Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
har gobe hanyar a ratattake take sosai. Amman ko da muka shiga jos kafin mu isa Ƙauyan maza munyi tafiyar fin awa uku. Ƙauye Maza wani ƙauyene daga cikin ƙauyukan jos, yawancin mazauna ƙauyen Maza ba musulmai bane, musulman ƙalilanne. Ada duk musulman ƙauyan sun watse, sakamakon yaƙin ƙabilanci da aka lashe shekaru masu dama ana zabgawa, amman yanzu birnin na Jos Alhamdulillah kowa na zaune lafiya babu taraddadi. A bakin wani shirgegen tsutse mai abun tsoro muka tsaya, jikin dutsen ciyayine sosai, harda manyan bishiyoyi, duk da bana gani sosai, sakamakon hazon daya rufe gari, ga kuma hadari yayi baƙi sosai. Kallon Mabaruka nayi nace. Munzo inda bokan yake kenan ko?" Dariya tayi tace. "Za dai muzo, kinga wannan dutsen sai mun haureshi mun gangareshi, sannan zamu yanki hanyar gidan bokan, an faɗa miki abun na wasane wai? Zagewa zaki yi dan sai mun yi tafiyar data share awa biyu gaba jeji baya jeji." Naji tsoron dutsen sosai, dan dutsene gari guda, amman haka muka soma hawa dutsennan, muna hawa gansa kuka na zamar damu, ni dai jikina in banda rawa babu abunda yake yi. Ita kanta Mabarukan jikin nata rawa yake yi ita ma kenan da ta saba kawo ziyara, sai Allah kawai nake ambata, amman zuchiyata tayi taurin da babu abunda zai sata laushi, face inga na raba Bulama da dukkan masu raɓarshi, ita kuwa Amaryarshi kashinta ya riga ya gama bushewa, dan har hasaso irin azabtar da'ita da zan yi, dan wallahi Mabaruka bata komai, dan ni ba sauƙi a cikin lamarina. Da ƙyar muka gama hayewa tsaunin nan, dan dutsen yafi kama da tsauni, bayana na dafe. Wash Allah Mabaruka wallahi na gaji, bayana kamar zai rabe gida biyu, wai Allah, yanzu ya zamu yi mu gangare dutsennan? "Ki zauna ta zaune miki, garin kallon ruwa kwaɗo yai miki ƙafa, ke duk macen da kika ga ta kafa kanta a gidan mijinta, to sai fa data dage, kuma ko da Asiri sai an haɗa da kissa irin tamu na mata, farkon zuwana wajannan, wallahi dana koma gida saida Adam ya gargasamun jikina, ke dai daure mu gangara cikin likkafa, tafiyace miƙaƙƙiya a gabanmu." Haka mukaita faman gangarawa, tun ina salati a zuchi, har na soma yi da mugun ƙarfi, ban ankaraba, naji tuntuɓe da wani ƙaramin dutse, ai kuwa na gungura. Wayyyyo Allah na mutu na lalace, Mabaruka zan mutu" Cikin ihu gami da kururuwa nake magana, sai wata ƙatuwar bishiyace taimun burki na saki wawuyar tusa ji kuke buuuut, guiwata da hannayena duk sun kukkuje. Mabaruka sai ƙarfafani take yi, a taƙaice mun sha ɗan banzan wahala kafin mu gangare wannan dutsen. Muka yanki jeji, shima yi muke, yi muke kamar ma bama yi, duk tsoro ya gama kamani, sai karo muke da wasu irin tiƙa_tiƙam tuɓaɓɓun arna marasa riga, masu jan idanu, sai ƙanƙame Mabaruka nake yi, su kuma sai sannu suke yi mana da gurɓatacciyar hausarsu, a haka muka iso wata bukka, inda muka tarar da mata su biyar a kan layi, sai wasu manyan maza su uku, da ganinsu masu muƙamine sosai, dan suturarsu da yanayin murjewar fatarsu ta nuna hakan. Matan kuma guda biyun hajiyoyine da ganin yanda suke, sai kuma su biyun irinmu ne, masu fafutukar neman na rufin asiri. "Sannunku bayin Allah, waye ƙarshe dan Allah?" Cewar Mabaruka, dan ni tuni na samu gefe na zauna ina faman haki, wata mata tace. "Nice ƙarshe kinga yanzu na iso, tsoron da nake ji ma, kamar kwana zai iya kamani a cikin jejinnan, to ko yanzu ma ƙarfe biyar na yamma har tayi, yaushe ka gama har ka tafi, duk da daga nan Bauchi nake bani da nisa" Ɗayar hajiyan tace "Aini ban taɓa zuwa nan na tafi a ranar ba ni nafison kwanan ma, sabida amun aiki da kyau ba cikin sauri ba, daga Abuja nake zuwa. Yana da ɗakunan da yasa aka gyara na sauƙar bakin kwana." Ni dai ina zaune sai ajjiyar zuchiya kawai nake, faman saukewa. Mabaruka ta dube ni tace. "Ki kwantar da hankalinki a gindin magalin duk matsalolinki kike, ai ada ba juya Bulama kike yi ba, lallaɓashi kike yi, shi yasa ƴan uwanshi suka yi azarɓaɓin cusa masa ƴar uwarshi. Note ( Mata muji tsoron Allah. Ki sani bin bokaye halakace, bin bokaye babu abinda zai haifar miki face dana sani wanda hausawa suka kirayeta da keya ce. Akwai mallakar ta fisabilillah da mace zata yi ma mijinta, ta hanyar yi mishi biyayya, jawo ƴan uwanshi a jika, yima iyayenshi biyayya da hidima, girmama kanki. Da abubbuwa ire irensu masu yawa, wannan itace mallakar dana sani ta tsakani da Allah. Ki sani bin bokaye shirka. Kuma ki sani in kika mutu kina shirka, a wutar jahannama zaki dauwama ba faɗata bace. Ya ke ƴar uwata an faɗa miki wutar ubangiji wasa ne, ko kuma meye ya shiga kanki da har kika mance da mutuwa, kwanciyar kabari, hisabi? Wallahi wallahi in baki tuba kin dena bin bokaye ba kina ruwa, kuma kin shiga uku, ƙarshenki tun a duniya ba mai kyau bane. Ina kira ga duk macen data ci karo da wannan littafin tayi ƙoƙarin siyen nata kafin in kammala free page dan jin yanda ƙarshen wannan labarin zai kasance, na tabbatar zaki ilimantu, zaki kuma wa'azantu. Ki neme ni ta pc kawai mu sasanta, koma nawa ne da ke. Sannan karfa ku mance labarinnan ya faru a gaske ba ƙirƙirarshi nayi ba.....) MRS BUKHARI CE [26/07, 2:35 p.m.] +234 806 874 8984: MAI IDO A TSAKAR KA (DUNIYA) BADI'AT IBRAHIM MRS BUKHARI (B4B) GAWURTATTU UKU 8 YAHANASU: Mun samu kyakkyawan tarba sosai a gidan Aminin Ba Bakura Alhaji Munka'ilu, tare da matarshi Hajiya Ramlatu. "Allah sarki Mama Gana naji daɗin wannan ziyarar taku sosai, jiya ya kirani muka yi magana shi Bakura ɗin, yake sanar dani abun arzikin da aka haɗa, mun jima ba muyi wayar ba ma. Bulama Babba kuwa, wallahi bai zuwa, na tura yara gidan ma, amman dai basu samu tarba mai kyau ba a hannun ita matar tashi, ita kanta iyalina Hajiya Ramlatu tana dai zuwa amman bata samun sakin fuska. Duk yaran Bulama Babban da'ita akayi sunansu duka. Ni kaina ina zuwa wajan Bulama Babba a Bankinsu ina kai mishi ziyara, Allah ya sanya alkairi, Allah yasa hukuncin da aka yanke ya zama shine mafi alkhairi" Cewar Alhaji Munka'ilu kenan, Mama Gana tace. "Ai wallahi Yaya Munka'ilu in dai Bulama Babba ne bazai zo ba. Yaje gida ma can Damaturu, wallahi matarshi ta shiga ta fita ta hana, sabida Bulama ba haka yake ba, yarone mai ƙawazucin iyaye da ƴan uwanshi, muna fatan wannan haɗin da akayi ya zama shine silar dawo da hankalin shi ga iyayenshi da ƴan uwanshi" Hajiya Ramlatu tace. "Adda'ar daya dace ayi kenan. Ita kuma yarinya ta kula da ibadarta, kar tayi sanya da kai kukanta ga Allah. In sha Allah zamu dinga zuwa dubata, akwai Zainab Auta zan haɗata da'ita zasu yi sa'a da juna. Sannan Alhaji Bakura ya faɗa mana a sama miki aiki, kuma fannin jarida kika karanta. Ta kwana miki gidan sauƙi, dan ina ɗaya daga cikin shuwagabannin gidan talabijin dake kan faifayin tauraron ɗan Adam, ki ba da takaddunki, in sha Allah kin samu aiki, nan da sati biyu in kin gama amarcinki sai ki kirani a waya, saiki soma zuwa aiki in sha Allah " Godiya muka shiga yi sosai da sosai, dama tafi da gidanka mu kayi, takaddun nawa Mama Gana ta ɗebosu dama, karɓa Hajiya Ramlatu tayi, Alh munka'ilu ya dudduba takaddun ya mayar mun da abuna. Sunyi ciye ciye sosai a gidannan, ni dai ina azumi nera dubu goma Alhaji Munka'ilu ya bani, ya ba su Mama Gana dubu sha biyar, Hajiya Ramlatu kuma ta basu dubu biyar, nima ta bani dubu biyar, sannan ta bani lalle na gargajiya, da baƙin salateb me yawan gaske. Sai da muka sallaci Azahar muka yi musu sallama, muka doshi gida. Nan kuma suka shiga gyare gyaren BQ, jere har da su Wakil, sun dage sai kafa gado suke yi. Ni dai ina zaune a falo nayi jigum, ni zazzaɓi ne mai ƙarfi ma a jikin nawa, ga zuchiyar ba daɗi sam. Tunda wannan ƙaddarar ta riskeni, na tsinci kaina a cikin wannan sabon yanayin, wanda bashi da daɗi sam, haka kurum sai inji zuchiyata tana rayamin in raunata kaina, ko in hallaka kaina ma baki ɗaya, gabana yaita dokawa kuma, bana samun nutsuwa har sai nayi karatun Qur'ani, ko kuma in kunna a wayata in saurara, bacci wannan bana samun yi, abubbuwa a lokaci guda duk suka kwaɓemun. Muna zaune da Hajja Fati muna tattaunawa, su Wakil suka fito daga uwar ɗakin da suka kafa mun gado, suka fice a gidan baki ɗaya. Mai gadi ne yayo sallama bakin ƙofa, Hajja Fati tace. "Kamar sallama nake jiyowa, bari in duba" Tashi tayi ta fita, ta bar mun ɗiyarta, a wajena bata jima da fita ba, sai gata da manyan ledoji cike da take away da lemukan sha. Fanda ta shiga ta miƙama, ta barni a zaune ni kaɗai, ina wajan su Wakil suka shigo kici kici da kitchen kabinet wanda ake ajjiyewa a ƙasa kawai, doguwa sosai. Cike da mamaki nake ta kallonsu, mai aikin fanfo dama tun kafin su fita yake ta aikinshi ta bayan windon wajan daining ɗin a wajan daining suka fitarmun da Kitchen mai kyau, an saka mun abun wanke_wanke a wajan an jawo ruwa ta wajan. suka yi jeren kayan kitchen, wajan ya bada tsari mai kyau, aka saka labule mai raga raga wanda bai tare komai ba, an dai sa shine dan ado. Falonma aka gyareshi tsab, sai ƙamshin turaren wuta ɗan asali yake fitarwa. sai magriba suka gama komai, duk muka yi wanka, mu kai Sallah sannan mu ka ci abinci,na kai azumina lafiya. Bamu jira komai ba, muka shige ɗakina, Su Wakil suka shige ɗakin da muka kwana jiya. Ni dai ina kwance hawaye na suntiri a gefen kumatuna, damuwoyin da suka aureni a darennan da yawa suke, yanzu inaji ina gani gobe duk Kowa zai watse ya barni, ni da ko bacci bana iyayi, ya rayuwata zata kasance shine ni kaina ban sani ba, gashi ina gudun yin abunda zai ɓata zumuncin iyayenmu, da kashe kaina zanyi, koma in gudu a nemeni a rasa. Amman in sha Allah duk rintsi duk wuya zan juri zama da Bulama Babba da matarshi, kuma zanyi musu biyayyar da suke nema daga gareni, fatana shine Allah ya dafamun. Bacci daya gagareni saina tashi na ɗauro alwala. Bulama Babba: Bayan gama wayata da Zubaina a cikin kantin sai da sutura na mudassar. Ina sayen takalma da jakunna, sai nayi maza na koma office, dan ma'aikacin banki bashi da lokacin ɓatawa, a ofishina na taradda Ahmad a zaune yayi jigum. Ahmad wannan jigum jigum ɗin da kayi na menene wai? Gashi ni kaina a cikin tsananin damuwa nake, Allah Allah nake yi in zo in same ka dan kaji halin da su Ba Bakura suka jefa ni a ciki. Ni na rasa wanne irin tsana sukaima Zubaina, ni kuma banga abunda Zubaina ta taɓa yi musu ba. Amman wallahi ko Damaturu na kaita, babu mai sake mata fuska, a takure muke cinye hutunmu mu dawo gida. Ajjiyar zuchiya Ahmad ya sauke ya dubeni yace. "Tun dana taso daga Lagos nake cikin tunani da ɗimuwa, Bulama mata masifane, kuma lallai zasu iya saka a cikin ukun da baka isa ka fitar da kan ka ba. In kaga rikicin da mu kai ni da Hajara za kai mamaki, Hajara sabida na bata damar kasuwanci shine take ganin a yanzu data kama ƙasa tafi ƙarfina, dan kawai Allah ya jarabceni da rashin aiki. Kuma fa kar ka mance duk a sanadiyyarta da iyayenta na faɗa cikin bala'in da Allah yasa ka fiddani da ƙyar, wai yau ni Hajara take ɗagama murya." Duban Ahmad nayi, ina jinjina abunda Hajara tayi mishi, mata kenan, yarinyar daya tsinceta a titi da farantin tallan mangoro har itace tayi kilin haka take gasa wanda yai mata komai a rayuwa? Take naji jikina ya mutu mus, dan ni kaina ina cikin kwatankwacin halin da Ahmad ya tsinci kanshi, naci bashin banki nera million biyar ba tare da saninsu ba, gashi har yau ko ragewa ban soma yi ba, ga bashin million biyu ma na kuma karɓa a yau ɗinnan, inason inyi ma Zubaina hidima dashi, dan ta samu raugwamen raɗaɗin da na yi imani da Allah zai dameta. Dukkan wata wahalata akan Zubaina da danginta nake yi, dan iyayena da ƴan uwana basu mori komai daga dukiyata ba,iska na fesar a bakina. Ahmad kayi haƙuri a bisa abunda Hajara tayi maka. Da ba dan kaine ka sanar dani da bakinka canjawar da Hajaran tayi ba, da wallahi bazan yarda ba. Wato sabida taga a yanzu ta fika arziki shine wulaƙanci zai biyo baya, waye ya ɗaurata akan tsanin har ta samu arzikin ba kai ba? Ta bani mamaki amman ka daɗa haƙuri ka kuma bata lokaci, zan kirata in sha Allah, ina to ka baro yaran? "Suna gida yaran tare da ƙanwata, na ɗauki Zulaihat na tafi da'ita Lagos ai tana karatu a hannuna, kusan ita ke kula da yaran ma, Hajara kasuwanci tasa a gaba, da nayi magana sai tace ai ita ke ciyar da gidan, kuma kuɗin makarantar Yara ita ke biyan rabi in biya rabi, wallahi ni gabaki ɗaya auren Hajara ya gama fice mun a raina" Da sauri na tare shi nace" Kai haba ka dena cewa haka Ahmad, ko babu komai Hajara tana taimakonka, tunda ta ɗauke ɗawainiyoyinka da yawa, sannan ko babu komai su Aneesa suna tsakaninku, ka daɗa haƙuri kasan mata hukunane su sai da lallashi. Ni fa aure su Ba Bakura su kai mun, ba da sanina ba sabida tsabar mulkin mallaka. Kuma kasan su rasa wacce zasu aura mun sai Yahanasu ƴar lukuta wannan mummunar yarinyar ƙanwar su Dala fa, ai ka ganeta ko wannan mai ƙibar? Ita fa aka aura mun, babba dani Ahmad, dan ma sauƙin dana samu Zubaina ba tai mun rikici ba, tayi ba zata sosai Gaskiya " Tsuru Ahmad yayi yana kallona, sannan yace. "Bulama bari in faɗa maka wannan gaskiyar dai wacce baka so, wacce take sawa mu rabu tsiya tsiya. Iyaye sun wuci gaban wasa fa, ya kamata ka dawo hayyacinka ka sani matarka bata isa ta kama ƙafar ƴan uwanka ba ma, balle iyayenka. Sannan ka sani suna da damar da zasu aura maka mata uku ba tare da saninka ba. Sabida sanda suka haifeka ai ba sanar da kai su kai ba. Ni a gaskiya lamarin yanda kayi watsi da dangi da iyaye abun ya ɗaure mun kai, domun ban sanka da hakan ba sam, nasan kai mai bala'in son danginka ne. Yarinyar da suka aura maka ƙanwarka ce, gashi ta zama matarka ni dai ina roƙonka ka riƙeta da amana, kar ka ruguza muku zumuncinku mai daɗi da ban sha'awa, ka riƙe ƴar mutane da gaskiya, kaine dai shugaba, ni wallahi sai in ga kamar tsoron Kofur Zubaina kake yi mijin police ko dai kashi take baka ne a ɗaki?" Ya ƙarashe zancen nashi da barƙwanci, Ahmad Abokinane tare muka taso mu kai wasan ƙasa dashi, a bayan layinmu a Damaturu yake, ada shima yana aikine a kamfanin rodi dake garin Kaduna, daga baya kuma sai ya bar wajan, ya koma Lagos da zama, a ƙarƙashin kamfanin shinkafa, daga baya kuma aka kamashi da yi ma kammani ɓarnar dukiya, Kamfani tace bazata yarda ba, shine har firzin. Da taimakon Allah dai na shiga na fita, aka siyar da motarshi da gidanshi na nan Kaduna, aka biya kamfani kuɗinta, shine har ya samu ya fito,amman aiki yaƙi samuwa, sai ƴar buga buga da yake yi a can Lagos ɗin. Matarshi Hajara kuma itama ƴar Damaturunce. Munyi aure da Zubaina da shekara biyu ya Auri Hajara, soyayyar da su kayi bata wuce ta wata shida ba, Ahmad ya aureta, ya kawota garin Kaduna suna zaune a hayin malam Bello, wajan makarantar silver bright. Yaransu Uku Biyu mata, sai Namiji da take goyonshi a yanzu. Harara na zabga mishi nace dashi. Ahmad kenan, ni sai in dinga tantama anya kuwa ka damu da farin cikin rayuwata kuwa? Allah shi ya halicceni ya kuma halicci so, wallahi so ɗaya ne tak kuma Zubaina nake yi ma shi, bazan iya kasa shi kashi biyu ba. Amman bazan iya cutar da Yahanasu ba kaima ka sani, sai dai fa ni bazan iya zaman aure da'ita ba." Nan mu kaita muhawara a tsakanina da Ahmad ko wannne cikinmu ranshi ya ɓaci, yana nuna mun hanya, amman ƙaunar Zubaina da son danginta ya makantar da rayuwata, irin makantar da bana iya tantance fari balle baƙi. A zuchiye Ahmad ya fita ya barni, hankalina sai ya tashi kuma, dan Ahmad masoyine kuma Amini ɗan ƙwarai, na dinga kiran wayarshi ban samu ba sam, Zubaina ma na yi yunƙurin in kirata amman wayarta ban samu ba. Jinjina nayi a jikin kujera ina tuno rayuwar da nayi da iyayena, da ƙannena masu ƙaunata, sai inji babu daɗi inna tuno da cewar na kan share tsawon watanni ba tare da na kira wayarsu na ji lafiyarsu ba. Kuɗina bazan iya tuna yaushe rabon da ya shiga hannunsu ba, in je in gansu abun ya zamemun nauyi. Wunin yau ban yi aikin kirki ba, lokacin tashi nayi na fice a office ɗin na nufi gida, kai tsaye na shige ɗakina, sabida tsabaragen damuwar data fitineni, ko masallaci na kasa zuwa a ɗaki nayi magriba nayi isha, bana fatan abunda zai sa in haɗu da ƴan uwan nawa ma, dan haushin kowa nake ji, kuma gobe ma da sassafe zan bar gidan, sai dai in ba Zubaina saƙo ta basu. Asiya da Nafisa ne suka bani abinci, na karɓi Bakura da Maryam a hannunsu na shinfiɗesu a gadona, nasan tunda naga Zubaina ta kai yanzu bata shigoba, tana da aikin dare kenan, dan case ɗin ɗan luwaɗinnan ya tsaya mata a wuya ainun, shi yasa ma ban kirawo wayarta ba, dan kar in dameta tana bakin aikinta, kuma dama haka muka saba gudanar da rayuwarmu." Zubaina: Har wajajen Magriba ma bamu samu ganin boka ba, ga mata biyu a gabanmu, mazan kuma duk bokan ya gansu tun ɗazu harma sun tafi. Wani saurayine ya fito, yake mana bayani da gurɓatacciyar hausarshi "Baba yace ya tashi aiki. Ku shigo muje in Kai ku wajan Ungo, ta baku masauki zuwa gobe sai ya soma duba ku" Ni dai wallahi duk na gama sarewa, ga tsoron wajan daya cika mun rai na, ko sallar azahar gashi bamu yi ba, ga magriba tayi. Mabaruka tana riƙe dani muka shiga cikin gidan bokan. Gidane ƙaton gaske, anyi ma gidan ginin dutse, suna kiwon aladu, da karnuka da akuyoyi a gidan, ga mata da yara masu yawa a gidan. Saurayinnan ya kaimu wajan Ungo uwar gidan boka. "Ungo baƙin Baba ne na kwana, a basu masauki." Matar Bokannan ta dube mu tace. "Ku biyoni muje" Muna biye da'ita ina ƙara ƙarema gidan kallo, mutanen cikin gidan ma ganinsu nake yi kamar ba mutane ba. Matan da suke gabanmu kuwa naga su babu fargaba sam a tare dasu. Mabaruka kuwa ita kanta tsurewa tayi. Cikin wani ɗaki ta shiga damu, ɗakine mai ɗauke da gadon ƴan boarding mai hawa hawa, guda biyu, ga kafet shinfiɗe malala a ƙasan ɗakin. Matar bokan tana fita na cabki hannun Mabaruka. Mabaruka ni wallahi tsoro nake ji, yanzu kina nufin a gidan bokannan zamu kwana?" Mabaruka tace. "Haba Zubaina to yaya zamu yi? Kinsan dai ba zamu iya shiga cikin surƙuƙin jejinnan ace zamu tafi ba ko? Kiyi haƙuri in dai da matsala kika zo, matsalarki ta kau." Ɗaya daga cikin matan da muka shigo tare tace. "Baiwar Allah banso na shiga cikin maganarku ba. Amman kin ganni nan,. Sau uku ina kwana a ɗakinnan da mata ƴan uwana musulmai, harma da arnan, babu abunda zai faru dake, da dukkan halamu ke sabon shigan zuwa wajan bokace, ashe sai kin yi fitsari zuwa gobe in kika shiga cikin inda bokan yake. Amman dai in duniya kike nema, ki kwanta kiyi barcinki da munshari dan kin sameta a tafin hannunki. Sai dai fa wannan boka aikinshi akwai tsada, yanzu_yanzu sai ya talautaki, amman ni tsabar iya aikinshi ne ma yasa nake zuwa wajanshi. Dan ban taɓa faɗa mai matsala bai magance mun ba" Ajjiyar zuchiya na sauke, na dubi wannan mata nace. To ya kuke yi ku yi sallah a gidan waɗanda ba musulmai ba kuma? Kinga ko azahar ba mui ba" Dariya ta saka mun tace. "Ki nemi waje ki zauna kinji Zubaina. Allah dai ya yafe, gobe in kika koma kya rama sallar a nitse, dan a cikin gidannan baki ba sallah" Rashin sallar ya jijjigani sosai. Amman haka matannan da Mabaruka su ka haɗu su kai ta fahimtar dani, ala tilas nayi haƙuri. A daren ranar nasha labarai daga bakunan matannan, da irin muguntocin da suke ta aikatawa, da kuma nasarorin da suka samu a rayuwa, da burukansu duk da suka cinma. Wannan hira tasu ta ƙaramin kaifin ilmi, dan na koyi darrussa masu tarin yawa a ciki, haka bacci yai awon gaba dani cike da zabarin son ganin gobe. Bulama kuma text nayi mishi cewar aikine ya riƙeni a office, acan zan kwana, amman gobe da safe zan dawo gidan, ya ba su Mama Gana da Amarya haƙuri" WASHE GARI: Tun asubar fari uwar gidan boka ta shigo tace. "Me gida yace wacce zata soma shiga ta je, ku kuma sauran ku koma kan layi" Da sauri nace. Inason zan zagaya makewayi in kama ruwa" Dan da fitsari tab marata na kwana, amman tsoro da muggan mafarkai sun hanani ko da motsawane" Bayan matar boka nabi, tai mun nuni da ɗan wani lungu. A ƙyamace na shiga nayi fitsarin, gashi ba ruwa, ni tsoron tambayar ruwan nayi tun farko. Ɗan kwalin kayana na cire, shi nasa na goge gabana na miƙe da sauri, dan sai naji kamar ana tawowa. A waje na samu Mabaruka, da Kattume a zaune a layi, Mansa itace ta shiga wajan boka. Tafi awa guda kafin ta fito, Kattume ta shiga. "Mansa ki tsaya mana sai mu rage miki hanya, ba kince a Ƙauyan Kamuru kike ba? Ai muma kadunan muka nufa" Cewar Mabaruka. Mansa ta yashe bakinta tace. "Ai kuwa na gode sosai, kunga ma shiga ku ga inda nake zaune ma, mayi zumunci duk da dai na girme muku nesa ba kusa ba. Amman ko babu komai ma dinga bama juna shawarwari. Zama tayi a gefe na, ni dai na ƙosa mu shiga wajan wannan boka. Kattume da yake tace magani da godiya tazo ta yima Boka bata wuce mintuna talatin ba ta fito, Mabaruka tayi mun jagora zuwa cikin bukkar tashi. Muna haɗa idanu cikina ya kaɗa, jikina ya shiga rawa, bokan na ganshi tiƙeƙen gaske sosai, ga idanunshi yayi biyar ɗin na Bulama a ja. Gashi na ganshi ba riga sai zani daya ɗaura, shima zanin iya guiwa, wani irin mugun wari ɗakin yake yi. Ga wasu gumakai masu abun tsoro takota ina a ɗakin ni dai jikina sai rawa yake yi. Uwar gidan boka tace. "Ku samu waje ku zauna, sai kuyi mun bayanin abunda yake tafe daku, in sanar mishi. Take bakina ya shiga kakkarwa, na kasa furta komai. Bokanne naji yayi ma uwar gidanshi yare, yana yi yana zare idanu,

Chapter 8 of 11