ba amma yanzu gani ai na daw..! Maganar ta shi ne ta maƙale lokacin da yayi tozali da Hajiya Hindu a gaban shi tamkar an jefota tana wani irin huci...✍️
SHARE FISABILILLAH🙏🙏
Zeey yar mutan zazzau ce🥰🥰
[10/5, 10:11 AM] Zzz Yar Mama: 😭
KISAN RUƊU😭
Wane yayi kisan?
TSARAWA DA RUBUTAWA
ZAINAB SALIHU YARIMA
(sarauniyar kanawa)
GODIYA
Dukkan godiya ta tabbata ga Allah ubangijin talikai mai kowa mai komai, wanda ya bani ikon kafa alƙalamina domin rubuta wannan labari, ya ubangiji ka haneni rubuta ba dai-dai ba, ka bani ikon rubuta abun da al'umma zasu anfana da shi.
SADAUKARWA
Littafin nan tun daga farkon shi har ƙarshen shi sadaukarwa ce wa kaina ni Zainab, kuma littafin free ne, sai dai duk wanda ya karanta ina buƙatar ya sani a addu'a Allah ya biyamun buƙatuna na alheri, ya yayemun damuwa ta.
GARGADI
Wannan labarin ƙirƙirarren labarine, ban yarda wani ko wata su juyamun labarina ko su ɗoramun a wata manhaja ba tare da izinina ba ko su siyar mu da labarina ba saboda haƙƙinane basirata ce saboda haka don Allah a kiyaye.
FATAN ALHERI ZUWA GAREKA
Yaya na mai ƙaramun ƙwarin gwiwa koda yaushe HUSSAINI M YERO(GARKUWAN UBAN GARIN ZAZZAU).
Page 3
BISSMILLAHIR RAHMANIR RAHEEM
Sosai Mutane suka cika police station ɗin, ƴan sanda sai tura mutane suke suna faɗin, "ya isa insha Allah akwai hujjoji da muke tattarawa da zaran mun kammala zamu miƙata kotu alkali ya yanke mata hukunci dai-dai da abun da ta aikata."
Da ƙyar police suka shawo kan mutane suka hakura don wasu ma sunƙi tafiya sai da suka fara watsa musu tiyagas suna harbin bindiga sannan mutane suka fara guduwa.
************************
WASHE GARI
"Hajiya ni ce lawyer ki wacce zan kareki saboda haka nake so ki faɗamun gaskiyar duk abun da ya faru, karki ɓoyemun komai."
Dago ido Hajiya tayi, idon ta yayi luhu luhu ga damuwa ga rashin barci, gaba ɗaya duk masifar hajiya amma tayi sanyi sosai, kamar ba ita ba ce wannan Hajiya ƴar gayu mai isa ga gadara da masifa da dukiya ta taka duk wanda take so, ta sha sawa ana tsare mutum akan laifin da bai taka kara ya karya ba, wai yau ita ce a cikin wannan hali, tabbass rayuwa juyi-juyi ce kwaɗo ya faɗa a ruwan zafi.
"Hajiya kina jina kuwa.?
Cewar Barister Khasheefa, firgigit Hajiya tayi ta fara girgiza kai tana faɗin, "Barister banƙi taki ba amma ki barni kawai a yanke mun hukuncin da ya dace, don in duk jikina bakine ba wanda zai yarda ba ni na kashe Hajiya Saudat ba."
"Hajiya kiyi haƙuri ki faɗamun me ya faru a dare, bai kamata ki sare haka ba, ni na miki alkawarin in dai har baki da hannu a kisar nan zan yi iya ƙoƙarina ganin na kwato miki hakkin ki insha Allah."
"Wallahi Tallahi Barister ba ni na kashe ta ba, duk masifa ta da bala'ina ba zan taba iya kashe mutum ba, ni dai abun da na sani kawai shine ranar da zata mutu da daddare ta zo ɗakina ta sameni in da ta gaidani ni kuma dama tun farko ba son ta nakeyi ba tun da ɗana ya aure ta na ɗauki karan tsana na ɗora mata a kullum tsakanina da ita mugayen furuci ne da hantara, sai dai bata taɓa daga kai da sunan ramawa ba kullum cikin mun biyayya take saboda ita macece mai haƙuri da kawaici ga uwa uba tarbiya, bayan ta gama gaidani duk da ban amsa ba ta nemi guri ta zauna ta ce mun dama ta zo ne muyi wata magana game da rabon gadon Mijin ta da za'ayi gobe akwai wani sirri da ya kamata ta faɗamun duk da Alhaji ya ce ko bayan ba ran shi kar in sake in tona wannan sirrin amma ya zama dole in bayyana hakan ko da Alhaji zai samu salama a cikin ƙabarin shi, har ta gama magana ban tanka mata ba ina rike da wayata ina latsawa haka ta tashi jiki ba kwari ta tafi, bayan tafiyar ta da kamar awa uku na kwanta nayi wani mummunar mafarki wai gashi Saudat na bina da wuƙa hakan yasa na tashi a firgice na nufi ɗakin ta zuwana ɗakin kenan na ga Saudat na juye juye da wuƙa a cikin ta gaba ɗaya na ruɗe kawai sai na riƙe wuƙar na zare dai dai da shigowar Aneesa, kuma yayi dai dai da mutuwar Saudat, wannan shine abun da ya faru ban da shi ban san komai ba game da mutuwar ta."
Kaka ta ƙarisa maganar tana zubar da hawaye tamkar famfo, nisawa Barister tayi ta ce, "karki damu Hajiya insha Allah na miki alkawari sai in da karfina ya ƙare sai an binciko wanda ya aikata kisar nan, na barki lafiya insha Allah in da wasu tanbayoyin ko wani abu da ya kullemun kai zan zo in sameki."
"Insha Allah ni kuma zan faɗa miki gaskiyan abun da na sani."
*************************
KWANA BAKWAI DA MUTUWAR HAJIYA SAUDAT.
Yau akayi addu'an bakwai in da daga ranar da akayi mutuwar zuwa ran da akai bakwai ɗin Aneeesa gaba ɗaya ta zabge ta fita hayyacin ta ko abinci sai ƙannin Momy sun sata a gaba take ci, kullum kuka shine aikin ta, yau ta kama bakwai bayan anyi cincirodan addu'an bakwai daga masalatai zuwa gidajen radio da makarantun islamiyu sai aka taru da ƴan uwan daddy da na momy suka ce to yanzu suna so a basu Aneesa su tafi da ita, su zauna a gurinsu tana ɗebe musu kewar ƴar uwar su, dangi daddy da kyar suka amince, sai maganar raba gado aka ce a bari har sai an ga yadda shari'a ta kaya kura ta lafa sai a raba, kowa ya amince da shawarar da aka yi, a ranar kowa ya watse aka rufe gidan, mutuwa kenan mai yankar ƙauna yau gashi tayi ma Aneesa yankar ƙauna ta raba ta da mahaifan ta, da ta waigo ta kalli gidan sai ta ƙara fashewa da kuka, haka Addah Mariya ta rungumeta a jikin ta tana lallashin ta.
SHARE FISABILILLAH
Zeey yar mutan zazzau ce🥰🥰
[10/5, 10:12 AM] Zzz Yar Mama: 😭
KISAN RUƊU😭
Wane ya yi kisan?
TSARAWA DA RUBUTAWA
ZAINAB SALIHU YARIMA
(sarauniyar kanawa)
GODIYA
Dukkan godiya ta tabbata ga Allah ubangijin talikai mai kowa mai komai, wanda ya bani ikon kafa alƙalamina domin rubuta wannan labari, ya ubangiji ka haneni rubuta ba dai-dai ba, ka bani ikon rubuta abun da al'umma zasu anfana da shi.
SADAUKARWA
Littafin nan tun daga farkon shi har ƙarshen shi sadaukarwa ce wa kaina ni Zainab, kuma littafin free ne, sai dai duk wanda ya karanta ina buƙatar ya sani a addu'a Allah ya biyamun buƙatuna na alheri, ya yayemun damuwa ta.
GARGADI
Wannan labarin ƙirƙirarren labarine, ban yarda wani ko wata su juyamun labarina ko su ɗoramun a wata manhaja ba tare da izinina ba ko su siyar mu da labarina ba saboda haƙƙinane basirata ce saboda haka don Allah a kiyaye.
FATAN ALHERI ZUWA GAREKA
Yaya na mai ƙaramun ƙwarin gwiwa koda yaushe HUSSAINI M YERO(GARKUWAN UBAN GARIN ZAZZAU).
Page 6
BISSMILLAHIR RAHMANIR RAHEEM
Wani irin kallo take jefa mai, gaba ɗaya ta fita hayyacin ta idon ta sun sauya kala, ji take tamkar zuciyar ta zai faɗo gani take tamkar mafarki takeyi wai yau ita ce Alhaji ya ƙara ma kishiya, kishiyar ma budurwa, aiko yau akwai ƙaramin yaƙi a gidan nan, juyawa tayi ta kalli yarinyar da Alhaji yake kira da Amarya kallon tsaf tai mata tun daga sama har ƙasa, kwata-kwata ma wannan yarinyar batayi kala da matan da zata iya zaman kishi da su ba.
Gefe guda kuma Alhaji Mailafiya ba in da jikin shi bai rawa duk da Ac da ke fallon bai hanashi haɗa zufa ba, da sauri ya ƙarasa kusa da Amaryan shi ya tare tsakanin ta da Hajiya Hindu don yasan tabbas komai zai iya faruwa, wani kallon baka da hankali ta ma Alhaji nan da nan ya ƙara duƙar da kai.
"Ki faɗa mun ko nawa kike so zan baki matuƙar zaki rabu mun da mijina domin mijina wa ni ƙaɗai aka halicce shi, kai kuma sannu ƙasurgumin munafuki maci amana har ni zaka ci amana ko, to wallahi tallahi sai ka san ka ci amanar Hindu, kuma na rantse da Allah sai ka saki matar nan yau ba sai gobe ba, ke kuma na baki zaɓi ko ki rabu mun da miji ta salama ko kuma ki rabu da shi ta tsiya shawara ya rage na ku."
Tana gama maganar ta ta juya hankali tashe ta fita.
"Alhaji dama kasan matar ka ba tasan zakayi aure ba ne ka auro ni,? gaskiya na tsorata da yanayin matar ka, kuma na tabbata zata iya yin komai a kan ka, don Allah ka bar da ni gidan nan kar ta illatani da abun da ke cikina."
Haseena ta ƙarisa maganar tana mai zubar da hawaye, gaba ɗaya sai jikin Alhaji mailafiya yayi sanyi ya rasa ma mai zai ce, fita yayi zuwa garden ɗin da ke cikin gidan ya zauna a cikin wasu kujeru yana jingina kan shi haɗi da lumshe idanun shi.
---------"Hello Hajiya Jamila kina ji na kuwa,? ina cikin tashin hankali wai tafiyar nan da nayi Alhaji kishiya yaje ya ƙaromin, don Allah in kina da lokaci ki fito kawo ki jirani zan zo in ɗaukeki mu tafi gurin boka zalumu ai ba haka mukayi da shi, ok tom gani nan zuwa, eh yanzun nan ma."
Ajiye wayar tayi ta nufi bedroom ɗin ta drower ta buɗe ta ɗebo kuɗi bandir ɗin ƴan dubu dubu ta zira a jaka ta ɗauko key ɗin mota da mayafi ta fice zuwa haraban gidan.
Tafiyar awa ɗaya sukayi sai gasu a bayan dutsen madarkaci can nesa suka ajiye motar ta su suka fara takawa da kafa har suka isa dai dai wani kogo da ke jikin dutsen da baya da baya suka shiga, wani tsamurarren mutum ne a zaune a kan wani buzu jikin shi ba kaya sai ganye da ya ɗaure a ƙugun shi.
"An gaida la'anannun bil'adama, an gaida wa'inda basu da raban rahman ubangiji, an gaida ɓatattu iyalan shaiɗan, nasan duk abun da ke tafe da ku, tabbass kinyi sake tun da har mijin ki ya riga yayi aure kuma har da rabo a tsakani, domin tana ɗauke da ciki na tsawon sati takwass ɗa namiji ne a cikin, sannan in har kika sake ɗan nan ya zo duniya sai ya fi ɗan da zaki haifa ɗaukaka, gashi mun duba munga dole sai ya zo duniyar, kuma mijin ki ba zai taɓa sakin ta ba, hanya ɗaya ce kawai mafitar ki shine za'a haukata ta tabi duniya, kuma za'a shafe ma kowa tunanin ta har abada, kin amince ko a'a.?
"Eh! eh! boka na amince ni in dai zata fita a rayuwar mijina kome za'ayi ayi kawai taje can takarata ta haifa cikin a yawon haukanta."
"Hahahahahaha tabbass ki cika la'ananniya tabbass aiki anyi an gama ku ta shi ku tafi tanbaɗaɗɗu watsattsu hahhhahah."
Jiki na rawa suka miƙe ta ajiye mai rafar kuɗi a wani ƙoƙon kan mutum suka fara tafiya da baya da baya suna rawa har suka fita daga kogon, suna fita gurin ya koma ya shafe tamkar ba kowa.
*************************
Washegari Haseena tana zaune a falon ta kawai ta ji tamkar ana kiranta haka ta tashi ta fita ba takalmi balle mayafi, lokacin kuma dai dai lokacin salar Azahar ne duk an shiga masallaci har ta fita daga gidan ba wanda ya ganta, tun daga wannan rana kowa ya mance da ita ba wanda ya ƙara tunawa da ita, sosai Hajiya Hindu ta ƙara miƙe ƙafa tana rainan cikin ta yau basu Dubai gobe basu Saudiya jibi suna ingila, haka suka dunga yawo har lokacin Haihuwar ta ya zo, suka tafi ƙasar India a can ta sankato ɗan ta kyakkyawa irin shi ɗaya da mahaifin shi, farin ciki tamkar ya kashe Alhaji Mailafiya washegari suka iso Nigeria kafin ka ce mai gida gabaɗaya ya cika da dangi da abokan arziki, haka Alhaji mailafiya ya dunga kyauta tamkar bai san zafin kuɗi ba.
Ranar suna ta zagayo aka sama yaro suna Mubasshir, tun daga lokacin Hajiya Hindu da Alhaji mailafiya suka ɗauki son duniya suka ɗorama yaronsu.
Shekaru na tafiya rayuwa tana shuɗewa muna ta cin kwanakinmu kwanci ta shi bai da wuya agurin ubangiji har gashi yau shekaran Mubasshir tara a duniya in da duk wani halayen shi na mahaifin shi ya ɗauko kuma shi yana matuƙar san dangin shi hakan yasa suma dangin suke son shi sosai, kuma hakan ba ƙaramin ƙona ma Hajiya Hindu rai yakeyi ba, don ita ba ta so yana hulɗa da dangin su, saboda duk dangin su mijin ta yafi kowa arziki, shiko Mubasshir bai son halin maman na shi ko kaɗan.
Zaune yake a tanƙasheshen falon su yana rubutu, sai ga mai kula da shi ta shigo tana faɗin, "ƙarami Alhaji ga tea ɗin da ka ce in haɗa ma.
Ɗagowar da zai yi kawai ya bige kofi da kanshi gaba ɗaya tea ɗin ya zubo mai a jiki dai dai Hajiya Hindu tana saukowa daga sama, wani salati ta saka haɗi da kwaso gudu.✍️
SHARE FISABILILLAH🙏
Zeey yar mutan zaxxau ce🥰🥰
[10/5, 10:12 AM] Zzz Yar Mama: 😭
KISAN RUƊU😭
Wa ya yi kisan?
TSARAWA DA RUBUTAWA
ZAINAB SALIHU YARIMA
(sarauniyar kanawa)
GODIYA
Dukkan godiya ta tabbata ga Allah ubangijin talikai mai kowa mai komai, wanda ya bani ikon kafa alƙalamina domin rubuta wannan labari, ya ubangiji ka haneni rubuta ba dai-dai ba, ka bani ikon rubuta abun da al'umma zasu anfana da shi.
SADAUKARWA
Littafin nan tun daga farkon shi har ƙarshen shi sadaukarwa ce wa kaina ni Zainab, kuma littafin free ne, sai dai duk wanda ya karanta ina buƙatar ya sani a addu'a Allah ya biyamun buƙatuna na alheri, ya yayemun damuwa ta.
GARGADI
Wannan labarin ƙirƙirarren labarine, ban yarda wani ko wata su juyamun labarina ko su ɗoramun a wata manhaja ba tare da izinina ba ko su siyar mu da labarina ba saboda haƙƙinane basirata ce saboda haka don Allah a kiyaye.
FATAN ALHERI ZUWA GAREKA
Yaya na mai ƙaramun ƙwarin gwiwa koda yaushe HUSSAINI M YERO(GARKUWAN UBAN GARIN ZAZZAU).
Page 7
BISSMILLAHIR RAHMANIR RAHEEM
Rufe ƴar tsohuwar tayi da duka ko ta ko ina tana faɗin cewa, "kashe mun yaro zakiyi da zaki ƙona shi da ruwan zafi.!
"Momy ya isa haka! haba momy wannan tsohuwar a haife ta haifeki amma ki rufe ta da duka, bafa da sanin ta bane, kuma ni na bige kofin nan, kuma tea ɗin ba wani zafi ai ya huce."
Yana ƙarasa maganar ya ƙarisa gurin tsohuwar da take durƙushe a ƙasa ta kasa ɗagowa saboda irin dukan da hajiya Hindu tayi mata ga kuma jikin tsufa, "Kaka ki tashi kinji ki yi haƙuri don Allah laifi na ne."
Ya ƙarisa maganar ya na ruƙo hannun tsohuwar ta miƙe da kyar suka nufi sashin su na masu aiki suna shiga ya ga Saudat tana zaune tana wasan ta hankalin ta kwance da gudu ya saki Kaka ya ƙarisa gurin Saudat ɗin yana faɗin Cutie wasa kikeyi, ki zo muje part ɗin mu muyi wasa da kayan wasa na kin ji.
"A'a ni ba zanje ba inna je momyn ka zata bigeni," yarinyar ta ƙarasa maganar ta cikin gwaranci, tsohuwar ne ta ƙariso ta ce ma Mubashir, "ƙaramin alhaji ka koma sashin ku kar momyn ka tayi ma faɗa, kuma kaga ma rubutu kakeyi ka je ka ƙarisa."
"A'a ni wasa zamuyi nida Cutie."
"Daddah ki barsu suyi wasan su ba'a raba yaro da yaro ai."
"Malam kasan halin uwan yaron nan yanzu sai ta zo tayi mana tijara ta kan hakan."
"Eh duk da haka ki kyalesu suyi wasan su.
************************
Shekaru sun ja rayuwa na daɗa tafiya, yayin da Alhaji mailafiya ya ɗauki Saudat tamkar ƴar shi saboda kawai son da Mubasshir yake mata, hakan yasa har makaranta tare aka sa su, gefe guda kuma hajiya Hindu ta ɗauki karan tsana ta ɗora ma Saudat da iyayen ta wanda asalin su ƴan Taraba ne zamane ya kawo su kaduna har alhaji ya ɗauki Baffan Saudat aiki ita kuma matar shi sai ya ce ta dunga kula da Mubasahir tun da ita hajiya Hindu ba ta cika zama bane ba ta Abuja bata kaduna, yaran Dadda shida ne duk mata ne, kuma suna aure ne a can Taraba dukansu suna auren masu hannu da shuni ne kuma ba abun da suka ragi iyayen su da shi, sai dai shi Baffa mutum ne wanda yake dogara da kan shi, bai jiran wani ya bashi hakan yasa ya ke aiki a gidan Alhaji mailafiya a matsayin driver, duk da ƴaƴan shi kwata kwata ba sa son wannan aikin, Saudat ita ce Auta a gurin su hakan ya sa yayyin ta da iyayen ta suke matuƙar son ta, Autan Baffa suke ce mata.
Kwanci ta shi ba wuya a gurin ubangiji yau gashi Mubasshir ya gama secondry school in da Saudat take aji ukun secondry, sosai soyayya ya shiga tsakanin Saudat da Mubasshir mutane da yawa ana ɗauka ƙanwar shi ce don komai tare sukeyi, hankalin Hajiaya Hindu yayi matuƙar ta shi har gurin boka zalumu ta koma ya tabbatar mata da baza'a taɓa iya raba Saudat da Mubasshir ba in dai aka rabasu tabbas zai iya mutuwa, tun daga lokacin Hajiya Hindu ta ƙara ninka tsanar da take ma Saudat hatta iyayen ta bata kyale ba, tuni ta matsa sai an kai Mubasahir ƙasar waje karatu ita a tunanin ta zata rabasu ta haka, bata san cewar tun bayan gama makaranatr Mubasshir Alhaji mailafiya ya nema mai Auren Saudat a gurin Baffa tuni Baffa ya bashi kuma, auren ya kasance ba wanda ya sani tsakanin Daddah da Hajiaya Hindu iyakan maza da dangin kawai suka sani sai shi Mubasshir ɗin don ko ita Saudat ɗin bata sani ba, sosai ake shirin tafiyan Mubasshir karatu ƙasar India in da zai karanci aikin likita a bangaren mata ranar da ana gobe zai tafi da daddare ya kira Saudat ɗakin shi bayan ta zauna ya fara magana, "cutie ki riƙemun amanar kan ki karki manta duk duniya baki da masoyi sama da ni, ba zan taɓa yafe ma kaina ba matuƙar kika kula wani, domin ke ɗin mallakina ne."
Tuni ta fashe da kuka ta rungume shi tana faɗin "Hamma na zuciyata taka ce mallakin ka ne komai dadewa duk runtsi duk wuya ba zan taɓa dena son ka ba."
"Rungumewar da Saudat tayi ma Mubasshir shine silar komai na kaddarar su, abun ka da lafiyayyen Namiji wanda yake kan gabar tashan balaga a lokacin tuni labari ya canza gaba ɗaya ya ɗauke wuta a tare wani bakon al'amari ya ziyarce su, take ya kasa haƙuri ya fara yawo da hannun shi a sassan jikin ta tuni suka fara aika ma juna sako da salo na irin wanda suka dade suna muradin juna, gaba ɗaya sun kasa control ɗin feelling ɗi da ke tattare da su, gaba ɗaya saudat ta gama narkewa a jikin shi inda tuni tufafin da ke jikin su sukayi ƙaura, haka suka cigaba da aika ma juna da sako mai narkar da zukatan masoya, tuni mai aikuwa ta auku a tsakanin su in da gaba ɗaya Saudat ta fita hayyacin ta tun tana kuka tana kaima Mubasshir doka har ta koma ajiyar zuciya, sai da komai ya lafa ne Mubasshir ya tuna da abun da ya aikata a ruɗe ya ɗauke ta ya nufi banɗaki da ita ba abun da takeyi sai binshi da kallo da kyar ta iya buɗe baki ta ce mai, "Hamma mai yasa ka aikata mun haka, ko a mafarki ban taɓa tunanin zaka iya karɓa abu mafi daraja a tare da ni ba tare da an ɗaura mana aure ba, yanzu fa zunubi muka aikata Allah na fushi da mu, kasan abun da ya mu'allim ya faɗamana lokacin da yake mana karatu ya ce wutan mazinata da banne wayyo Allah na kaicon mu ina tarbiyar da aka daɗee ana bamu."
Tana gama faɗan haka ta fashe da kuka ta fara kai ma Mubasshir duka in da shi kuma ya tsaya ya kasa hanata ko yin mata magana domin ji yakeyi in ya buɗe baki ya ce zaiyi magana kuka zai yi, haka dai ya dage ya mata wanka ya gasata da kyau yasa tayi wankar tsarki shima yayo wanka a daddafe saboda wani zazzaɓi da yake neman rufeshi, haka ya lallaɓa saudat ya rakata zuwa sashin su sai da ya tabbatar ta shiga ɗaki ba wanda ya ganta sannan yayi ajiyar zuciya ya koma bangaren shi, tun da ya kwanta juyi kawai yakeyi ya kasa barci ga zazzaɓi da ya lulluɓeshi da kyar ya tashi ya ɗauko first aid box ɗin shi ya dubo magani ya sha ya koma ya kudundune a kan gado da kyar barci ya ɗaukeshi cike da mafarci ƴar amaryar shi da fara more sadakin shi tun kafin a kai ko ina, gefe guda kuwa Saudat kwana tayi tana kuka da nadamar abun da ta aikata, gani take shikenan yanzu da kyar Hamman ya yarda ya aure ta don ta sha jin ƙawayenta na labari akan cewa in har kika yarda namiji ya sanki kafin aure to ba zai taɓa auren ki, shikenan ita yanzu ta kaɗe in ya ce ba zai aureta ba mai zata ce ma mijin da ta aura game da budurcin ta tana tuna haka sai ta ƙara fashewa da kuka, kafin safe tuni fuskarta ya kunbura yayi jajir abunka da farar fata ga zazzaɓi mai zafi.
WASHE GARI
Karfe shida na safe jirgin su Mubasshir ya daga sai India, in da kafin ya tafi ya shigo har sashin su Saudat tana jin muryan shi sai ta ƙara rufe ido tamkar mai barci haka ya daɗe yana tsaye yana ƙare mata kallo sannan ya ciro wani zoben dimon a aljihun shi ya kama hannunta ya sa mata ya duƙa ya sunbaceta a goshi ya fice da sauri yana share kwallar da ke idon shi, a airpot suka haɗu da momyn shi ta kammala mai komai suna isowa shi da daddyn shi aka fara kiran matafiya tuni jirgin su ya daga sai India.
*************************
BAYAN WATA UKU
Saudat ne take zaune ta zabga tagumi ta faɗa duniyar tunani, yau wata uku da tafiyar Hamman na ta amma bai kirata ba ko sau ɗaya, gashi tun bayan tafiyan shi da kwana biyu take fama da zazxaɓin dare kullum dare bata iya barci ga wani matsanancin felling da take fama da shi ta rasa gane kanta.
Dadda ne ta shigo ɗakin nata riƙe da plate ɗin abinci in da take bin autar na ta da kallon tausayi duk ta rame tayi zuru zuru tamkar wacce tayi shekara tana jinya ƙarisowa tayi ta zauna kusa da ƴar tata wacce tayi nisa cikin duniyar tunani ba ta ma san Daddah ta shigo ba sai da ta taɓe ta tayi firgigit.
"Haba Autan Baffa ki rage tunanin nan addu'a da fatan dawowa lafiya zaki ma yayan naki