Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
ce , ni gaskiya wannan Honey Moon ɗin ba ta ishe ni ba " " hum, amma ai da farko ce wa ka yi ba ka so " hannu ya kai ya fara sosa bayan keyarsa ya na kauda kai murmushi mai dan sauti Malik ya yi kafin ya lumshe idanunsa ya na a haka ya ji Prince ya kwantar da kansa saman shoulder din shi a sanyaye ya ce " Daddy , I'm sorry , na san ka yi kewa ta sosai tsawan shekarun nan da ba na zama tare da kai " " na yi kewar ka sosai , amma hakan ya sa na ji irin kewar da Daddyna ya ji lokacin da na nan , da sauki ni na san halin da ka ke ciki , shi ko bai da ma tabbacin in ina raye , na sani ba laifinka ba ne , kuma ni ba na fushi da kai tun da ga shi yanzu ka dawo " " I love you my Daddy " ya faɗa ya na zagayo da hannayansa a kugun Malik ya rungume shi ta gefe , ya lumshe idanunsa sai da ya saki wani dan karamin murmushi sannan ya juyo ya manna mishi kiss a forehead ya na fadin " I love you too , my baby " shiru Prince ya yi bai ce mishi komai ba , ajiyar zuciya kawai ya saukewa ƙassa ƙassa ya na a haka ya ji Malik ya zagayo da hannunshi a bayansa ya na fadin " Ba ka fada min ya Honey moon ɗinku ta kasance ? " " So Sweet " ya fada a takaice da alamun ya manta da wa ya ke zaune dan zaro idanu Malik ya yi jin abun da ya ce ko kunyar sa bai ji ba , shi kuma ya ci gaba da tambayar shi ya na fadin " kenan yarinyar mutane ka taɓa ? " " na ga ai Mallaka min ita a ka yi , har gaban Allah tawa ce " da ga haka ya ware idanunsa ya na kallon Malik , ya ci gaba da fadin " amma ka san wani abu Daddy ? ban taba jin irin wannan dadin ba , Allah Daddy sai da na dinga ganin wasu stars " Bushewa da dariya Malik ya yi har sai da idanunsa su ka ciko da ruwa bai da labari , amma Allah Prince ya cika dan Duniya , ko kunyar Malik bai ji ya fadi wannan abun , ai da farko da a ka ba shi auren ce wa ya yi ba ya so shi ya sa Malik ya bushe da dariya , yanzu ya fara jin dadin d'iyar mutane har da ganin wasu taurari sai da ya gama dariyarsa sannan ya ce mishi " ka na ji , idan ka kai makura ba stars kadai za ka gani ba , sai ka ga universe din ma baki daya , Allah ya sa dai ba ka takura mata " " to ba ita ta ce za ta iya ? dole ta yi hakuri tun da ta lasa min zuma " " hakan na nufin you love her ? " " Yes Daddy , ina son ta , fiye da yadda na ke jin ina son kaina , but I love you more than her " ya fada ya na kara matse Malik wata yar karamar dariya Malik ya yi kafin ya rungume shi tsam shi ma , a haka har barci ya yi gaba da su ☆ AFTER SOME HOURS ☆ ▪ INAYA 👑 a hankali ta turo kofar dakin ta shigo ta na sallama a sanyaye ta na shigowa idanunta su ka sauka kan Malik da Prince kwance , Prince na kankame da Malik kamar wani ya ce zai kwace mishi shi har sai da ta saki wani cool murmushi ba ta da labari dan ta manta last time da ta gan su manne da juna haka a hankali ta ci gaba da takowa bakin gadon , ta sa hannu a hankali ta janye hannun Malik da ke saman bayan Prince sannan ta dan bubuga kumatun Prince , kassa kassa ta ce mishi " Prince , ba za ka je ka yi wanka ba ? " cikin magagin barci ya ce mata " please Baby , barci na ke ji " wata yar karamar dariya ta yi kafin ta murde kunnesa ta na fadin " wake up , ba ita ba ce , Maza tashi min da ga saman gado " cikin wata siririyar murya ya ce mata " ashhh , Cutie da zafi fa " " sauko to " ta fada ta na sakin kunnensa a hankali ya tashi da ga jikin Malik ya sauko da kafafunsa kassa ya zauna bakin gadon ya na kallon ta ya na yamutse fuska hararrar shi ta yi kafin ta nuna mishi kofar fita da hannu bai ce mata komai ba ya juya ya manna wa Malik kiss a kumatu , sannan ya mike tsaye ita ma ya yi mata kiss a kumatu kafin ya sa kafa ya fice, ya baro part din baki daya sai da ya fita sannan ta saki wani dan karamin murmushi , ta tako a hankali ta kwanta in da ya tashi , ta rungume Malik kawai sai jin saukar hannunsa ta yi a bayanta , ya juyo su na fuskantar juna ya bude idanunsa a hankali , dama ba barcin ya ke ba , tunanin MALIKAT INAS ya hana shi barci a sanyaye ya ce mata " me ya sa za ki korar min babyna ? ba ki ga barci ya ke ba ? " cikin shagwaba ta ce mishi " ni kuma fa ? ni ma barci na ke ji " wani dan karamin murmushi ya saki kafin ya matse ta tsam a jikinsa ya lumshe idanunsa ita ma lumshe idanunta kawai ta yi ta na sauke ajiyar zuciya ▪IZZAT zaune ta ke gaban mirror din bedroom din ta , ta buga wani uban tagumi , tun safe ta ke kiran Queen ta ce fada mata MALIKAT INAS ta mutu amma har yanzu shiru har ta gaji da jira ta na wannan zaman jiran ta ga duk lamps din dakin sun mutu lokaci guda wata doguwar ajiyar zuciya ta sauke ta na fadin " tun dazu na ke jiran ki , sai yanzu ki ka yi niyar zuwa ? " ta na gama fadar haka Queen ta fito cikin mirror kamar kullum saman chair din ta , inuwarta kawai a ke gani cike da isa ta ce " kiran me ki ke min ? MALIKAT INAS ce na sani da ta mutu " " to sai ki fada min abun da zan yi na gaba , tun da har step na farko ya cika " " idan ki koma wajen Izayn , zai fada miki abun da za ki yi " ta na gama fadar haka ta bace da ga cikin mirror din , lamps din dakin duk su ka kunnu............ *WANNAN LITTAFIN NA BIYA NE , WANDA YA SHIRYA BIYA ZAI IYA TABO WANNAN NUMBER +22795577612 , ₦500 NE KUDIN SHIGA PAID GROUP ƊIN* *HAR ZUWA RANAR FRIDAY ZAI KASANCE ₦ 200* ❤⚘ 𝐍𝐀𝐘𝐄𝐋⚘❤ THE BIGINING 🕊👑❤ ❤👑 𝑴𝑨𝑳𝑳𝑨𝑲𝑰𝑵 𝑴𝑬𝑬𝑹𝑨𝑯 ❤🕊 https://whatsapp.com/channel/0029VaGhJCqKmCPUvpvIJ80i _______________________________________________ [ FREE PAGE ___ 24 🕊👑❤ ] wani dan karamin tsaki Izzat ta ja kafin ta mike tsaye ta na fadin " gaskiya na gaji da wannan aikin , ga shi sun bar ni cikin duhu , sun ki fada min abun da su ke son aikatawa " ta kai karshen ta na Hayewa saman bed din ta ta yi rub da ciki ( 🙄🙄🙄 ba ke kadai ba har da ni , har yanzu na kassa tantance me su ke hari , micece manufarsu dan tabbas akwai abun da su ke hari cikin masarautar , ko daukar fansa ko kuma ganin bayan ahalin Malik 🤔🤔 ) ☆AFTER SOME HOURS ☆ ▪ALEESHERH 👑💞 Duk yinin ranar a part din MALIKAT INAS ta share shi , sai wajen karfe 8 sannan ta tashi ta koma part din su da sallama a bakinta ta shigo parlourn part din su , ya na gyare sai qamshi ke tashi wani dan karamin murmushi ta saki kafin ta ci gaba da takawa ta nufi corridor ta shiga bedroom din ta sam ba ta kawo a ranta ta duba bedroom din shi in ya na ciki ko ba ya ciki ko da ta wuce bedroom din ta toilet ta shiga ta yi lafiyayen wanka sannan ta fito ta shafa shafa lotion din ta dan perfume ta wuce dressing room jim kadan ta fito sanye da wata Abaya white color ko veil babu a kanta , ta saki kyakyawan gashinta a baya sai tashin qamshi ta ke yi fitowa ta yi da ga cikin bedroom din ta na taku a sanyaye har ta juya za ta baro corridor din ta ga kofar bedroom din sa a bude kadan haske na fitowa da alamun akwai mutum ciki wani dan murmushi ta yi kafin ta nufi bedroom din sa , ta tura kofar a hankali ta shigo ta na sallama nan ta gan shi zaune tsakiyar gadonsa , da ga shi sai short da singlet , da laptop saman kafafunsa ya na aiki a hankali ta tako ta tsaya bakin gadon ta na fadin " Baby ? " " Yes , me ya faru ? " ya fada ba tare da ya kalle ta ba zama ta yi bakin gadon sannan ta kai hannu a hankali ta rufe laptop din sa bai ce mata komai ba ya dago kai a hankali ya kalle ta ya na daga mata gera a sanyaye ta ce mishi " i'm sorry , Aleenah ta fada min abun da ya faru " gyada mata kai kawai ya yi kafin ya juya ya bude laptop din sa ya ci gaba da aikinsa sake rufe laptop din sa ta yi ta na fadin " Baby , ba ka bukatar wani abu na kawo maka ? " sai da ya sauke ajiyar zuciya kafin ya kalle ta ya ce " No , just ina son na kammala aikin da na ke yanzu " " and me ? " ta fada ta na marairaice mishi face " you , what ? me ki ke so ? , ki bari na kammala aikina ko ? " ba musu ta janye hannunta da ga saman laptop din sa ta juya mishi baya ta fara latsa wayar hannunta har ya bude laptop din sa zai ci gaba da aikinsa kawai ya ji zuciyarsa ta yi wata muguwar bugawa wadda bai taba jin irin ta ba da sauri ya saki laptop din sa ya diro da ga saman gadon ya nufi dressing mirror har ya tuntunbe ba karamar razana ta yi ba ganin yanayin da ya sauko da saman gadon ta mike ta bi bayansa ta na fadin " Baby , me ya faru ? " ko sauraron ta bai yi ba ya nufi dressing mirror ya tsaya ya sa hannayansa ya fidda singlet din sa , ya na kallon kirjinsa sai ya ga sunan da ta rubuta mishi a kirji ya na rufewa da kansa , kirjinsa ya dawo kamar ba ta yi mishi rubutu ba , hankalinsa bai gama tashi ba sai da ya ga gashin kansa ya koma white duk hankalinsa ya bi ya tashi sai wani nunfashi ya ke ja sama sama ya na zaro idanu ita dai Aleesherh ta na tsaye gefensa ta na kallon shi ba ta ma san abun da za ta ce ba , tun da ta ke ba ta taba ganin irin wannan abun ba , ba laifi in a ka ce mata sunan da ta rubuta mishi ya goge amma wannan abun it's not normal , a ce lokaci guda haka ya rufe kamar bai taba samun rauni a wajen ba slowly ya juyo ya kalle ta ya ce " me ya faru ? " " ni ma ban sani ba " ta fada a dan razane wani dan karamin tsaki ya ja kafin ya daura hannu saman kansa ya fara shafa gashinsa , shi bai ma san irin tunanin da zai yi ba , ga shi ko bai da wanda zai ba shi amsa ya yi nisa duniyar tunaninsa ya ji ta rungume shi ta kontar da kanta a bayansa ta na fadin " ka kontar da hankalinka baby " " ta ya za ki ce na kontar da hankalina , ki na ganin abun da ya faru , my hair is White , ko ba ki gani na ? " " na gani " " ina son magana da Cutie " ya fada ya na shirin rabawa ta gefenta ya wuce da sauri ta rungume shi ta na sakin kuka ta ce " please kar ka tafi , ka tsaya , so ka ke hankalina ya gama tashi ? " wani dan karamin tsaki ya ja kafin ya rungume ta shi ma ya na dan bubuga bayanta cikin sigar rarrashi sannan ya ce " please stop crying , babu in da zan je " wata yar karamar ajiyar zuciya ta sauke kafin ta fara rage sautin kukanta , ta fara shigewa jikinsa ta na shafa bayansa a hankali , ta na goge face din ta a kirjinsa wata doguwar ajiyar zuciya ya sauke kafin ya sa hannayansa ya dauke ta cancak ya nufi gadonsa kai tsaye ya kwantar da ita sama , sannan ya bi ta ya yi mata runfa da kirjinsa wani dan karamin murmushi ta saki ta na daga mishi gera guda bai ce mata komai ba ya kai hannu ya riko zib din Abayarta ya zuge shi har kassa , sannan ya dago hannu ya kashe lamps din dakin baki daya ( 🙄🙄🙄 Okay , kora ta a ka yi ko ? No problem na tafi ni ma , 🙄🙄 amma ka ji wa yarinyar mutane ciwo kar ka neme ni ) ▪PRINCESS 👑💜 zaune ta ke cikin garden , duk da cikin dare ne ba ta jin tsoron zama nan ita kadai , ta yi kuka har ta gaji ta na zaune ta zubawa waje guda ido , Allah kadai ya san abun da ta ke tunani ta na zaune a haka Junior ya iso wajen ya na yi mata sallama , ya na sanye da kayan barcinsa , Wajen Prince ne ya so tafiya amma ya na ganin ta ya ji zuciyarsa na bukatar kasance wa da ita sai da ta sauke wata doguwar ajiyar zuciya sannan ta dago kai ta kalle shi ta na murmushi ta ce " Hi Junior , ba ka yi barci ba ? " " ta ya zan yi barci rabin raina bai yi barci ba " ya fada ya na karasowa gefenta ya zauna wata yar karamar dariya ya yi kafin ya ce " na ji shikenan " " me ya sa ba ki yi barci ba ? ki na tunanin Ammie ko ? " gyada mishi kai ta yi a hankali ta ce " har yanzu ba kassa yarda ta tafi kenan , you know how much i love her , yanzu wa zan dinga tsokana ? " " ba ga ni ba " ya fada ya na riko hannunta wata yar karamar dariya ta yi kafin ta kontar da kanta saman shoulder din sa ta ce " a yanzu , na san duk lokacin da ka yi aure za mu daina ganin juna , za mu daina tafiya shan ice cream da shopping , sai dai ka tafi da matarka " " wa ya fada miki ? ko auren na yi tare za mu dinga tafiya shan ice cream , mu na tafiya Shopping da sauran wajaje " " hmmm , kai ka na ganin matarka za ta yarda , duk da ni kanwarka ce , amma in dai ta na son ka ba za ta ji dadin ganin ka da wata ba " shiru ya yi bai ce mata komai ba ya zuba mata ido , har yanzu ya kassa tantance me ya sa ya ke son ta haka ba , duk da sun tasso a matsayin brother and sister , amma duk lokacin da ya ke tare da ita ya na jin wani feeling da bai taba ji tare da wata macen ba , that's why ya yarda da cewa tabbas son ta ne ya ke , amma ya ga alamun ita sam ba ta lura da hakan sai da ya sauke wata nanauyar ajiyar zuciya sannan ya kira sunanta a Sanyaye " uhm " ta amsa mishi ba tare da ta dago kanta ba da ga saman shoulder din sa ya dan dauki lokaci kafin ya bude baki cike da shakku ya ce mata " Princess , za ki aure ni ? " Dam ta ji zuciyarta ta buga ta dago kai ta na kallon shi ta ce " What ? ka san me ka ce ? " gyada mata kai ya yi kafin ya ce " na sani , please ki fada min za ki aure ? " " aure fa ka ce Junior ? anya kanka guda kuwa ? , ko dai wassa ka ke yi min ? " " No , ba wassa na ke ba , please ki daina kallon abun wani iri , na ga ai akwai aure tsakanin mu , kuma ni ina son ki , I love you more than you think , please ki yarda ki aure ni " iska ta furza da ga bakinta kafin ta mike tsaye ta na shirin barin wajen dan ita a ganinta ta yi wa Junior tsufa gaskiya , ba ta taba tunanin zai bude baki ya yi mata irin wannan tambayar ba watarana ba ta yi taku biyu ba ya riko hannunta ya tsayar da ita da cewa " please kar ki tafi ba ki ba ni amsa ba " juyowa ta yi a hankali ta kwace hannunta ta ce " me ka ke so na ce maka ? ta ya za ka min irin wannan maganar ? kuma ni gaskiya ba zan iya auren ka ba , na yi maka tsufa " " and so what ? na ga ba laifi ba ne dan ka auri wadda ta girme ka ba , kuma na ga shekarun mu guda , asali ma na ba ki wata hudu , kuma kar ki manta , Annabi Muhammad ( S.A.W ) matarsa ta farko ta girme shi , why mu ma ba za mu yi koyi da shi ba ? please accept to marry me " kauda kai gefe ta yi ta furza iska da ga bakinta , ba ta ma san abun da za ta ce mishi ba , da ga gani tsakani da Allah ya ke yi mata maganar nan riko hannayanta dukka biyu ya yi , ya matso kusa da ita , a sanyaye ya ce mata " Princess , you don't love me ? " " I love you , but like my brother " ta fada ta na dawo da kallonta gare shi " it's not a problem , tun da har ki na so na a matsayin dan uwanki , cikin sauki son zai juya ya koma soyayya ni ma dan haka na fara , ko ba ki jin dadin zama da ni ? akwai wani abu da na ke da ba ki so ? na yi miki alkawari ko ma minene zan gyara kawai ki amince " " Junior , ko ni na yarda ka na ganin Daddy zai yarda da auren mu ? na sani ba za su taba yarda " " Daddy da Uncle duk sun yarda , kuma kafin na fara yi miki maganar nan sai da na yi musu ita kuma sun amince , kawai ba su fada miki ba ne saboda su ba ni dama na shawo kanki da kaina " shiru ta yi ba ta ce mishi komai ba na dan lokaci kafin ta ce " yanzu me ka ke so na ce ? " " kin yarda za ki aure ni " ya fada ya na sakin murmushi murmushi mai dan sauti ta saki kafin ta ce mishi " amma ai ka san ba haka a ke neman mace aure ba ko ? " cikin rudu ya ce " kamar ya ? " " ka yi kneel down mana " wata yar karamar dariya ya yi kafin ya saki hannayanta ya zube saman guyiwowinsa , ya mika mata hannu ya na fadin " ki yi hakuri ban sayo ring ba , but i promise gobe ina sayo miki , Nailah , za ki aure ni ? " nade hannayanta a kirji ta yi ta na sakin murmushi ta kauda kai gefe " pleaseeeee my Princess " ya fada ya na marairaice mata fuska ya na gama rufe bakinsa ya jiyo Muryarta ta na fadin " Faaz ? " " Faaz ? " ya maimaita sunan shi ma kafin ya ce mata " me ya faru Baby ? " da sauri ta ce mishi " Junior , look , Faaz ne ya ke kokarin fita masarautar " ta fada ta na nuna mishi Faaz da ke ta biyar bango ya nufi hanyar fita masarautar a hankali ya mike tsaye shi ma ya na kallon shi riko hannunshi ta yi ta na fadin " mu bi bayansa " " what ? no ki nari har ya dawo mu tambaye shi ina ya je , ba ki ga dare ya yi ba ? " " please ba abun da ya faru , don Allah mu bi bayansa " ta fada ta na jan sa ba yadda ya iya ya bi bayanta su ka bi bayan Faaz dan ya na tsoron ya bar ta haka wani abu ya same ta duk abun da ya faru Malik na tsaye ya na kallon su cikin part din sa , ba karamin sanyi ba ya ji cikin zuciyarsa ganin su haka musaman lokacin da Junior ya zube saman guyiwowinsa , kawai ya tsaya ya na jiran ta daura hannunta saman nashi , amma sai ya ga ta ja shi su ka bar wajen , bai kawo komai a ransa ba dan a tunaninsa wani abu ne su ka gani bangaran su kuwa , cikin sand'a su ke biye da bayan Faaz , duk da akwai mutane cikin masarautar dan lokacin bai wuce karfe 10 na dare ba haka su ka fara bin bayansa ya na tafiya in ya gaji ya yi gudu , ya na tsalle kamar ya na wassa sai rokonta Junior ya ke su koma amma ba ta jin sa , ba abun da ta ke so kamar ta ga ta kama Faaz , tun lokacin da ta sauke ido saman shi ta ji bai konta mata ba , in har wani abu ya ke shirya musu ya kamata ta sani sai da su ka yi wajen 30 minutes su na biye da bayansa , kafin su ga ya sha wata kwana da sauri Ta janyo Junior su ka yi kwanar amma kawai sai ta ga mutum ya bace , babu shi sama da kassa , ga shi kuma hanyar doguwa ce babu kwana dan ita ce hanyar da za ta kai Prison din masarautar cikin rudu ta ce " Ina kuma ya shiga ? " riko hannunta Junior ya yi da karfi ya janyo ta su ka bar wajen ya na fadin " ya isa haka , mu koma gida yanzu " " Junior please , a ka je wani mugun abu ya ke shirya mana kuma fa ? " ko sauraron ta bai yi ba ya ci gaba da jan ta har su ka dawo kan titi nan ya tsayar musu da wani mai mota dan ya meda su Daular , cikin sa'a ko ya amince dan sarai ya gane su , ya meda su har cikin Daular , sannan su ka sauka Junior na yi mishi godiya Princess kuma ta na saukowa ta nufi part din MALIKAT INAS da gudu da Sauri Junior ya

Chapter 18 of 23