Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
kwairai kumakunsani shahararu goma aduniyan kayan mata m zee ce dakanta 08063845136 ko 07019551505 Kar abaki labari. Sannan maganin sanyi ba Sai kinada infection zakiyi amfani dashi ba Dole ne ga KOWACE mace maganin sanyi ya zama daya daga cikin abinda ba a rasata dashi a gidanta sannan kuma AMARYA MAI JEGO WACCE ZATAYI KOME Dolene kiyi amfani da maganin sanyi kafin ku hadu da miji wannan Dole ne indai kinason kiji dadin muamala da miji. Duk amaryar da aka kaita dakinta batayi amfani da maganin sanyi ba toh tabbas tayi babban kuskure hakama duk Mai jego data haihu har ta Bari tayi arbain suka Hadu da mijinta batasha magani sanyi ba itama ta tapka babban kuskure. Wllhy kaya na aiki kinga ikon Allah Wai😂🔥🔥🔥🔥🔥ance wanda y iya y huta toh wanda y siya ma wllhy yafi kowa hutawa Allah dai y biya. Ku tuntuɓe ni a wannan number domin ƙarin bayani, muna aika kayanmu ƙasa-ƙasa gari-gari. Sayen nagari mai da kuɗi gida. 08063845136 sai kunzo. [26/07, 2:34 p.m.] +234 806 874 8984: MAI IDO A TSAKAR KA ( DUNIYA) GAWURTATTU UKU BADI'AT IBRAHIM MRS BUKHARI (B4B) 5 SANARWA SANARWA SANARWA. ZAKU UMMU MAHEER MISS GREEN SHIRU BATA POSTING ƊIN LITTAFINNAN NATA MAI SUNA ZULFA, WANDA YAKE ƊAYA DAGA CIKIN TAWAGAR GAWURTATTU UKU. AYI MATA AFUWA, WAYARTA CE TA SAMU ƊAN MATSALA, DA ZARAN TA GYARA ZAKU JITA. MUN GODE DA ZAƁAR GAWURTATTU UKU. BULAMA BABBA Yahanasu, da Fanda, da Hajja Fati. Sai ka nuna musu ɗakin naka su kwana a ciki. Mu kuma iyaye, sai a kaimu ɗakin tsintattun mage mu kwana acan. Su Bulama ƙarami sai ka kaisu BQ ɗin su kwana acan. Tunda kai baka lissafi darajarmu ma baka sani ba." Jikina a mace yake da maganganun Mama Gana, nasan dole ta kasance cikin fishi, kuma dama itan mai zafi ce. Iso nayi ma Su Mama Gana ɗakin su Asiya. Su kuma su Yahanasu na kaisu ɗakina, na fito naja su Wakil zuwa BQ. Wai wannan kayan da na gani a mota fa Bulama ƙarami na wanene, daga ma ina kuke naga kamar biki zaku je ko?" Bulama ƙarami nake tambaya. Yace dani. " Ba biki zamu je ba, daga Damaturu kai tsaye nan muka tawo, mu kam gobe da asussuba zamu koma, Mama Gana da Yanunu kaɗai zamu bari anan. Su Baguji sunce a gaisheka. In an kira wayarka Bulama Babba baka ɗagawa sam, haka watan can daya wuce Ba Bakura yaita kiranka baka ɗaga ba, baka kirashi ba kuma. Wai akwai wani laifin da mu kayi maka ne daya sa ka guje mu? Bamu saba da kai a haka ba, tun muna yara kake kula damu, kai ke nan kullum a cikin goyanmu" Hawayene ya gangaro a kumatun Bulama ƙarami, Wakil kuwa idanunshi sun kaɗa sun zama jawur dasu, kamar zasu zubo da ruwa. Kasancewarshi mai taurin zuchiyane yasa kukan bai zubo mishi ba. Jikina yayi sanyi sosai, bani da amsar tambayar ƴan uwana, kuma wallahi ina tunowa dasu duk kwanan duniya, aikine da hidimar Zubaina da ƙannenta yake sha mun kaina. Kuyi haƙuri dan Allah Bulama ƙarami, da wakil, in sha Allah zan dinga kiranku, kuma ku ba su Ba Bakura haƙuri, suci gaba da yi mun adda'a. Dana samu hutu zan zo in sha Allah. Ya su Ba Modu, da Ba Baana, ina Ya Hajja Gana, yaya su yagaji suke, su Fanna? Haka naita jero tambayar ƴan uwana ina tuno da fuskokinsu. Hawaye ya cika idanuna tab. Wakil bari in barku kuyi wanka, sai muje masallaci, magriba ta kawo kai, kafinnan an gama abinci." Da murna na baro ɓangaren saukar baƙi zuwa cikin gidan. Asiya na tarar a falon tana kunna turaren tsinke, Zubaina kuma, fitowarta daga kitchen kenan hannunta ɗauke da ƙaton farantin silver cike da kayan abinci. Da sauri na ƙarɓeta na ajjiye farantin silvern a ƙasan kafet. "Am Dan Allah Bulama taya ni kawo musu ruwa, so nake gudu_gudu inje in yo wanka, in anyi sallah sai in kirasu suci abincin. Suna BQ ɗin dukkansu ko? Asiya ta share duka ɗakuna biyun dake ciki." Murmushi nayi mata. Sannu da aiki Maman Maryam, Allah ya baki lada, kin shiga aikin baƙi ba shiri." Dariya kawai tayi mun, amman da dukkan alamu akwai wani abun da akayi mata wanda ya ɓata mata rai. Ban dai ce komai ba akan wannan. Ai Mama Gana taƙi fur su je BQ, Su Wakil ne kawai suke BQ. Mama Gana suna ɗakin su Asiya. Su kuma yaran matan suna ɗakina. Kiyi haƙuri da sha'anin ƴan uwana, fitina garesu, musamman Mama Gana fitinanniyace ta gaske." Wucewa nayi ɗakinta dan gabatar da alwala, naji ana kiraye kirayen sallar Magriba, a tsaye na bar Zubaina bakinta a wangale." Zubaina: Kusun uwa, kai ya sa ƙannen miji akan gadon mijina, kuma dan kuturun wulaƙanci shi hakan bai dameshi ba? Tabb lallai Bulama yana wasa da ni wallahilƙudrat ba za ta saɓu ba bindiga a ruwa, nasan da wanne kalar ƙulunboton suka zo mun ma Ga uban kaya da suka shigo dashi cikin mota, kona uban meye oho, fuuuu na bi bayan Bulama." Yahanasu: Jikina a mace murus yake, tsoro da fargabar da nake ciki a bayyane yake. Ɗakin Bulama Babba na bi da kallo, lallai wato Bulama Babba haka ya yi kuɗi mu bamu da masaniyar hakan. Tabbb abun mamaki baya ƙarewa a duniya, a rayuwa da mun ɗauka Bulama Babba shi zai maye gurbin iyayen mu bayan ƙasa ta rufe idanuwansu. Sai gashi tun ƙasar bata rufe idanun nasu ba, yasa ƙafa yayi fatali da ƴan uwanshi. Ga matarshi da gani yana tsantsar sonta, dan sai haba_ haba yake yi da'ita. Zubaina kyakykyawar macece, mai duri sosai, farace fes wanke hannu ka taɓa, gata da hanci, gata da idanu masu kyau, ta kere mun gudu sosai ta ko wanne fanni babu wani abu dazan nuna mata, gata da kyan jiki, ba kya ce ita ta haifi yaranta ba. Hmmm na sauke ajjiyar zuchiya, tare da kallon ƙofar ban ɗakin da Hajja Fati ta fito, alwala ta ɗauro. "Yahanasu wai har yanzu uban tunanin kike yi ne? Karfa kije ki jefa rayuwarki a matsala. Haba Fanda ya kamata ki dinga bata baki ai ko?" Fanda ta dubi Hajja Fati tace "Kinsan Allah jikina yafi na Yahanasu macewa, dauriya kawai nake yi. Ke da ganin Bulama Babba da matarshi, kinsan da wuya matarshi ta bari ayi zaman lafiya. Ke kinga yanda zuwanmu ya ruɗa ta kuwa, jikinta da muryarta fa har rawa yake yi, sanda take gaisawa dasu Ya Bagulaji. Kina ganin data miƙe bin bayanta yayi da kallo bai dawo da hankakinshi kanmu ba har sai da ta ƙule. Yahanasu ni abunda zan faɗa miki shine ki yi haƙuri ki karɓi zaren ƙaddara ki saƙa a duk yanda kalar zaren yazo miki, me haƙuri shi ke dafa dutse har yasha romonshi. Ki riƙe adda'a, ki kuma riƙe azumin monday da alhamis kamar yadda kika taso kika samu Ya Innana tana yi. Sauran shawarwarin zamu baki, ki bari muci abinci, muyi wanka yau zamu raba dare ni da Hajja Fati muna miki darasi akan aure, dan kisan asalin girman zamantakewar aure, labari kawai kikeji, ƴan mata basa fahimta, da dama hangen dala ƴan mata suke ma rayuwar aure, musamman ma waɗanda suka auri masu mata, ki tashi kiyo alwala " Miƙewa nayi, bance komai ba, na shiga bayan gidan na ɗauro alwala na fito, Fanda ta shiga. Hajja Fati tana zaune a ƙasan kafet tana waya, da dukkan halamu da mijinta take waya. Tsuru nayi mata da idanu, ina kallon yanda take sharar ƙwalla. "Shikenan Baban Nasiba, tunda dai haka kace, kuma baka son in fadi gaskiya shikenan. Ni bani da kuɗin motar dawowane, shi yasa ma kaga ban dawo ba. Kuma nayi maka magana kace, in iyayena sun gaji da zamana su biya mun in koma ɗakina. Kasan Mama fama suke suma da kansu, nera biyar bana magani. Amman inna koma Damaturun zan nemi kuɗin mota in dawo" Galala ta sauke wayar a kunnenta. Kuka mai sauti ta fashe dashi. Cike da tausayinta nace Kiyi haƙuri Hajja Fati, ai da kin faɗa mun baki da kuɗin mota, dana baki, bai kamata ki dinga sa damuwa a ranki ba haka" "Hmm Yahanasu bazaki gane bane, kar Allah yasa rayuwarki ta ɗanɗani azabar ɗa namiji, ke maza da yawansu ko azzalumai ne. Mugun miji Allah ya haɗa ni dashi, mara tausayi, da tunani. Amman ba komai, bazan bari ciwon zuchiya, da hawan jini su kasheni a banza ba." Tana kaiwa nan, sai naga ta miƙe da sauri ta ɗauki jakar hannunta, ta ɗebo wasu magunguna, fin guda goma ta zuba a bakinta, tabi da ruwa. Tambayarta nake shirin yi, sai Fanda ta fito daga banɗaki. "Kukan wa nake ji ina bayan gida?" Ta tambayemu tana tsatsaremu da idanu. Kukan Hajja Fati ne, ita da Baban Nasiba ne fa" Kai ta kaɗa tace. "Allah ya kyauta, maza duk yanda ka kai da kyautata musu, sai sun gano inda ka gaza, Allah dai ya bama mata haƙuri da juriyar shanye ƙunci da hawan jinin namiji. Mu yi Sallah muje mu samu su Mama Gana, ni yunwa ma duk ta bi ta isheni." Hijabai ko waccenmu ta zura, muka soma sauke farali. Kofur Zubaina: Cikin ɓacin rai da huci na sameshi a cikin ɗaki, fitowarshi daga bayan gida kenan. "Wai Abban Maryam da gaske kake yi, ƙannenka sabida raini a ɗakinka zasu kwana? Bari kaji wallahi baza su kwana a ɗakinka ba, bazai ma yiwu bane. In ba dai da wata manufar suka zo ba, me yasa zasu kwanta a ɗakinka. Kenan ni bani da wani mutunci da ƙima a idanka ma kenan ko, to su Asiya ina zasu kwanta su?" Kukan munafurci na fashe dashi, duk da inajin mugun ɗaci a zuchiyata. Naso danne baƙin cikina na ganin danginshi, amman sai da suka turani har zuwa bango hankalinsu ya kwanta. Tsattsareni da idanu Bulama yayi, yana nazartata. Cikin kissa na isa gareshi na faɗa ƙirjinshi, ina shessheƙa. Sabida Allah fa Bulama, ina laifi dan sun sauka a masaukin baƙi su ƴan matan, ɗaki biyu ne da falo fa acan. Ai bai kyautu ace a ɗakinka zasu kwanta ba. A gadon fa muke kwanciyar aure, kuma kawai sai ƙannenka su kwana a kan gadon? Haba Bulama na. Sannan ni abinda ban gane ba, na gansu da sababbin kayan ɗaki cikin mota, wai daga ina suke, kayan kuma na waye?" Duk wannan maganar da nake yi, cikin karya harshe nake yinta, ko da asiri sai an haɗa da kissa, duk da ina da tabbacin Bulama bazai taɓa ganin aibuna ba, domun a hannu yake ram, bashi da tsumi bashi da dabara sai abunda nace mishi shi yake aikatawa. Hannuna kuwa yaja zuwa bakin gadonmu. A cinyarshi yaimun masauki. Dubana yayi da kyau, harda murmusawa yace. "Iya rigima, yanzu akan wannan matsalar shine harda kuka? To a mayar da wuƙar, ni kaina sanda Mama Gana tace wai su Yahanasu su kwanta ɗakina, naji irin abun bai dace ba. Amman dai na barsu sun shigane a lokacin sabida in kauce faɗan Mama Gana, wallahi duk ta bi ta fitineni. Zasu koma BQ su ɗin, amman Mama Gana in ba so kike ta tara mana jama'a ba, a barsu a ɗakin su Asiyan shikenan kukan ya ƙare? Su Asiya sai su kwanta a nan ɗakin, ke kuma sai ki kwanta a ɗakina" Ɓoyayyar ajjiyar zuchiya na sauke, nayi Murmushi mai cike da kissa tare da shafo gemunshi nace. Shikenan kuwa, ai kasan ina kishin shimfiɗar mijinane, sirrinmu ne fa, ko kusa bai dace ƙannenka su hau kan gadonmu na sunna ba. Sai maganar kayan da suka tawo dashi a mota fa?" Na ƙagauta inji na meye kayan. Su kam bansan na meye ba gaskiya, dana tambaya ma sai Mama Gana tace wai sai da safe naji. Uhm bari muje masallaci da su Bulama ƙarami saina dawo" Miƙewa yayi ya fice. Ƙugu na riƙe tare da bin bayanshi da uban harara. Hmmmmm Bulama kenan. Karen haukane ya cije ni da zan bar ƙannenka su kwana a cikin ɗakinka? Kalan suje su yi mun birne _birne, ko su tono mun nawa binne_binnen da nayi. Tabb lallai ma waɗannan to wai me suke nufi da nine wai?" Tsaki naja mai ƙarfi, na shige bayi, wanka nayo tare da ɗauro alwala na fito. Asiya da Nafisa ne suka shigo rai a dagule. Da kallo nake binsu, ina son jin meke faruwa. "Wallahi Anty kiyi ma dangin mijinki magana fa, ni wallahi zan ci uwar tsohowane babu abunda ya dame ni. Dan na fita zafin kai fa. Sun zo sun cika ma mutane gida da ƙauyanci, sai yare suke ta mana munafukai" da sauri nace. Wai meya haɗaku da su ne Asiya?" "Daga shiga ɗakinmu fa. Muka same su sai faman zaginki suke yi. Shine fa wata shegiyar tsohuwa mai bakin aku ta daka mana tsawa, wai mu fita mu basu waje, an turomu jin gulma. Ke ki ji fa, naji tana cewa wai Abban Maryam ɗin zai shigo ya sameta ne" Kai kawai na shiga jijjigawa, ina ta'ajibi. Baƙin ciki tare da neman tudun dafawane ya hanani magana sam. Zama nayi a bakin gado hannuna riƙe da haɓata. Wato ma zagina da suke yi a Damaturu bai ishesu ba, har sai sun zo gidana sun zageni, sun hanani rawar gaban hantsi ko? Da kyau, zanyi maganinsune ki barni dasu kawai dani suke zancan. Ku zauna bari in yi Sallah. Maganganu cunkushe a zuchiyata nayi Sallah, na sake kayan jikina daga atampa, zuwa doguwar rigar lace, hoda fara kawai na murza a fuskata. Ina zaune a gaban mirror Bulama Babba ya shigo "Kune anan Asiya, yau su Maryam sunyi muku tawaye ko, sun shiga dangi? Dubanshi nake yi, ina karantar yanayinshi, sai wani murna yake yi da ganin ƴan ƙauyen danginshi, cike da kissa nace. Dan Allah ka ɗan shiga ɗakin su Asiya, ka fito musu da akwatinsu zasu je gida?" Da sauri yace. "Sabida me zasu je gida, ba nace su su kwanta anan ba?" E kace. To kayansu suka je ɗauka a ɗakinsu. Shine su Mama Gana sukaita zaginsu, wai ka tara karuwai a gidanka, sun rasa gane wacece ma mai gidan a ciki. Babban abinda banji daɗinshi ba ma shine, Baba da sukaita ƙundumama ashar yana kabarinshi." Na ƙarashe maganar ina hawayen kissa. Shi kuwa take yanayinshi ya sauya, daga farin ciki izuwa baƙin ciki. Idanunshi suka kuma yin ja, dama jajayene idanun nashi. " Kuyi haƙuri, zanyi musu magana. Babu inda zasu je, ina zuwa" Fuu ya fice. Na yi Murmushi kawai na share hawayena, na fita falon nima, dan in kalli bidiri" Bulama Babba: Cikin zafin rai na fita falo. Wakil da Bulama ƙarami na gani a zaune suna kiciniyar buɗe gidauniyar abincin da aka dire musu. Ƙofar ɗakin su Asiya ce tayi ƙara. Su Mama Gana ne suka fito, jin ƙaran ƙofar yasa su Fanda suma suka fito, duk suka shigo falon. Zubaina ma fitowarta kenan. Jikina sai naji yayi mugun sanyi, na zuba ma ƴan uwana abun ƙaunata idanu ina murmushin da bansan sanda ya subce mun ba. "Bulama sa ƴar dokar matarka ta kawo mana babban faranti, yau abincin tare zamu ci, a falonnan. Allah sarki Bakura yana shiga farin ciki, in yaga wani shashi daga cikin iyalanshi sun haɗe waje guda suna cin abinci a akushi guda. Dariyar farin ciki nayi, ko babu komai na shiga farin ciki jin furucin Mama Gana. Zubaina ɗakko mana faranti maza" Zama nayi a kusa da Wakil, ina zama Maryam ta dawo cinyata ta zauna. Zubaina ta kawo farantin Fanda kuma ta juye taliyar a faranti, ta kwarara miyar akai. Gabaki ɗaya muka matso tare da yin bismilla dan soma cin abinci. Salab naji abincin a bakina, abunda ban saba ji game da girkin Zubaina ba kenan, gashi miyar tayi ruwa, bata ko kama taliyar ma. Dubanta nayi, tana zaune ta jawo laptop ɗinta tana aikinta. "Wannan wanne irin girkine haka kamar an wanke kan mahaukaciya, haka kake gasuwa da irin wannan girkin? To ina ma zata iya girki tana aikin police, aikin da a tarbiyya na maza ne aikin, ina matar aure ina kama ɓarawo ko ɗan ta'adda." Da sauri na tari Mama Gana da cewa Kiyi haƙuri Mama Gana kefa uwace, karki zubar da kimarki a gaban yarinyar nan." "Dalla rufa mun baki shanyayyen kawai, wa yake neman daraja a wajan marar daraja irin azzalumar matarka? Ahir ɗinku damu wallahi Bulama. Kuma wallahilƙudrat in baka ce baƙar almurar matarka ta fice mun daga nan ba, saina ci ubanka Bakura" Da sauri na juya, muka haɗa idanu da Zubaina wacce fuskarta ta jiƙe sharab da ruwan hawaye. Laptop ɗinta ta ɗauka tare da wucewa kamar kububuwa. "Haba Mama Gana in hankali ya gushe hankali ake turowa ya nemo shi. Kai kuma Bulama ƙarami kuje ku siyo mana abinda zamu ci yinwa muke ji. Allah ya bamu lafiya, ni dai Bulama bazan sake tako ƙafata da sunan zuwa gidanka ba, ko mai zai faru da kai. Ka zauna da matarka kaita ma danginta hidima." Cewar ya Bagulaji kenan, Yanunu tace. "A haɗu ayi haƙuri dai, mu iyayene, mu kai zuchiyarmu nesa dan Allah, ke Gana kiyi ma Allah ki dena magana. Sannan shi Bulama Babban yaje ya nemo mana abincin da zamu ci, a bar mata abincinta." "Ai wallahi har in bar gidannan bazan sake cin abincin matarshi ba, ya san yanda zai yi damu, shashsha wanda baison mutunci ba. Albasa dai batai halin ruwa ba" Fuu Mama Gana ta shige ɗaki tana gama magana. Su Ya Bagulaji suka mara mata bayanta. Kaina ya ɗauki caji sosai, na dubi ƙannena duk ransu a jagule, Fanda da Yahanasu har hawaye suke zubarwa. Inason ƴan uwana bana son ganinsu a wannan halin. Dan Allah kuyi haƙuri ƙannena, ku dena kuka Zubaina bata kyauta ba, kuma zan yima tubkar hanci. Wakil ku zo muje mu kawo musu abinci, kar yinwa tai musu lahani. Tare muka fita, bamu daɗe ba muka shigo, Kaji gasassu da masa na siyo musu hilimi guda. Muka shigar musu da abun sha. Ni kuma muka wuce masallaci dan gabatar da sallar isha. Yahanasu: Bayan fitarsu Bulama Babba da kyar na dena kuka, sai da su Mama Gana sukaita lallashina. Ni tsorona Allah, tsorona su barni a wannan gidan, tare da makirar matar Bulama Babba. Mama Gana tace. "Dalla ki share hawayennan, tun yanzu so kike su gano logonki, wallahi in kika bari matarshi ta takura miki ke kika so Yahanasu. Kema fa mata ce, kuma bugu da ƙari ƴar uwarshi, kima saki jikinki, kafin in tafi saina tabbatar tsintattun magenan sun bar gidan, dan zasu iya haddasa muku fitina a zamanku." Nan sukai ta bani baki, ana haka su Wakil suka kawo mana abinci. Sai da mu ka yi sallah sannan Hajja Fati ta je kitchen ta ɗakko mana faranti muka baje kaji, da masarnan. Bamu ci ba har sai da su Wakil suka dawo sallah. A ɗaki muka ci, a faranti ɗaya, Bulama Babba sai Murmushi yake yi. Mama Gana wannan zaman saiya tuna mun da gida, lokacin ina ɗan sakandare, mama Gana kin tuno? Ni sai ince sai da su Wakil zanci abinci. Lokacin suna yara dan in ban mance ba, Su Wakil da Bulama ƙarami da Bulama Fari, da su Ahmada, da Dala duk dai yara yaran maza suna firamare, hanci duk majina. A lokacin su Yahanasu, su Fandau suna yara ƙanana, Fanna da Yabulu, da Ba'a kaka duk goyonsu ake yi su kuma a lokacin. Haka za'a zuba mana Buski da miyar kuka, muita ci. In an aikeni kai niƙa sai na goya Fanna ko Yabulu nake zuwa. Kafin a haifesu kuma su Yahanasu nake goyawa. Akwai wata rana da kare ya biyoni ina da goyon Yahanasu a bayana. Naje ɓarjin Masarar buski. Na ɓarar da masarar naita gudu, Yaha na bayana sai kuka take yi. Muka faɗa kwata, har kanta ya fashe, sai da akai mata ɗinki, bazan mance da wannan lokacin ba" Dariya muka saka dukanmu, Wakil yace. "Ni ina tuno lokacin da muke tsaiwa a bakin get muna jiran dawowarka, ka bamu biskit ko abincinka daka rage. Ahmada gashi da shegen kwaɗayi. Kai kuma kana zuwa sai ka tsugunna a gabanmu ka rarraba mana biskit guda guda" Bulama Babba yace. Lokacin sabida ku saida na dena kashe ko sisi a makaranta, biskit ɗin ku nake siya ma. Abincina kuma, rabi nake ci in kawo muku rabin. Abokina Jabir Dauda da mun sha kwanar layinmu, zai ce Bulama Bakura ga mayun ƙannenka can masu nacin tsiya suna jiranka" Dariya dukka aka kuma sakawa. Mama Gana tace. "Ai kaso ƙannenka sosai, mu a lokacin har mamaki kake bamu. A kwai lokacin da aka haifi Yahanasu, to tunda aka haifeta sai aka haifeta da shawara, ko idanu bata iya buɗewa. Ganin hakan sai aka riƙeta a asibitin. A lokacin kana wajena ni kuma nazo Damaturu sabida haihuwar Innana ɗin. Muna shiga da kaga Yaha da ƙarin ruwa a hannunta, sai ka fashe da kuka ka ƙanƙame Modu kana cewa. Ba Modu a cire mata tana jin zafi. A lokacin munyi mamaki sosai bana wasa ba, yanda ka tausaya matan shi ya bamu manaki" Ya Bagulaji tace. "Ai Baluma yayi abubbuwa sosai, tun yana yaro ƙannenshi suke jin maganarshi. Sabida duk abunda aka bashi su yake rabewa shi ya haƙura baki ɗaya ma. Ko wanne yaro ɗan gatan Bulama ne. Kullum a cikin saima su Dala tamaule yake. Kullum kuma in aka fita sai an ɓatar, amman bai taɓa gajiyawa ba" Munyi hira sosai, irin hirar da aka jima ba'ayi irinta ba. Sai kallon Bulama Babba nake yi. Sai nihaɗi da jin daɗi yake yi, tausayinshi ya kamani ainun. Gashi yanzu ya ware kanshi da danginshi, ko kira iyayenshi basa cin albarkacin haihuwa ya kira su, in ma suka kira, sai yayi ra'ayi zai ɗaga. Na ci alwashin da ƙarfin adda'a in Allah ya amince zai dawo da Bulama Babba ainihin Bulaman da kowa ya sani. Iyayenshi sai sun yi alfahari da wannan haɗin da suka yi. Ko banci ribar komai ba a zamana da Bulama. Inason inci ribar dawo da tunaninshi cikin iyaye da dangi, nayi wannan alwashin, ko da hakan zai zame mun ƙarshen numfashina. Zan sa Hajja gana farin ciki, da Ba Bakura. Domin su ɗin mutanene na gidi, kuma su suka tsaya ma rayuwarmu har muka kai matakin da muke kai. Ba Modu ya bamu labarin irin faɗi tashin da Ba Bakura yayi dan ganin ya tallafi rayuwarsu, ya ɗaurata akan turba ta gari. Alhamdulillah ya ɗaurasu bisa tartibiyar tarbiyya, ya basu ilimi, ya aurar dasu, ya basu wajan zama, ya ba ƴaƴansu ilimi. Madallah da babban wa irin Ba Bakura. Sai wajajen ƙarfe sha ɗayan dare Bulama yace zai je ya kwanta, gobe monday yana da zuwa aiki. Tare muka fito harda su Wakil. Muna shiga ɗakin Bulama Babba mu ka ga Zubaina a zaune akan wani teburi tana danna laptop. "Kun gama hirar ne? Cike da fara'a tayi maganar kamar ba ita bace ɗazu ta shige cikin gida fuu da hawaye a fuskarta ba. "Bulama bai faɗa muku zaku kwanta a BQ ba ne? Ai an riga an gyara muku ɗayan ɗakin" Fanda ta riƙo hannuna muka fita. A falon muka tarad da su Wakil, a tsayenma hira suke yi. "Lafiya kuma kuka fito Fanda?" Wakil ke tambayarmu. "Zamu je BQ

Chapter 5 of 11