Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
ne ɗayan ɗakin mu kwanta acan kawai, mu jenku ko?" Fanda ta bashi amsa. Bulama Babba baice komai ba, mu kai mishi sallama a wajan mu dai muka barshi, yana bin bayanmu da kallo" Bulama Babba: Ajjiyar zuchiya na sauke, ban gushe ba har sai da suka fice a falon. Na rufe ƙofar falon, tare da kakkashe wutacen gidan. Ɗakina na nufa kai tsaye. Tana kan table ɗin da nake aiki, itama aikin take yi. Jin shigowata ne, yasa ta ɗago ta zuba mun idanu, tana mun kallon sai yanzu ka tuno dani. Sai tausayinta ya kamani, ta bar falo ɗazu tana kuka, Mama Gana taci mata fuska, amman ban sake waiwayarta ba. Ashe kina ciki, su Nafisa sun kwanta a ɗakinki, da su Maryam ko?" A ido a ido nake kallonta, tare da karantar yanayinta, Murmusawa tayi kawai, bata ce komai ba." Mrs Bukhari gidan ƙamshi ce. *MAMAN ZEE ƘAMSHI AND KAYAN MATA!* Shahararu goma kenan aduniyan kayan mata munsan kanmu munsan kayanmu bah ako inazakisamu kayan shahararu goma aduniyan kayan mata sai awajen m zee kamshi kayan mata available online Gakayanmu kamarhaka Tafi budurwa duniyane Tsumin lahaula Gombar bujenki jagab Shu Umar zumarmu Mumuna da,aeki Makalemata Hadin me jego d amarya d uwar gidan d bazauwara Dahuwar kaza cicibin kala kala Shu,mar humra baka d Fara namatan aure ne kawai akwai Nayan mata Turare wuta kala kala saiwanda kikazaba kayanmu batarkace kayane na matan kwairai kumakunsani shahararu goma aduniyan kayan mata m zee ce dakanta 08063845136 ko 07019551505 Kar abaki labari. Sannan maganin sanyi ba Sai kinada infection zakiyi amfani dashi ba Dole ne ga KOWACE mace maganin sanyi ya zama daya daga cikin abinda ba a rasata dashi a gidanta sannan kuma AMARYA MAI JEGO WACCE ZATAYI KOME Dolene kiyi amfani da maganin sanyi kafin ku hadu da miji wannan Dole ne indai kinason kiji dadin muamala da miji. Duk amaryar da aka kaita dakinta batayi amfani da maganin sanyi ba toh tabbas tayi babban kuskure hakama duk Mai jego data haihu har ta Bari tayi arbain suka Hadu da mijinta batasha magani sanyi ba itama ta tapka babban kuskure. Wllhy kaya na aiki kinga ikon Allah Wai😂🔥🔥🔥🔥🔥ance wanda y iya y huta toh wanda y siya ma wllhy yafi kowa hutawa Allah dai y biya. Ku tuntuɓe ni a wannan number domin ƙarin bayani, muna aika kayanmu ƙasa-ƙasa gari-gari. Sayen nagari mai da kuɗi gida. 08063845136 sai kunzo. [26/07, 2:34 p.m.] +234 806 874 8984: MAI IDO A TSAKAR KA (DUNIYA) GAWURTATTU UKU BADI'AT IBRAHIM MRS BUKHARI (B4B) 6 takowa tayi har inda nake ina kwaɓe rigata, ta kama rigar ta taimaka mun na cire, kamar yadda ta saba yi mun a ko da yaushe. Ina samun kulawa fiye da tunani, Zubaina bata rageni tako ina ba. Zamanmu mai daɗine, kuma abun koyi, amman muna samun saɓani kamar yadda rayuwa take tafiya, kuma tana da yawan fishi sosai, da zaran wani abu ya haɗamu mara daɗi, take ƙaurace mun akan shinfiɗa, sannan duk tarairayar da nake samu a wajanta, ajjiyewa take yi a gefe, hakan ba ƙaramin galabaitamu yake yi ba dukkanmu, dan a ranar da muka shirya komawa muke yi tamkar mayu a shinfiɗa. Tunanina ta katse mun da cewa. "Ka shiga ka samu kayi wanka, na haɗa ma ruwan wanka, in ka fito ina da magana da kai." To Zubaina ta na gode, ina kuma ƙara gode miki" Ban ɗakin na shiga nayi wanka, tare da yin brosh, na ɗauro alwala. A zaune na fito na same ta, agogo na kalla, sha biyu saura kwata na dare. Wai kaddai wannan case ɗin ɗan luwaɗinnan kiketa faman yi har yanzu?" Kallona tayi taja dogon tsaki. "Kai dai ka bari, har yanzu bamu gama tattara bayanan daya dace mu tattara a kan mutumin ba, gashi A S P ya bamu lokaci, D P O ɗinmu gani yake kamar bama ƙoƙari akan case ɗin. Amman gobe zani kaciya ni da yara, zamu ziyarci gidan wasu yara biyu da shi mutumin yai musu fyaɗe, suna ƙarƙashin kulawar asibiti, sai ɗayan yaron dake anguwan dosa, sauran yaran sun mutu, amman mun tattauna da iyayensu. Ni bama wannan ya ɗaga mun hankali ba. Wallahi damuwata shine wannan kayan dake cikin mota, wanda ƴan uwanka suka zo dashi, amman Bulama ziyara kawai suka kawo mana kuwa, ni naga sunyi yawa ne ace ziyarace wannan kawai fa, sannan ga kaya cikin mota, duk da naga ba'a taɓa kayan ba, amman duk da haka na kasa samun nutsuwa" Zama nayi a kusa da'ita, na jawo hannunta ta dawo kusa dani. Ziyarace kawai, a gidanmu haka muke yi, in dai gidan ɗaya daga cikin dangi zamu je. Maganar kaya da kike yi, ni kaina bansan kayan meye ba maganar gaskiya, amman bai kamata kayan su ɗaga miki hankali ba ai, koma na meye, ko na waye dole zasu faɗa mun, zaki ji. Sai dai banji daɗin abinda ya faru ɗazu a falo ba. Kiyi haƙuri da dukkan maganganun Mama Gana, kuma kiyi taka tsantsan da ɓacin ranta, naso in taso in rarrasheki gudun fitinane yasa na zauna, amman zuchiyata tana tare dake. Amman Zubaina garin Yaya abincinki ya zama haka?" "Ni kaina ban sani ba, su Asiya na bari akan miyar, sabida an kirani daga wajan aiki kan maganar case ɗin ɗan luwaɗinnan, to kafin in fito sun gama miyar, kayi haƙuri bansan haka suka yi ba. Sannan ka bata haƙuri su ci abincina hakan ba zata sake faruwa ba" Murmushi nayi. Baki san Mama Gana ba ne. Ai bata haƙuri da zanyi shi zai sa ta zazzage kwandon faɗa, kuma tunda tayi rantsuwa ko kin dafa abincin bazata bari kowa yaci ba. Karki damu zan dinga siya musu har zuwa lokacin da zasu tafi. Su Wakil ma da asuba zasu juya kamar yadda suka ce mun. Gobe ƙarfe nawa zaki fita office?" Kuka ta fashe mun dashi. "Bansan me nayi ma ƴan uwanka suka tsaneni ba Abban Maryam, wallahi ni kuma ina ƙaunarsu sosai, dan Allah in akwai wani halina da ƴan uwanka basa so ka sanar dani in gyara" Rarrashinta na shiga yi, ina jin zafin kukan da Zubaina take yi. Aikin faranta mata rai na shiga, dan nasan shine kaɗai zai kwantar mata da hankalinta. Yahanasu: Ɗakin baƙi muka shiga kai tsaye. Katifa ce babba a yashe a ƙasa, sai ban ɗaki, shikenan abunda ke cikin ɗakin. A bakin katifar na zauna, Fanda ta zauna kusa dani, Hajja Fati ta zauna a ƙasa tana ba ɗiyarta nono. "Yahanasu zaman aure fa haƙuri da juriya shike rayar dashi. Da wasa kar ki sake ki zama mai raki da ƙorafi, sannan ki koyi tursasa zuchiyarki wajan ɓoye sirrin gidan aurenki. Fitar da laifin Bulama Babba ko laifin matarshi, ka iya jawo targaɗe ko karayar aurenku. Mu dukka dangin junane, abinda ya yi ki, shi ya yi Bulama Babba. Ba Bakura tamkar mahaifi yake ga su Ba Modu. Kiyi ƙoƙarin ganin kin sa Ba Modu a cikin farin ciki, ta hanyar tattala musu zumuncinsu. Da zaran kin fitar da magana, a kwana a tashi, za'a iya samun rashin daidaito, ko kuma gagarumin RIKICIN CIKIN GIDA. Bulama Babba bazai cutar dake ba, a hannunshi duk muka girma, tun bai mallaki hankalinshi ba, yake yi mana hidima, ni tausayinshi ma nake ji wallahi. Sabida da kin ganshi, kinga wanda baya cikin hayyacinshi, matarshi ƴar duniya ce, ko a fuska duniyancinta ya fito, ki bi su a hankali, ki kwantar da kai kiyi tsantsar biyayya ga mijinki, ɗan uwanki, dan Allah ki rufa mana asiri. Ki duba sabida halin dattaku irinna Ba Bakura,ya haɗa aurenki da Bulama Babba ne sabida ya sama miki sauƙin rayuwa a cikin ƙunci, duba da iftila'in da ya yi kotse a cikin rayuwarki, muma ya taɓa zuchiyoyinmu, ki dinga tunawa da wannan." Jikina sai naji ya sake macewa mus, har nake jin ko da yankar naman jikina Bulama Babba yake yi, shi da matarshi, zan bishi zan zauna dashi, ko dan in faranta ran mahaifana, kuma in kare dagulewar zumuncinsu mai kyau ta dalilina. Hawayene yashiga zarya a kumatuna, Hajja Fati tace dani. "Kuka ba naki bane, bai kuma kamace ki ba. Yahanasu ki dage akan adda'ar Allah ya baki yaddar mijinki, ya kare ki daga sharrin dukkannin wasu masharranta. Ki yi haquri, muma da mu kai auren soyayya kina ganin yanda muke fama, ni kaina gudun kar in tsunduma Mama a halin damuwa ne yasa nake zaune da Baban Nasiba. Amman wallahi zaman cutuwa nake yi. To Mama tana da ciwon Suger, ga hawan jini, kullum nasiharta dani shine, in zauna inyi haƙuri a gidan mijina. Shawararki dai kawai zan ɗauka, na komawa makaranta, zan nemi ƴar sana'a in kama dan in samu in dinga biyan kuɗin makarantar. Mata da kike ganinsu a taron gidan biki ko suna, ko makaranta, ko ma'aikatu. Damuwowinsu na gidan aure wata da zata huda miki cikinta, kiji halin da take ciki tsakaninta da mai gidanta. wallahi sai kin ɗauka ba'a duniya kike ba, tsabar firgici. Maƙwociyarmu Maman Binta, bari kiji abunda ya faru da ita. Bazawarace Allah yayi ma mai gidanta na fari rasuwa. Suna zaune a wani ƙauye a nan Yola. Bayan rasuwar mijinta, ta shiga takaba, tana da yara uku da shi, biyu maza Babbar itace Binta mai shekara goma sha biyu. Data gama takaba, sai dangin mijinta mai rasuwa, su ka sa akai rabon gadon ƴar gonarshi da ya bari. Aka raba aka faɗi na kowa, harda nata tumunin takaba. Sisi basu ɗauka sun bata ba, sai suka ce da dukiyar, da yaran nasu ne, zasu haɗa su riƙe. Suka bata tuminin takabarta, ta kama hanya ta dawo Yola. Bata jima ba ta yi aure, aka kawota nan kusa da gidana, ana zumunci da'ita. Mijin data aure mai ƙaramin ƙarfine, kuma bama ita kaɗai bace matar tashi, mai gadine a wani asibiti, ganin haka sai maman Binta ta nemi aikin shara da wankin ban ɗaki a asibitin da mijinta ke aiki, cikin yardar Allah ta dace. Tare suke zuwa su dawo tare, a haka ta haifi yara biyu. Data je ƙauye ganin su Binta, sai ta nemi tawowa da Binta, dan ta ɗan sata a makaranta, ta kuma dinga kama mata aikin gida. Ta tawo da Binta, ana nan ana nan sai Binta ta shiga ciwo, tana ɗaukar Binta ta kaita asibiti, gwajin farko akace ciki take ɗauke dashi. Maman Binta ta shiga tashin hankali tare da tuhumar Binta wanda yai mata cikin. Hmm abun mamaki mijin Maman Binta ne ashe yake lalata da Binta, sau uku yanai mata ciki, suna zubarwa, a na huɗunne Allah ya tuni asirinsu duka, tunda ba tursasama Binta yayi ba, da son ranta komai ya dinga gudana. Kunji fa ƙarshen duniya, da ire_iren halin da wasu matan suke ciki a gidajen aurensu, wannan ba komai bane wallahilƙudrat akan halin da wasu ke ciki. A razane na dubi Hajja Fati nace. Kuma ya makomar aurensu ta kasance Hajja Fati?" Murmushin takaici tayi mun tace. "Kema kinsan makomar rabuwace kawai ai, amman ya cutar da'ita. Haka suka tattara suka koma gidan iyayenta. Yarinyar harta haihu ma, gashi maman itama tana da yara biyu dashi, amman dasu ta tafi, dan har kotu suka shiga. Hmmm Yahanasu nifa kaina a cikin matsaloli masu tarin yawa nake, daga wannan ya lafa sai wannan ya ɓullo, wallahi har ya zame mun jiki." A wannan daren kamar yadda suka ce, zamu raba dare suna bani magana. Hakan kuwa akayi, kuma na ƙaru gaya. Amman ni har su kai bacci idanuna biyu. Alwala na ɗauro na shinfiɗa ɗankwalina, na soma kai roƙona ga mahaliccina, buwayi gagara misali. Na yi sallah har ƙafafuna sai da suka kumbure. Kuka nayi shi a gaban mahaliccina, tare da roƙonshi ya bani juriya, da ƙarfin zuchiyar ɗaukar duk abinda zai tunkaroni a zaman aurena. Ya bani hanyar ɓullewa ba tare da naje gaban waninshi na durƙusa dan neman tallafi ba. Ya bani juriyar kawaici, da yakana kamar Ya Innana. Daga ƙarshe na tashi, na sha ruwa dan ɗaukar azumin nafila. Saini na tashi su Fanda dan su yi sallar asuba, idanuna sun kumbura da ganina, kasan nayi kuka har hawayena sun ƙafe. Ina jiyo muryar Bulama Babba yana magana da su Wakil. Sallar Asuba muka gabatar dukkanmu, ina zaune ina azkhar, na jiyo dawowar su Wakil. "Fandau ku yi maza, asubar fari muka so tafiya. Amman Ba Bakura yace muje gidan Amininshi Alh Munka'ilu tare dukka." Bulama ƙarami ke magana da Fandau, fita tayi taje ta same shi. Yarinyar Hajja Fati sai canyara kuka take yi, Hajja Fati ta shiga aikin jijjigata, da ƙyar ta koma bacci. Wai ni Hajja Fati wannan maganin da naga kin sha jiya, na menene wai?" Dariya tayi mun. "Maganin cire damuwa, da sanya nutsuwane, da in na sha, sai in kwan in wuni ina cikin bacci, amman yanzu ya riga ya bi jikina, in ba haɗe haɗe nayi masu yawa ba, baya sani bacci. Sai dai in na kwanta bacci ina samun yin lafiyayyen bacci, hakan yana taimakamun wajan sauke mun hawan jinina, kinsan masu hawan jini anason su dinga samun bacci lafiyayye, musamman na dare." Idanu na zare nace Ke nan kwayar da masu shaye_shaye suke sha ne, kema kike sha Hajja Fati, har matsalar da kike ciki takai wannan ne?" "Tafi yanda kike tunani, kina cikin halin rashin samun bacci mai kyau kema, tun sanda akai miki fyaɗe, zaki fahimci ciwon rashin bacci shi kaɗai masifa ce. Ga baƙin ciki da takaicin ɗa namiji. Da zaki sha guda ɗaya bacci zaki yi mai kyau, a ƙalla zaki rage wani zugi daga cikin zuchiyarki, kuma kanki zai rage nauyi, zan baki ki ajjiye ƙila yai miki amfani" Murmushi nayi. Haba dai Hajja Fati, babu amfanin da zai yi mun. Duk da nasan rashin bacci, ciwone babba, ni bama shi kaɗai ke damuna ba, harda rashin son ganin kowa a kusa dani wallahi, yanzu haka jina nake yi kamar in kurma ihu fa. Sasaucin da nake samu shine karatun Qur'ani da nake yi, a duk sanda naji zuchiyata ta raya mun cewar, in kashe kaina zan huta. Amm...... Kukane yaci ƙarfina sosai, ga kaina kullum a cikin ciwo yake a ko da yaushe, sakamakon rashin samun lafiyayyen bacci. Rabon da inyi bacci mai tsayi, tun kafin wannan ƙaddarar ta dirarmun, tunda wannan abun ya faru dani, zuchiyata bata sake samun nutsuwa ba." Rarrashina Hajja Fati ta shiga yi, tana bani baki. Hawayena na share, muka fito falo. A nan muka samu su Wakil da Fandau suna tattaunawa. Duk idanu suka ƙura mun. "Lafiya idanunki da fuskarki suka kumbura haka Yaha? Nifa ina tsoron damuwar da zaki shiga bayan tafiyarmu, ga rashin son shiga mutane da kike yi, in muka tafi kar ki je ki kashe kanki da tunani" Wakil ne yake yi mun Magana cikin nuna kulawa." A'a bazan kashe raina da tunani ba. In kunji kabarin mutuwa ta, to daga rabbissamawati ne, kar ku damu ƴan uwana, na gode da kulawarku, zan iya kulawa da kaina ni fa ba yarinya bace" Bulama ƙarami yace. "Kajita fa Wakil, wai ita ba yarinya bace, yaushe yaushe yarinyarnan, ita da su Ba'a Kaka muke zuwa ɗaukosu a makarantar firamare?" Wannan maganar da ya faɗa ita tasa duk muka kwashe da dariya, nan sukaita ɗan jana da raha, har sai da na saki jiki dan kaina. Ƙarfe shidda muka shiga ɓangaren su Bulama Babba. Mama Gana da Yanunu, da Bagulaji muka samu a falon, suna saman kujera Bulama Babba yana gurfane a gabansu kamar mai ɗaukar gafara, faɗa mama Gana take yi sosai, Bagulaji da Yanunu sai bata haƙuri su ke yi. Dubanmu tayi tace. "Ku shigo ku zauna. Kai kuma ka biyo mu ɗaki dan akwai muhimmiyar magana da zamu tattauna da kai. Tunda dukkan ku fita aiki zaku yi ku barmu jiran gidan, tunda baka san mutunci ba, wallahi ka bini a hankali daga kai har matarka da ƙannenta na faɗa maka kenan. In banda iskanci har mu kake faɗama akwai muhimmin aikin da zata je ta gabatar, da uwarta ce tazo gidan ai bazata hofantar da'ita haka ba. Kuma wa zai bamu abincin da zamu karya kumallo dashi tukunna?" Ya Bagulaji tace. "Mama Gana ki bar yaronnan ya huta haka na roƙe ki, sannan ke kika ce bazaki kuma cin abincin matarshi ba, muma wallahi bama so akai kasuwa. Kai kuma Bulama kaci gaba da bin maras kunyar matarka Allah ya bamu lafiya. Kuma tunda baka ƙaunar zaman mu, zamu tattara mu bar maka gidanka yau ba sai gobe ba, ni dai bazan sake tako ƙafata in zo ai mun rashin daraja ba. Mama Gana mu shiga daga ciki mu sanar mishi abinda ya kawo mu, dan karma yayi tunanin dan kuɗin daya tara muka zo mishi gida" Da kuka ta ƙarashe maganarta, tare da shigewa ciki, suma baya suka mara mata. Shi kuwa Bulama Babba ba guiwa haka ya bi bayansu, idanunshi sun kuma rinewa, hawaye tab gurbin idanuwanshi. Ni kuwa tuni hawaye ya gama wanke mun fuskata, da sauri na fice a falon, na koma B Q ina kukan fitar hayyaci" Bulama: Gabaki ɗaya zuwan su Mama Gana ya zame mun matsala, tun sassafe an tusani gaba da tijara, sai kace wani ƙaramin yaro, ko iyayena naga ai sun shafa mun lafiya. Ɗan guntun tsaki naja a fili, bayansu nabi zuwa ciki. Sharar ƙwallar dana shigo na tadda suna yi, sai ya karya mun guiwa. Gurfana nayi a gabansu, ni dai bance komai ba, akwati na gani sabo fil a gabansu, a buɗe akwatin yake kayan maza na hango a cikin akwatin, harda su huluna zanna. Ya Bagulaji tace. "Wannan zuwan da kaga munyi, umarnine daga wajan Bakura, da Hajja Gana ba wai yin kanmu bane, kai baka bimu ba amatsayinmu na iyayenka, ai kuwa baka isa mu mu biyoka ba,. Wannan akwatin daga gani a gabanka, kayane wanda al'adar Kanuri ta tanadarwa ango, wanda yake fitowa daga dangin Amarya . A cikin akwatin akwai shaddajo, akwai yadika, wasu kayanma anyi musu ɗinki irin na sarakai, akwai takalma, turare, agogo, huluna, sallaya da Qur'ani. Dukka naka ne Bulama Babba. Ga Yahanasu nan Ba Bakura ya aura maka ita, ma'ana matarka ce ita a halin yanzu. Yayi hakanne dan sanin cewar ya isa da kai, kuma shi ya haifeka, ya ɗau jirimin tarbiyantar dakai, da baka ilimi. An haɗa aurenne a sakamakon ƙaddarar data gibta cikin rayuwar Yahanasu, aka samu wani azzalumi ya keta mata haddinta, yai mata fyaɗe. Anyi taro sosai kafin a haɗa aurenka da'ita. Kai dai jininta ne, muna da tabbacin in dai kana cikin hayyaci, da nutsuwa, baza ka bari wani ma ya cutar da Yahanasu ba, ballentana kai a kan kin kan ka ace ka cutar da'ita. Ya rage naka in ka hofantar da ƴar uwarka ka rungumi bare. A wajanka ne kaɗai zata samu nutsuwa, ba tare da ta fuskanci ƙalubale dangane da ƙaddarar data faɗo mata ba" Tunda ta soma magana jikina da hantata suke rawa, kalmar Aure data faɗa ya firgita tsigar jikina, ya jijjiga duk wata tsokar dake jikina. Maganar fyaɗe yasa na ɗimauta, harma na rasa wanne tunani zanyi, damuwata shine taya zan tunkari Zubaina da wannan zancan, sannan a matsayina na wan Yahanasu ya zamu yi mu gudanar da rayuwar aure, a rasa da wanda za'a haɗata saini, saida akai mata fyaɗe bata da wata daraja sannan za'a liƙa mun ita, mummuna da'ita ƴar lukuta wannan ai abun kunya ne ma a gareni ace Yahanasu ƴar lukuta matata ce, anya kuwa Ba Bakura suna ƙaunata kuwa? Ciwon kan da nake fama dashine ya kuma tsananta, sai tsalle zuchiyata take ta faman yi, in haɗiye yawu ma in samu salama abu ya gagara, sai dambe nake da yawun bakina. Ina cikin wannan saƙe saƙen na kuma jiyo muryar Mama Gana tana cewa. "Sannan Bakura yace mu sanar maka, in har ka kasa riƙe Yahanasu tsakani da Allah, to bazai yafe maka ba, ya kuma da cewa in kayi sanadiyyar wargajewar zumuncinmu, bazai yafe maka kan wannan ba. Da munso mu ni da Yanunu muyi ma Yahanasu zaman bakwai. Amman a halin yanzu mun canja ra'ayi, tafiyar da su Wakil zasu yi yau, na dakatar da'ita. Su bari zuwa gobe in muka gama yi ma yarinya jere, sai mu ɗunguma mu tafi baki ɗaya, sannan inaso ƙannen baƙar tijararriyar matarka su bar gidannan kafin mu tafi, domun hakan zaifi muku alkhairi baki ɗayanku. Ni dai na kasa cewa komai, sai ta'ajibi nake yi a zuchiyata, da ƙyar na ka da baki nace. Amman to a ina zata zauna ita Yahanasun, gidana na zaman mutum ɗaya ne, sai masaukin baƙi da nake dashi, kuma ƙannen Zubaina suna zuwa suyi mana hutun makaranta, acan suke sauka. Sannan Mama Gana kiyi haƙuri kar kice na yi miki rashin kunya. Amman su Asiya anan zasu ci gaba da zama tare damu, domun ni nake kula da su, kuma nauyin karatunsu akaina ya rataya" "Rufe ma mutane baki gafara, rashin kunya kuma na nawa, ai baka cika ɗan iska ba tunda baka haɗesu ka auresu dukka ba ƙarshen zama kenan. ƙannen Zubainar banza da wofi. A can BQ ɗin zamu jera kayan ita Yahanasun, sai ta zauna a can, ita kuma mai sarautar birnin zuchiyarka saita ci gaba da zama a nan, tunda dama nata ne, kar a takura mata, su sakata su wala da ƙannenta. In ƙannen nata maza sun zo hutun sai ka basu naka ɗakin su kwana, akwai wani gyara ko fenti da BQ ɗin yake buƙata ne?" A'a baya buƙatar gyaran komai, baifi wata ɗaya ba dana sabunta fenti, sai dai babu kitchen a ciki, bansan yaya zata yi ba" Ya Bagulaji tace. "Zamu ga dabarar da zamu yi mata dangane da wannan, maganar abincin kari fa Yaya zaka yi damu?" Me gadi zai kawo muku waina, tun ɗazu ya tafi siyowa, ni zan tafi office sai na dawo" Ficewa nayi a ɗakin, ina jin kaina kamar zai buga, ji nake yi kamar a mafarki, wai ni aka aurama Yarinyar da akaima fyaɗe, hmmm gaskiya iyayena ba ƙaunata suke yi ba. Ba wanda na kalla a falon, ɗakina na wuce kai tsaye, dan shirin fita office. Zubaina na samu a ɗakin tanai ma Maryam wanka, Bawa kuwa har ma ya sa kayan makaranta. Kallon Zubaina nayi, idanuwana sai wani zugi suke yi mun. "Meke faruwa Bulama, naga fuskarka ta sauya, duk da dai ina jiyo yanda ƴan uwanka suka dura a kan ka. Ka yi haƙuri kasan fa sai haƙuri da ƴan uwa, amman bana jin daɗin yanda suka tsangwameka, kuma duk dan sabida nine" No ba sabida ke bane Zubaina, ba sona suke yi ba. Tunda suka zo basu barmu mun huta ba. Ni wallahi bana farin ciki da zuwan nasu, shi yasa ma bana son zuwa inda suke. Mtwss. Naja dogon tsaki mai sauti. Kaya na sake, ko karyawa bana ƙaunar yi, Zubaina tayi tayi dani in karya, amman naƙi, jikina wani irin ɓari yake yi. Tsoron Zubaina na barazanar kekketa mun zuchiyata. "Maganar kayan da suka zo dasu cikin mota fa sun sanar da kai na menene, tunda sunce sai da safe? Ni har mafarkin kayan sai da nayi" Gabana ya yanke ya faɗi, amman bana iya ɓoyema Zubaina komai, kuma ko na ɓoye zata sani dan bama abun ɓoyewa bane. Bawa kuje ku samu su Asiya a ɗakin Momy ko maza yanzu zan zo sai mu tafi" Zubaina tace da Bawa. "Kace su baku tea ku sha, maza kuje" Nutsuwarta ta dawo dashi gareni tace. "Ina sauraranka, baka da lokaci, dan ka kusan yin latti" Jim nayi,

Chapter 6 of 11