Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
da kai , kuma ko hakuri ka ba ni ba zan hakura ba " riko kunnuwansa ya yi , ya yi Kneel down , ya na fadin " I'm sorry my Cutie , please forgive me , ba zan sake ba , ba na jin dadin fushin da ki ke min " " Zan yi hakuri amma da sharadi " ta fada ta na dawo da kallon ta gare shi da sauri ya ce " Eh na yarda ko ma minene " wani dan karamin murmushi ta yi kafin ta nuna mishi gefenta da hannu a hankali ya mike ya zauna geffenta hannu ta kai saman face din sa , ta dago kai ta manna mishi kiss a forehead ta na fadin " ka sani ba ka da kirki ko ? ka san yadda Daddynka ya yi kewar ka kuwa ? kullum sai ya kira lambarka ya na sa ran za ka dauka , amma shi ne za ka gudu ka bar mu " " I'm sorry Cutie , i promise ko zan sake tafiya ba zan wuce one week zan dawo " " you promise ? " ta tambaye shi ta na murmushi gyada mata kai ya yi a hankali ba tare da ya ce komai ba kara fadada murmushinta ta yi kafin ta matso a hankali ta rungume shi ta na fadin " na yi kewar ka sosai my baby " " ni ma haka Cutie " ya fada ya na kontar da kansa saman shoulder din ta su dai MALIKAT INAS da sauran sun zuba musu ido gwanin burgewa โคโš˜ ๐๐€๐˜๐„๐‹โš˜โค ________________ แด›สœแด‡ ส€แด‡แด›แดœส€ษด แดา“ แด‡xษชสŸแด‡แด… แด˜ส€ษชษดแด„แด‡ THE BIGINING ๐Ÿ•Š๐Ÿ‘‘โค TAP THIS LINK TO JOIN MY COMMENT SECTION https://chat.whatsapp.com/JTfho9QngpG5Ax4LM4d4sK _______________________________________________ _ PAID BOOK N500 [ FREE PAGE ___ 9 ๐Ÿ•Š๐Ÿ‘‘โค ] sai da su ka dauki lokaci a haka kafin su raba jiki , Inaya ta ce mishi " tashi ka tafi wajen Daddynka , ya na part din Uncle " yamutse fuska ya yi ya na fadin " no Cutie , gaskiya a gajiye na ke zan so na tafi na yi wanka na huta " " ka na so kara wa kanka laifi , amma ba ruwana tashi ka je " ta fada mishi ba musu ya mike ya fara takawa zai fita da sauri RIANNA ta ce mishi " yanzu kenan Prince ba za ka rungume ni ba ? " ko sannu bai ce mata ba ya sa kafa ya fice parlourn sai da ya fita sannan Inaya ta ce mata " sorry Aunty RIANNA , kin san halin yaronki da mugun kishi , may be dan ya ga Faaz ne a jikinki ne ya sa ya miki fuska " kallon Faaz RIANNA ta yi ta na cewa " yanzu ka yi min adalci , ka hana ni tarbar babyna ? " cike da shagwaba ya ce mata " momy kenan ni ba babynki ba ne ? " ya fada kamar zai yi kuka wani dan karamin murmushi ta yi kafin ta ce " no , kai ma babyna ne , just na jima ban gan shi ba , na yi kewar sa sosai , amma ka ga saboda kai ya min fushi ko kula ni bai yi ba " " yi hakuri momy , bari na je na ba shi hakuri " ya fada ya na raba jikinsa da na RIANNA ya tashi da gudu ya fito part din ba ta yi kokarin tsayar da shi ba sai ma murmushin da ta ke yi sai da ya fita sannan Nesrine ta mike ta na fadin " Ammie zan koma part di na " gyada mata kai MALIKAT INAS ta yi ta na fadin " shikenan , ki kula da mijinki , sannan ki tabbatar ya sha maganinsa " wata yar karamar dariya Nesrine ta yi ta na cewa " Ammie wlh ina fama dan kamar karamin yaro ya ke , magani ma sai na matsa mishi ya sha " " sai kin hada da hakuri " MALIKAT INAS ta fada a sanyaye murmushi kawai Nesrine ta yi mata ta fara takawa ta nufi kofar fita har ta karaso bakin kofar Faaz ya shigo da gudu ya na kuka ya dafe kumatunsa na dama da hannu kai tsaye RIANNA ya nufa ya fada jikinta cikin rudu RIANNA ta shiga tambayar shi lafiya ya na kuka cikin kukan nashi ya ce mata " momy , Uncle ne , na je na tambaye in zai zama abokina kawai , kawai sai ya mare ni , momy uncle ba shi da kirki , he is wicked " rungume shi RIANNA ta yi ta ma rasa abun da za ta dan ta rarrashe shi ba ita kadai ba har MALIKAT INAS da Inaya musaman Inaya , ta san halin yaronta ya na da zuciya kuma ba ya son takura amma abu me wuya ne ya ce zai daga hannu ya bugi mutum , bare ma dan karamin yaro kamar Faaz , gaskiya zuciyarta ta kassa yarda da Prince ya mare shi a hankali ta mike tsaye ta na fadin " Ammie ina zuwa " da sauri MALIKAT INAS ta ce mata " no , koma zauna kyale shi zai dawo ya same ni " " No Ammie ba wajen sa zan je ba , yanzu ina zuwa " ta fada ta na nufar kofar fita ta fice ta bar RIANNA da MALIKAT INAS su ka shiga rarrashin Faaz โ–ชPRINCE ๐Ÿ‘‘ bayan ya baro part din MALIKAT INAS kai tsaye part din Malik ya nufa dan dama cen a ka kai kayansa ko da ya isa a floor na uku ya wuce ya shiga bedroom din sa , ya sa hannu ya fara rage kayan jikinsa , sai da ya rage da ga shi sai short sannan ya nufi toilet sai da ya yi wajen one hour a ciki kafin ya fito daure da towel a kugunshi , ya karaso wajen dressing mirror daukar lotion din sa ya yi ya fara shafawa , bayan ya gama ya shiga dressing room jim kadan ya fito sanye da kayan barcinsa white color ya saki wannan lalawsan gashin kansa irin na Malik , kai tsaye gadon ya nufa ya Haye ya konta rub da ciki kafafunsa ko ida Hayewa gadon ba su yi ba , a haka har barci ya yi gaba da shi โ–ชINAYA ๐Ÿ•Š bayan ta baro part din MALIKAT INAS kai tsaye part din Diya ta nufa dan ta san Malik na cen a wannan lokacin ta ko yi sa'a , su na zaune a harabar part din , har da Abdoul wani cool murmushi ta saki kafin ta karaso wajen ta na yi musu sallama a tare duk su ka amsa mata , har Abdoul ya bude baki zai yi magana wata kyakyawar budurwa ta fito da ga cikin parlourn Diya ta na sanye da wata gown pink color babu ko veil a kanta , ta saki wani golden hair din ta mai mugun laushi kai da ga gani ka san a na kashe mishi kudi ta na kama tak tak da Junior da Diya , a shekaru za ta kai 18 years haka , fara kal da ita jinin larabawa kamar ka taba jini ya fito , Azmat kenan , autar Malik Diya karasowa ta yi wajen babu ko sallama ta ce " Daddy , ka cewa Big bro ya ba ni bank card di ta , shopping na ke " dafe forehead Diya ya yi ya na fadin " Ya Salam , wai da wane zan ji ?rigimar Junior ko taki ? tafi bedroom di na ki dauki tawa bar shi wannan " daga kafa ta yi ta buga a kassa ta na fadin " No ! ni tawa na ke so , ka ce mishi ya ban abuna tun da ba shi ya ban ita ba " ta fada cike da shagwaba a hankali Inaya ta matso in da ta ke tsaye ta daura hannu saman kanta ta na fadin " Azmat , har yanzu ke ma ba ki daina wannan rigimar ba ? shikenan mu je na karbo miki " " yawwa momy mu je ki ja mishi wadanan manyan kunnuwa nashi " ta fada ta na jan hannun Inaya su ka koma parlourn tare sai da su ka bar wajen sannan Abdoul ya ce wa Diya " Diya ina ga ya kamata ka yi wa babynka aure yanzu " " ko na ce na yi mata ita da momynta ba za su yarda ba , sai da na yi mata maganar amma ta ce wai mu bari har ta kammala karatunta " haka dai su ka ci gaba da hirarsu har zuwa lokacin da su ka fara jin kiran sallat Malik da Abdoul su ka tashi su ka nufi part din su dama Inaya ta jima da tafiya Malik Kuwa a floor na uku ya tsaya ya nufi corridor ya shiga har ya wuce kofar bedroom din Prince ya tsaya ya juyo a hankali dan ya ga haske na fitowa a hankali ya shiga bedroom din ya na sallama kassa kassa nan ya ga Prince konce rub da ciki sai sharar barci ya ke gaskiya ba karamin sanyi ba ya ji cikin zuciyarsa ganin yaronsa har wani cool murmushi ya saki kafin ya tako a hankali ya zauna bakin gadon ya kai hannu saman kansa wani dogon nunfashi Prince ya ja ya na mika sannan ya ware idanunsa slowly , sai saman Malik ko su ka sauka " sannu agogo Sarkin aiki , sai yanzu a ka samu lokacin hutawa ? " Malik ya fada cikin sigar zolaya a hankali Prince ya matso ya kontar da kansa saman laps din Malik ya na fadin " Daddy , tun yaushe ka ke nan ? " " yanzu na shigo , tashi ka yi wanka mu tafi Mosque lokacin sallat ya yi " " uhm " ya fada a sanyaye kafin ya sauke kansa da ga kan laps din Malik ya sauko da kafafunsa kassa ya mike tsaye sai tangal tangal Ya ke kamar zai fadi mikewa tsaye Malik ya yi ya riko hannunsa ya na fadin " what happened ? " " nothing Daddy " ya fada ya na kai hannu saman ido ya na murza wa wani dan karamin murmushi Malik ya saki kafin ya fara jan hannunsa ya nufi toilet da shi kamar wani karamin yaro sai da su ka iso bakin kofar sannan ya saki hannunsa ya ce " shiga ka yi wanka ina zuwa " ya kai karshen ya na juyawa zai bar wajen da sauri Prince ya ce " Daddy ? " cak Malik ya tsaya ya juyo a hankali ya na daga mishi gera alamun minene kawai rungume shi Prince ya yi ya na fadin " na yi kewar ka sosai Daddyna " rungume shi tsam Malik ya yi ya na sumbatar kumatunsa , sai da su ka dan dauki lokaci a haka kafin Prince ya raba jikinsa da na Malik kawai ya juya ya shiga toilet ba tare da ya ce mishi komai ba haka shi ma Malik juyawa ya yi ya fice ya shiga bedroom din sa ya na shiga nan ma ya tardo Cutien sa , konce saman gado sai barci ta ke , bai yi kokarin tashe ta ba kawai ya shiga toilet โ–ชMASARAUTAR YEMEN ๐Ÿ‘‘ โ–ชAL-SAYID ๐Ÿ‘‘ zaune su ke cikin parlournsa tare da familynsa, Sayida Ahlame da Sayida Fadwah su na zaune saman sofa guda Aleesherh da Aleenah kuma su na zaune a kassa saman carpet sun sunkuyar da kai cikin nitsuwa Al-Sayid ya ce " abun da ya sa na kira ku nan , a kan maganar auren ku ne da na bawa Malik din Saudiya , kuma ya karba hannu bibiyu ya kuma ce in sha Allah gobe yaronsa za su zo nan masarautar in ya so Next week a yi auren , mai dakin Gabas da ke da mai dakin yamma zan so ku shirya tarbar su , a gyara musu part gudu cikin bangare na , sannan kuma yaranku ku shirya su sannan ku koya musu yadda za su tarbi mazajensu , zan so a yi auren bi sa tsarin al'adun mu na Yemen , dan haka ku fara shirye shiryen " a Sayida Ahlame da Sayida Fadwah su ka amsa mishi da cewa " in sha Allah ranka shi dade " su na gama fadar haka su ka jiyo Muryar Aleesherh ta na fadin " zan iya tafiya ? " ta fada kai a sunkuye " ban ida da ke ba , Aleenah ke dama kin ce ba ki da matsala da auren da haka za ki iya tafiya " fadin Al-Sayid ba musu ta tashi ta fice parlourn dan ita ma ta gaji da zaman nan sai da ta fita sannan Al-Sayid ya ce wa Aleesherh " ina boyfriend din da ki ka ce ku na soyayya da shi ? " ba ta ji tsoron komai ba ta ce " babu shi , dama karya na yi maka saboda ba na son auren nan , amma yanzu na amince a yi auren " murmushi mai dan sauti Al-Sayid ya yi kafin ya ce " Allah ya shirye ki , tashi ki tafi to " ba musu ta tashi ta bi bayan Aleenah su ka koma part din su sai da su ka bar wajen sannan Sayida Ahlame ta mike ta na fadin " ranka shi dade zan je na yi wa ma su kula da kitchen magana a kan abun da za a shirya musu gobe " gyada mata kai kawai ya yi kafin ba tare da ya ce komai ba , ita kuma ta sa kafa ta fit sai da ya fita sannan ya kalli Sayida Fadwah ya ce " Gimbiyata , me kuma ya faru ? na ga kwana biyu duk kin sauya " kamar dama jira ta ke ya tabo ta kawai ta buda mishi wuta ta na fadin " to me ka ke so na yi ? na sani ba ni na haifi Aleesherh da Aleenah ba , amma ko ba komai ni Mahaifiyarsu ce , ina da hakki a kan su , ta ya za ka yanke irin wannan shawarar ba tare da ka sanar da ni ba ? ka na son nunawa Jama'a ni ban da hakki a kan su ne kenan ? tun yaushe na ke yi maka magana a kan Abdoul-Jalil ya ce ya na son auren Aleesherh , amma ka rufe ido ka ce a'a kawai dan ya na yaron babban yayana kuma ba a Yemen ya ke zaune ba , yanzu kawai ka tashi wani wanda ba mu san shi ba , ba mu san halayansa ba ko sunansa ma su sani ba ka bashi auren yaran nan , ka yi min adalci kenan ? " shi dai ya yi zaune ya zuba mata ido ya na murmushi sai zuba ta ke , cike da bacin rai sai da ta gama maganarta sannan ya ce " tun da kin fadi abun da ke cikin zuciyarki yanzu sai ki tashi ki je ki sa a shirya musu wajen da za su sauka " ya fada cikin tsare gida cike da izza alamun ba wassa sai da ta ja tsaki sannan ta tashi ta fice parlourn ta koma part din ta โ–ชALEESHERH ๐Ÿ‘‘๐Ÿ’ž bayan ta baro parlourn Al-Sayid kai tsaye part din su ta koma ko da ta koma ta tardo Aleenah tsaye saman gadon sai tsalle ta ke kamar wata karamar yarinya gashinta na tashi sama ba ta bi ta kanta ba ta zauna a nan saman sofa ta fiddo wayarta ta fara latsawa ta na zama Sayida Ahlame ta shigo ta na sallama da sauri ta ce wa Aleenah " ke madam sauko kar ki ji ciwo " ko sauraron ta Aleenah ba ta yi ba ta ci gaba da tsallen ta na dariya murmushi mai dan sauti ta yi kafin ta karaso ta zauna gefen Aleesherh ta na fadin " Alee , lafiya na ga kin sauya haka ? me ke damun ki ? " " ba komai " ta fada a takaice cen kassa kassa. hannu Sayida Ahlame ta kai ta kwace wayarta ta na fadin " fadin gaskiya , me ke damun ki ? " sai da ta ja tsaki ta na fadin " momy Allah ba na son auren nan , amma....... " " ba fa ke kadai za a yi wa auren nan ba , har da Aleenah amma duba hankalinta a konce ya ke " " to ai momy Aleen ki ka ce ba ni ba , why Daddy zai yanke irin wannan hukuncin , na sani ba na jin maganarsa har na koyawa Aleen amma yi min aure ba ita Ce solution din ba , at least ku bari na kammala karatuna " murmushi mai dan sauti Sayida Ahlame ta yi kafin ta ce " ba fa karamin mutum ne ba za ki aura , magajin kujerar mulkin kassar Saudiya baki daya za ki aura , ki yi tunani wane matsayi ne za ki samu , matsayin MALIKAT fa , in har Allah ya ba ku baby boy kin zama MALIKAT AL'UMU , babu wanda zai ba ki umarni bayan mijinki ko shi in ki ka mallake zuciyarsa sai kin dinga ba shi Umarni , ki tsaya ki yi tunani mai kyau, kin fi son ki auri wani dan kasuwa da it's not sure ya ba ki irin rayuwar da mahaifinku ya ba ki , kar ki bari zuciya ta debe ki ki yi babbar assara " shiru Aleesherh ta yi na dan lokaci kamar mai tunanin wani abu kamar da ga sama ta jiyo Muryar Aleenah ta na fadin " momy ba auren ne ba ta so , akwai wanda ta hadu da shi kuma ta kamu da son sa , amma ba ta san in da ya ke ba " a dubu dari Aleesherh ta juya ta wurga mata wani mugun kallo ta na shirin magana Sayida Ahlame ta ce " What ? Aleesherh maganar me ta ke ? " " gaskiya ne momy , akwai wani wanda na gani kuma na kamu da son shi , lokacin da Daddy ya tado min maganar nan na yi kokarin yi mishi magana a kan abun da ke cikin zuciyata amma bai saurare ni ba , yau da safe na sake komawa wajen sa amma na tarda ba ya nan ya bar kassar , shi ya sa ma na hakura na karbi maganar auren " " Alee , na san irin abun da ki ke ji cikin zuciyarki ba zan yi miki karya ba , ko ni a lokacin da na ke da shekarun ki akwai wanda na ke soyayya da shi , amma lokaci guda iyayena su ka ce za su aura min mahaifinku , da farko har kokarin kashe kaina na yi dan ba na son sa , amma bayan an aura auren Allah ya ba ni ku na ji ba wanda na ke so a duniyar nan sama da shi , ni wlh na ma manta sunan wanda na ke soyayya da shi da farko , may be ya na raye ko a mace Allah kadai ya sani " " yanzu momy kun yarda na shiga gidan wani bayan kuma akwai wanda na ke so ? ki na ganin na yi mishi adalci ? ni ko ban samu wanda na ke so ba please a janye maganar in sha Allah zan fitar da mijin aure da kaina " ta fada ta na marairaice fuska kamar za ta yi kuka hannu Sayida Ahlame ta kai saman kumatunta ta shafa cike da shauki ta ce " ki yi hakuri tun da har an saka rana nan da one week , kuma yanzu in mahaifinku ya ce wa Malik ya janye maganar wane irin kallo ki ke son ya yi mishi ? ba ki san yadda Ikon Allah ya ke ba , a ka je shi wanda za a aura miki ki kamu da son shi da kallo guda kawai har ki manta wancen " wani dan karamin murmushi ta saki ta na kauda kai murya kassa kassa ta ce " hmmm har na fara ganin sa dai " sarai Sayida Ahlame ta ji abun da ta ce amma ba ta tanka mata ba , ta juya ta kalli saitin kofar shigowa part din ta ce " za ki iya shigowa " ta fada da dan karfi ta na gama fadar haka wata budurwa ta shigo wajen da ba za ta wuce 30 years ba rike da wani tray da wani dan karamin bowl a sama ta karaso wajen su ta ajiye bowl din saman table kanta na sunkuye sannan ta juya ta fice sai da ta fita sannan Sayida Ahlame ta kai hannu ta dauki bowl din cikin rudu Aleesherh ta ce mata " minene wannan momy ? " " scrub ne , zai gyara miki skin ta kara haske na dukka jiki ne , ki fara shi tun yanzu kafin Ammienku ta zo , in Aleenah ta farka sai ta yi ita ma " ta fada dan fa Aleenah barci ya riga da ya sace ta gyada mata kai kawai Aleesherh ta yi tare da fadin " sai na cire kayana ? " gyada mata kai Sayida Ahlame ta yi kafin ta kai hannu cikin scrub din mikewa tsaye Aleesherh ta yi , ta zuge zip din rigarta ta yi kassa da ita ta fidda ta bar underwear kadai ko kunyar Sayida Ahlame ba ta ji ba , sannan ta daure gashin kanta a baya ta koma ta zauna ta na zama Sayida Ahlame ta debo scrub din ta shafa mata a face , ta murza da kyau sannan ya shafa mata a saman hannayanta duk ta bi jikinta ta shafa mata har saman wuya da cinyoyi bayan ta gama shafa mata ta tashi ta shiga toilet ta wanke hannayanta ta kuma tara mata ruwan wanka da perfume da suaran su ta fito ta ce mata nan da 30 minutes sai ta shiga ta yi wanka โคโš˜ ๐๐€๐˜๐„๐‹โš˜โค ________________ แด›สœแด‡ ส€แด‡แด›แดœส€ษด แดา“ แด‡xษชสŸแด‡แด… แด˜ส€ษชษดแด„แด‡ THE BIGINING ๐Ÿ•Š๐Ÿ‘‘โค ๐Ÿ•Š๐Ÿ’ž ( ๐™ฐ ๐™ท๐™ด๐™ฐ๐š๐šƒ ๐šƒ๐™พ๐š„๐™ฒ๐™ท๐™ธ๐™ฝ๐™ถ ๐™ป๐™พ๐š…๐™ด ๐š‚๐šƒ๐™พ๐š๐šˆ , ๐š๐™พ๐™ผ๐™ฐ๐™ฝ๐šƒ๐™ธ๐™ฒ , ๐™ธ๐™ฝ๐™น๐š„๐š‚๐šƒ๐™ธ๐™ฒ๐™ด & ๐™ณ๐™ด๐š‚๐šƒ๐™ธ๐™ฝ๐šˆ) ๐Ÿ’ž๐Ÿ•Š โค๐Ÿ‘‘ ๐‘ด๐‘จ๐‘ณ๐‘ณ๐‘จ๐‘ฒ๐‘ฐ๐‘ต.๐‘จ๐‘ด๐‘ฌ๐‘ฌ๐‘น๐‘จ๐‘ฏ ๐‘จ๐‘ฉ๐‘ซ๐‘ถ๐‘ผ๐‘ณ๐‘จ๐’€๐‘ฐ๐Ÿ‘‘โค ( ๐‘จ.๐‘ฒ.๐‘จ ๐‘ด๐‘ฌ๐‘ฌ๐‘น๐‘จ๐‘ฏ ) โค๐Ÿ•Š TAP THIS LINK TO JOIN MY COMMENT SECTION https://chat.whatsapp.com/JTfho9QngpG5Ax4LM4d4sK _______________________________________________ โ–ช๏ธŽPAID BOOK N500 [ FREE PAGE ___ 10 ๐Ÿ•Š๐Ÿ‘‘โค ] da to kawai Aleesherh ta amsa mata , da ga haka Sayida Ahlame ta sa kafa ta fice part din ta na fita Aleesherh ta mike ta shiga toilet ta zauna bakin bath din ta na kuka kassa kassa ita dai Aleenah ba ta ma san duniyar da ke faruwa ba sai barcinta ta ke cikin konciyar hankali har da wani dan karamin murmushi a face din ta bari na koma Saudiya kafin su kammala to โ–ชMASARAUTAR SAUDIYA ๐Ÿ‘‘๐Ÿ”ฅ โ–ชMALIK ๐Ÿ”ฅ zaune ya ke cikin parlourn part din sa a floor na uku , Prince da Junior su na zaune su ma kowane ya na rike da wayarsa sai saman latsawa ya ke cikin nitsuwa Malik ya fara magana ya na fadin " Prince , ina fatan Junior ya fada maka sakon da ya iso mana da ga Daular Yemen ? " ya fadi hakan dan a lokacin da letter din ta iso gare shi Junior ya na wajen nan take yanayin face din Prince ta ida sauyawa duk da ba wani murmushi ne a kai ba , kamar zai yi kuka ya ce " Daddy i'm sorry in hukuncin tafiyar da na yi ne ka yi hakuri ba zan sake tafiya ba , amma gaskiya ban shirya yin aure ba " " okay , ka ba ni hujja uku da za ta hana ka yin aure a yanzu , in har sun

Chapter 8 of 23