kuma sai su turo screenshot na katinsu Mtn ta wannan no ɗin👇🏽
08104335144
*GA MASU SON A TALLATA MUSU HAJARSU A DUKKANIN SHAFINMU na facebook,whattpad,telegram,youtube,group da status,zamu tallata muku ne akan farashi me rahusa
10K ne kacal.
Sai ku tuntuɓe a numbobinmu kamar haka👇🏽👇🏽👇🏽
08104335144
07068606171
08179523215
Domin tallata muku hajojinku a cikin littafinmu na sati ɗaya ya kama👇🏽👇🏽👇🏽
2K
sati biyu
3k
idan kuma kanason har mu gama book muna ɗora maka ya kama
10k kacal.
Mun gode da zaɓar gawurtattu uku ako da yaushe.🙏🏼
[26/07, 2:34 p.m.] +234 806 874 8984: MAI IDO A TSAKAR KA
(DUNIYA)
GAWURTATTU UKU
BADI'AT IBRAHIM MRS BUKHARI (B4B)
3
Ina miƙa saƙon godiya a gareku masoyana na haƙiƙa, naji daɗi sosai da yanda kuka so littafin mai ido a tsakar ka duniya. Ina alfahari da masoyana na faɗin duniya.
Masoyana na niger ban barku a baya ma, ni da ku son so fisabilillah.
Saƙon gaisuwata a gareki.
Fatima Sulaiman, nagode da soyayya.
_*YADDA ZAKI BURGE MIJINKI*_
_1⃣-Garin Nahal_ babban cokali 2.
_2⃣-Garin yayan bagaruwa Qaramin cokali 2._
_3⃣-Garin kanimfari cokali 1._
_4⃣-Garin almiski ko ruwan almiski._
_Zaki kwabasu gaba daya, yayin da zakije gun mai gidanki sai kiyi turarensu ki tsuguna ya shiga gabanki, Insha Allah maganar birgewa gun mai gida kin gama dashi ko harararki ake daga sanan an daina......_
BA BAKURA:
"Da farko inaso in soma da ku mazan gidan. Masu iyali da waɗanda suke shirin ɗauko iyalin. Yarane ku masu ilimi, kuma masu taimakon iyaye da ƴan uwa. Duk kun haɗe kawunanku, ku ke ciyar da gidan, mu ƴan kuɗaɗenmu in mun samu sai dai muyi ma kanmu hidimar da muke so, da matanmu, da taimakon masu buƙata. Kune kula daci da shanmu, kune kula da abun hawanmu, sutura, kula da ƙannenku, kula da iyayenku matan duka. Alhamdulillah ko a yanzu na faɗi na mutu, na cika wasiccin da iyayenmu suka bar mun, cewar in kula da ƙannena. Na kula dasu, na kula da matansu, na kula da yaranmu duka. Gashi kuna kulawa damu a Yanzu, dama duk ɗan daya samu tarbiyya daga wajan iyayenshi, da izinin Allah, Allah zai dafa ma iyayen ta hanyar shiryar musu da wannan yaron, domun ya kula da tsufansu, mu kam Alhamdulillah shine abunda zance. Abinda zanja kunnenku akai shine, kar kuyi sake da adda'a kamar yadda ɗan uwanku Bulama Babba yayi sake da yin adda'a, har Matarshi taci nasarar rabamu dashi. Yau shekara biyu bansa Bulama Babba a idanuna ba, a wannan shekarun baifi sau huɗu mukai waya ba, shima wayar da muka yin, ni na ke soma kira, sannan saiya kirani. Babu ciwon da yafi wannan, ka haifama duniya ɗa, ya tare a jikin matarshi da danginta, yasa ƙafa yayi fatali damu. Mahaifiyarshi, kusan kullum saita zubda hawayen damuwar rashin ɗanta. Ta ɗauka ban sani bane, ina sane, kuma ina gani. Kuyi ƙoƙari karku yi sake a raba mu daku. Ku kuma matan, da masu auren da waɗanda suka ɗaura ɗambar shiga gidan aure. Kuji tsoron Allah ku mutumta mazajenku ku mutumta iyayen mazajenku, ku mutunta dangin miji, kar ku bari muyi kuka daku. Duk da nasan kab ɗinku babu wanda yake auren bare, acikin ku masu auren. Marasa aurenma babu wanda ya zaɓi bare, duk ƴan uwan junane, aurene na zumunci wanda aka haɗa da kyakykyawar niyya, dan ganin mun haɓaka zuri'a da kuma haɓaka zumunci. Wanda a wannan lokacin zumunci yayi ƙaranci, badan komai ba, sai dan dena auren zumunci da akayi. Yara kansu ya waye, sunfi ƙarfin ace musu suyi, suyin. Zamani yazo da sauye sauye, waɗannan dalilan su suka rushe mana zumunci, mu kuma in Allah mun ɗaura ɗambar haɓaka zumuntarmu. Yahanasu itama tabi sawon Bulama Babba, Nasiru dai Kanuri ne, amman ba danginmu bane. Duk da dai auren ma reto yake yi, dan gane da abunda ya faru, gani nake yi kora da hali iyayen yaronnan suke son suyi mana. Ni kuma na yanke hukuncin cewar mun haƙura, zamu mayar musu da kuɗin gaisuwar da suka kawo. Sannan babban maƙasudin wannan zaman dana tara yau, sabida Yahanasu ne, da kuma tunatar daku girman zumunci, da girman kula da iyaye da ƴan uwa. Allah ya isa akan duk wanda yayi yunƙurin rushe mana farin cikin gidannan. A matsayina na uba a gidannan, ba a wajan Yahanasu ba harma a wajan Innana da Modu. Zan ɗaura auren Bulama Babba da Yahanasu, za'ayi biki irin wanda ake yima duk wata ƴar gata. Amman bana fatan wani daga cikinku ya sanar da Bulama Babba wannan lamarin. Mama Gana, kece zaki kai Yahanasu Kaduna ɗakin mijinta. Ki faɗa mishi ban yafe mishi ba, in yabar ɗiyata ta zubar da hawaye, ban yafe mishi ba in ya bari sanadin aurenshi da Yahanasu ya kawo rabuwar kan zuriyar Bulama Bukar. Me magana yayi, dan ina ganin dukkan abunda zan faɗa, ya ƙare kuma, ina mai ba Yahanasu da Innana haƙuri a bisa wannan hukunci dana zartar, amman wannan aure babu makawa."
Yahanasu:
Gabana sai dukan uku_uku yake yi. Tunda Ba Bakura ya furta zai haɗani Aure da Bulama Babba. Hantar cikina ce ta soma disko, wani irin jiwa na ɗibana daga zaune. Ta ina zan soma da namijin da matarshi ta rabashi da mahaifanshi, ni wanne irin zama zanyi dashi kenan? Innalillahi wa'innailaihil rajiun, rana zafi ina ƙuna, ni Yahanasu da wanne zanji? Haƙiƙa Ba Bakura ubane, kuma ba'a taɓa ƙetare umarninshi ba, tunda ya haɗa aurennan nasan kamar anyi an gama ne. Amman nasan rayuwata zata dawo abun tausayi da kwatance ne. Sai dai Ya Innana ta horar damu, juriya da haƙuri, da ɗaukar dukkan wani abun da zai samemu na tashin hankali, ya zama ba komai ba. Lokaci ɗaya, manyan al'amura suka sameni masu girman gaske. Na rasa darajata, gashi za'a aurad dani ga mijin tace. Hawaye tuni ya gama wanke mun fuskata. Satar kallon Ya Innana nayi. Itama hawayene ke fita da ga idanunta, tana yi tana sharewa da hannun lafayarta daga ganin fuskarta bata so wannan haɗin ba. Dan tasan cutuwa zanyi sosai. Ba Baana ne yayi gyaran murya yace.
"Ni abunda nake gani shine, ko za'a tambayi Bulama Babba tukunna aji ra'ayinshi dangane da hakan? Sabida gudun kwaɓewar zumuncin. Kunga dai yaronnan fa sai abinda matarshi hamshaƙiya tace, kar mu zo ayi abunda daga baya za azo ana cizon yatsa. Bakura kayi haƙuri bawai ban girmama umarninka bane, face gudun abunda ka je ka zo" Yana cikin jawabi Mama Gana tace.
"Zancan ɓur kenan inji tusa. Baana baka gane inda aka dosa ba ga dukkan halama. Ni abunda na fahimta shine. Zamu jefi tsuntsu biyu da dutse ɗaya ne . Zamu haɗa auren Bulama Babba da Yahanasu sabida zumunci, sannan shi ɗan uwanta ne zai fi bare riƙe ta da daraja, duba da asarar budurcinta da ta yi. Zamu haɗa auren Yahanasu da Bulama Babba sabida ta shiga rayuwarshi wala Allah ta sanadiyyarta shima ya samu rangwame, Allah ya kuɓuto dashi daga hannun azzalumar matar da yake aure, sannan zai kare mutuncinta a matsayinta na wacce ta rasa darajarta ta ɗiya mace, sai yafi kowa sanin kimarta, tare da taya ta jin ciwon abunda ya farun da'ita. Kuma shine kaɗai yake da nisa, kuma shi kaɗai yake auren bare, wannan aure da Bulama Babba yake yi da kofur Zubaina, kowa yasan tun fil azal babu wanda yaso haɗin, kanuri sai kanuri." Ba Modu yace.
"Koma dai sabida menene. Ba Bakura shike da iko akan kaina, dama iyalan nawa. Ni bani da ja akan duk abinda zaka zartar. Kaine da wuƙa da naman, Yahanasu taka ce Bulama Babba naka ne, tuwo na mai na. Fatanmu shine Allah yasa ayi damu. Allah yasa hakan shine mafi alkhairi a garemu baki ɗaya." Ba Bakura, ya fashe da kuka shi da Hajja Gana. Haƙiƙa kukansu ya bayyanar da zafin da zukatansu suke yi akan ɗansu ƙarara. Take a wajan naji cewar zanyi biyayya irin biyayyar da iyayenmu sai sunyi alfahari dani. Da yardar Allah zan share ma Ba Bakura hawayenshi, in sashi farin ciki da walwala." Alkhairi akaita sanyawa haɗina da Bulama Babba. Daga bisani Mama Gana ta rufe taron da adda'a. Mu yara da iyayenmu mata, duk muka fito. Su kuma su Ba Modu suna wajan ɗan uwan nasu, suna ƙoƙarin kwantar mishi da hankalinshi. Jikina a saɓule na zauna a kujera. Ya Innana ta zauna a kujerar dake fuskantata. Bulama ƙarami yana zaune a kujerar da nake, Wakil yana jogane a hannun kujerar da muke. Fanna, da Fanda suna ƙasa. Kowa jikinshi a mace, duk wanda na kalla, sai in ganshi cikin damuwa. Ya Innana uwa ta gari wacce bata nuna sarewarta tace
"Ina horanki da yima iyayenki biyayya. In har kina son rayuwarki tayi albarka, to kibi iyayenki. Ki riƙe adda'a da tsaiwar dare,ki lizimci karanta Qur'ani mai girma ba dai mutum ba sai dai Allah, ki dinga haɗe saukar Qur'ani duk sati, kinga dai yadda nake yi ai. Karki bari sanadinki a ɓata wannan zumuncin. Kome zai faru dake ki jure, kar ki tunkari kowa da ƙorafi, Bulama Babba ɗan uwanki ne, duk abinda ya miki mara daɗi ki shanye. Ki nutsu ki riƙe gidanki da mijinki. Ga Fanda, duk abinda ya shige miki duhu ki sanar da'ita. Ke kuma Fanda kiji tsoron Allah ki ba ƴar uwarki nagartacciyar shawara. Yahanasu ki nutsu ki zama mai girman daraja a idanun mijinki. Karki gaza wajan yi mishi hidima. Aljanna kika je nemowa, duk wuya ki ɗau jumurin shanyeshi. Ki samama Ba Bakura da Hajja Gana farin ciki. Ki shirya Wakil ya kaiki gidan Yanunu ƙanwata, tai miki gyara, sabida kina buƙatar gyara na musamman. Zata baki wasu surrukan da dabarun zama da miji, da abokiyar zama." Gabaki ɗaya nasihar Ya Innana ta ɗaure ƙashi da jijiyoyin jikina. Dajin muryarta kinsan tana cikin tsananin tashin hankali da damuwa.
Ya Innana, na rungumi zaɓi iyayena, ina fatan ya zame mana alkhairi baki ɗaya. Ƴan uwana gudunmawar da zaku bani shine adda'a, ku yawaita mun sadaka da nufin Allah ya kareni da dukkan wani sharri." Kuka na rushe dashi mai ciwo. Dan har wani ɗaukewa numfashina yake yi. Sai yamma Wakil ya fitar mun da akwatina, ni kuma na shiga cikin gida yima matan gidan sallama, sannan na fito muka tafi
Ya Innana:
Wayarta taja bayan fitar su Yahanasu ta doka kiran ƴar uwarta. Ƙara ɗaya_biyu aka ɗauka.
"Assalamu alaikum Yaya, an wuni lafiya, ya Ƙarfin jikin Yahanasu?" Ajjiyar zuchiya Innana tayi tace.
"Jiki da sauƙi, sai rashin sakewa, da rashin son magana yanzu da take fama dashi. Ga wani babban al'amari daya ɓullo cikin rayuwarta. Bansan ta inda Yahanasu zata iya wannan rayuwar ba. Ba Bakura ne ya haɗata da Bulama na wajanshi, zai musu aure. Shi kanshi Bulaman sai yanda matarshi tace mai fa yake yi, shine za'a aura mishi mace,macen ma Yahanasu, ina cikin damuwa Yanunu, yanzu haka ma Wakil zai kawo miki Yahanasun, suna hanya, amman zasu biya su sauke ƴar uwar tasu a gidanta. Ta zauna a wajanki. In bikin ya gabato, ta dawo cikin gidan, ki yi mata dukkan gyaran da zai farfaɗo mata da darajar gabanta." Yanunu tace.
"Kuma Yaya haka kina ji kina gani za'a bama yaronnan Auren Yahanasu, bakwa tunanin makomar rayuwarta ne, koko me? A cikin zafi da raɗaɗin fyaɗe take fa, yarinyar da take cikin tsananin damuwa shine za'ayi mata auren dole, a wannan halin da take? Yaya asiri fa gaskiya ne, tunda yaci ma'aikin Allah."
"Yanunu nasan asiri gaskiya ne, tunda yaci ma'aiki Arrasul ( S A W) amman bani da ikon yin jayayya da umarnin da Ba Bakura ya yanke. Ko Modu bashi da wannan ikon balle ni. Wallahi ni kaɗai nasan a irin tashin hankalin da nake ciki, dukan yayi mana yawa, shi yasa ma na turo miki ita, in ina ganinta tausayinta zai iya ingizani in bijirema Modu." Sun jima suna tattaunawa, amman mafita dai basu da ita, sun shige damuwa ainun"
Yahanasu.
Tunda muka fito, zazzaɓi ya rufeni mai zafi, zuchiyata sai naji kawai tana raya mun, in kashe kaina kawai in huta. Wata zuchiyar tace, gara in gudu. Wata tace mun in buɗe murfin motar da nake ciki in faɗo ƙasa.
Innalillahiwainnailaihilrajiun innalillahiwainnailaihilrajiun innalillahiwainnailaihilrajiun innalillahiwainnailaihilrajiun itace kalmar da naita jaddadawa a hankali, ina dafe da ƙirjina. Ahankali nake jin ina dawowa dai'dai. Amman har muka iso gidan Yanunu ban dawo haiyacina ba. Muna shiga na zarce ɗakinta, bance dasu komai ba. Su kansu basa son cewa dani komai. Zama nayi a bakin gado, ina tunano fuskar Bulama Babba, da matarshi Kofur Zubaina. o ikon Allah, a ƙirji da cinyar Bulama Babba na gama wasannina, domun ya kasance mai son yara. Daga mazan har matan, babu wanda bai goya ba. Ni kuwa, ina tuno lokacin da ake goya ma Bulama Babba ni, muje kai niƙa. Hawayena na share .
Na rasa darajata, farin ciki ma gashi ina dab da rasashi, wato haka rayuwa take faruwa, dole mutum mai rai, wata rana ya faɗa cikin jarabawar rayuwa, duniya juyi juyi kwaɗo ya faɗa a ruwan zafi, duniya zancen banza, duk wanda ya bari duniya ta ruɗeshi yayi wawa, duniya mai idanu a tsakar ka. Yanunu ce ta shigo hannunta riƙe da plate cike da wani irin farfesun nama.
"Cinye wannan cicciɓin Yahanasu. Ki share hawayenki, da kaina zanje in samu Ba Bakura ɗin, muyi magana, aurennan bazai yiwu ba, ai wanna ma zalunci ne, kuma mahaifinki ya zura idanu ya kasa cewa komai." Dubanta nayi nace.
Dan Allah Yanunu karki je, zan aureshi, nima na amince, babu bawan daya isa ya zaɓarma kanshi rayuwar da yake so, kuma ace ya samu hanyar ba gargada. Ƙila aurena da Bulama Babba shine abunda yake rubuce a allon ƙaddarata. Na rasa ma darajata, na fauwalama Allah komai. Babu wani zafi da raɗaɗin da zanji wanda ya wuce zafin fyaɗen da akayi mun." Ina kaiwa nan sai kuka. Na tashi hankalina sosai. Ni kenan a cikin kuka, da kulle kaina a ɗaki. Yanunu ta rasa yanda zata sani. Ni kaina fatan mutuwa nake yima kaina sosai. A hakan take ta gyarani da magunguna, wasu naci, wasu nasha, wasu kuma na wanka. Ga kullekham ta matan aure, da shu'umar humra da nake shafawa, sabulun wankana ma, ƙamshinshi bana wasa bane. Ni ɗince dai bana cikin hayyacina. Kullum a cikin kai kukana ga Allah nake. Ƴan gidanmu duk wanda ya kawo mun ziyara da kuka yake tafiya. Hakan da na gani ne yasa na daddage na aro nutsuwa na ɗamfara ma kaina, shine na soma ganuwa. Nasiru kuwa bai ƙara ganina ba, bai kuma jin muryata ba,ni banma san yanda aka ƙare da zancenshi ba. Wata ranar juma'a ina zaune a uwar ɗakin Yanunu, na jiyo muryar Hajja Fati ƙawata, suna gaisawa da Yanunu kamar a mafarki.
"Ki shiga tana ciki, sai kika ji abunda ya faru da'ita ko?" Hajja Fati tace.
"Wallahi jiya na shigo gari, ummanmu take labarta mun abunda ya faru, Allah ya kiyaye gaba."
"Uhmm Ameen, ki shiga tana cikin wancan ɗakin" Ni dai ina jiyosu, saiga Hajja Fati ta shigo da gandamemen ciki a jikinta. Ganin cikin ya sani jin sanyi da farin ciki a raina. Dan Shekara biyar da auren Hajja Fati, amman ko ɓatan wata bata taɓa yi ba. Magunguna babu irin wanda bata sha ba na samun ciki, daga na Gargajiyar, harna asibitin. Har aure mijinta ya sake sabida rashin haihuwar nata. Hajja Fati ƙawata ce ta ƙut da ƙut, maƙotanmu ne, kuma tare mukai karatu, tun daga primary har sakandare, Ba Bakura ne ya biya mata kuɗin karatu, kasancewar mahaifinta ya jima da rasuwa.
Hajja Fati kece da safennan haka, sai kace wacce tayi mafarkina? Sai naga abun arziki ashe an samu, shine ko a waya baki bani labari ba" Jikinta a mace ta zauna.
"Yahanasu kece kika rame kikayi duhu haka, kin ganki kuwa yanda kika zama? Ki ɗauki dangana mana Yahanasu, ki yi fatali da abunda ya faru dake, ko dan kwanciyar hankalin Ya Innana. Naga ita kanta tayi rama sosai sai wuya" murmushi nayi mata kawai, sannan nace.
Na riga na dangana, dan da'ace ban dangana ba. Da yanzu na biye ma sharrin zuchiya na halaka kaina. Hajja Fati wannan ramar tana da nasaba da rayuwar dake tunkaroni a gaba, abunda ya faru a baya ya shige ai, mikin dai yana cikin zuchiyata abadan. Ta yaya zan soma rayuwa da Bulama Babba, alhalin sai abinda matarshi tace mishi. Duk da kullum a cikin adda'ar neman dacewa nake, amman kuma zuchiyata a cikin zulumi, da taraddadi take a ko da yaushe Hajja Fati" Ajjiyar zuchiya ta sauke tace.
"Zahiri maganarki abin a duba ne Yahanasu. Auren soyayyarma yaya yake cikawa balle auren dole? Ni kaina abubbuwan da nake fuskatanta a wajan Ahmad ai abun bana wasa bane. Yahanasu tunda Ahmad yayi aure, na zama banza, sharar gidana ta fini daraja a idanunshi. Allah ya dubeni ya soma bani ciki kafin amaryar. Nayi tunanin hakan zai sa Ahmad a farin ciki. Amman wallahi ta cikin amaryarshi yake yi. Kwanakin baya na dawo gida ai nayo yaji. A ranar Umma ta mayar dani. Yahanasu Umma taƙi ta saurareni in faɗa mata halinda nake ciki ma. Sai cewa take yi in riƙe maraicina in dubeta. Ke ga ciki, ga damuwa, hawan jini ya rufar mun, da naga zan mutu ba shiri na soma shan kayan maye. Su kaɗai nake sha in samu nutsuwa a zuchiyata Yahanasu, to in ban sha ba, mutuwa zanyi, takaicin ɗa namiji dubi yanda ya zubar mun da ajina, duk gaye na. Amman yanzu dubeni fa" Da kallon mamaki na bita. Da ace a bakin wani naji labarinnan bazan taɓa gasgatawa ba. Hajja Fati da Ahmad wata soyayya suka gudanar mai ban sha'awa kafin aure. Duk wanda yasan Ahmad, to dole yasan Hajja Fati. Haka itama duk wanda ya santa, ya san Ahmad. Amman yau shine ya juya mata baya, har take shirin halaka kanta sabida shi?
Haba Hajja Fati, me ya kaiki shan kayan maye, adda'a ya dace ki kama, amman ba ki kama abunda zai iya taɓa duniyarki ba. Ya kike ganin randa Umma zata san halin da kike ciki zata ji? Karki bari ki halaka kanki a kan namiji" Dariya tayi mun.
"Bafa zaki gane bane Yahanasu. Sai lokacin da tsananin damuwa ya kamani ne, nake shan abun maye, da zaran nayi bacci na farka, sai kiji zuchiyata sawai da'ita, shi kanshi kaina sai yayi fayau. Kuma raba dare nake yi, ina adda'ar Allah ya bani mafita Yahanasu. Takaicin ɗa namiji, da kishiya yafa wuce tunaninki. Balle ke mai mugun sa abu a ranki, maganar da ba wata magana ba ma, saita hanaki bacci. Harfa Deepretion ne ya kamani lokacin cikina yana wata na huɗu." Dubanta na kuma yi cikin sarewa nace da'ita.
Ki dai kiyaye, kuma ni ina ganin ki koma makaranta ki haɗa digiri ɗinki, ki ɗan samu aiki. Rashin lokaci zai iya rage miki matsala. Amman sai anyi biki zaki koma dai ko?" Dariya tayi.
"Har Kaduna saina kaiki ai Yahanasu." Ganin Hajja Fati yasa na ɗan saki jiki na, sai hira muke yi na yaushe gamo. A wajena ta kwana, sai washe gari Sannan ta koma gida.
Innana:
A ɗakin Bagulaji matan gidan duk suka taru, harda Innana, Mama Gana tana ta tsara yanda al'amarin bikin ƴan matan zai kasance.
"Ni ina ganin ayi jeren yarannan da wuri sabida a huta. Maganar kayan katako kuma, zuwa gobe Ni da Bagulaji zamu je Kasuwa, sai mu zaɓa musu abunda ya dace. Ke kuma Yaguji, ke da Ya kura. Sai ku duba mana kayan kitchen. Ɓangaren Labulaye da su kafet kuma, sai Innana ta ɗauka, tunda ta iya zaɓe, mu samu mu gama komai cikin tsanake, Ba Bakura ya tura mun kuɗin duk abunda za'a buƙata. Cewar Mama Gana kenan. Innana tace.
"Maganar cincin, da su nakiya kuma, nayi ma Umman Hajja Fati magana, tunda dama ita ke yi sana'arta ce. To na faɗa mata gobe Wakil da Bulama ƙarami zasu kawo mata buhun fulawa bakwai, na cincin, da dublan, buhu ɗaya na alkama domun yin alkaki, sai buhun sikari. Sai buhun shinkafar tuwo,da rabin buhun suga, da kayan ƙamshi. na siya an kai gidan Baba Gwamma, maganar nakiya da zata yi. Sabida a samu a kammala komai, kafin gidan ya cika da Baƙi. Abincin biki kuma Hajja gana tace. Tayi ma wata mata, mai yin sana'ar abincin biki. Zata yo abinci kala uku ranar ɗaurin auren, sabida baƙi. Bagulaji tace.
"E nima tayi mun magana, sabida ta bani wasu atampopi da lace tace in ba telana ya ɗinka ma Yahanasu su. Shine da nake karɓan kuɗin dinkin take sanar dani maganar abincin ƴan ɗaurin auren. Allah yasa ayi damu wannan bikin. Ba Bakura yana kashe ma wannan biki kuɗi sosai gaskiya. Kamar ba'a taɓa yin biki ba a gidan haka yake ji. Dariya suka yi dukkansu. Shirye_shirye sosai suke yi, abun babu kama hannun yaro. Ana biki saura sati guda, gabaki ɗaya an gama komai, amaren anje anyi musu jeransu. Mazan kuma, ko wanne ya gyara inda zai ajiye matarshi. Gida ya soma cika da baƙi, ƴan Pataskum ne, ƴan maiduguri ne, ƴan yobe ne, jama'ar Yola ne. Duk kowa ya tawo,duk inda ka gilma yaren kanuri da kamshin humra ke tashi, duk matar da ka gani, zaka ganta saye cikin lafaya, hannu da ƙafarta kuwa yasha ƙunshi baƙi. gidan kuwa yasha fenti sabo. Iyayen amare, da angwayen kuwa ko wacce ɗanta ya gyare mata ɗakinta, anyi musu fenti. Atampa super sukaima iyayen nasu Anko, na ranar ɗaurin auren kenan. Dan akwai walima da zasu gudanar a cikin gidan ranar ɗaurin auren kamar yanda dama suke yi, duk aure. Ga tarin al'adun auren Kanuri da ake gudanarwa, babu ko guda ɗaya da ake bari, sabida al'adune masu dogon tarihi, a cikin yaren Kanuri.
Yahanasu:
Tun biki saura sati guda, Yanunu ta dawo dani gida. Can ɓangaren Ya Bagulaji kishiyar Ya Innana ta kaini, sabida kara. Ƙawayena duk muna can, Yaguji ƙanwata ɗiyar Ya Bagulaji ita kuma ta koma ɗakinmu ita da nata tawagar. Ni dai na dawo kalar tausayi, babu wuya sai kuka, gabaki ɗaya na sare. Ga gidan ya cika dam babu masaka tsinke, duk inda ka ratsa yare ke tashi. Hajja Fati tana tare dani, da ƴan tsirarin ƙawayenmu data gayyata. Haka aka shiga gudanar da al'adun biki iri daban daban....✍🏻
Mrs Bukhari ce.
Ya kuka ji labarin? Yawan comments zai iya sawa zuwa yamma ku sake jina da sabon feji, dan kuji yadda wannan biki zai kaya...
Ina da humrori da turarukan wuta irin da kanuri da sudanawa, siyan na gari mai da kuɗi gida, kayana ingantattune sai kin gwada zaki tabbatar.
_GAWURTATTUN UKU🔥🔥🔥2023
_1-NIHLATUL-KHAIR_
👇🏽
*(Ummu Affan)*
_2-ME IDO A TSAKAR KA duniya_
👇🏽
*Badi'at Mrs bukhari*
_ZULFA_
👇🏽
*Ummu maher(miss green)*
_Littafi ɗaya;400_
_Littafi biyu;800_
_Littafi uku;1000_
Ga masu son tura kuɗinsu ta acc sai su tura a wannan acc ɗin👇🏽👇🏽👇🏽👇🏽
0037219728
Fatima Rabiu Sunusi
StanbicIBTC Bank
Sai ka tura da shaidar biyanka ta wannan no ɗin👇🏽👇🏽👇🏽
08104335144
Masu tura kati kuma sai su turo screenshot na katinsu Mtn ta wannan no ɗin👇🏽
08104335144
*GA MASU SON A TALLATA MUSU HAJARSU A DUKKANIN SHAFINMU na facebook,whattpad,telegram,youtube,group da status,zamu tallata muku ne akan farashi me rahusa
10K ne kacal.
Sai ku tuntuɓe a numbobinmu kamar haka👇🏽👇🏽👇🏽
08104335144
07068606171
08179523215
Domin tallata muku hajojinku a cikin littafinmu na sati ɗaya ya kama👇🏽👇🏽👇🏽
2K
sati biyu
3k
idan kuma kanason har mu gama book muna ɗora maka ya kama
10k kacal.
Mun gode da zaɓar gawurtattu uku ako da yaushe.🙏🏼
[26/07, 2:34 p.m.] +234 806 874 8984: MAI IDO A TSAKAR KA
(DUNIYA)
GAWURTATTU UKU
BADI'AT IBRAHIM MRS BUKHARI B4B
4
*BABBAN ALBISHIR GAREKU MASOYA LITTATTAFAN GAWURTATTU UKU. AKWAI KYAUTA TA MUSAMMAN DA MUKA SAKA DOMUN KU MASOYANMU. WAƊANDA SUKA JAJIRCE WAJAN TAYA MU SHARE ƊIN LITATTAFAN MU DOMUN SOYAYYA. AKWAI KYAUTAR BAN GIRMA DA MUTUM UKU DAGA CIKI ZASU SAMU. BUGU DA ƘARI ZASU SAMU DAMAR KARANTA LITTATAFAN GAWURTATTU UKU NA WANNAN ZANGON KYAUTA. BUGU DA ƘARI MUTANE BIYAR DA SUKA BIYA KUƊIN BOOKS ƊINSU DA ZARAN MUN GAMA FREE PAGE, SUMA SUNA DA KYAUTAR BAN GIRMA DA GAWURTATTU UKU ZASU BASU.