fuskarshi a dasauri abun yataɓa kanshi ihu yasa sabida zafin dayaji, sukuma mutanen sunaji yayi ihu ɗayan yace yataɓa idonshi?
Dakai ɗayan ya amsa mishi alamar Eh.
Ita kuma Minal hankalinta akan wayarta da aka kira da sabuwar numba jin ihu da Bilal yayi yasa ta tashi afirgice tana kallon meya faru,
Ganin mutanen data gansu ɗazu tayi suna fitowa, dagudu ta iso wajen tana ganin ɗayan ze bugeta tayi saurin rike riganshi tana bugunshi gashi fuskarsu duk sun ɓoye da bakaken abu,
Ganin yarinyan zata tara musu jama'a yasa yaciro ragowan Acid ɗin yawatsa wa Minal a idanu, saurin sakeshi tayi tasa wani irin ihun daya ɗaukin cikin unguwar GRA gaba ɗayanta tace Wayyo IDONA dasauri me mashin ɗin yashigo gidan yaga Minal Kwance tana ihun idonta,
Hanunta yarike yafita da ita dasauri tana ihu tana murza idonta, dasauri yasata amashin ɗin yaja yabar unguwar da ita.
"Bilal kuwa yanajin sunce yataɓata idonshi? Se yayi pretending kamar a idonshi abun yasameshi, yasan cewa wannan shiri ne kuma yaji ihu amma idan yabuɗe idonshi yasan zasu watsa mishi a ido domin alamu sun nuna makantar dashi sukeson suyi, daidai lokacin da mutabe suka shigo gidan jin anyi ihu,
Sukaga Bilal kwance yana murza ido dasauri suka karasa inda yake suna tambayarshi meya faru? Yace Acid a idona sun watsamin shikenan namutu kutaimaka min".
_✔ote Comment & share pls_
✍🏻 *JIDDAH S MAPI*
🌸🌸🌸🌸🌸🌸
*MAKAUNIYA CE*
🌸🌸🌸🌸🌸🌸
(An heart touching story)
*Written by*
Jiddah S Mapi
*بسم الله الرحمن الرحيم*
*🌈🇰AINUWA 🇼RITER'S✍🏼*
*🇦SSOCIATION🤝🏻*
_wannan littafin sadaukarwa ne ga yayata Maryam S Mapi_
*WATTPAD*
_Jiddah S Mapi_
*Page* 6
"Mutane sun taru makil akofar gidan Alhaji Umar shikuma Bilal ganin haka yasan da haɗin bakin nakusa dashi awannan lamarin kuma yanada tabbacin idonshi suke nema su ɓata, daidai lokacin motar Alhaji Umar yadanno kai cikin gidan, dasauri yafito amotar yana tambaya meyafaru? Wanine acikinsu yace ranka shidaɗe wasu mutanene suka shigo gidannan suka watsawa Bilal Acid a ido, Acid!!! Cewar Alhaji Umar, garin yaya haka tafaru? Wani mara mutuncinne yashigo har cikin gidana yawatsawa ɗana Acid a ido? Lalle kuwa sai hukuma sun shigo lamarinnan saina kulle duk wani wanda yakeda sahanu, haka Alhaji Umar yayita matsifa kamar dagaske Amma acikin zuciyarshi wani irin daɗi yakeji,
Karasawa inda Bilal yake yayi yana zuwa yafashe da kuka yace yanzu Bilal shikenan sun makantar min dakai? Yanzu baka ganin kowa? Innalillahi wa'inna ilaihiraji'un,
Bilal yanajin maganar Daddy abun yabashi mamaki matuka, ganin haka yasashi cewa Eh wallahi Daddy haka Allah yakaddara min zan kare rayuwana amakanta yanzu idaduna basa ganin komai, Bilal yafaɗi haka yana me hawaye, idan kaga yanda Bilal yake acting zakace da gaskene yataɓa idonshi amma shi azuciyarshi yasa kudirin saiyayi bincike alamarin,
Suna cikin wannan halinne saiga Latif yana zuwa yafara tambayar meyafaru? Daddy ne yayi mishi bayanin komai, shiru Latif yayi sannan yace yanzu Bilal baka ganin komai? Bilal yace Latif bana ganin komai kutaimaka ku kaini ɗakina, latif ne yace wallahi saina gano duk waɗanda sukayi maka wannan aika-aikar koda kuwa zan rasa raina ne,
Jin haka yasa zuciyar Daddy tabada wani sauti Dummm yasan idan bincike yayi bincike dolene aganoshi"
"wani irin kallo Daddy yake yiwa Latif, hannun Bilal Latif yarike domin kaishi ɗaki, mutane sunata Allah wadai da wanda suka aikata mishi haka".
"Minal damai mashin kuwa asibiti suka nufa, suna zuwa aka nunawa me mashin ɗakin dazasu samu babban likita, Hannunta me mashin yake rikewa suna tafiya har suka iso office na babban Doctor"
Bubbuga kofar me mashin ɗin yayi daga ciki akace "yes coming"
Shiga sukayi ciki wani bakin mutum ne me jikin gaske yake zaune akan kujeran doctor.
"Meke tafe daku?
Yallaɓai wasu mutanene suka watsa mata Acid A ido shine nace bari nakawo ta aduba karya zame mata matsala,
Shiru doctor yayi yazubawa Minal namujiya can yacewa me Napep ɗin wannan fine girl ɗin aka watsawa Acid a ido? Kai gaskiya banji daɗi ba amma ɗan fita kabamu waje mana"
Fita me mashin yayi a office ɗin wanda har zuciyarshi be kawo komai ba.
Tashi doctor yayi awajen zamanshi yaje dab da Minal yazauna, Minal kawai sai jin hannun mutum tayi yarike hannunta, saurin janye hannunta tayi tace "Malam me haka?"
Haba 'yan mata yanda kike dakyau ai dolene in kosa, yanzu nasan bakya kallon komai Right?
Minal tace eh sai me?
"Relax Baby bawani sabon abu bane awajen 'yan matan zamani ace tana harka dame kuɗi kinsan zata huta, zan taimaka miki idan har zaki bani haɗin kai sannan babu wanda zesan abu haka yafaru tsakaninmu...."
"Tashi Minal tayi dasauri tace haba doctor, kaida mukazo kadubani amma zaka tsaya kanamin maganar banza? Hakika da ina ganinka babu abunda ze hanani tsinka maka mari mugu azzalimi..." kafin takarasa taji ya rike hijabinta yana kokarin cirewa".
Kokawa suka fara dashi aɗakin tana kokarin janye hijabinta shikuma yana cirewa, rokanshi Allah da Annabi tafara akan yabarta amma ina sam sam mutumin bashida Imani. Ganin yanason cire mata kayanta yasa tafara ihu tana kiran "Me mashin!!! "Me mashin!!!
Toshe bakinta yayi da hannunshi daidai lokacin me mashin ɗin yabuɗe kofar dasauri, saurin sakinta doctorn yayi yaja dabaya.
Me mashin ne yace Doctor menake gani haka? Me kake kokarin aikatawa?
"Shiru doctor yayi yafara kame kame amm.. Amm.. Dama idontan nakeson dubawa amma taki yadda..."
"Kaji tsoron Allah Doctor kaji tsoron ranar haɗuwarka dashi, kana tsoran mutum amma baka tsoron Allah? FYAƊE fa kakeson kayimin, bakaji kunyar Allah ba kanajin kunyar mutum? Allah ya isa, bazan yafe maka ba, abunda kayimin Allah yasa ayiwa 'yarka,
me mashin kataimaka kakaini gida dama nasani rayuwata tana cikin haɗari, babu masu taimako dan Allah saidan wani abu dazasu samu ajikinka, Allah ya isa"
Dama ai Allah isashe ne kufita kubar asibitinnan kafin nakira muku security.
"Hannun Minal me mashin ɗin yakama sukabar office ɗin,
Ya tambayi Minal inane unguwarku? Tace bayan kasuwa"
Me mashinne yataimakawa Minal yakaita har gida kafin yatafi,
Lokacin dataje gida Umma bata dawo ba haka tazauna a inda take tayi ta razgan kuka.
"Wannan wace irin rayuwace? Yanzu irin talauci da kuncin rayuwar damuke ciki ace wannan kaddarar tasake afkuwa"
Waze taimaka miki Minal?
Kin cuci kanki, kin ɓata rayuwarki akan wanda besan dazamanki ba, wanda yatsaneki, Duk maganar nan tanayi ne azuciyarta yayinda take kuka kamar hawayenta ze kare.
"Tana cikin kukane taji sallaman Umma, Saurin share hawayenta tayi domin batason Umma tasan abunda yake faruwa, Aa Minal meyafaru naga kin zauna shiru haka? Keda nagi zaton kina gidansu Madina, meyafaru?
Shiru Minal tayi tana kokarin maida hawayen dasuka taru a idonta.
Wai me yake faruwane Minal?
Umma bana ganin komai!!! "
Bakya ganin komai kamar yaya? Ban ganeba kiyimin bayani dalla-dalla in fahimta.
"Hawayen dasuka taru a idon Minal ne suka wanke mata fuska, Ahankali tabuɗe bakinta kamar batasonyin magana tace Umma Acid aka watsamin a ido,
Acid!!!? Garin yaya? Suwaye suka watsa miki? Ki amsamin suwaye??
Firgita Minal tayi da yanayin maganar Umma"
Bazaki faɗamin ba Minal ina kikaje?
Umma Dama ina zuwa gidansu Madina ne shine wasu samarai suka watsamin Acid takarashe maganar tana kuka sosai.
Ba kuka na tambayeki ba Minal amsa nakeson kibani ina kikaje yau?
Umma wallahi gaskiya nafaɗa miki ki yadda dani, cewar Minal
Ok bazaki faɗi gaskiya ba kenan?
Umma gaskiya nafaɗa miki.... Tassss kakeji Umma tawanke Minal da mari Bazaki fafamin gaskiya ba Minal yanzu kinzama makauniya wace irin rayuwa kikeson muyi? Nashiga Uku ni Maryama.
Kuka Umma tafara itama an rasa me lallashin wani.
Ta rungume Minal suna kukan bakin ciki.
"Ɗaki Latif yakai Bilal zaunar dashi yayi akan gado yace Bilal kaɗauki kaddara aduk yanda yazo maka alkhairi ko sharri, karkasa komai aranka insha Allah zaka fita daga wannan rayuwar, ba karamar jarabawa bace ace mutum yanada ido ada amma yanzu babu, saika daure kakai zuciyark da nisa kafin kaci wannan jarabawar.
Haka Latif yayita kwantarwa Bilal hankali"
Daddy kuwa yau babu wanda yakaishi farin ciki jiyake kamar yahaɗa party till down, waya yaciro yakira Alhaji Nura yace "Alhaji Nura aiki yayi kyau zaka samu babban kyauta daga gareni, saidai fa akwai matsala!"
Matsalar me kuma Alhaji Umar?
Latif zaibi diddigin abinda yafaru sabida yace koda zai rasa rayuwarshi saiya gano wanda ya aikatawa Bilal haka.
"Haba Alhaji Umar akan wannan shine zaka ɗaga hankalinka? Nawa Bilal yake balle Latif?
Idan bazaka damu ba muhaɗu a guesthouse nawa mana Cewar Alhaji Umar,
Ok ba matsala zanzo da karfe bakwai nasafe.
Nan suka gama shawararsu suka kashe wayar...
_✔ote Comment & share_
✍🏻 *JIDDAH S MAPI*
🌸🌸🌸🌸🌸🌸
*MAKAUNIYA CE*
🌸🌸🌸🌸🌸🌸
(An heart touching story)
*Written by*
Jiddah S Mapi
*بسم الله الرحمن الرحيم*
*🌈🇰AINUWA 🇼RITER'S✍🏼*
*🇦SSOCIATION🤝🏻*
_wannan littafin sadaukarwa ne ga yayata Maryam S Mapi_
*WATTPAD*
_Jiddah S Mapi_
*Page* 7
"Kamar yanda Alhaji Nura da Alhaji Umar suka yanke shawarar haɗuwa a guest house hakan tafaru, da karfe 7:00 ciff motar Alhaji Nura yadanno kai cikin guest house ɗin, wani wajen shakatawa me kyau naga yanufa, yana zuwa yasamu wuri yazauna akujerar dake fuskantar Alhaji Umar"
Barka dazuwa cewar Daddy,
Yawwa barka Alhaji,
Alhaji idan har Latif ze zame mana matsala meze hana muyi gaggawar ɗaukan hukunci.
Wani irin hukunci zamu ɗauka kenan Alhaji Nura?
Kasan banason abunda ze kawomin cikass awannan lamarin, nasa an makantar da Bilal sabida dukiyarshi inason yanuna min komai kafin daga baya insa akasheshi gaba ɗaya yabar duniyar nan.
Amma Wannan Latif yana neman jazamin aiki
Narasa mafita.
"Inada mafita Alhaji"
Mecece mafitar?
Cewar Daddy
Meze hana ayi mishi sharrin shiya turo mutane su watsawa Bilal Acid, munemo mutane biyu su ɓoye fuskarsu sai suyi videon cewa Su suka watsa mishi kuma Latif ne yaturosu kaga saiya kare rayuwarshi agidan Yari"
Daddy ne yagyara babban rigarshi yace "wato Alhaji Nura ban taɓa zaton zaka kawo good idea kamar haka ba, to Amma baka ganin hakan zai kawo matsala?"
Babu wata matsala Alhaji kaidai muyi abinda nace kawai.
To shikenan amma idan zeyi gobe nakeson ayi videon domin da zafi-zafi ake dukan karfe,
Karka samu damuwa cewar Alhaji Nura, nan sukayi ɗan hira kafin daddy yaɗibo wasu maƙudan kuɗi acikin baƙar jaka yabawa Alhaji Nura, Alhaji Nura yayi godiya yatafi"
"Bilal tunanin daya dami zuciyarshi shine Wayake neman hallakashi? Meya tarewa meshi? A iya saninshi bashida abokin gaba, to wayene wannan, wayake kokarin illatamin rayuwa?
Haka yakarashe tambayoyinshi babu me bashi amsa, filo yaɗauko yarungume yana kallon silin ɗin ɗakin, tunowa yayi da kanwarshi Nabila wanda duk lokacin data ganshi cikin damuwa hankalinta baya taɓa kwanciya, Runtse idonshi yayi yana mejin bakon cikin rashin 'yar uwarshi da iyayenshi, hawayene suka fara fita a idonshi wanda yake ganin hakan shine maslaha agareshi, awannan yanayin idan beyi kuka ba zhciyarshi zata iya fasa kirjinshi tafito,
Yana cikin wannan yanayin Daddy yayi sallama yashigo, yadai Bilal?
Lafiya Daddy cewar Bilal,
Zama Daddy yayi agefen gadon yariko hannun Bilal yana shafawa yace "my Son Banaso kasa kanka cikin damuwa, da nayi niyan nakaika India aduba idonka konawa zan kashe idan lafiyar idonka zata samu ashirye nake nakashe, amma kash mumunan labari ɗazu munyi waya da Doctor Shankar babban likitan idanu dake kasar India, nayi mishi bayanin abunda yafaru yace ai idan an watsawa mutum Acid a ido kuma yamurza idon sosai Aciɗin yabi cikin kwayar idanunshi to bazai taɓa samun sauki ba sai wani ikon Allah,
Bilal am sorry nazama Helpless akanka nakasa taimakonka da'ace zan iya baka nawa idon wallahi dana baka Bilal sabida kai saurayi ne nikuma girma yazo, kayi hakuri Bilal Daddy yakarashe maganar yana kuka kamar dagaske"
"Bilal shiru yayi yana jin maganar Daddy yasan cewa duk duniya babu wanda yakesonshi bayan Family ɗinshi sai Daddy,
Daddy kadaina kuka Haka Allah yatsaramin rayuwata, amma dan Allah Daddy inason kayimin amsar tambaya ɗaya"
Zuciyar Daddy wani irin bugawa tayi dakarfi yace am am.. am wace tambaya ce wannan Bilal?
Daddy shin mahaifina yanada Abokin gabane?
Shiru Daddy yayi yana tunani,
Daddy please answer my question,
Ajiyar zuciya Daddy yasauke yace "my son mahaifinka yanada abokin gaba guda ɗaya wanda nasani amma yanzu sun shirya suna abota kamar ba waɗanda suka taɓa gaba ba,
Daddy wayene wannan?
Abban Latif!!!! Cewar Daddy,
Abban Latif kuma?
Aganina shine aminin babana kuma babana ya aminta dashi sosai.
Bilal wannan abotar tasu ta BOGE ce bata gaskiya ba,
Mahaifinka yanada tarin dukiya wanda har wani lokacin yakan manta da wasu kadarorinshi, sun kasance abokai sosai da Abban Latif amma me? Sai kawai wata rana Abban Latif yayiwa mahaifinka babban sata satar Company Uku.
Da Mahaifinka yagano hakan saiya koreshi a aiki tun daga wannan rana gaba me tsanani yashiga tsakaninsu, nine nakirasu nayi musu nasiha kafin mahaifinka yabashi hakuri sukaci gaba dazama tare.
"Nabaka wannan labarine sabida karka Aminta da mutum sosai, wanda ka amince mishi shine wanda ze cutar dakai"
Abban Latif kuma? Cewar Bilal.
Daddy ganin yasa shakku azuciyar Bilal ba karamin farin ciki yayi ba, yasake ɗaurawa da "Bilal banaso kafaɗawa kowa wannan labari kaji?
Bilal yagiɗa kai,
Yawwa sakko muje downstair kadaina zama kai kaɗai aɗaki sabida yawan tunani?
Bilal yace to Daddy"
Hannunshi Daddy yakamo suka nufi kasa, Afrah nakwance a falo daga ita sai wata 'yar karamar riga da wando skin tired Kanta babu ɗankwali tana cin cingom kasss kass kass rike da wata ƙatuwar waya tana chat da friends nata, ganinsu Daddy yasa ta tashi daga kwancen tazauna tareda cewa "Daddy kazama ɗan jagora ne?
What are you saying Afrah yayanki nefa kaddara tasameshi, keda kike sonshi ai kuka yakamata kiyi..... No no no Daddy ai ni nadaina sonshi yanzu, mezanyi da makaho? Ai kawayena sai suyimin dariya. Daddy ni raina ma ya ɓaci .... Bye
Tana gama faɗin haka ta mike santal santal santal kamar nakasasshen rakumi tayi gaba.
Bilal har cikin zuciyarshi yaji zafin kiranshi makaho datayi amma ba komai zanyi maganinki.
Daddy ya katse mishi tunani dace "Bilal sai kayi hakuri da Afrah kasan yarinya ce"
Eh Daddy ba matsala.
Yawwa yanzu ina makullin Companyn yake kabani saina nemi wanda ze zauna madadinka, koda shike ga Hafiz nanma ai kaninka ne saiya zauna kawai right?
Mamaki ne yakama Bilal ko kwana biyu beyi ba an farakarɓan makulli? Yace to Daddy ka kaini ɗaki in ɗauka mishi.
_✔ote comment & share_
✍🏻 *JIDDAH S MAPI*
🌸🌸🌸🌸🌸🌸
*MAKAUNIYA CE*
🌸🌸🌸🌸🌸🌸
(An heart touching story)
*Written by*
Jiddah S Mapi
*بسم الله الرحمن الرحيم*
*🌈🇰AINUWA 🇼RITER'S✍🏼*
*🇦SSOCIATION🤝🏻*
_wannan littafin sadaukarwa ne ga yayata Maryam S Mapi_
*WATTPAD*
_Jiddah S Mapi_
*Page* 8
"Ɗakinshi Daddy yakaishi domin ɗaukar makullin, suna zuwa Bilal yaɗauko makullin har zai mikawa Daddy amma kome yayi tunani Oho, sai yace Daddy ina hanunka ga makullin, hannu Daddy yamika mishi yakarɓi makullin yana wani irin murmushi wanda shi kaɗai yasan ma'anarshi. Azuciyarshi kuwa yace gaba kaɗan rayuwarka zaka bani Yaro"
************
Da yamma suna Zaune afalo Daddyne yashigo falo a rikece yana kiran Bilal? Bilal? Bilal, Hajiya Salamatu ce ta amsa tace lafiya kuwa kake kiran Bilal da ihu haka?
Hajiya ina Bilal yau Allah yatona Asirin Wanda suka aikata mishi haka, yana faɗin haka ya karaso inda suke ya buɗe wata Video awayarshi yace kalli kugani wanda kayarda dashi shizai cuceka,
Sa Videon yayi a handsfree yanda kowa zeji me ake cewa,
Wasu mutanene guda biyu sun rufe fuskarsu da baƙin kyalle suna cewa Ai Latif ne ya aikasu su watsawa Bilal Acid a idonshi sabida wani dalili nashi wanda basu sani ba.
What!!! Latif cewar Bilal, no Daddy ban yadda ba Latif bazai taɓa cutar dani ba..... Dakata!!! inji Daddy kai wani irin mutum ne? Baka jin abunda suke faɗane? Ko sharri zasuyi mishi? Aina suka sanshi dazasuyi mishi sharri? Shi kaɗaine aduniyar dazasu tsallake kowa suzo kanshi?
"Kalamun Daddy sunyi matukar tasiri akan Bilal,
Magana yakeson yayi amma bakinshi yana rawa tsabar firgitan dayayi.
ganin haka yasa Daddy juyawa yasaki wata murmushi wanda shikaɗai yasan dalilin yinta.
azuciyarshi yace Yanzu aka fara wasan"
*************************
"Minal tana cikin kuncin rayuwa, babu inda Umma bataje neman aiki ba amma takasa samu, kamar kullum yauma suna zaune acikin gida suna hira Minal ce tace Umma?
Umma tace Na'am 'yata.
Umma inason in fara zuwa BARA.... Bara kuma Minal? Yaushe kika fara son duniya? Meyasa bazaki hakura da halin damuke ciki ba?.
Minal ce tafara zubar da hawaye tace "Umma ya bazanyi bara ba? Kiduba irin halin damuke ciki abinci ma neman gagararmu take, hannayenta biyu taɗaga tace ya Allah ka karɓi rayuwata, Allah kana ganin duk abinda yake faruwa, Allah ka gaggauta ɗaukan rayuwata kafin ta ɓaci gaba ɗaya... Ta karashe maganar tana wani irin kuka mecin rai, rungumeta Umma tayi sukaci gaba da kukan tare gwanin ban tausayi"
"Latif? No... Kodai mafarki nake ne Daddy? Bilal durkusawa yayi agaban Daddy yarike kafafunshi yace Dan Allah Daddy kafaɗan gaskiya Latif ne yake neman hallaka rayuwata? Latif ne ya makantar dani?"
Ɗagoshi Daddy yayi ya rungumeshi yana bubbuga bayanshi yace "my son idan baka gani ai kanaji, kasan dai babu yanda za'ayi mutanennan suce shiya aikesu, may be ma kuɗinsu ne be basu ba, amma insha Allah yau Latif baze kwana agida ba, agidan yari ze kwana sabida yayi kokarin kisan kai"
Aa Daddy kar ayi saurin yanke hukunci, ayi bincike tukunna kar muzo muna dana sani.... Enough! Karka kara samin baki acikin maganarnan, kai Amana ne awajena idan har nazuba ido wata rana kasheka zasuyi, wallahi, Wallahi, wallahi, nayi rantsuwa sau uku kuma nasan muhimmancin rantsuwa, bazan bar Latif da Abbanshi ba dukansu saina kai karansu kotu kuma dolene ayanke musu HUKUNCIN KISA!!! sabida sunyi kokarin kashe ran da babu hakki.
idan kaga Daddy alokacin zakayi zaton babu masoyin Bilal kamarshi,
Bilal gyara glass nashi yayi yaci gaba da kallon Daddy aɓoye, dashike yanzu yanasa baƙin glass irinna makafi.
Yace "to Daddy duk abinda kayanke daidai ne sabida kai amatsayin uba kake awajena, bayan iyayena babu wanda nakeso saikai Daddy,
Na Amince akama Latif amma ina neman alfarma ɗaya awajenka"
Faɗi alfarmar dakake so nikuma nayi maka alkawarin zanyi maka.
"Bilal yace Daddy dan Allah kar ayiwa Latif HUKUNCIN KISA!!! Ayi mishi horo iya abinda yayi niyan aikatawa......
_✔ote comment & share_
✍🏻 *JIDDAH S MAPI*
*بسم الله الرحمن الرحيم*
*____________________________________*
*🌈KAINUWA WRITERS✍🏼 ASSOCIATION*🤝🏻
```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}```
https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation
*domin shiga shafin mu na Bakandamiya danna nan*👇🏻
https://bakandamiya.com/group/71/kainuwa-writers-association
*____________________________________*
MAKAUNIYA CE
Na
Jiddah S Mapi
Page 9
"Shikenan babu matsala zanyi yanda kace. Godiya Bilal yayiwa Daddy daganan Daddy yafita yabar mishi ďakin cikin Farin ciki, kwanciya Bilal yayi yana tunani wannan wani irin jagwalgwalon rayuwane? Lumshe idanunshi yayi me ďauke da Zara Zaran eyelashes dafe kirjinshi yayi sabida wani irin zafin dayake mishi".
Minal yau ta tashi da ciwon ciki me tsanani dama kowani wata haka yake mata dazaran lokacin period nata yazo, kwance take akan katifarta tana murd'e murd'e fuskanta duk yajike da zufa ita kad'ai tasan me takeji idan period nata yazo, tana cikin wannan halin Umma tayi sallama, meya sameki Minal? Umma ci...ci....takasa karasa maganar tsabar azaba ganin yanda take rike cikine yasa Umma tagane me yake daminta, hannunta Umma tarike suka fito cikin gida, zaunar Da ita tayi
All Chapters
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 3 Chapter of 14