ya mutu, ki ɗaukeni tamkar mahaifiyarki duk abun da kikeso ki mun magana ki saki jikin ki nan tamkar gidan ku ne kinji ƴata."
Haka momy hafsat ta dunga kwantar ma da Aneesa hankali har tayi shiru, momy hafsat ta shiga toilet ta haɗa mata ruwan wanka ta kamata ta kaita ta ce mata tayi wanka ita kuma momy hafsat ta fito toilet ta rufo mata kofar taje drawer ta ɗauko mata kayan sawa ta ajiye mata akan gado ta fice, ba ta daɗe da fita ba ta dawo ɗauke da tray cike da abin karyawa, zama tayi a bakin gado tana jiran fitowar Aneeesa, fitowar Aneesa kenan daga wanka tana goge jikin ta da wani towel taje gaban mirrow ta fara shafa bayan ta gama ta sanya kayan ta ta ƙariso kusa da Momy Hafsat ta zauna ta jingina jikin ta a jikin Momy Hafsat ta buɗe baki da kyar ta ce, "momy ina jin yunwa."
Ta faɗa a shagwaɓe, riko hannun ta Momy tayi ta zaunar da ita a lallausan kafet ɗin da ke gefen gadon ita ma ta zauna ta jawo farantin abinci ta haɗa tea ta fara bata.
*************************
KADUNA
"Barrister Zainab ni ban taɓa ganin shari'a irin wannan ba a rayuwa ta, ni kin san ma mai yafi ban mamaki da zargi ni ina tunanin kamar fa Matar nan bata mutu ba, don ina zargin wani abu."
"What Barrister Khasheefa kin san me kike faɗa kuwa,? kin taɓa jin wanda ya mutu ya dawo, kin san hakan ba zai taɓa yuwuwa."
"Barrister Zainab kenan ni dai taimako ɗaya zaki mun game da shari'ar nan, kawo kunnenki ki ji, matsowa Barrister zainab tayi ta raɗa mata wani abu a kunne sannan ta miƙe ta ɗauki jakarta tayi mata sallama ta ce, "ƙawata bari in koma office akwai binciken da nake so in ƙarasa."
"Ok ƙawata sai mun haɗun kawai, karki samu damuwa zan baki haɗin kai ɗari bisa ɗari."
*************************
DUBAI
Alhaji Khaleelullah kallon Kaka kawai yakeyi hango irin kamar da takeyi da Mahaifiyar shi sai dai ita jikin tsufa da kuma wahalar rayuwa da ta maida kaka haka, sannan ba kowa zai iya gane kamar da sukeyi da Hassenat ba sai makusancin ta kuma wanda ya san ɗaya daga cikin su sosai, ƙarisawa yayi sai ya samu kanshi da duƙawa har ƙasa yana gaida kaka, cikin dauriya da kuma jin wani faɗuwar gaba da sarawa da kan ta yakeyi kaka ta amsa da kyar, yayi mata ya jiki ta ce da sauki, ɗagowa yayi ya zubama Mubasshir da yake tsugunne a ƙasa yana gaisheshi ido, ƙarisowa yayi ya ɗago shi ya rungumeshi a jikin shi ya ce ma kaka, "kaka wannan yaro naki yayi matuƙar kama da ni da kuma wani yarona wanda shine Babban ɗana, tun da na ɗora idona a kan shi naji ina matuƙar ƙaunar yaron a raina don Allah kaka ko zaku iya bani labarin ku a taƙaice.?
Alhaji Khaleelullah ya ƙarisa maganar yana mai ƙure kaka da ido, a zahiri kallon kaka yakeyi amma a baɗini kallon Mommah yakeyi a cikin fuskan kaka, Mubasshir ne yayi saurin faɗin, "mai zai hana mu baka labarin mu," ya faɗi haka ganin kaka taki cewa komai, da sauri duk suka waiga suna kallon Mubasshir Alhaji ya kalli mutanen da suke tare ya ce su fita su basu guri, bayan fitarsu ne ya kalli Mubasshir ya ce, "ɗana ina jin ka."
Kwashe labarin su tsaf yayi ya faɗa ma Alhaji iya abun da Kaka ta faɗa mai, sosai kaka take kuka ita kaɗai tasan kukan da takeyi, matsawa kusa da ita yayi ya ce ma kaka, "Kaka kiyi haƙuri insha Allah wahalar ku ta zo ƙarshe zan baku gurin zama sannan zan ƙara ma yaron ki albashi akan yadda ake biyan shi kuma nayi alƙawarin na ɗauki nauyin karatun shi har ya kammala."
Sosai Kaka tayi farin ciki sai gashi ta sauko har ƙasa zata duƙa da sauri Alhaji Khaleelullah ya ɗagota, nan ya ce a nemomai likitocin asibitin ana suna zuwa ya nemi sallama aka sallamesu yaje ya siyamusu magunguna suka hau mota ya nufi wani unguwa ce na marasa karfi sosai gidane ɗan dai dai mai kyau ya tsaya suma motocin securityn shi ma suka tsaya suka firfito dama kafin su iso ya tura wasu daga cikin securityn shi akan suje kasuwa su siyo duk abun da za'a buƙata, suna shiga cikin gidan ba jimawa wanda Alhaji ya aika suka dawo suna zuwa aka fara shirya gidan nan da na komai yayi tsaf ga kayan abinci da Alhaji ya jibge musu, sosai sukayi godiya, bayan tafiyar su Kaka ta shige ɗaki ta faɗa duniyar tunani.
*************************
ƘASAR CAMEROON
Babban birnin Yawundi, wani Mahaukaci ne yake zaune a gefen wata magudanar ruwa, can kamar an tsikareshi ya tashi ya ɗauko wani gwangwani ya ɗibi ruwar kwatar nan ya sha bayan ya gama sha ne ya shimfiɗa wani tsumma ya kwanta, duk in da ka kalli wannan mahaukaci sai ka tausayamai ga tsufa ga hauka, can ya tashi ya zauna ya fara jera hamma alamu yana jin yunwa, wata yarinya ce ba zata wuce shekara bakwai ba take tafiya tana waige-waige jikin ta sanye da unifoam ɗin makaranta riƙe take da Lunch basket na makaranta da yake ɗauke da kulan abinci da plask na silba na ruwan zafi, can ta hango mahaukacin zaune ya zabga tagumi cike da farin ciki ta nufeshi tana zuwa mahaukacin ya fara farin ciki yana murna da ganin ta, ta shi yayi ya fara karkaɗe gurin ya koma ya zauna ita ma ta zauna a gefen shi ta buɗe abincin ta debo ta fara bashi a baki ta tsiiyaya tea ɗin a murfin plask ɗin ta tana bashi yana karɓa yana cinyewa da sauri da sauri sai dariya take mai shiko yana ta wasa da beat ɗin kitson da ke kan yarinyar a haka har ya gama cin abincin ta curo ruwa a jakar ta ta bashi ya sha nan suka fara wasa, ɗauko text book ɗin ta tayi ta fara yin Home work ɗin da aka basu, tayi tayi tayi wani math ta kasa shiko mahaukacin na ta wasa abun shi, can ta ɗago ta miƙa mai book ɗin ta ce, "na kasa yi Didi yi mun."
Karɓan littafin yayi da pensil ɗin ya fara yi mata, abun gwanin mamaki kuma irin rubutun yarinyar yayi, ya miƙa mata murna tayi ta rungumeshi, dai dai isowar wasu mutane biyu gurin a mota suna faɗin, "kai gatanan fa a gurin wannan shegen tsohon mahaukacin nan faɗin driver motar, da sauri Suka fito baki ɗayan su suka nufo gurin da suke, mahaifiyar Amal na zuwa ta nufi gurin su ta fizgo Amal a jikin wannan mahaukaci ta ɗauketa da wata gigitacciyan Mari, hakan yasa Amal ta kwalla wani ƙara, take jikin mahaukacin nan na rawa ya miƙe ya rufe maman Amal da duka gabaɗaya mutanen gurin sun ƙasa kwatan ta, Amal ne ta zo ta ruƙe shi ta ce da ƙarfi, "Didi ka bari haka momy ne fa.!
Da sauri ya saki matar ya koma bayan Amal ya tsaya yana zazzare ido, sosai Maman Amal take tsine ma wannan mahaukacin ta ce sai ta kwaso mai ƴan sanda, tuni mutane suka taru a gurin kowa na faɗan albarkacin bakin shi, haka dai su Amal suka shige mota sukayi na gida an bar Momyn Amal da tsamin jiki sai da ta sha magani.
A daren ranar mahaukacin nan na barcin shi aka zo akai mai dukan kawo wuƙa an wayi garine aka ganshi jina jina mutanen gurin sukayi karo karo aka tafi da shi Asibiti.
A can gida kuwa Momyn Amal ne ta ja ma Amal kunne ta ce duk ranar da ta ƙara zuwa gurin mahaukacin nan sai ta yanke mata ƙafa, sosa Amal ke kuka tamkar zata shiɗe, tana fita ta ce ma driver ya kira mata daddyn ta da rawar jiki kuwa ya kirashi yana ɗauka Amal ta fashe da kuka.
"************************
NIGERIA KADUNA
Mugune ya kalli matar da take zaune a gefen gado ya ce mata, "Hajiya yanzu ya kike jin gefen cikin na ki, saboda yau likita zai zo ya warware miki ɗinkin na ki."
Yana gama maganar ya fice yaja ƙofar ya rufe da makulli, girgiza kai matar tayi ta koma ta kwanta.
Barrister Khasheefat ne take tafe a motar ta tana amsa waya take faɗin, "ina so ka bibiyan mun duk wani motsin shi da kiran da zaiyi, saboda akwai zargin da nakeyi a kan shi yanzu haka ina hanya zani gidan driver Hajiya Hindu ne."
Tana kammala wayar wani kiran ya ƙara shigowa wayarta, dauka tayi tana sauraren maganar da wanda yake kirata yake faɗa mata, "Barrister Hasashen ki ya zama gaskiya domin yanzu haka muna maƙabartan kuma mun tabbatar da hakan."
"Good Zainuddin amma kun tabbatar nan ɗin ne bakuyi missing ba.?
"Sosai ma kuwa Barrister karki manta da ni fa akayi jana'izan ta."
"Ok to shikenan ba damuwa in na dawo zan biyo in karɓi evidence ɗin da sauran abun da ya kamata mu tattauna domin yanzu haka ina hanyar zuwa Hayin ɗanmani ne, ok tom sai ka ji ni nagode sosai."
Murmushi Barrister Khasheeefa tayi, "tabbass tunanina da lissafina zai zo dai dai."
*************************
DUBAI
Yau an ci sa'a su Ayrah sun fito daga kulle kansu da sukayi, sai dai sun ƙi kula kowa.
Shigowar Baffah ya yi dai dai da fitowar Ummi daga kichin hannun ta riƙe da yankakkun fruit da sauri ta ƙariso ta ce ma Baffah, "well come Noorey, ɗan rungumarta Baffah yayi ya sumbaceta a goshi ya ce, "yauwa hayateey ya gidan ya yaran fatan duk kuna lafiya."
"Muna lafiya," kamo Baffah tayi ta zaunar da shi, taje ta ɗauko ruwa mai sanyi ta zuba mai a kofi sannan ta rage mai falmaran ɗin jikin shi da takalmi, sannan ta tashi taje ta haɗamai ruwan wanka ta dawo suka shige domin yin wanka.
Zaune suke da Kaka suna cin Abinci kwano ɗaya, can Mubasshir ya ɗago kai ya kalli kaka ya ce mata, "kaka ko hoton iyayena baki da shi to.?✍️✍️✍️
DON ALLAH KU SANI A ADDU'OIN KU ALLAH YA CIKAMUN BURINA NA ALHERI.
SHARE FISABILILLAH🙏
Zeeey yar mutan zazzau ce🥰
[10/5, 10:26 AM] Zzz Yar Mama: 😭
KISAN RUƊU😭
Wane yayi kisan?
TSARAWA DA RUBUTAWA
ZAINAB SALIHU YARIMA
(sarauniyar kanawa)
Ƴan Comment group Comment ɗin ku na tsumani tabbasss ina yinku son son🥰🥰🥰🥰ƴan kisan ruɗu fans group kuma comment ɗin ku na sani nishaɗi tabbass amma kun sako mun Aneeesa a gaba kunɗan raga mata🤣🤣🙄🙄eheee kuma iya wuya son so nake muku🥰🥰🥰🥰a cigaba da gashi suya sai ranar sallah.
*Leeyert Hijabs and Fancy Socks*
*At affordable price*
*Nation Wide Delivery*
*Hurry up and get yours here* 😊😊 *Location: Zaria*
*Email: www.raleeyaty@gmail.com*
*09132110903*
*akwae different design/style like : Egyptian hijabs, 2 cap hijabs,Rubber hijabs,Dubai Hijabs etc*
Ina ƴan kaasuwa masu so a tallata musu hajar su ku hanzarto ga dama ta samu, aka kuɗi ƙalilan, ku tuntuɓeni ta wannan number 08037420816 sai na jiku.
Page 16/17
BISSMILLAHIR RAHMANIR RAHEEM
CAMEROON
"Daddy Momy ne ta zaneni, kuma ta hanani zuwa gurin Didi na," ta ƙarisa maganar tana fashewa da kuka.
"Oh Amal rigima kiyi shiru ba wan da ya isa ya rabaki da Didin ki yau zan dawo insha Allah, ki share hawayenki kije makaranta in kin tashi ki je gurin Didi inna dawo ma da kaina zanje in ɗauko shi in dawo da shi gidan mu, kina so ai ko."?
"Eh daddy ina so mana sosai ma kuwa."
Miƙa ma driver wayar shi ta yi tana tsallen murna ta shige mota suka nufi makaranta, ana ta shi wurin Didi ta wuce yau bata ganshi ba sai tarkacen kayan haukan shi, sosai ta dunga neman shi har da kukan ta ita dai ta san Didi bai zuwa ko ina, amma yau gashi baya gurin, a cikin mutanen da ke gurin ne wani ya taso ya zo in da take zaune saboda gaba ɗaya ƴan gurin sun san Amal saboda zuwa gurin Didi da irin shakuwar da sukayi ya ce mata, "yarinya gara ma ki tashi ki tafi domin kuwa wanda kika zo nema ya Mutu jiya wasu suka zo suka mai dukan tsiya da daddare bayan mun kai shi Asibiti rai yayi halin sa, zaro ido Amal tayi ta kalli mutumin cikin kwaɓa fuska irin na sangartattun ƴaƴa ta ce mai, "kenan Didi ya tafi in da ba'a dawo kamar in da ƙanwata ta tafi, shikenan fa ba zan ƙara ganin shi ba kake nufi.?
"Sosai ma kuwa gara ki tashi ki tafi."
Bai gama rufe baki ba suka ga yarinya ta sulale a gurin ta faɗi tamkar matacciya.
*************************
DUBAI
"Mubasshiru kayi haƙuri akwai abun da nake jira zan baka labarin ko mu waye kuma har iyayen ka ma zan nuna maka ba wai hoton su ba, insha Allah."
"Shikenan kaka Allah ya nuna mana lokacin."
'Ameeen ɗan albarka."
"Hayateey yau na ga abun mamaki, wani yaro na gani ba zai wuce sa'an Ayrah ba ko zai girmeta bai fi da watanni ba, suna bala'in kama da Ameeenullah kama sosai na ƴan uwan ta ka, kuma tun da naga yaron nan naji wani irin ƙaunar yaron ya shiga raina tamkar jinina, kuma kin san asalin su daga ina suke,? to daga Nigeria suke, hakan yasa na fara tunanin anya ban da alaƙa na jini da yaron nan.?
"Hayateeey kenan kai har yanzu kana nan akan bakanka na cewa sai ka nemo dangin ku kai da Mommah Alhalin gamu mun isheku rayuwar duniya mahaifiina ya ɗaukeku tamkar dangi ɗaya, in har su ƴan uwan na ku na son ku zasu kawo hakane basu neme ku ba, karfa damuwar son ganin dangin ka yasa kaje ka ɗauko wanda zasu wargaza mana farin ciki mussaman ƴan Nigeria ba wanda ya kai su rashin gaskiya da cin amana.
"Ya isa haka! kin san dai ko ya suke kasata ce, kuma ina son ta kuma ina kishinta duk da ban taɓa zuwa ba har yau duk kasuwancina da tafiye tafiye ɗina, don dangin mu basu nememu ba hakan ba shi zai sa ni in ki nemansu ba, kuma insha Allah zamu haɗu da su a lokacin da ya dace domin ni ina ji a jikina, ba'a son ransu suka rasamu ba."
Baffah na gama maganar shi ya tashi ya fice ya bar Ummi zaune tana cika tana batsewa, saboda ita in da abun da ta tsana a duniya ta ji mijin ta na zancen dangin shi ko Nigeria tafi so suyi ta rayuwar su a haka.
Washegari Ayrah ce ta fito riƙe da jaka a hannun ta ranar ta riga kowa shiryawa saboda zasuje gidan su Mubasshir, hakan ba ƙaramin ba ƴan gidan mamaki yayi ba har Akheee Abdallah yake tsokanar ta, "to fa yau za'ayi ruwa da ƙanƙara, wai yau Ayrah ce ta riga kowa shiryawa, Anwar zo ka ga mutumiyar ka yau kamar tayi makuwa."
Abdallah ta ƙarisa maganar ya dariya ƙasa-ƙasa, kuka ta fara tana bubbuga ƙafar ta a ƙa sani tana faɗin, "Ummi kinga su Akheee suna zolayata ko."
"Ba dole su zolaye ki ba yau munga abun mamaki ne wanda bamu saba gani ba."
"Kai Hajjah har da ke a tsokanar mun Auta ko."
Cewar Baffah da shigowar shi falon kenan, Pappah ne shima ya sauko daga sama daga nan aka fara gaisuwa cikin farin ciki da ƙaunar juna kasancewar su family masu tsananin son junan su, haka suka dunguma zuwa teburin cin abinci kowa ya zauna, sai da sukayi addu'a sannan suka fara ci, bayan sun kammala ne kowa ya nufi hanyar makaranta yayin da Baffah da Ameeenullah suka nufi gurin aiki, kowa ya fita cikin farin ciki.
Mubasshir ne zaune a sit ɗin shi yana duba Assignment ɗin da aka bada da bai zo ba, shigowar ta aji kenan shi ta fara hangowa gurin shi ta nufa cike da fara'ar ta hannun ta riƙe niƙi-niƙi da kayayyaki ta ce mai, "nayi kewarka kwana biyu, ya mai jikin i hope taji sauki."
Ta ƙarisa maganar tana zama kusa da Mubasshir, matsawa yayi da sauri ya ƙara ɗaure fuska, cike da miskilanci ya ce mata, "ke tashi a nan gurin, sannan kina da matsala da mai jikin ne da zaki dunga tanbayata.!
Ya ƙarisa maganar cikin kauda kai tamkar wanda aka sa yayi maganar dole, kuma ba zaka ce shi ya yi maganar ba, ɓata fuska tayi cike da shagwaɓa ta ce mai, "Allah ya baka haƙuri, dama in ji ya ta ƙara ji ne fa, sannan ga wannan a kai mata, kallon da ya watsa mata ne sai da ƴan hanjin ta suka juya jikin ta na rawa ta tashi nan da nan idon ta ya kawo kwalla, domin duk surutun Ayrah tana da bala'in tsoro ga saurin kuka, juyawa tayi zata tafi da kayan ba zato taji ya ce mata ajiye an gode da sauri ta juyo taga bama ita yake kallo ba tamkar ba shi yayi maganar ba, haka ta ƙariso ta zo ta ajiye kayan jikin ta a sanyaye ta miƙa zata bar gurin ta ji ya ƙara ce mata i am sorry, da sauri ta ƙara waigowa ganin shi tayi yana rubutu kan shi a duƙe tamkar ba shi yayi maganar ba don dai kawai ta riga ta riƙe muryan shi ne a kwakkwalwar kan ta da zata ce ba shi yayi ba, tunanin yake yi meyasa yake yi ma yarinyar nan haka duk da yana jin ta tamkar ƴar uwar shi ta jini, tsaki ya ja to shi meye ma haɗin shi da ita, shi ya tsane mutum wanda ya cika shegen surutun tsiya, wata zuciyar kuma ta ce ai tana da kirki gashi tana kama da Kaka, kai haba ta ina ma taga kyan kaka, haka ya dunga tunani har malami ya shigo ajin na su.
Bayan tashi makaranta yau Abdallah ya zo ɗaukar ta saboda Anwar sun tafi wani Excussion, "yauwa Akheee kaga wanda ya shiga taxi ɗin can don Allah mu bishi kagani in nuna ma wani abu."
"Ayrah kina da matsala wallahi."
"Please Akheee."
Ta ƙarasa maganar tana dunkula hannu alamar roƙonshi.
*************************
NIGERIA KADUNA
Likita ne tsaye a kan matar yana goge mata gurin ciwon da ke gefen cikin ta in da da ka kalli gurin zaka san ɗin ki akayi, bayan ya gama kwance ɗinki ne ya fara dressing ɗin gurin har ya kammala ya basu magungunar da ya kamata ta sha ya musu bayani ya fice wata dake tsaye kusa da Namiji ta fita sai gata ɗauke da tray ɗin abinci da ruwa ta ajiye a gaban matar suka fice suka kulle kofar, girgiza kai matar ta yi ta ɗauki abincin ta fara ci.
"Barrister Zainab tafiya zuwa Taraba ya kamani yanzu haka ina hanya ina so zan je in ga yarinyar Hajiya Saudat domin akwai tanbayoyin da zan mata, shiyasa na kiraki in faɗa miki ki kulamun da office ɗina insha Allah jibi zan dawo."
"Ok karki damu ƙawata sai kin dawo."
Suna gama wayar Barrister Zainab ta tashi da sauri ta buɗe wani drawer ta ɗauko number waya ta fara sawa a wayar ta da sauri da sauri, bugu ɗaya yayi aka ɗauka, "hello eh ni ce Barrister Zainab ƙawar Barrister Khasheefat, eh yanzu haka ta kama hanyar zuwa Taraba don yanzu mukayi magana da ita, saboda haka kusan duk yadda zakuyi ku hana ta zuwa, don akwai matsala sosai in har ta isa zata iya fahimtar wani abu daga gurin yarinyar nan, domin ita ɗin gwanace a gurin bincike, ok tom ba damuwa sai na jika rankaya dade.✍️✍️✍️
SHARE FISABILILLAH
Zeeey yar mutan zazzau ce🥰🥰
[10/5, 10:28 AM] Zzz Yar Mama: 😭
KISAN RUƊU😭
Wa ya yi kisan?
TSARAWA DA RUBUTAWA
ZAINAB SALIHU YARIMA
(sarauniyar kanawa)
*Leeyert Hijabs and Fancy Socks*
*At affordable price*
*Nation Wide Delivery*
*Hurry up and get yours here* 😊😊 *Location: Zaria*
*Email: www.raleeyaty@gmail.com*
*09132110903*
*akwae different design/style like : Egyptian hijabs, 2 cap hijabs,Rubber hijabs,Dubai Hijabs etc*
Tabbass naga ruwan ƙauna a gareku masoya masu kirana da masu mun text message kuna mun ya jiki ina matuƙar godiya Allah ya saka da alheri ya bar zumunci son son iya wuya ana tare.🥰🥰🥰🥰
Page 19
BISSMILLAHIR RAHMANIR RAHEEM
*************************
"Umma ina buƙatar addu'ar ki agareni domin addu'ar ki shi ke sa nake ƙara samun nasarori a rayuwata, insha Allah yau na ke son zan tafi Taraba yin wani bincike amma jirgin karfe huɗu zan bi shiyasa na ce bari in zo in faɗa miki, ki mun addu'an da kika saba domin addu'an uwa karɓaɓɓene ga ƴaƴan ta."
Murmushi ƴar farar tsohuwar tayi ta ƙara gyara zaman farin medical glass ɗin da ke idon ta ta ce, "Khasheeefat ba zan taɓa gajiyawa da miki addu'a ba domin ke ɗin ɗiya ce tamkar da dubu a ko ina zan bigi ƙirji in nu naki a matsayin ƴata da na ke alfahari da ke a duniya, wacce na san ko bayan rai na na bar baya mai matuƙar anfani, duk da ba'a shedan yaran yanzu amma nikam ina shaidar ƴa ta na bata tarbiya na koyar da ita gaskiya da ruƙon amana na bata ilimin addini da na zamani, na haneki da cin hanci da rashawa ko cin haram duk ƙanƙantanshi, domin har na gama aikin gwammnati na a matsayin shugaban lauyoyi ban taɓa karɓan cin hanci ba, ina fatan ƴata ma zata kasance haka, Allah ya miki albarka ya kareki a duk in da kike ya baki miji nagari wanda zai riƙemun ke da amana domin duk duniya kece dangina, ban da kowa sai ke sai Allah."
Umma ta ƙarisa maganar tana mai zubar da kwalla, ta ke jikin Khasheefa yayi sanyi, ta rungume Umma tana mai share mata hawaye, "kiyi haƙuri Umma komai na duniya mai wucewa ce ya ci a ce kin cire wannan damuwar a ran ki."
Bayan wasu awanni Khasheefat ne ta fito riƙe akwatin ta tayi ma Umma sallama ta kama hanyar Airport, tana zuwa minti biyar jirgin su ya ɗaga sai Taraba.
*************************
CAMEROON
Sosai Daddyn Amal yake kallon Didi shi dai yasan fuskar nan, amma ya rasa ina ya san shi bayan Didi ya farfaɗo ya ga Amal, da sauri ya miƙe ya cire ƙarin ruwan jikin shi ya ɗauki Amal yana ta cillata sama yana dariya, ita ma dariyan ta ke yi, can ya sauke ta ƙasa suka fara rawa da fareti sosai Daddyn Amal da Nurses suke kallon su cike da burgewa da mamakin irin wannan shaƙuwa na su, doctor ne ya kalli daddyn Amal yace, "tun da ma mara lfiya ya ji sauki kawai za'a sallameshi, ga takardar magungunan shi kuje ku siya sannan wannan takarda biyan kuɗin gado ne kuje ku biya shikenan sai ku zo office a baku takardan sallama, da sauran wasu shawarwarin da ya kamata a dunga kiyayewa domin sanyi ya fara kamashi."
"Ok Doctor bari in je in biya in dawo, baby Amal zo muje a siyomai magani mu dawo."
"A'a Daddy ni ba zan tafi ba Didi ya ƙara guduwa ya barni ka je ka dawo sai mu ɗaukeshi mu tafi da shi gidan mu."
Girgiza kai Daddyn Amal yayi ya fita yana mamakin irin wannan shaƙuwa tsakanin Amal da wannan mahaukaci da basu haɗa komai da shi ba.
*************************
DUBAI
Da gudu Mubasshir ya ƙariso ya tare kaka da take shirin faɗuwa, tuni jikin Ayrah ya fara rawa duk ta ruɗe, ajiye kaka Mubasshir yayi a kan kujera ran shi a ɓace ya nufo Ayrah gadan gadan da gudu ta juya ta nufi mota tana zuwa ta ce ma Akheee Abdallah "mu tafi akheee da sauri