da yafi muhimmanci yanzu shine muyi ƙoƙari mu gano in da aka ɓoye Mahaifiyarki."
"Barrister ka dakata ni Hajiya Saudat ba Mahifiya ta ba ce, domin na riga naji komai a lokacin da Hajiya Hindu take faɗa ma Mallam ɗin unguwar dosa komai dai dai ni kuma lokacin zan wuce na jita, tun daga lokacin naji na ƙara tsanar Hajiya Hindu nake so a yanke mata hukuncin kisa in da kunga ba wanda yasan maganar cewa ni ba ƴar daddy da momy ba ne sai Malam ɗin unguwar Dosa in da shima ya kamata ya mutu domin yana shiga rigar malanta yana tafka ɓarna a doran ƙasa, domin shi ya zo ya sameni kan cewa zamu haɗu mu kashe Momy sannan mu ɗora ma Hajiya Hindu daga nan kuma sai mu raba dukiyar su Daddy biyu ni da shi, bai san ni ko kar nake kallon shi ba, tuni nima na siye wanda ya turo akan yayi kisan akan in ya zo kar ya sake ya soki momy a in da ya san zata mutu ni kuma zan bata maganin barci wanda ko an soketa ba zata sha wahala ba domin duk da ba ita ta haifeni ba ina son ta kuma ina mata kallon mahaifiya, bayan na zuba mata maganin barci a cikin lemu ta sha sai ta fara barci tuni naje na siye maigadi da duk sauran ma'aikatan gidan da kuɗi shi kuma wanda Baba Malam ya turo ya shigo gidan bayan na dakatar da duk wani cctv camera na gidan har sai da ya caka ma Momy wuƙar sannan na ɗauki waya na kira Hajiya Hindu nayi tamkar muryan Momy ina faɗin Hajiya ki zo ki ceceni ina ajiye wayar nayi sauri na fice naje na kunna cctv ɗin gidan na koma ɗaki sai da na tabbatar da cewa Hajiya ta shiga kuma plan ɗina ya tafi dai dai sannan na fito."
Aneeesa ta ƙarisa maganar tana zubar da hawaye, "nayi kewar Momy na mai ƙaunata da gaskiya Allah sarki baiwar Allah ta raini ƴa mare asali ko ya rayuwar nata ɗan ya kasance oho, ni yanzu ba damuwata in ga momy ba damuwata a yanke ma Hajiya Hindu hukuncin kisa.!
Tana gama maganar ta ɗauki jakarta da glass ɗin ta tayi hanyar ficewa, da sauri Barrisster Zainab da take laɓe da abun ɗaukan magana a hannun ta tayi sauri ta juya ta ɓuya, har Aneesa da sauran suka fice sannan itama ta fito ta nufi bakin titi ta tari abun hawa sai Asibiti, tana zuwa ta tarar da Hajiya da Barrister Khasheeefat suna hira, har Barrister Khasheeefat tayi sauri ta kooma ta kwanta tamkar barci takeyi sai taga ashe Barrister Zainab ce sai ta miƙe ta jingina tana faɗin, "a'a ƙawata ya ake cikine to akwai wani labari ne,"
Murmushi Barrister Zainab tayi ta zauna kusa da Hajiya ta fara gaisheta sannan ta dubi Barrister Khasheeefat ta ce, "ai ƙawata komai ya zo last domin duk wani bayani da muke buƙata daga gurin yarinyar gaba ɗaya yau ta warware mun, kin san wani abun ƙarin mamaki kuwa wai ashe ƙanin Mijin Hajiya Hindu wanda suke Uba ɗaya duk shi ya shirya wannan kitimurmuran, bari dai ku ji komai, kunna musu recording ɗin tayi suna ji sai da suka gama ji tass gaba ɗaya suka numfasa Hajiya Madina ta ce lallai wannan family akwai rikici da yawa a cikin ta, kenan yanzu ita Aneesa ta san ba ƴar gidan ba ce shiyasa take son ta yagi rabon ta kafin wasa ya tashi, to ni damuwata ma gaba ɗaya ina ita Hajiya Saudat ɗin, su wa suka haƙota tabbass itama Aneeaasan akwai wanda yake munafurtan ta a gefe."
"Tabbass Hajiya nima ina tunanin haka bayan ni da nake bibiyan ta akwai wasu daban kuma, amma da sannu zamu binciko komai insha Allah ni zan wuce gida ƙawata Allah ƙara lpy."
"To ɗiyar Albarka, Allah ya albarkace ku ya kareku a duk in da kuke ki gaidamun da Umman ta ki."
"Ameeen ya Allah Hajiya, zataji Insha Allah."
*************************
Hajiya Saudat ne ke sauraran duk bayanin da Aneeesa ta keyi a cikin Audio ɗin da aka kunna mata take sauraro, gaba ɗaya hankalin ta ya tashi, to in har Aneeeasa ba ƴar ta ba ce ina ɗan ta yake kenan Momy Hindu ta san komai, aiko ba zata taɓa yafe ma Hajiya Hindu ba, tasa ta raini ƴan da ta zama bala'i a cikin al'umma har take iya tunanin a haɗa kai da ita a kashe wani, ita in da Aneeesan ta faɗa mata ko nawa take buƙata zata mallaka mata, taji bala'in mamaki akan cewa wai har da Baba Malam wanda kaf dangin mijin ta ba wanda yafi nuna mata ƙauna irin shi, kai tabbass sai yau tasan ɗan adam ba abun yarda ba ne, miƙama Hamida wayar tayi ta koma ta yi zaman ƴan bori nan da nan taji zazzaɓi ya lulluɓeta.
*************************
UNGUWAN DOSA
Sosai Baba malam ke cikin tashin hankali tun bayan kallon labaran da yayi shekaran jiya ko barci ba ya iya yi, matar shi tayi mai tanbayar duniya ya ce ba komai, in da gefe guda kuma aka tura mai maganar Aneeeaa ta whatsaaap nan ma ya ƙara kiɗimeeawa.✍️✍️✍️✍️✍️
KUYI HAƘURI DA NI WLH RASHIN WUTA KE DAMUN MU, AMMA DUK DA HAKA IN INA GANIN COMMENT ZAN DUNGA ƘOƘARIN GANIN INA YI MUKU AKAN LOKACI, TO MASU ƘIN ANEEESA MASU ƘIN BARRISTER ZAINAB HAR YANZU KUNAJIN HAUSHIN NA SU KO KUN DAINA🤣🤣🤣🤣🤣INA SO IN GA RUWAN COMMENT DON ALLAH SHIYASA NA DAGE NAYI DA ƊAN YAWA KOWA INA SON YA TOFA ALBARKACIN BAKIN SHI KI BA YAWA🤣🤣💃💃💃
Share fisabilillah🙏🙏
Zeeeey yar mutan zazzau ce🥰🥰🥰
[10/5, 10:29 AM] Zzz Yar Mama: 😭
KISAN RUƊU😭
Wa ya yi kisan?
TSARAWA DA RUBUTAWA
ZAINAB SALIHU YARIMA
(sarauniyar kanawa)
*Leeyert Hijabs and Fancy Socks*
*At affordable price*
*Nation Wide Delivery*
*Hurry up and get yours here* 😊😊 *Location: Zaria*
*Email: www.raleeyaty@gmail.com*
*09132110903*
*akwae different design/style like : Egyptian hijabs, 2 cap hijabs,Rubber hijabs,Dubai Hijabs etc*
Page 32/33
BISSMILLAHIR RAHMANIR RAHEEM
*************************
NIGERIA KADUNA
Malam ne zaune a ɗakin shi na sirri da wani fai-fai da ke ɗauke da wani ƙasa mai matuƙar laushi yana ta wasu zane-zane a cikin ƙasan da ya zana sai ya goge da ya zana sai ya goge duk ya haɗa uban zufa duk da AC da ke kaɗawa a cikin ɗakin na shi, can ya miƙe a zabure yayi fatali da fai-fan ƙasa haɗi da furzar da wani huci mai zafi yana faɗin, "ina hakan ba zai taɓa yuwuwa ba, ba zan bar hakan ya faru ba kai kai.!
Ya ƙarisa maganar cikin tsananin ɗimuwa da tashin hankali, "in dai ina numfashi zuri'ar Usman ba zata taɓa dawowa ta tafi kenan, taya ma wai za'a ce duk tsawon Shekarun nan Usman na raye amma ƙasa bata taɓa nuna mun haka ba tabbas ƙasa kin ci Amanata kuma kin karya alƙawari,! da sauri ya ƙara duƙawa ya fara tattara ƙasan tamkar wadda ya tuna wani abu.
*************************
"Ina so ki sani Hajiya Saudat ban ɗauko ki nan don in cutar da ke ba sai dai don in tseratar da ke kan sharrin ƴar ki da ƙanin sirikin ki sannan kuma don in ɗauki fansa akan Hajiya Hindu, har abada ba zan taɓa iya cutar da ke ba domin ke ɗin kin kasance mace ce adala mai tausayi da jin ƙai, cikin haka nima kin taɓa taimaka mun game da Mahaifiyata duk da ita ɗin bata cancanci taimakon ki ba, domin mahaifiyata tana ɗaya daga cikin wanda suka cutar da ke a rayuwa, ita ɗin Aminiyar Hajiya Hindu ce ƙut da ƙut domin duk wani makirci tare suke ƙullashi abun na mun matuƙar ciwo inna ga mahaifiyata suna aikata wani abun duk wani biye biyen malamai da bokaye tare sukeyi da Mahaifiyata, sai watarana kwatsam sunje gurin wani boka da Mahaifiyata ya ce buƙatan su ba zata taɓa biyaba sai yayi anfani da ɗaya daga cikin su, Hajiya Hindu ta ce ma Mahaifiya ta taje yayi anfani da ita kasancewar ita ta fita yarinta kuma tayi mata alƙawarin zata bata kuɗi masu yawa, kasancewar mahaifiyata ta kasance mayyan kuɗi akan kuɗi zata iya aikata komai, gashi dama mahaifin mu ya rasu ita take fafutukar ɗawainiya da mu kasancewar dangin mahaifin mu sun watsar da mu, haka mahaifiyata taje suka aikata masha'a da wannan boka wanda shine sanadiyar tarwatsewar rayuwar mahaifiyar mu da mu baki ɗaya, bayan wasu watanni Hajiya Hindu taƙi ba mahaifiyar mu kuɗin da tayi alkawari ta fara mata yawo da hankali, kwatsam mahaifiyar mu ta fara wani ciwo mai matuƙar firgitarwa wasu manya manyan kuraje ne suka fito mata a cikin farjin ta da sun fashe sai wari mai tsanani haka mukaje Asibiti sukayi iya yin su suka rubuta mana magunguna muka dawo gida ta fara sha sai gaba ɗaya ƙurajen suka mutu, a lokacin da ta fara ciwon kwata kwata Hajiya Hindu ta daina zuwa gidan mu tun da ta zo sau ɗaya taga halin da mahaifiyata take ciki ta bani dubu ashirin bata ƙara zuwa ba ko mahaifiyata ta kirata bata ɗauka wataran ma sai ta kashe wayar sosai abun ya ba mama na mamaki bayan taji sauki ta shirya taje gidan ku sai Hajiya Hindu tayi mata korar rashin mutunci ta ce ma masu gadi karsu ƙara barin ta ta shigo ko ta zo, muna cikin wannan hali ciwon mahaifiyata ya ƙara dawowa fiye da na baya don wannan karan gaba ɗaya jikin ta ne, haka muka koma Asibiti, haka muka dunga zarya har gaba ɗaya kuɗin da mahaifiyata take da shi suka ƙare asibiti suka koremu kwatsam sai gaki shine ki ka taimaka mana kika biya kuɗin aka cigaba da kula da mahaifiyata bayan wasu watanni ciwo sai gaba yakeyi ba wani sauki har ƴan kuɗin da kika biya suka ƙare, hakan yasa doctor ɗin cewa su sun gaji zai sallamemu na dunga roƙon shi amma yaƙi saurarata daga baya yace mun in har zan bashi kaina za'a cigaba da kula da mahaifiyata kyauta har taji sauki, saboda shi rayuwan yanzu taimakekeniya akeyi in taimake shi in kashe mai ƙishin shi shima ya taimakeni ya kula da mahaifiyata, hakanan ban da zaɓi na amince tun daga ranan dr Sameer ya maidani tamkar matar shi ko dare ko rana ya buƙace ni haka zai kirani in je tun ina kuka har na zo abun ma ya daina damuna, sai ya kasance ma ko bai nemeni ba ni zan nemeshi, daga nan idona ya ƙara buɗewa sai na fara bin wasu mazan irin alhazawan nan saboda ɓarin kuɗi da suke mun, sai in kwana biyu ban leƙa naga ya jikin mahaifiyata ba, in ko na leƙa a daddafe ina yi ina liƙe hanci, haka mahaifiyar tawa zata bini da kallo tana girgiza kai tana hawaye ni ko ko a jikina a gabanta dr Sameer zai rungumeni ya mun kiss kuma ko damuna hakan baiyi, sai da mahaifiyata tayi shekara ɗaya da rabi tana jinya sannan ta mutu, daga lokacin ni kuwa duniya ta zama mun sabo, rikici muka fara da dr Sameer da naji cewar zaiyi aure bayan ya mun alƙawarin aure, aiko ƙiri ƙiri ya ce ba zai auri raguwar maza ba, maganar tai matuƙar ƙona mun rai alhalin shi ya fara lalatamun rayuwata.!
Hamida ta ƙarisa maganar tana mai sakin kuka, da sauri Hajiya Saudat ta taso ta rungumeta a jikinta tana ta, bata hanata kukan ba sai da tayi mai isar ta sannan tayi shiru, ta cigaba da magana, "shiyasa naƙi barin ki ki fita domin a yanke ma hajiya Hindu hukuncin da zata tozarta a idon duniya na cewa ta kashe sirikarta, amma don Allah ki gafarceni."
Ta ƙarisa maganar tana kallon Hajiya saudat.
"To amma taya akayi har kika san shirin Aneesa, sannan taya akayi kukaje kuka haƙoni.?
"Nasan shirin Aneesa ce ta hanyar ƙawarta wacce ta yarda da ita wato Marry, ita ta sanar da ni komai bayan na bata maƙudan kuɗaɗe, sannan wani yarona da ke mun aiki tare da shi akaje maƙabarta kai ki bayan kowa ya watse shi bai tafi ba yayin da dama mun riga mun sanar da maigadin maƙabartan komai shima mun bashi wasu kuɗaɗe shiya taya yarona suka haƙo ki aka ɓoyeki a maƙaɓartan aka fara baki taimakon gaggawa saboda a lokacin kin zubar da jini sosai, sai da dare yayi muka bar da ke maƙabartan saboda idon mutane."
.************************
"Amma ban taɓa sanin cewa ke butulu ba ce sai yanzu! har ni zaki ci amana Aneesa kin san dai na fiki wayau da komai zan iya zame kai na a cikin lamarin nan sannan in rufta da ke ciki kinga kinyi biyu biyu kenan kuma duniya zata san cewa ke ba jinin mu ba ce.!
"Hhhhh to sai me! na ce sai me to malam yakubu.
[10/5, 10:29 AM] Zzz Yar Mama: 😭
KISAN RUDU😭
Wa ya yi kisan?
TSARAWA DA RUBUTAWA
ZAINAB SALIHU YARIMA
(sarauniyar kanawa)
Masoyana da masu bibiyar labarina, da masu kira na a waya duk Ina godiya, Alhamdulillah insha Allah na dawo kuma Zan cigaba daga in da muka tsaya, son so nake muku fans.
34/35
BISSMILLAHIR RAHMANIR RAHEEEM
*************************
NIGERIA KADUNA
Zaune suke baki d'ayan su sun mi'ka hankalinsu da natsuwar su suna sauraran Hajiya game da maganar da take musu, "Khasheefat dole zaki tafi Dubai kiyi mana kwakkwarar bincike game da wadan nan familyn da muka gama kallo, domin jikina ya na bani akwai kwakkwaran ala'ka a tsakanin su da iyalan gidan Mailafiya, domin wancan tsohon da aka daukeshi tabbass hoton shi ne a falon gidan Alhaji Mailafiya."
Nisawa gaba d'ayan su su sukayi, sannan Barrister Zainab ta Fara magana tana fad'in, "yanzu momy kina ganin Harbeebarty zata iya zuwa Dubai ita kad'ai ga shi bata dad'e da warkewa ba,? me zai sa ba zamu tafi tare ba.?
"Zainab ba zaku tafi tare ba, domin kema akwai aikin da zaki mun domin Ina bukatar in san meye dalilin da yasa wancan yarinyar Hamida taje ta sa aka hako Hajiya Saudat, da kuma Ina ta 'boyeta domin shine abun da yafi muhimmanci a yanzu, bayyanar Hajiya Saudat shi zai warware duk wani kulle-kulle na su Aneeesat da shi kanshi Malam yakubun."
"To yanzu Momy yaushe ne Zan tafi Dubai d'in,? bayan kin San yau saura kwana bakwai a koma kotu, sannan kina ganin momy a cikin kwanaki bakwai d'in nan zan iya kammala binciken da naje yi har mu samu abun da muke so.?
"Sosaima kuwa y'ar momy ban San ki da karaya ba, kisa a ran ki zaki iya."
"Shikenan Momy Allah ya taimakemu, zan tafi dare nayi insha Allah gobe da safe zan shigo da wuri sai a shirya komai yadda ya dace, 'kawata Allah ya 'kara lafiya mu had'u a chat anjima akwai labari."
Zainab ta 'karisa maganar tana kashe ma Barrister Khasheeefat ido, harara ta ballara mata, ta fice tana dariya girgiza kai Momy tayi tana ma yaran nata dariya, had'i da mikewa ta shige ciki.
*************************
Kaiwa da kawowa Aneesa take ta yi a dakin, hankalinta a matuk'ar tashe, juyawa tayi ta kalli Marry ta ce mata, "Marry Ina matukar jin tsoron Malam na unguwar Dosa domin shi din ba k'aramin hatsabibi bane ga iya munafunci ko wata macen albarka, gashi har yanzu mun kasa samo in da Momy take."
"To yanzu Aneesa ya kike so ayi, dole fa sai mun gano in da momyn ki ta ke."
Nisawa gaba dayansu sukayi.
*************************
DUBAI.
MAJEED FAMILY.
Bayan kwana biyu da faruwar lamarin, komai ya lafa, kowa ya dawo hayyacin shi, sannan Papi ya tara kowa da kowa domin aji ta bakin kowa, gaba dayansu suna zaune a babban falon gidan kowa yayi shiru da abun da yake sakawa a ran shi, Papi ne yayi karfin hali ya ce, "Sheick ya kamata ka bude mana wannan taron da Addu'a kafin mu fara abun da ya taramu."
Bude bakin sheick Sudaes ke da wuya zai fara magana sai akayi sallama a kofar falon gaba daya suka juya don ganin mai yin sallaman.✍️✍️
Zeey yar mutan zazzau ce🥰🥰
[10/5, 10:29 AM] Zzz Yar Mama: 😭
KISAN RUDU😭
Wa ya yi kisan?
TSARAWA DA RUBUTAWA
ZAINAB SALIHU YARIMA
(sarauniyar kanawa)
Masoyana da masu bibiyar labarina, da masu kira na a waya duk Ina godiya, Alhamdulillah insha Allah na dawo kuma Zan cigaba daga in da muka tsaya, son so nake muku fans.
Page 36&37
BISSMILLAHIR RAHMANIR RAHEEEM
NIGERIA KADUNA
Zaune ya ke a cikin wani daki mai cike da tarkace irin na su na masu buga kasa, k'asace a gaban shi ya na ta wani zane-zane a ciki yana gogewa duk ya hada uban zufa, can ya mike ya fara kaiwa da dawowa a cikin daki, yana surutai.
Malam na unguwar dosa kenan yau kimanin kwanan shi uku a kulle a daki ya na bincike game da iyalan Majeed family da ke Dubai, amma ya kasa gano komai saboda kasa ta ki ba shi hadin kai.
*************************
"Hello Hamida kina ji na ko,? Aneeesa ta bude wuta akan binciken lallai sai ta gano in da Hajiya ta ke, kuma ta fara zargina, saboda haka dole a canja salon tafiyar, in da hali ma ki dauke Hajiya daga wannan gidan ki canja mata waje."
"Good Merry aikin ki na kyau karki damu Aneesa ba zata taba gano in da muke ba."
" OK to shikenan ba matsala sai kin ji ni."
Juyawan da Marry zatayi sai jin bindiga tayi a kan ta, a firgice ta dago ido tana kallon Aneesa da ta dora mata bindiga a kan ta, sannan fuskar ta tamkar bata taba dariya ba.
"Kinyi babban kuskure Merry da kike tunanin zaki ci Amanar Aneesa ki zauna lafiya, tabbass sai kin san kin ci Amanata."
"Please Aneesa ki tsaya ki saurareni wlh ban ci Amanarki ba, ni kawai..!
"Keep quiet ki rufemun baki ko in fasa miki kai da bindigan nan.!
*************************
Tafe take cikin wani katafaren mall tana dauke da abun zuba kaya, hannun ta ta kai zata dauki wani turare dai-dai lokacin da Barrister Zainab ta kai hannu ita ma zata dauka hannun su ya hadu da na juna, juyowa Hameeda tayi suka hada ido da Barrister Zainab a tare suka sakin ma juna wani tattausar murmushi, Barrister Zainab ta ce ma Hameeda, "Woww ke ma kina son turaren nan kenan.?
"Sosai ma kuwa ni shi ne turarena, akwai shi da kamshi mai dadi."
"Sosai ma kuwa."
Jerawa sukayi suka cigaba da hira tamkar wanda dama sun san juna, har suka kammala siyayyar suka jero suka fito tare, bayan sun fito ne sukayi exchanging number kowa ta shige motor ta.
*************************
YAU SAURA KWANA BIYU A SHIGA KOTU.
"Momy na samu dai na samu number kuma ta zo gidan mu jiya nima nayi alkawarin yau zanje gidan ta."
"Ok ba damuwa y'ata haka nake son ku Allah ya muku albarka."
"Ameeen Momy, yauwa Momy kin samu kawata Kuwa,? don ni na Kira ta bai zuwa."
"Eh ta kirani da zu kuma ta fadamun kamar da alamun nasara a tafiyar tata."
"To Alhamdulillahi Momy Allah ya dawo mana da ita lafiya."
"Ameeen ya Allah."
*************************
Kwanci ta shi ba wuya a gurin Allah domin yau ne ta kama za'ayi zaman kotu wanda ake sa ran shine zama na karshe da za'a yanke ma kowa hukunci ya girbi abun da ya shuka, ga shi har yau Khasheefat ba ta dawo ba kuma number ta bai shiga.
Kotu ta cika makil da jama'a da yan jaridu an zauna kowa ya natsu a fara gabatar da karan kenan sai ga wata ta shigo kotun kaman an jefota fuskar ta jina-jina da jini tana zuwa tsakiyar kotu ta fadi kafin alkali yayi magana da sauran yan kotun sai ga Barrister Khasheefat ta shigo da wasu mutane.✍️✍️✍️
Kash na gaji amma Inna ji ruwan comment zaku ji ni, da dai nayi tunanin Anya ba Zan maida littafin nan na kudi ba kuwa sbda wasu dalilai domin akwai saura labari da yawa da yuwuwan in mai da shi 1&2 two din ya zama na kudi amma kuma in har naga kun nunamin one love gurin sanbado comment nima Zan nuna muku one love gurin barin shi free.😂🥰
Zeeeey yar mutan zazzau ce🥰🥰🥰
[10/5, 10:29 AM] Zzz Yar Mama: 😭
KISAN RUDU😭
Wa ya yi kisan?
TSARAWA DA RUBUTAWA
ZAINAB SALIHU YARIMA
(sarauniyar kanawa)
Masoyana da masu bibiyar labarina, da masu kira na a waya duk Ina godiya, Alhamdulillah insha Allah na dawo kuma Zan cigaba daga in da muka tsaya, son so nake muku fans.
Page 38&39
BISSMILLAHIR RAHMANIR RAHEEEM
*************************
KOTU
Hajiya Hindu ce ta zaro ido tana nuna bayan Barrister Kasheefat jikin ta na rawa ta ke fad'in, "Alhaji Usman dama kana raye,,,,? Maganar tata makalewa tayi sakamakon shigowar Barrister Zainab da Hajiya Saudat da Alhaji Mubasshir Mai lafiya, luuuu Hajiya Hindu ta tafi ta sume, yayin da kotu ta hargitse da hayaniya sakamakon bayyanar Alhaji Mubasshir Mai lafiya da Matar shi Hajiya Saudat Mai lafiya, kasancewar shi sanannen mutum ne mai taimakon Al'umma, kuma shekara biyu da suka wuce kowa ya san cewa Alhaji Mubasshir ya rasu, haka Hajiya Saudat ma an san ta rasu, watannin baya wadda ya kasance yanzu akan mutuwar ta ta ce ake tafka wannan rudadden shari'a mai cike da rud'ani, gaba d'aya Aneeesa ta shiga rud'ani sakamakon ganin mahaifin nata da Mahaifiyarta a raye, to in har Daddy bai mutu ba kenan su Daniel sun ci amananta kenan, to tsawon shekarun nan Ina suka b'oye Daddy, bata gama rudewa ba sai da taga ana k'ok'arin d'aukar mutanen da suka sussume zuwa Asibiti don basu taimakon gaggawa, Marry ce ta d'ingiso ta zo kusa da Aneesa ta ce mata, "Madam Aneeesa ya kika ga kalan namu makircin, tabbass kin yi babban kuskuren Amincewa da mu, kin san meye,? Ni da Daniel jami'an bincike ne na farin kaya, ke baki ji mamaki ba a ce kamar mu muna da girman mu muna secondry school,? To ki sani Mahaifin ki shi ya wakilta mu domin mu shiga rqyuwar ki karki lalacewa sai dai kash lokacin da muka fara bibiyanki muka tararr kin riga kin lalacen domin a lokacin ba abun da bakya sha, hhhh Madam Aneeesa kin yi kuskure Babba fa amma lokaci yayi da zaki girbe abun da kika shuka, Officer Arrest her.!
"Yes ma."
Luuuu Aneeesa ta yi zata sume Marry ta tsinka mata wasu lafiyayyun Mari guda biyu wanda yasa ta farfadowar dole, sa mata ankwa akayi aka tasa keyarta, waigowa ta yi tana nuna Merry da hannunta tana fad'in, " ni kuka cuta ko tabbass zan fito zaku gane kuranku dukkanku sai naga bayan ku.!
Ta fad'a cikin karaji, tana wani irin ihu da ya jawo hankalin mutanen da ke cikin kotu, gaba d'aya kallo ya dawo kan ta, haka dai aka tafi da ita tana zage-zage tamkar mahaukaciya.
*************************
*KAUYEN DAN DAURA*
"Wayyo Allah zan fad'a! zan fad'a!.
"Ke Asabe wai lafiyanki kuwa,? Ki ta shi daga barcin Asarar nan da kikeyi kullum ga shi duk in kin kwanta kin dunga ihu kenan kina zaki fad'a."
Wacce aka kira da Asabe ce ta ta shi daga kan wani yagwal-gwal d'in katifa tana murza ido duk ta had'a zufa kashirb'an, kallon tsohuwar da take tsaye a kanta ta yi fuskar ta cike da damuwa ta fara magana, "Inna ina cikin matsananciyar damuwa akan wani abu da na aikata shekara goma Sha takwas baya, Wanda ya zama dole in koma Kaduna domin bud'e abun da ke burne ko na samu salama, hak'ik'a na cuci kawata Tasalla kuma na ci amanar wata mata." tana kaiwa nan a zancen ta sai ta fashe da kuka.
*************************
KADUNA GARIN GWAMNA.
Gaba d'aya kotu fa ta rud'e hakan yasa dole aka dakata da shari'ar da ake sa ran yau za'a kammalata sai ga shi ta k'ara zuwa da wani rud'anin da dole sai an k'ara tsaida shari'an, haka dai Kotu ta watse kowa na fad'in albarkacin bakin shi, yayin da y'an