ai cikina sai ya ƙara ɗurar ruwa kamar fitsari zai zubo mun. Uwar gidan boka tace.
"Yara Boka yace ku nutsu, ki faɗi damuwarki, in kuma kina jin tsoro ku fice ku bashi waje. Mabaruka tayi carab tace.
"A'a Ungo wannan dai ƙawata ce, tana zaune da mijinta lafiya iyayenshi suka aura mishi ƙanwarshi, sabida basa son ƙawar tawa. Shine muka zo munason a mallaka mana mijin a hannu, sai yanda ƙawata ta juya shi, daga shi har danginshi, kuma a mantar dashi ƴan uwanshi. Ko iyayenshi ne suka faɗa bama so yayi, sai abunda matarshi tace mishi, duk da cewar daman kusan a hakan yake. Gaula dolo muke so a mayar dashi. Itama Amaryar ta zama sai abunda Zubaina tace mata, ta zame mata kamar baiwa, kuma a rufe mata bakinta karta kuskura ta kai ƙarar Zubaina, a sa mata kwarjininta, da tsoronta a zuchiyarta. Sannan muna son a lalata mishi gabanshi, ta yanda in ya je kwanciyar Aure da Amaryar zai koma kamar lagwani, in ya xo kwanciyar Aure da Zubaina sai ya zama namiji. A taimaka mana." Matar Boka data gama ji, sai ta zayyane ma boka dukkannin abunda yake tafe damu. Yayi magana amman ba mai yawa ba, cikin yarenshi na Tubi. Uwar gidan boka ta dube mu tace.
"Yace duk abinda kike buƙata zaki samu, amman da sharaɗin duk abinda zai biyo baya kar ki zargi kowa. In dai mallakar miji da kishiyane kin samu, kuma har ki mutu kece sarauniya a gidanki" Da sauri nace.
Na yarda da duk abinda zai biyo baya in dai ba mutuwa ko hauka, ko rasa Bulama bane, ni kuma a shirye nake ko nawa ne in kashe, ko da zan tafi tsirarane" Uwar gidan boka ta isar da saƙona ga boka. Dariya yayi, ya ɗaga hannayenshi dukka biyu sama, ya dinga wasu surkullen maganganu da ƙarfin tsiya. Sai ga wata ƙwarya ƙarama da wani tsumma ƙulle a hannunshi. Ƙwaryar ya sauke, ya miƙo ma Uwar gidanshi, tasa hannu ta amsa ta miƙo mun. Da sauri nasa hannu na karɓa. Wani irin maganine mai mugun warin tsiya, ga wani irin hunhuna da tsutsa a saman kwaryar. Amman haka uwar gidan boka tace in shanye maganin tas. Dana kafa kaina, na runtse idanuna ban ɗago ba, har sai da na shanye. Ƙwaryar na ajjiye ina ɗaga kaina sama dan wani irin amai ne naji yana taso mun. Wani ƙullukan magani ta karɓo a hannun boka ta ajjiye a cikin tsumma a gabana.
"Wannan wanka zaki yi dashi da kin je gidanki. Wannan kuma kwalline wanda aka haɗa da kitsen maciji, da kitsen biri, shi kuma a ko da yaushe idanunki ya zama yana saye da kwallinnan, sharaɗin shine daya ƙare zaki dawo a baki wani. Wannan kuma hayaƙin gidanki zaki yi dashi, ki tabbatar mijin naki, da ita amaryar sun shaƙi hayaƙin a dai dai sanda yake tashi. In zaki zuba hayaƙin a wuta, ki ambaci sunan mijinki sau uku, kishiyarki sau uku, sai ki zuba hayaƙin. Wannan kuma a abinci zaki zuba musu, an gama in dai sun ci. Shi kuma wannan layar, a bayan ɗakin baccin mai gidan naki zaki tona rami ki birne kuma tsirara zaki yi sanda zaki birne layar, kar ki kuskure, sannan kar ki bari kowa ya ganki. Kuɗinki million ɗaya. In zaki dawo karɓar kwalli da wasu hayaƙin kuma dubu ɗari biyu zaki riƙo duk zuwa." Cike da murna na zuge jakata nayi ƙarkaf, Allah ya soni ma kuɗin sun kai, har da ɗoriyar dubu goma sha ɗaya, duk na tarkata na ajjiye musu. Muka fito da baya, kamar yadda aka umarce mu. Mansa na ganinmu ta miƙe tana yashe baki.
"Har kun fito, sai mu je ko?" Jerawa mu ka yi, muna tafe Mabaruka na yi mun Dariya. Mansa tace.
"Ai daga yanzu kin dena bin ƙananun bokaye, shifa akwai biyan buƙata, sai dai ƴan siyasa da masu sarauta sun ɓata shi da tsadar tsiya, ni yanzu dubu ɗari biyu ya chajeni na magani kawai, banda sauran ƙananun abubbuwa. Sai dai fa zuwa wajanshi na sa talauci. Dan wallahi da mijinmu mai arzikin gaske ne, amman a halin yanzu komai nashi ya ja baya, kuma ya tabtabkar asarori masu tarin yawa manya_manya. Amman wallahi ko nawa ya samu a gabana yake zube mun su, ni ke siya ma kishiyoyina hatsin da zasu ci, in fa naga dama kenan. In kuwa banso ba, sai dai ko wacce ta yi surfau ko wankau ta ciyar da kanta da yaranta." Mabaruka tace.
"Ni kaina sanadin zuwana nan, na rasa abubbuwa da yawa, hatta Adamu sai da samun kuɗinshi ya ragu. Amman babban farin ciki shine ka mulki miji, ka juya kishiya yadda ranka ya so, kuma sai yanda ka tsarama mijinka sannan zai bi" Ni dai bana ma jin me suke cewa sosai, hankalina yana gida, burina in isa gida, ko dan in soma zartar da aikin da boka ya bani"
MRS BUKHARI CE. Ina siyar da turaren wuta da humra, da KULACCHAM, ƙamshi nauyi da ban daban. Akwai shu'umar humra ma, ga turarukan tsugunno, ga turaren turara jiki, dana turara kaya, mopping musk, Arebian Roomfresher, turaren kafet da dai sauransu Mrs Bukhari ta tanadar muku domun samun nutsuwarku. Mai buƙata ya tuntuɓeni (08179523215) ina maraba da masu sayen ɗaya ko sari.
_GAWURTATTUN UKU🔥🔥🔥2023 July 20 in sha Allah._
_1-NIHLATUL-KHAIR_
👇🏽
*(Ummu Affan)*
_2-ME IDO A TSAKAR KA duniya_
👇🏽
*Badi'at Mrs bukhari*
_ZULFA_
👇🏽
*Ummu maher(miss green)*
_Littafi ɗaya;400_
_Littafi biyu;800_
_Littafi uku;1000_
Ga masu son tura kuɗinsu ta acc sai su tura a wannan acc ɗin👇🏽👇🏽👇🏽👇🏽
0037219728
Fatima Rabiu Sunusi
StanbicIBTC Bank
Sai ka tura da shaidar biyanka ta wannan no ɗin👇🏽👇🏽👇🏽
08104335144
Masu tura kati kuma sai su turo screenshot na katinsu Mtn ta wannan no ɗin👇🏽
08104335144
*GA MASU SON A TALLATA MUSU HAJARSU A DUKKANIN SHAFINMU na facebook,whattpad,telegram,youtube,group da status,zamu tallata muku ne akan farashi me rahusa
10K ne kacal.
Sai ku tuntuɓe a numbobinmu kamar haka👇🏽👇🏽👇🏽
08104335144
07068606171
08179523215
Domin tallata muku hajojinku a cikin littafinmu na sati ɗaya ya kama👇🏽👇🏽👇🏽
2K
sati biyu
3k
idan kuma kanason har mu gama book muna ɗora maka ya kama
10k kacal.
Mun gode da zaɓar gawurtattu uku ako da yaushe.🙏🏼
*MAMAN ZEE ƘAMSHI AND KAYAN MATA!*
Shahararu goma kenan aduniyan kayan mata munsan kanmu munsan kayanmu bah ako inazakisamu kayan shahararu goma aduniyan kayan mata sai awajen m zee kamshi kayan mata available online
Gakayanmu kamarhaka
Tafi budurwa duniyane
Tsumin lahaula
Gombar bujenki jagab
Shu Umar zumarmu
Mumuna da,aeki
Makalemata
Hadin me jego d amarya d uwar gidan d bazauwara
Dahuwar kaza cicibin kala kala
Shu,mar humra baka d Fara namatan aure ne kawai akwai Nayan mata
Turare wuta kala kala saiwanda kikazaba kayanmu batarkace kayane na matan kwairai kumakunsani shahararu goma aduniyan kayan mata m zee ce dakanta 08063845136 ko 07019551505 Kar abaki labari.
Sannan maganin sanyi ba Sai kinada infection zakiyi amfani dashi ba Dole ne ga KOWACE mace maganin sanyi ya zama daya daga cikin abinda ba a rasata dashi a gidanta sannan kuma
AMARYA
MAI JEGO
WACCE ZATAYI KOME
Dolene kiyi amfani da maganin sanyi kafin ku hadu da miji wannan Dole ne indai kinason kiji dadin muamala da miji.
Duk amaryar da aka kaita dakinta batayi amfani da maganin sanyi ba toh tabbas tayi babban kuskure hakama duk Mai jego data haihu har ta Bari tayi arbain suka Hadu da mijinta batasha magani sanyi ba itama ta tapka babban kuskure.
Wllhy kaya na aiki kinga ikon Allah Wai😂🔥🔥🔥🔥🔥ance wanda y iya y huta toh wanda y siya ma wllhy yafi kowa hutawa Allah dai y biya. Ku tuntuɓe ni a wannan number domin ƙarin bayani, muna aika kayanmu ƙasa-ƙasa gari-gari. Sayen nagari mai da kuɗi gida. 08063845136 sai kunzo.
[26/07, 2:35 p.m.] +234 806 874 8984: MAI IDO A TSAKAR KA
(DUNIYA)
BADI'AT IBRAHIM MRS BUKHARI (B4B)
GAWURTATTU UKU
9
Yahanasu:
Tun asuba su Yanunu suka kammala shirin tafiyarsu tsab, harma su Bulama ƙarami ya saka musu jakunkunansu a mota. Ni kuwa ina kwance ina hawaye, ga wani irin mayen zazzaɓi wanda dashi nake tashi a bacci. Wakil ne ya leƙo ɗakin da muke yace.
"Yahanasu mu kam sai Allah ya ƙaddara saduwarmu, sai kun zo ganin gida, aita haƙuri. Ba Bagulaji Bulama Babba ya ba mai gadi dubu hamsin wai a baku, shi ya tafi wajan aiki. Matar gidan ma a wajan aiki ta kwana, ƙannenta da yaranta ne a cikin gidan. Mama Gana wacce ke tsaye tana gyara tsaiwar lafayarta tace.
"Kamar yadda ya bar ma mai gadi sallahu, nima ga sallahu ka bayar a ajjiye mishi. Dan ubanshi tun kafin yazo duniya muke ta'amali da kuɗi, da wannan kuɗaɗe aka gina mishi rayuwarshi ta fannin ilimin addini dana zamani, dan haka ba kuɗi bane ya kawo mu, a bar mishi kuɗinshi. Yanunu, Bagulaji ku tawo mu tafi." Fita su ka yi duk rayukansu a jagule ba daɗi, Fanda ta dafani taji jikina kau.
"Subuhanallahi Yahanasu naji jikin naki da zafi sosai ai" Ina sharar hawayen da ya zame mun jiki nace.
Babu damuwa zan lallaɓa in sha magani, in naji jikin babu daɗi zan yi ma Bulama Babba magana ya kaini asibiti." Allah ya ƙara sauƙi tayi mini ta fita, Kuɗi na ciro nera dubu goman da Alhaji Munka'ilu ya bani, na danƙama Hajja Fati.
Gashi nan ki kama sana'a kuma da zaran sana'arki ta kafu, sai ki yi ƙoƙarin komawa makaranta ki kammala karatunki, da zaran kin soma aiki, wasu matsalolin sai su kau" Karɓan kuɗin tayi tana godiya. Takaddar magani fara ta miƙomun cike da magunguna, nasa hannu na karɓa.
"Yahanasu, karki bari kaɗaici da tunani, da takaici ya haifar miki da ciwon hawan jini, ko ciwon zuchiya, ki kashe rayuwarki a banza da wofi. Ciwon rashin bacci shi kanshi yana iya haukata mutum, wannan maganin baccine, da zaran kin kasa bacci ki sha guda biyu kawai, dan ki samar ma kanki da ƙwaƙwalwarki hutu da sauƙi. Bazai gusar miki da hakali ba sam, zaki yi normal bacci daga dare izuwa safiya, kuma duk cunkushewar da zuchiyarki tayi, zakiji nauyin yayi ƙasa wanda in a sikeli za'a ɗaura a auna bai wuce nauyin kwalin omo ba" Hannu nasa na karɓi maganin na ja durowar gefen gado na jefa. Tare da Hajja Fati muka fita, nayi sallama dasu, Ba Bagulaji sai hawaye take yi, ina tsaye a wajan har suka fice mai gadi ya rufe get ɗin gidan. In ɗaga ƙafa in koma ɓarayina abun yaci tura, kuka kawai nake yi, ina tuno mahaifana da dangina. Ƙannen Zubaina ne suka zo suka wuce ni, hannunsu jaye da yaran. Sai habaice_ habaice suke yi, suna zage _zage. Juyawata nayi na koma ɓarayina, a kujerar falo na kwanta, nan jikina ya shiga rawa, gashi bani da mataimakin da zai taimakeni.
Kofur Zubaina:
A ɗakin Mansa mu ka rama sallolin da ake binmu, dan ni dai kam sun riƙe mun wuya sosai. Anan muka ga irin mulkar abokan zama da Mansa take yi, dakama kowa tsawa take yi harda mai gidan, hakan ya ƙara mun ƙaimi sosai. Anan mu kai musayar number waya, muka kama hanyar Kaduna. Muna shiga Kaduna wayata ta soma ring, Bulama ke kirana.
Allah ya taimaki mai taimakona, barka da safiya ango mijin amarya. Wato ko ɗan kiran da ka saba mun in zanyi aikin night jiya ba kai mun ba ko, harma na soma fuskantar canji kenan Bulama, duk ƙoƙarin danne kishina da nayi dan samun nutsuwarka? Ina kaiwa ƙarshe na fashe da kukan makirci har ina wani jan majina. Gabaki ɗaya na gama rikita kan Bulama, dama abu kaɗan ke ruɗashi, bashi da jumurin shanye abu, murya a raunace kamar mai shirin yi mun kuka yace.
"Haba rayuwata, uwar ƴaƴana kiyi haƙuri ki share hawayenki, ni wannan yarinyar bata sani a idanunta ba wallahi, dan ko su Mama Gana ban bari mun haɗu ba." Jin ya furta haka sai nayi cak da kukan da nake yi mara hawaye, na karya murya nace.
Nayi haƙuri uban ƴaƴana kishine ya motsa mun raina, kai kasan ina sonka, kuma kaine gatana, gatan dangina ma."
"Nasani Zubaina ta, ina sonki, babu wani abu da zai iya taɓa sonki a zuchiyata, ni kin ganni a office ma. Dan da asuba na fice a gidan, yau zasu tafi, na dai ba da saƙon dubu hamsin ma mai gadi, nace in sun fito zasu tafi ya basu" Wani tuƙuƙin baƙin cikine ya turniƙe ni. Amman sai na shiga jero mishi adda'ar buɗi a bisa ƙoƙarin da yake dashi.
"Babu komai matata, da daddare sai mu je mu dobo atampopin in mun dawo aiki ko? Sannan zan turo miki dubu ɗari ki riƙe a hannunki kya biya kuɗin ɗinki dasu. Far nayi da idanu nace.
Godiya nake yallaɓai Allah ya ja kwana. Cikin taushin murya yace.
"Ameen matata, bari inyi aikina, dan inna biye miki ke da zaƙin muryarnan taki, sai jikina duk ya mace" Dariyar da nasan in nayi ina motso mishi da duk wata sha'awar kasancewa tare dani nayi, kana nace.
Ka shirya, domun yau zan kai ka ɗakin amarya ni da kaina, dan har kazar Amare ni da kuɗina zan siya ma, kai dai ka sha kuruminka. Ƙit ya datse wayarshi. Dariya muka saka ni da Mabaruka harda tafawa, tace.
"Ƙawata bakya wasa da maza, ƙawata yanzu fa da ba dan kin cabki Bulama ba ko? Hmm yau da zai yi kwanan ɗakin Amarya wallahi da kinga kumumelesi. Ke ni fa ranar da Adam ya kwana a ɗakin Sagira kin san dan munafurci na maza har wani ihu ya saki, mutumin da ko nishi bayayi sai gashi ya ɓige da ihu. Jin wannan ɗan ƙara da Adam ya saki sai naji zuchiyata kamar zata tarwatse, banyi ƙasa a guiwa ba na fito saɗab saɗab na laɓe a tagar uwar ɗakinsu. Hmm takaici wallahi Zubaina ashe sambatu Adam ya shiga yi ma Sagira har yana ce mata yanzu yasan yayi aure, ashe mata suna suka tara. Ke haukatani fa Adam yayi, kiga yanda na fige na rame ni da gidana fa a lokacin" Ajjiyar zuchiya na sauke nace.
Amman lallai maza basu da mutunci akan son ransu, yanzu yana nufin kenan Sagira ta fiki komai kenan a wajanshi,mu da muke aika kuɗin magungunan mata har togo. Hmm ai ni bazan lamunci ganin takaici ba, yanzun ma ji nake kamar bazan iya barin Bulama ya dinga yi mana wani rabon kwana ba"
"Ƙawata wai ashe har yanzu tantama kike yi a aikin bokannan, duk abinda kika gani a gidana, da wanda kika gani a gidan Mansa, dana bakunan mutanen da muka haɗu duk baki gamsu ba wai? Hmmm ranar da nayi duk abubbuwan da bokannan ya sani, daga ranar har rana mai kamar ta yau Adam bai sake kusantar Sagira ba. Ɗan data haifa ma Allah ya ƙaddara zai zo duniya ne, tun a ciki nake aika mishi da boma bomai, shi yasa kika ga yazo ba lafiya, aikinane fa" Baki na washe ina dariya nace.
Gaskiya ƙawata baki da dama, kinci dubu sai ceto." Ƙaran kiran wayata ne ya katse mana hirarmu A S P ke kirana, nasan akan case ɗin ɗan luwaɗinnan ne yasa ya kirani, ni nama sha'afa. A ƙofar gidan Mabaruka na tsaya, sannan na ɗaga wayar. Adam ne ya zo ya buɗe ma Mabaruka ƙofar mota ta fita, ya amshi jakarta suka wuce, suka barni da sakakken baki. Daga nan aiki kuma na shiga, naje na gabatar da duk binciken daya dace, a hanyar zuwa office na tsaya na sai waina da miya, lokacin har azahar tayi, ni nama mance ko karyawa bamu yi ba, in banda shayi da mu ka sha a gidan Mansa. Daga nan na wuce office na soma gudanar da aiyukana. Da yamma na fito na tafi gida. Duk a gajiye nake tulus sosai. Harara na doka ma BQ ina jin wani tururin kishi na rufe ni. A guje Maryam da Bawa suka tare ni, sunata murnar ganina. Kawunansu na shafa, ina jin farin ciki sosai. Babu abunda yake burgeni sama da kasancewa a cikin iyalaina. Asiya ta amshi jakata, Nafisa tace.
"Anty tun ɗazu fa Mama take zaune tana jiranki."
Ah da gaske Nafisa?" Nafisa tace.
"Ai ta jima sosai a ciki" Da sauri na shiga cikin falon. Na tarar da Mama tayi baje baje a ƙasa tana cin shinkafa da miyar kaza, ga lemon kwalba da ruwan faro a gabanta. Wani daɗi naji sosai. A ko da yaushe in Mama tazo gidana tana santin irin daɗin da Bulama yake bamu, sai inji na tausaya mata, a lokaci guda kuma sai inji daɗi dana samu damar mallakar Bulama, dan ya tsamoni daga cikin ƙangin talauci, dama dai dani kab ƴan gidanmu suka dogara, ni kaɗaice nake aiki, su ko karatun kirki basui ba, in banda yanzu da Bulama ya ɗauki nauyin karatun nasu har zuwa jami'a.
"Zubaina kin dawo? Ke zauna inna gama fasa ƙashinnan mayi maganar" Dariya na saka mata nace.
Mama amman muje can ɗakina, dan Bulama ya kusan shigowa, kinga biyar ta gota, duk yanda akayi go slow ya samu a hanya ma." Abincin na ɗaukar mata muka shige ɗakina tare da banko ƙofar. Anan na labartama Mama duk halin da ake ciki, da magungunan da aka bani.
"Da kyau ƴarnan ai ba'a bori da sanyi jiki. Jiya banyi baccin kirki ba, sai mafarkai nake yi, wai Bulama ya sakeki yayi miki korar kare yayi miki kafirin duka." Bakinta na toshe.
Haba Mama wannan mafarki yayi tsauri da yawa. Aini da Bulama tamkar takone da ƙafa, mutuwa kaɗai ke iya rabasu." Magunguna ta sunto a bakin zaninta tace.
"Kinga wannan, a cikin abun sha zaki zuba mishi, yai ta sha. Wannan kuma da jinin al'ada ake haɗawa a kwaɓa, na ranar farko, sai ki gasa naman saniya dashi ki bashi yaci. Shikenan fa ƙurunƙus" Godiya na shiga yima Mama. Haka na shiga store na haɗo musu kayan abinci rigijib, na je na sauketa a gida, a gurguje na dawo. Nako ci sa'a Bulaman bai dawo ba. Wanka na faɗa nayo da wannan garin maganin. Na tsara kwalliya na fito fes dani a cikin goduwar rigar kanti baƙa, na rambaɗa kwallin wajan boka, na fito shar. Daddumar cin abincinmu na nufa na buɗe kular miya na barbaɗa garin magani, miyar kajine zuƙu zuƙu. Ina miƙewa Bulama ya shigo kici_kici da manyan ledojin shagonshi dake kan titin isa kaita, shagon saida dogayen riguna na mata da maza irinna ijib. A guje Bakura da Maryam suka fito daga ɗakin su Asiya, sun riga sun haddace dirin motarshi. Sakin ledojin yayi a ƙasa, ya ɗaga Maryam sama yana ta juyi da'ita suna dariya. Bawa kuma ya kama mishi ƙafafunshi sai tsalle yake yi. Daya sauke Maryam sai ya ɗaukeshi shima.
Sannu da dawowa Yallaɓai, yau me ya tare ka ka makara?" Ɗagowa yayi ya dubi tsakiyar idanuna:
BULAMA:
Kallon Zubaina nayi cike da so da kulawa, gabana ya bada wani bugu mai ƙarfi, take kaina ya sara mun, har sai da na ɗan kanne idona na gefen hagu. Sannan na sauke ajjiyar zuchiya, na kuma dubanta, sai Murmushi take zabgawa tayi kyau sosai, sai ƙamshin turaren Dubai gold take yi.
Ke dai bari, kece kika sani makara, dan naje shagone na ɗebo miki wasu dogayen riguna da aka kawo su yau, wannan ledar kuma ki miƙa ma su Asiya suma ƴan mata su saka. Wow kinyi kyau fa gimbiyata" Dariya mu ka yi duka. Ɗakina na nufa, ita kuma na barota a tsaye tana kiran Asiya. Wanka nayi da ruwa mai zafi, kaina naji yana ta tsananta ciwo sosai, ga zazzaɓi da ke shirin kamani. A daddafe na ɗauro alwala na fito. Baƙar jallabiya na zura, ina kan fesa turarena mai suna one million sai ga Zubaina ta shigo. Gabana tazo ta tsaya, ta ƙura mini idanu, yau idanun nata sai naji kaifinsu tamkar yana kekketamun jikinane.
Yallaɓai mun fa gode sosai da irin wannan ɗawainiya da kake yi, ubangiji Allah kar ya gajiyar dakai wajan kula damu." Hannu nasa a ƙugunta na hankaɗota jikina ta kuwa rumgumeni. Kaina wani irin saramun yake yi sosai, ba shiri na sake ta, na zauna a bakin gado dafe da kaina wanda nake jin kamar zai tarwatse.
"Lafiya kuwa Abban Maryam naga ka dafe kan ka?" A hankali nace mata.
Kai nane yake wani irin ciwo, sai sara mun yake yi. Kwakwalwar tawa kamar zata huje haka nake ji" Take Zubaina ta ruɗe ta shiga yi mun aikin sannu, gashi sai kiraye_kirayen sallah ake yi. Amman bana jin zan iya zuwa masallaci. Magani ta ɓallo ta bani da ruwa.
"Gashi kasha, sai ka ɗan kwanta, inya lafa maka sai kayi sallar." Baki na buɗe ta zuba mun ƙwayayon maganin guda biyu, ta bani ruwa na kora. Sai taga na miƙe kuma. Da zafin nama ta zaunar dani.
"Ina kuma zaka a cikin wannan halin?"
Sallah kina ji har an shiga Masallaci, kinsan ita Magriba lokacinta ƙanƙanine" Kai ta girgiza mun tace.
"Ina sai dai kuwa kayi sallarka a gida, komai sai da lafiya ake yi ai." Dadduma ta shinfiɗa mun, sai da na tada sallah sannan ta fita. Raka'ar ƙarshe sai a zaune na kawota, dan ciwon kan sai tsananta yake yi. Ina idarwa na kwanta a kan sallayar. Da sallama Zubaina ta shigo, hannunta ɗauke da babban farantin silba, da kuloli biyu a kai, da sauran tarkace.
"Sannu ya kan?"
To gashi nan dai. Zazzaɓi ma nake ji dai" Jikina ta taɓa, ai kuwa ta same shi kau.
"Subuhanallahi ko asibiti zaka taso in kai ka ne, jikin naji da zafi kau? Janyota nayi jikina, na ƙanƙameta tsam sam bana fatan abunda zai sa ta motsa, ɗan dama dama na soma ji. Da ƙyar dar na daure naci abinci, dan kar in ɗaga mata hankali sosai.
"To abu na farko da za'ayi shine, ya kamata kaje kaga halin da Yahanasu take ciki ko? Sannan sai ku tawo nan taci abincinta. Daga nan kuma ni da kai sai muje mu siyo kazar sayen baki, in kai ka ɗakin Amaryarka." Ƙur nayi mata da idanu cikin ɓacin rai sosai, dan banji daɗin yanda ta dangantani da Yahanasu ba sam.
In hakan kike so ai shikenan, kin nuna mun baki damu dani ba, kuma bankai ki kiyi kishi akaina ba....." Shishsh ta ɗaura yatsanta akan laɓɓana, dole na dakatar da magana.
"Bana son musu, kai dai je ka kirawota ku dawo tare. Wannan yarinyar bazan so ka shiga hakkinta ba. Su Ba Bakura ne fa suka aura maka ita. Ya zamemun dole in tayaka kai musu biyayya, wala Allah sa dena ganin baƙina. Kai dai kayi abunda nace kawai."
Allah yayi miki albarka ƴar aljanna" Miƙewa nayi na fice a ɗakin, na nufi BQ ba don son raina ba, sai don in faranta ran Zubaina. A takure a kan gado na samu Yahanasu sai rawar ɗari take yi. Kaina na kawar nace mata.
Ki taso muje kici abinci" Ban jira me zata ce ba na dawo falo, sai kallon tsarin falon nake yi. Idona ya kai wajan daining da aka mayar mata kitchen yayi kyau sosai. Sanye cikin farin hijabi har ƙasa ta fito. Sai ƙamshin humra take yi. Ina gaba tana biye dani har zuwa falon Zubaina.
Yahanasu:
Ba dan inaso ba na biyo Bulama Babba. Na biyo shine dan bana son yin musu dashi. Da siririyar sallama na shiga falon, Bulama na gabana. Wani hayaƙi na shaƙa mai ɗan karen yaji, take naji na sheƙeshi