tambayar lafiya dai'dai lokacin da idanunta su ka sauka saman Prince da ke tsaye ya tsare su da ido
nan take ita ma ta sha jinin jikinta ta na muzurai da idanu
a hankali ya nade hannayansa a kirji , ya matse gera ya ce " wacece cikin ku ta shigo min bedroom a hotel ? "
shiru su ka yi ba su ce mishi komai ba sai muzurai su ke da idanu
" ba za ku ba ni amsa ba ? " ya fada ya na matse gera
da sauri ta farkon ta nuna kanta ta na fadin " ni ce , don Allah kar ka fadawa Daddy " ta fada ta na marairaice murya
wani dan karamin tsaki Aleesherh ta yi ta na fadin " ke don Allah yi wa mutane shiru , ba abun da zai yi , wuce mu tafi " ta fada ta na riko hannunta
da sauri ta ce mishi " ka yi hakuri don Allah "
" Aleenah , ki daina ba shi hakuri ba abun da zai yi , wuce mu tafi " Aleesherh ta fada ta na jan Aleenah su ka raba ta gefensa su ka bar wajen
ita dai Aleenah sai marairaice fuska ta ke ta na tsoron ya fadawa Al-Sayid ta shiga mishi bedroom , har a hotel ma , ta san shikenan ta su ta kare ba zai kyale su ba
ita kuwa Aleesherh ko a jikinta ko hakuri ba ta ba shi , ta san barazana ce kawai ya ke musu dan ya ba su tsoro
ko sannu Prince bai ce musu ba ya ci gaba da tafiyarsa , har ya karaso parking space din masarautar , ya shiga motarsa ya fice masarautar, kai tsaye hotel din da ya sauka ya koma ,
ya na isowa bedroom din sa ya ga P.A din sa tsaye cikin bodyguards din sa
ko sannu bai ce mishi ba ya shiga bedroom din sa
bin bayansa P.A din ya yi , ya shigo ya na sallama kafin ya ce " Good morning sir "
" me ya kawo ka ? " Prince ya fada a takaice ya na cire sneakers din kafafunsa
cikin nitsuwa P.A din ya fara fadin " Sir maganar meeting din nan ne "
cikin nitsuwa ya katse shi da cewa " ku soke ta kawai har na samu dama , next week zan koma Saudiya , in na je cen zan san abun yi "
" amma sir tun last week mu ka shirya zaman nan ya za a soke shi lokaci guda haka ? "
dago kai Prince ya yi a hankali ya zuba mishi wadanan hazel eyes din nashi irin na Malik
ya dan dauki lokaci kafin ya ce " ku soke ta kawai na ce , ba shawara na ke ba ka ba , now get out please ina son na huta "
" okay sir , ku na bukatar wani abu na sa a kawo muku ? "
" fruits " ya fada a takaice kafin ya mike ya nufi toilet ya shiga
ya na shiga P.A din nashi ya fito bedroom din
ten minutes bayan fitar sa wani server ya shiga rike da tray din fruits, kai tsaye ya nufi table din gaban gadon ya ajiye kafin ya juya ya fice
after SOME minutes Prince ya fito da ga cikin toilet din sanye da bathrobe kai tsaye ya wuce wardrobe
jim kadan ya fito sanye da wani trouser three cuter da t-shirt , ya saki wannan smooth hair din nasa ya haye gadon kai tsaye ya yi rub da ciki , ba jimawa barci ya yi gaba da shi dan a gajiye ya ke sosai
DAULAR YEMEN ๐
ALEESHERH โค๐ฅ
konce ta ke rub da ciki saman royal bed din ta , cikin wani makeken bedroom hade da parlourn baki daya ma dan cen gaban gadon na hango wasu tsadadun sofas irin na gidan sarauta har da Tv
ta na konce rike da wani book ta na zane , wayar ta na gefe music na tashi , ta na rera waka cikin konciyar hankali
cen na Hango Aleenah tsaye bakin gadon sai kai kawo ta ke yi , duk a tsorace ta ke kar a je Prince ya fadawa Al-Sayid
wani dan karamin tsaki ta ja kafin ta zauna bakin gadon ta kai hannu ta dan bubuga kafar Aleesherh ta na fadin " ke Aleesh , please ki tashi, wlh hankalina ya kassa konciya , kar a je ya fada wa Daddy, "
a takaice Aleesherh ta ce " ba abun da zai yi "
" why ? ba ki sani ba dai " Aleenah ta fada ta na marairaice fuska
" you know what ? i'm falling in love for him , he is so handsome , really i love him " Aleesherh ta fada cikin ko in kula
zaro idanu Aleenah ta yi ta na kallon ta , a rude ta bude baki ta ce " kin san abun da ki ke fada kuwa ? love fa ki ka ce ? how ? "
" Aleen i know what i say , wlh na kassa cire lokacin da na gan sa a kasuwa , kar ki so ki ga yadda ya taro ni , sai ki ce jarumin wani film " ta na gama fadar haka ta janyo pillow ta rungume ta na sakin murmushi
a hankali Aleenah ta kai hannu saman wuyanta , ta janye ta daura saman forehead din ta
cikin rudu Aleesherh ta ce mata " lafiya ? "
" dubawa na ke na ga in ba zazzabi ne ya kama ki ba "
wani dan karamin tsaki Aleesherh ta ja kafin ta sa hannu ta buge hannun Aleenah
janye hannunta Aleenah ta yi ta na fadin " ba ki da hankali wlh , mutumin da ko sunansa ba ki sani ba ki ce kin kamu da son shi "
" and so what ? i'm serious i love him , kuma ke za ki taimaka min na samu abun da na ke so "
" ni kuma ? " Aleenah ta fada cikin rudu
gyada mata kai Aleesherh ta yi ta na fadin " Eh , ke , yanzu fara fada min a wane hotel ya ke zaune ? "
da sauri Aleenah ta girgiza mata kai ta na fadin " nooooo , ba ruwana a cikin wannan maganar " ta kai karshen ta na kokarin tashi da ga saman gadon
da sauri Aleesherh ta mike ta bi bayanta ta na fadin " please my lovely sister , yanzu ba za ki iya taimakawa sister din ki ba ta samu abun da ta ke so ? kuma ai ba ke za ki tafiya ba , ni zan je please ki fada min "
a haka su ka shiga zagayen bedroom din , Aleesherh na rokon ta ta fada mata sunan hotel din
Aleenah kuma ta kafe ta ce ba za ta fada ba ta na tsoron ta janyo musu matsala , ita ko yanzu a tsorace ma ta ke
su na a haka wata mata ta shigo dakin ta na sallama
da gudu Aleenah ta gudu ta boye a bayanta ta na fadin " Anna , ki ce mata ta kyale ni tun dazu ta ke neman ta dake ni "
dan zaro idanu Aleesherh ta yi ta na kallon ta ta ce " ke dai yarinyar nan ba ki tsoron Allah , yaushe na ce zan dake ki ? "
wata yar karamar dariya Anna ta yi kafin ta ce " ya isa haka shikenan , yanzu ku je bangaran Mai dakin Gabas , mahaifinku na jiranku a cen "
" Daddy kuma ? " su ka fada a tare a dan razane
gyada musu kai ta yi ga na fadin " ku yi sauri ya na jiran ku " ta qarashe maganar ta na juyawa ta fice part din
kallon juna su ka tsaya yi su na zaro idanu
cen sai Aleenah ta marairaice fuska kamar za ta yi kuka ta ce " kin gani ko ? sai da ya fadawa Daddy , yanzu Allah kadai ya san abun da zai mana "
tsaki kawai Aleesherh ta yi kafin ta fara takawa ta raba ta gefenta ta wuce ta na fadin " tsaya nan , ni kin ga tafiyata "
da sauri Aleenah ta bi bayanta su ka fito part din
kai tsaye part din Mai dakin Gabas su ka nufa wato Sayida Ahlame wadda ita ce mahaifiyarsu kuma uwar gida ga Al-Sayid
da Sallama su ka shigo parlourn , murya a sanyaye kamar mutanan arziki
su na zaune ccikin parlourn , Al-Sayid ya cire Alkyabarsa , Sayida Ahlame kuma na zaune geffensa da Alkyabarsa saman cinyoyinta da alamar yanzu ya shigo wajen
sai da su ka karaso wajen sofar sannan su ka zauna saman guyiwowinsu su na fadin " sannu da hutawa Daddy , sannu da hutawa momy " su ka fada a tare cike da girmamawa
a takaice Al-Sayid ya ce musu " da ga ina ku ke ? "
" Daddy mu na part din mu mana , shi ne Anna ta je ta ce wai ku na neman mu " Fadin Aleesherh
" kafin nan ina ku ka je ?, da farko ta je amma ta ce min ba ta gan ku ba "
" Daddy da gaske ba mu je ko ina ba , na san lokacin da ta je mun tafi library ne shi ya sa "
gyada kai ya yi a hankali kafin ya ce " okay , kun san dalilin da ya sa na kira ku ? "
" a'a Daddy " su ka fara a tare
sai da ya dan dauki lokaci kafin ya ce " na kira ku ne dan na fada muku shawarar da na yanke a kan bayar da aurenku ga yaron Malik din Saudiya Nawfel Hicham bin Jaabar "
a dubu dari Aleesherh ta mike tsaye ta na zaro idanu , ita kanta Aleenah ba ta ji dadin wannan maganar ba amma ba za ta iya ja da mahaifinsu ba
โคโ ๐๐๐๐๐โโค
________________
แดสแด สแดแดแดสษด แดา แดxษชสแดแด
แดสษชษดแดแด
THE BIGINING ๐๐โค
TAP THIS LINK TO JOIN MY COMMENT SECTION
https://chat.whatsapp.com/JTfho9QngpG5Ax4LM4d4sK
_______________________________________________
[ FREE PAGE ___ 6๐๐โค ]
Dum ta ji zuciyarta ta buga a dubu dari ta mike tsaye ta na fadin " Daddy , aure ? why ? ni gaskiya ba na so "
cikin nitsuwa Al-Sayid ya ce mata " koma ki zauna ! " ya fada cike da isa sam ba wassa a tare da shi
ba dan ta so ba ta koma ta zauna ta na sunkuyar da kai
" Aleenah , Aleesherh , ba shawara na ke ba ku ba , umarni ne , na riga da na turawa Malik Letter dangane da maganar , dan haka ku jira amsar sa sati me zuwa ki fara shirye shirye "
nan take Aleesherh ta saki kuka ta na fadin " amma Daddy me ya sa za ku yi mana haka ? ni ban shirya aure ba gaskiya , kuma kuma.......... "
katse ta Sayida Ahlame ta yi da fadin " kuma me ? Aleesherh na lura ke sam ba ki jin magana , ki na neman ki fi karfin mu , dubi Aleenah ko kalma daya ba ta ce ba , kenan ke ki ke da bakin magana ? gwara ki tafi gidan mijinki ko shi zai iya gyara miki zama "
kuka Aleesherh ta saki ta na fadin " amma Daddy akwai wanda na ke so , akwai wanda mu ke soyayya da shi , don Allah Daddy ka janye maganar nan , wlh ba zan iya rayuwar aure in ba da shi ba " da alamun ta manta gaban wa take dan duk abun da ke cikin zuciyarta kawai ta ke fada
kallon juna Al-Sayid da Sayida Ahlame su ka yi kafin su juya su kalli Aleesherh cike da rudu
" ina ya ke shi wanda ku ke soyayyar , ya sunansa ? a ina kuma ya ke ? " Al-Sayid ya jero mata tambayoyin
wasu yawu ta hadiye kafin ta kai hannu ta fara goge hawayenta , karyar da ta yi ta na neman ta juye mata , to ita ina ta san sunansa , bare wajen da ya ke zaune har in da ya ke aiki
ta yi nisa duniyar tunaninta ta jiyo Muryarsa ya na sake tambayar ta
wasu wahalalun yawu ta hadiye kafin ta ce " um Daddy , yanzu ba ya cikin masarautar , ya tafi UK wajen aikinsa , kuma bai fada min yaushe zai dawo ba "
" okay , ki fada mishi ina son ganin sa , in kuma Magajin Malik ya riga shi zuwa sai dai ku yi hakuri da ke da shi dukka ku "
da sauri ta gyada mishi kai ta na sakin wani dan karamin murmushi ta saki " Eh Daddy zai zo "
gyada mata kai ya yi kafin ya ce " shikenan , Aleenah , ke kuma fa ? akwai wanda ki ke so ko babu ? " ya tambayi Aleenah ya na kallon ta
girgiza mishi kai ta yi kafin ta ce " a'a Daddy babu " ta fada murya cen kassan makoshi
" okay , za ku iya tafiya , sai da safe "
" Sai da safe Daddy " su ka fada a tare kafin su yi musu sallama su ka tashi su ka koma part din su
kai tsaye part din su su ka koma sai sauri Aleesherh ta ke kamar za ta tashi sama
ko da su ka shiga part din su ta riko hannayan Aleenah ta na fadin " please Aleen , ki fada min a wane hotel ne ya ke zaune , wlh in ban samo shi ba Daddy auren dole zai yi min , ni kuma wlh ina son sa har cikin raina " ta fada kamar za ta yi kuka har ruwa ke cikowa cikin idanunta
kwace hannayanta Aleenah ta yi , cikin sanyin murya ta ce " ko na fada miki ba abun da zai anfane ki da shi , saboda ba son ki ya ke ba , ta ya ma za ki kawo shi gaban Daddy matsayin wanda ku ke soyayya ? ki na tunanin zai amince ? a ka je kuma akwai wadda ya ke so ? "
" ni dai don Allah ki fada min , ni na san yadda zan yi , kenan kin fi son ya aura min wani cen wanda ban sani ba ko son sa ba na yi ? "
" kin dai ji fa ni da ke ya ce , ba ke kadai ba ya ce "
" na sani amma ai ke ba wanda ki ke so , kuma ai Malik yaro guda ne da shi , please ki ceci rayuwar yar uwarki guda , wlh in a ka yi auren nan kashe kai na zan yi " ta fada murya a sanyaye kamar za ta yi kuka ta na marairaice fuska
shiru Aleenah ta yi ba ta ce mata komai ba , ta san tabbas Malik yaro guda ne da shi , kuma dole Al-Sayid babbar cikin su zai fara ba shi , in har Aleesherh ta samu abun da ta ke so to tabbas ita za a bawa yaron Malik , yanzu zaba za ta yi tsakanin rayuwarta da ta Aleesherh , tun da har ta ce sai ta kashe kanta in har a ka yi auren nan to tabbas sai ta kashe kanta dan ta san yar uwarta da cika magana
wani dogon nunfashi ta ja kafin ta ce " a Sheba hotel ya ke , floor na farko , VIP room 3 "
wani kyawatacen murmushi Aleesherh ta saki kafin ta rungume ta tsam ta na fadin " na gode sosai my lovely sister , that's why i love you so muchhhhh "
wani dan karamin murmushi Aleenah ta yi kafin ta rungume ta
sun dan dauki lokaci a haka kafin Aleesherh ta sake ta ta juya da sauri ta na fadin " ina uniform din ki ya ke ? "
dan zaro idanu Aleenah ta yi kafin ta riko hannunta ta na fadin " ke Aleesh , da hankalinki kuwa ? cikin wannan daren ki ke son tafiya ? in a ka kama ki fa ? please ki bari har zuwa safe "
" Aleenah ba zan jima ba , please ki kyale ni na tafi , wlh rayuwata ce ke cikin hatsari in har ban je ba "
wani dan karamin tsaki Aleenah ta ja kafin ta saki hannunta ta nufi hanyar dressing room
jim kadan ta fito rike da uniform din ta irin na ma su aikin Sheba hotel
ta mikawa Aleenah ta na fadin " rike , amma wlh duk abun da ya same ki ba hannun Aleenah a ciki " ta fada ta na komawa bakin gadon ta zauna ta na nade hannayanta a kirji ta kauda kai
wata yar karamar dariya Aleesherh ta yi kafin ta karaso gefenta ta zauna , ta na fadin " ba abun da zai same ni saboda kyakyawar Twins di ta ta na nan , ke za ki taimaka min na fita ba tare da kowa ya sani ba , yanzu in an tambaye ni ki ce ina barci , in ban dawo ba nan da one hour ki je nema na , byeeeeee " ta fada ta na mikewa da gudu ta shiga dressing room
da kallo Aleenah ta raka ta har sai da ta shiga sannan ta ce " Aleesherh sai kin sa an kashe ni wata rana , wajen neman soyayyarki yanzu za ki saka rayuwata cikin hatsari " ta na gama fadar haka ta saki wani cool murmushi ta ce " Allah ya sa ni ma na samu wanda zan iya jefa rayuwata cikin hatsari dan kwatar soyayyarsa , kyakyawa mai kyakyawar zuciya "
ta na zaune a nan ita kadai har Aleesherh ta fito sanye da uniform din , kuma gaskiya sun yi mugun zauna mata fiye da Aleenah dan ta fi Aleenah cika da shape abun dai Masha Allah bare da ta saki curly hair din ta har tsakiyar baya gaskiya ba karamin kyau ta yi ba
a haka har ta karaso gefen Aleenah ta manna mata kiss saman kumatu ta na fadin " sai na dawo "
ta na gama fadar haka ta nufi wani closet na books da ke cikin parlourn
ta na isa ta sa duk karfinta ta tura closet din
nan na ga wata yar karamar door a baya
bude door din ta yi ta shiga , duk da wajen duhu ne amma sam ba ta ji tsoro ba dan sun saba bi ta nan
SHEBA HOTEL ๐จ
VIP ROOM 3
konce ya ke tsakiyar gadonsa , da Laptop saman laps din sa ya na faman latsawa
da ga shi sai short da t-shirt blue color , ya saki wannan smooth hair din nashi ya bazun mishi a shoulder sai tashin qamshi ya ke
ya na zaune a haka ya ji wayar landline din dakin ta fara ringing
hannu ya kai ya dauki wayar ya kai ta a kunne ba tare da ya ce komai ba
cikin nitsuwa ya nijo Muryar wani matashin ya na fadin " Sir , ga fruits din nan an kawo muku , za ku iya bude mata kofa ? "
" okay," ya fada a takaice kafin ya mayar da wayar , ya sauke laptop din da ga saman cinyoyinsa ya sauko kassa ya nufi kofar
hannu ya kai ya bude kofar sannan ya juya ya na fadin " za ki iya ajiyewa saman table " ya fada ya na nufar toilet
ba musu ta karaso cikin dakin ta na sallama da wata siririyar Muryarta
cak ya tsaya dan ko cikin duhu zai iya gane wannan Muryar
a rude ya juyo ya na zaro idanu ya na kallon ta tsaye tsakiyar dakin rike da tray din fruits
" what are you doing here ? ! " ya fada da dan karfi har sai da ta saki tray din hannunta dan ba karamar razana ta yi ba , ga shi dama ba wani kayan kirki ne a jikinsa
wani dan karamin tsaki ya ja kafin ya ce " please Get out ! "
wasu yawu ma su daci ta hadiye kafin ta bude baki murya har kerma ta ke ta ce " don Allah ka tsaya ka saurare ni , ina son mu yi magana , please "
cikin bacin rai ya tako gadan gadan gare ta
ta na ganin ya fara takowa ta fara yin baya ta na girgiza mishi kai har sai da ta kurewa bango
ya isowa ya kai hannu ya damko wuyanta , ya na kallon cikin idanunta ya ce " zan rufe ido , na kirga zuwa biyar , in har ba bude ido na gan ki cikin dakin nan , sai na yi miki abun da sai kin tsani kanki da kanki , sai kin mutu ki na nadamar hada hanyarki da ni , so get out tun kafin raina ya baci " ya na gama fadar haka ya saki wuyanta , ya kai hannu ya bude kofar dakin ya lumshe idanunshi ya fara kirge da ga 0
kuka ta saki hawaye na zubo mata bibiyu , kafin ta juya jiki a sanyaye ta fice dakin dai'dai lokacin da ya kai 5
ya na bude ido ya gan ta tsaye bakin kofar dakin ta juyawa kofar baya
da karfi ya meda kofar ya rufe ya na jan tsaki , kafin ya cusa hannu cikin gashin kansa dan ta na neman ta tayar mishi da hankali
wani dan karamin tsaki ya ja kafin ya juya ya na kallon fruits din da su ka zube cikin dakin duk wajen ya baci
wani dogon tsaki ya ja kafin , ya karaso bakin bed din sa ya dauki laptop din sa , da wayoyinsa
sannan ya bude box din bedside drawer , nan na ga wajen cike da magnetic card har wajen goma ko fi
duba su ya fara yi daya bayan daya har ya samu wadda ya ke so , sannan ya dauka ya nufi kofar fita dakin ya fice
ya na fitowa ya nufi room din da ke fuskantar wadda ya fito ya na ce ma Bodyguards din shi " Gobe ku medo kayana cikin wannan bedroom din " ya fada dai-dai lokacin da ya shige cikin dakin ya medo kofar ya rufe
DAULAR YEMEN ๐
ALEESHERH ๐๐
ta na konce tsakiyar bed din su , ta yi rub da ciki sai kuka ta ke yi kamar ranta zai fita
ita dai Aleenah ta na tsaye ta zuba mata ido, tun dawowar ta ta ke kukan nan , ta tambaye ta lafiya amma ta ki fada mata
wata yar karamar ajiyar zuciya ta sauke kafin ta zauna bakin gadon ta ce mata " ya isa haka kukan , ki fada min me ya faru a cen , ko bugun ki ya yi ? "
girgiza mata kai Ta yi a hankali ba tare da ta ce komai ba
" to minene matsalar ? sai kuka ki ke kamar wadda uwarta da ubanta su ka mutu " ta fada ta na dafa shoulder din ta
" Aleenah , i think i'm crazy " ta fada ta na kukan
a hankali Aleenah ta kai hannu ta tallabo ta , nan ta ga fuskarta a bushe ko digon hawaye babu
wani dan tsaki Aleenah ta ja ta na janye hannayanta ta ce " kin san Allah , in ba ki bude baki ki ka fada min abun da ke faruwa ba ba zan kara taimaka miki ba , sai dai ki san yadda za ki yi ke kadai "
wata yar karamar dariya Aleesherh ta yi har
All Chapters
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 5 Chapter of 23