cewa komai ba, a
sannan ne suka fara shaida dandazon abokan
gabar tasu suma su sarki Dujalu suka ankara da
tasu tahowar. Wohoho! Bala'i ba a sa masa
rana. ldan masife ta durfafo, to fe babu abin da
ya isa ya tsaide ita face yar uwarta masifa. Koda
sarki Dujalu ya dago kai ya hango su sarki
Maharaz sai ya kwarara uban ihu ya dakawa
162
TASKARNOVELS.COM.NG
dakarunsa tsawa yuna mai basu umarnin su tafi
su tari abokan gaba tun gabannin su Karaso
bakin tekum. Da jin wannan umarni sai
dakarun aljanu suka bude fuka- fukansu guka
nufi dandazon su Maharaz suna mugun ihu rike
da muggan makamai. Ihu nc wanda ka iya
sabautar da bil'adama su zauce domin gaba
dayan tsuntsayen da ke wajen ma wadanda ke
shawagi a sama sai suku kama fadowa kasa
matattu. Halittun da ke cikin ruwa kuwa sai gani
aka yi gawarwakinsu na tasowa sama saboda
masifar wennan inu na aljanu. Su kansu
jama'ar sarki Maharaz in ba don shi saki
Maharaz din ya taresu da Karfin sihirinsa ba da
nan take gaba dayansu za su kurmance ko su
haukace ko kuma duk su zube kasa matattu.
Lokacin da sarki Maharaz ya ga dakarun aljanu
na sarki Dujalu sun durfafo inda suke sai shima
ya baiwa nasa dakarun aljanun umamin su
taresu. Ai kuwa suma sai suka yi sama suka ruga
kansu tamkar an cilla kibiyoyi. Kafin kiftawar
ido rundunar biyu sun hade a sararin samaniya
sun kacame da fitinannen yaki wanda ya fi
gaban mai tunani ya tunano bare mai misali ya
misalta. Nan fa suma dakarum biladama da ke
kasa na kowanne 6angare suka falfalo da
163
TASKARNOVELS.COM.NG
matsannicin gudu ana kokarin a hadu. Kaico!
Inda ace mutum na nan a lokacin da wadannen
runduna biyu ta yunkura za a hadu ya ga irin
tsanonin yawansu sai ya y tsammemin cewa
gaba dayan mutanen duniya ne za su hade da
gaba dayan daboobin dunya.Ai kuwa bangare
biyun na haduwa a tsakiya aka ruguntsue da
azababban yaki mai dugunzumoa hankali da
tafasa kwakwalwa. Saboda jijigar da kasa tayi a
wann n r na sai da gaba dayan tekunan duniya
suka hausine guka kana ambahiyar ruwa
saboda tekun bahar Sufiya ne no babbar cibiya
na dukkanin tekunan duniya. Wohohol A
wannan rana an yi gumurzu, dauki ba dadi,
artabu, turnuku, ruguntsuni da fafatawa irin
wacce ba a taba yin kamanta ba a duniye, kuma
ba za a taba yi ba. Sai da aka kwana aka yini ana
ragargazar mazajen aljanu da na biladama aka
rinka asarar rayuka amma komai kwarin idon
mutum da iya kallon Kurillarsa bai isa ya iya
tantance 6angaren da ke samun nasara ba. A
duk sa'adda sarki Dujalu ya durfafi wurin sai dai
ka ga fili, duk inda ya sa gabansa sai ka ga maza
na zubcwa tamkar guguwar annoba ce ta fado
daga sama. Haka ma a 6angaren su sarki
Maharaz duk inda sadauki Inmal ya durfafa sai
164
TASKARNOVELS.COM.NG
dai ga yana banke mutane da kirjinsa,
hannaycnsa da kafafunsa suna zubewa kasa
tamkar ana sassabe a gona,an rasa wanda zai
iya tsayar da shi. Sarki Maharaz kuwa yana
amfani da karfin sihirinsa ne kawai domin duk
inda yai numi da sandarsa ta tsafi sai dai ka ga
kawunan bil'adama na gutsurewa suna faduwa
kasa. Sadauki Hibri ma ba a barshi a baya ba
domin shima ragargazar maza yake yana ta yin
ta'adi. A bangaren serki Dujalu ma akwai
wadansu zakwakuran mayakansa guda biyu
wadanda ake kira Matinu da Ratiju wadanda
summa sun addabi jama'ar sarki Maharaz, don
duk inda suka sa gabansu sai dai kaga maza na
ratattakewa. Lokacin da Mutinu da Ratiju suka
hango irin mummunar barnar da sarki Maharaz
da Hibru ke yiwa jama'arsu sai suka yi KUKAN
KURA suka ruga garesu aka ruguntsume da
wani masifaffen yakin. Matinu ya tari sarki
Maharaz shi kuwa Ratiju sai ya tari?
Hibru.Wani abin mamaki shi ne Matinu yana
takama da a karfin tsafi ne zalla ba wai
jaruntaka ba shi kuwa Ratiju tsagwaron
jarumtaka ce da shi kawai sai gashi duk su
biyun sun tari dai-dai da su don haka sai fadan
nasu ya zama abin sha'awa kuma abin tsorO
165
TASKARNOVELS.COM.NG
domin komai zai iya faruwa babu wanda yake
da tabbacin samun nasara akan abokim
gwaminsa saboda karfi yazo daya. Lokacin da
sarki Maharaz ya ga karfin sihirinsa ya zo daidai da na Matinu sai ya cika da tsananin
mamaki domin shi a zatonsa babu mai iya
karawa da shi a fagen yaki face sarki Dujalu
amma sai gashi daya daga cikiin yaran Dujalu ya
bashi mamaki. Abin da sarki Maharez bai sani
ba shi ne,Sarki Dujalu ya boiwa Matinu gabe
dayan Karfin sihirinsa ne yanzu yana wannan
yaki ne da zallar karfin damtsensa. Tab lallai
wani aiki sai cikakkun jarumai marasa tsoro,
duk da nima fa ina cikin jaruman tunda nine na
ke dauko maku rahoto. Zan ci gaba. Da fatan
mun wuni cikin koshin lafiya, sannan duk
wanda yake son complete zai iya tuntubata ta
wannan number 08138873799 kira ko
whatsapp. MAZAN JIYA Littafi na biyu 2 Part
K Na Abdulaziz Sani m gini Typing Abubakar
Saleh AlQuyraemey Kamar yadda Inmal ya
addabi dakarun Dujalu ya rinka ratsawa ta
cikinsa ta kowanne bangare yana ragargazarsu
haka shima sarki Dujalu ya addabi jama'ar sarki
Maharaz tamkar an auna barnar da suke yi tazo
dai-dai.Ana cikin haka ne sarki Dujalu ya hango
166
TASKARNOVELS.COM.NG
irin mummunar barnar da Inmal ke yi sai
hankalinsa ya dugunzuma kuma ya cika da
tsananin mamakin yadda Karamin yaro ya sami
irin wannan gagarumin karfi haka. Cikin
tsananin fusata sarki Maharaz ya tarwatsa
mazajen da ke gabansa ya falfala da gudun tsiya
tamkar ana shara da tsintsiya ya durfafi inda
Inmal yakc. Ai kuwa sai Inmal ya dago kai ya
hango tahowarsa. Nan take shima Inmal ya
tarwatsa mazajen da suka lullu6eshi ya falfala
da matsanaicin gudu yana banke mutane da
dawakai, rakuma da alfadarai da ke gabansa ya
nufi sarki Dujalu cikin dacin rai da kunar zuci
gami da mugun nufi domin su hadu. Ai kuwa
suna haduwa suka kacame da mugun yaki na
ban tsoro da ban al'ajabi. Tamkar jikinsu ba na
jini da tsoka bane haka suka rinka kaiwa juna
sara da suka cikin tsananin juriya, zafin nama
da bajinta. Sai gashi tsohon kashi ya hadu da
sabon kashi,naci da naci, zuciya da zuciya,
kowannensu yaki yake yi iya karfinsa tamkar ba
za su taba dainawa ba facc an tashi duniyar
gaba daya.Haka dai aka ci gaba da wannan
masifaffen yaki, har sai da rana ta fadi, gari ya
soma duhu. Kai saboda balain artabun da ake yi
a sama da kasa, wato aljanu nayi, mutane nayi
167
TASKARNOVELS.COM.NG
sai da wata irin gagarumar tsawa da walkiya
suka addabi kowa, tartsatsin wuta kuwa ya
rinka fantsama yana haddasa gobara har a cikin
tekun. Babu wani bangare da ke shirin ja da
baya a yakin. Mutane da aljanu suka rinka
zabga gumi, yunwa da kishirwa ta addabi kowa.
Gashi dai an zo da guzurin abincin kuma ga
ruwan teku ana gani amma sai ci da sha ya
gagari kowa saboda bala'in da ake ciki da
mugun tashin hankalin da ake fuskanta. Ba shiri
dan dole kowanne bangare suka busa kahon
janye yakin domin tsananin duhu da hayakin
wuta ya sa ba a shaida juna ha ta kai cewa
idanu sun rufe mnutane sun fara yakar yan
uwansu ma basu sani ba. Koda jin sautin kahon
na kowanne bangare sai duk aka ja da baya aka
daina yakin tamkar daukewar ruwan sama a
lokaci guda. A sannan ne matsafa suka samar da
hasken tsafi kowa ya iya ganin komai. Kaico!
Hakika yaki masifa.Da baiyanar wannan haske
sai ga gawarwakin mutane da aljanu zube a kas
ko ina rututu, babu inda mutum zai iya takawa
da kafarsa face ya taka gawa. Kai har akan
ruwan tekun gawarwaki ne barjik babu adadi
kuma ba kyan gani. Jini kuwa gashi nan yana ta
gudu da malala akan kasa har ya jirkita ruwan
168
TASKARNOVELS.COM.NG
tekun gaba daya yana neman rineshi. Komai
kallon Kurillar mutum bai isa ya iya tantance
6angaren da aka fi yiwa barna ba. A gaba dayan
mazajen da ke filin wannan yaki walau na
mutane ko na aljanu babu mahalukin da bashi
da raunuka a jikinsa,hatta manyan baraden
kuwa, wato su sarki Dujalu da su Inmal. Bayan
kOwanne bangare sun ja da baya nesa da juna
sai aka shiga aikin binne gawarwaki, masu kuka
nayi, masu bakin ciki nayi, kuma a sanann ne
kOwa ya rinka neman ruwan sha da abinci,
sannan kuma aka rinka sanya magani a raunika.
Masu karaya aka rinka gyarasu suna ihu bisa jin
radadi da zogin gyara. Manyan mazaje kuwa,
za ka ga sun yi shiru ko motsi basa yi. In ba don
albarkacin mata ba wadanda aka taho da su
wannan yaki da ba za a sami masu dawaniyar
kula da lafiyar mutane ba domin gaba dayan
mazajen babu wanda bai jigata ba ainun, wasu
ma kamar ba za su rayu ba wasu kuwa sun
gama zama nakasassu ba zama su iya ci gaba da
yaki ba. A 6angaren su sarki Maharaz
kuwa,bayan an kafa tantuna sai sarki Maharaz,
Hibru da Inmal suka taru a cikin tantin sarki
Maharaz kuyangi na sa musu magani a jikin
raunikan jikinsu, gimbiya Mulaifa ce da kanta
169
TASKARNOVELS.COM.NG
take sawa Inmal magani a jikinsa bata yarda
wata kuyanga ta taba shi ba. Bayan an tsaida
jinin da ke zuba a jikinsu kuma sun ci abinci
sun sha ruwa sun sami 'yar nutsuwa sai sarki
Maharaz ya ja dogon numfashi sannan ya dubi
sarkin yaki Hibru ya ce, "Ya kai abokina yanzu a
hangenka me kake ganin zai faru idan aka ci
gaba da wannan yaki?" Koda jin wannan
tambaya sai shima Hibru yai ajiyar zuciya
sannan ya dubi sarki Maharaz ya cc, "Ya
shugabana ni dai a ganina a Karshen yakin nan
RAGAS za a yi kowa da komai sai ya mutu, ka ga
ke nan babu bangaren da zai iya mallakar
wannan takobi ta Saiful Lujara da ke karkashin
tekun nan tun da gashi muna kallon tekun da
idanuwanmu amma shiga cikinta ma ya
gagaremu bare ayi laluben inda takobin take."
Koda jin wannan batu sai Inmal ya yi murmushi
saman ya dubi Hibru ya ce, "Haba ya Abbana
saboda me za ka yi waman batu, ai har abada
mutum ba ya fidda rai ga samun rabo muddin
yana numfashi a doron Kasa. Ni a rayuwata
zuciyata ba ta taba karaya ba bisa samun abin
da zuciyata ke so. Na yi imani da hakan dari
bisa dari saboda haka na Kudurce a raina idan
kowa da komai zai hallaka a bakin wamnan
170
TASKARNOVELS.COM.NG
tekun ya zamana saura ni kadai jal lallai sai na
lalubo takobin saiful Lujara a karkashin
wannan teku kodakuwa zan hallaka a kokarin
hakan. Ai rai ba a bakin komai yake ba muddin
akwai biyan bukata". Koda jin haka sai sarki
Maharaz ya yi murmushi ya cc, "Da kyau
jarumin jarumai, tauraron zamani, ka ci gaba da
jajirccwa bisa wannan Kuduri naka koda kuwa
gaba dayan jama'ata zamu karc ya zamana
saura kai kadai jal. Ka sani ccwa idan har ka
sami nasarar mallskar wannan takobi ta Saiful
Lujara sannan ka mallaki mashin Galilil Haras
da hular Lamsara ka ajiye abin tarihin da babu
wani mahalukin da ya ta6a ajiyewa a
duniya,kuma sai ka sami daukaka wacce babu
wanda zai samu. Ya kai abin alfaharina kuma
mafarkina na gobe kayi iya yinka don ganin ka
cimma buri ka sani cewa rayuwarmu gaba daya
a yanzu ta dogara da iyakar kokarinka domin
karfin sihirinmu da karfin damtsenmu ba za su
iya yin komai ba face kawai kara maka Kwarin
guiwa." Sa'adda sarki Maharaz ya zo nan a
zancensa sai Inmal ya cika da tsananin mamaki
ya dubeshi ya ce, "Ya shugabana ya ya ni da
nake yaro kankani a cikinku za ka ce rayuwarku
ta dogara a hannuna? Ka yi sani cewa ni kaina
171
TASKARNOVELS.COM.NG
na tsorata da al'amarin sarki Dujalu a lokacin
da muka fara fafata yaki ni da shi, domin ban
ta6a ganin mutum mai tsananin karfin dantse
kamar sa ba, gami da zafin nama. Sannan yana
da matukar juriya da naci fiye da yadda nake da
su. Duk da cewar zuciyata bata taba karaya ba
akan dukkan al'amari amma a wannan karon
akwai darsuwar kokwanto a cikinta". Sa'adda
sarki Maharaz yaji wamnan batu na Inmal sai ya
bushc da dariya sannan ya dubi 'yarsa Mulaifa
kuma ya dubi Inmal ya ce, "Ai kuwa idan har
nayi tsawon rai a waman yaki sadakin aurenka
na yata Mulaifa shi ne samun nasararka akan
dauko takobin Saiful Lujara a cikin Karkashin
wannan teku. Idan har ka kasa dauko wannan
takobi to har abada ba za ka auri 'yata ba".
Koda gama wannan jawabi sai sarki Maharaz ya
kishingida bisa shimfidar da yake zaune ya
lummshe idanunsa. Shima Hibru sai ya yi koyi
da abin da sarki Maharaz ya yi.Gimbiya Mulaifa
da Inmal kuwa sai suka Kurawa jumansu idanu
cikin tsananin tashin hankali da fargaba. Nan
take hawaye ya zubowa Mulaifa ta rungume
iNmal tana mai yi masa rada a kunne ta ce,
"Idan har kaunar da kake yi mini ta gaskiya ce
duk yadda za ka yi ka tabbatar da cewa ka
172
TASKARNOVELS.COM.NG
dauko wannan takobi ta Saiful Lujara. Idan
kuwa ka kasa bana tsammanin ccwa zan ci gaba
da rayuwa a duniya". Koda jin wannan batu sai
idanun Inmal suka zazzaro yaji hankalinsa ya yi
mummunan tashi, bai san sa'adda jikinsa ya
kama tsuma ba yaji kamar ya tashi ya ruga da
gudu ya dauki kahon yaki ya busa domin a ci
gaba da wannan masifaffen yaki. Wannan shi nc
abin da ya faru ga su Inmal bayan an fafata
azababben yaki tsakanin ruodunarsu da
rundunar sarki Dujalu a karo na farko a bakin
tekun bahar Sufiya. A CAN BANGAREN kuwa,
bayan sun binne na su su sarki Dujalu
gawarwakin kuma an kafa tantuna an duba
marasa lafiya kowa ya dawo cikin haiyacinsa
kuma an kafa tantuna sai sarki Dujalu ya
kadaita da yar uwarsa Hursiya a cikin tantinsa
inda ta rinka sa masa magani a jikin raunikan
da ke jikinsa. Koda ta ga raunikan sun kai guda
bakwai kuma duk masu zurfi ne, wasu ma sai
da ta dinke masa fatar sai zuciyarta ta karaya
bata san sa'adda ta fashe da kuka ba. Cikin
matukar mamaki sarki Dujalu ya dubi Hursiya
ya ce, "Ya ke 'yar uwata ina dalilin wannan kuka
naki?" Hursiya ta dago kai ta dubi sarki Dujalu
cikin tsananin damuwa ta ce, "Ya kai dan uwana
173
TASKARNOVELS.COM.NG
ka sani cewa a duniya bani da kowa face kai.
Zuciyata ta karaya bisa ganin wadannan
manyan raunika na jikinka har ina ganin cewa
abu ne mawuyaci mu sami nasarar wannan
yaki. Yanzu idan babu kai ya ya zan yi rayuwa a
diniya?" Sa'adda Hursiya ta zo nan a zancenta
sai sarki Dujalu ya kamu da tsananin tausayinta
har idanunsa suka ciko da Kwalla sannan ya ce,
Ya ke yar uwata kiyi sani cewa duk irin gumu da
bala'in da za a yi a wannan yaki a ba zan taba
mutuwa ba ammma bincike ya nuna mini cewa
zan shiga mugun yanayi kamar zan mutu da ni
da babban jarumi na cikin abokan gabarmu,
wato wannan yaro Inmal dan sadauki Hibru. Ni
da shi duk ba zamu mutu ba amma duk irin
yanayin da na shiga sai shima ya shiga.A cikin
binciken nawa na gani cewa mutum hudu ne
kacal za su tsira da rayuwarsu a wannan yaki
amma na kasa gano ko su waye, ragowar
mutum biyun bayan ni da Inmal. Abin da nake
so da ke shi ne, kafin a ci gaba da wannan yaki a
karo na biyu ki sulale ki bar wajen nan gaba
daya ki koma can nahiyarmu ki ci gaba da
mulkin Kasarmu ta Hawarul din in da muka
baro mata, yara da tsofaffi, domin idan har baki
koma ba gaba dayan jama'armu za su shafe a
174
TASKARNOVELS.COM.NG
doron kasa a manta damu har abada. Idan har
Inmal ya rigani dauko takobin Saiful Lujara, ki
sani cewa hadimina aljani Baizurul Aufan na can
a baya cikin dajin Saurul yana jiranki domin
tuntuni na shirya hakan.' Lallai za ku yi wannan
tafiya lafiya har ki isa gida babu wani tsautsayi
da zai sameki" Sa'adda sarki Dujalu ya zo nan a
zancensa sai Hursiya ta sake fashewa da
matsanaicin kuka kuma ta rungumeshi ta ce, "Ta
ya ya kake tsammanin zan iya tafiya na barka
anan ana wannan masifaffen yaki? Lallai ba
zanje ko ina ba in ba tare da kai ba, sai dai nima
ajalina ya riskeni anan din. Ai sadauki Hibru ya
yi bayanin gaskiya da ya ce rayuwa ba ta da
amfani idan babu masoyi. Ka sani cewa mulki
da dukiya ba za su taba haifar da kwanciyar
hankali ba a rayuwata muddin babu kai a kusa
da ni. Ka tuna cewa tun da na taso ban san
uwata ba kuma ban san ubana ba sai kai. Babu
wanda na shaku da shi a duniya sama da kai.
Babu irin jin dadin da baka bani ba a kullum
kana riritani baka son koda kuda ya sauka a
jikina. Waye zai iya yi mini irin wannan gata da
ka yi mini? Waye zai iya kare lafiyata kamar
yadda ka kare kuma waye zai soni kamar yadda
ka soni? Na ka-na ka ne har abada ba zan taba
175
TASKARNOVELS.COM.NG
samun madadinka ba. Ina tabbatar maka da
cewa idan zai zamo ni kadai ce na rayu a filin
yakin nan kuma na sami ikon mallakar takobin
Saiful Lujara, ba zan koma gida ba na ci gaba da
rayuwa sai dai na binne kaina a kusa da
kabarinka domin mutuwa ce kadai za ta iya
kawar mini da bakin cikin rashinka." Lokacin
da Hursiya tazo nana zancenta sai shima sarki
Dujalu ya fashe da matsanaicin kuka kuma ya
kankameta a kirjinsa yana mai cewa'Hakika
abin da ke shirin faruwa a gareni yana neman
ya zama dai-dai da yarda rayuwar sadauki
Shaddadu na birnin Kufa ta kasance." Koda jin
wannan batu sai Hursiya tayi wuf ta janye
jikinta daga cikin na sarki Dujalu suka fuskanci
juna sannan ta ce, "Mene na ya faru ga rayuwar
sadauki Shadaddu?". Sarki Dujalu ya sunkui da
kansa kas ya yi ajiyar zuciya sannan ya fara ba
ta labari kamar haka. AWANI ZAMANI can baya,
wanda ya zo dai dai da zamanin sadauki
Hantaru na bimin Kisra,an yi wani azzalumin
sarki a birnin Kufa wanda ake kira da suna
Lafaru ibini Hurdas. Sarki Lafaru ya mallaki
dukiya mai tsananin yawan gaske, kuma sai da
ya shekara arba'in a duniya bai ta6a yin aure ba
kuma bai taba yin rashin lafiya ba koda kuwa
176
TASKARNOVELS.COM.NG
ciwon kai na tsawon dakika daya. Sarki Lafaru
ya kasance sadaukin sadaukai mai dakawa maza
gumba a hannu domin a tarihin rayuwarsa ya
ziyarci yakoki guda dari da ashirin yana samun
nasara kuma ko karce jikinsa ba a ta6a yi ba a
wajen yaki.Saboda tsananin jarumtakarsa, zafin
namansa da kuma tsagwaron sa'a. A rayuwar
sarki Lafaru bai taba yin tsafi ba, kuma tsafi
baya cinsa, baya dogara da komai face
tsagwaron karfin damtse. A kasarsa gaba daya
ba a yin addini ko wanne iri, idan kuwa aka
kama mutum yana wani addini koda a 6oyene
sai an kashe shi. Sarki Lafaru na da wata
muguwar al'ada ta yiwa mata fyade, domin a
duk sa'adda ya ga kyakkyawar mace in dai ya yi
sha'awarta ko matar wa ce sai ya mangareta ta
sume sannan ya biya bukatarsa da ita. Daga
wannan rana sai ya sa a tsare wamnan mace
har tsawon wata shida sai an tabbatar da cewa
bata sami ciki da shi ba sanann zai sa a saketa.
Idan kuwa ta sami ciki ta ke zai sa a hallakata.
Dalili kuwa shi ne, ko kadan sarki Lafaru baya
son ya sami magaji a duniya saboda
jarumtakarsa ta gado ce iyaye da kakanni,
ma'ana babansa ya kasance, shima kakansa
haka yake kuma abin ya biyo salsala tun sarkin
177
TASKARNOVELS.COM.NG
kufa na farko. Lokacin da sarki Lafaru ya sami
tarihin wannan al'amari a cikin kundin tarihin
sarauta na gidansu sai ya kudurce a zuciyarsa
cewa shi ne zai zamo sarki na karshe mai
wannan baiwa ta jarumtaka da karfin lafiya,
don haka ba zai taba yarda ya haifi magajinsa
ba. Wani abin mamaki dangane da rayuwar
sarki Lafaru shi ne a duk shekara sau daya yake
sawa a nemo masa budurwa wacce babu
kamarta a fagen kyawu a kasarsa. Ana kawota
sai ya sumar da ita ya biya bukatarsa da ita.Sai
da ya shekara ashirin akan karagar mulki yana
wannan muguwar dabi'a. A cikin shekara ta
ashirin da daya ne al'amura suka zo da sauyi
domin a wannan shekarar ne aka kawo masa
wata tsaleliyar budurvwa mai suna Sharlis
wacce tsananin kyawunta ya fi gaban kwatance.
Da la'asar sakaliya sarki Lafaru na zaune a
fadarsa an kewayeshai ana fadanci sai ga
Sharlis an shigo da ita. Nan take gaba dayan
mutanen da ke fadar suka rude suka dimauce
bisa ganin tsananin kyawun Sharlis. Shi kansa
sarki Lafaru bai san sa'adda ya mike tsaye ba
jikinsa ya kama tsuma ya taka kafafunsa ya nufi
inda Sharlis ke tsaye sabanin yadda ya saba yi a
duk shekara, sai dai akai budur war har
178
TASKARNOVELS.COM.NG
gabansa. Sarki Lafaru ya iso daf da Sharlis ya
tsaya yana mai kura ma ta idanu a lokacin da
gaba dayan jikinta ke karkarwa saboda tsoro
kuma hawaye na zuba a idanunta. Sarki Lafaru
ya daga hannunsa da nufin ya make Sharlis
domin ta suma ya biya bukatarsa da ita amma
sai ya kasa dukanta. Al'amarin da ya matukar
baiwa kowa mamaki ke nan a fadar aka
mimmike tsaye ana al'ajabi. Koda ganin haka sai
kunya ta kama sarki Lafaru. Nan take ya yi
tsawa ga jama'a ya ce, "Kowa ya fice daga cikin
fadar". Cikin firgici jama'a suka fice da gudu ya
zamana saura su biyu kacal a cikin fadar. Nan
fa sarki Lafaru ya kamo Sharlis ya kwantar da
ita akan karagarsa ta mulki ya biya bukatarsa
da ita. Faruwar hakan ke da wuya sai yaji kansa
ya sara ya kama ciwo. Al'amarin da ya kama
matukar razanashi ke nan kuma ya harzuka.
Kawai sai ya zare takobi zai sare Sharlis. Bisa
mamaki sai ya ga ko gezau bata yi ba bare ta
firgita.Sharlis ta dubeshi a fusace ta ce'Mene ne
ya hanaka ka kasheni? Ai gwara ka kasheni
domin na huta da bakin cikin da ka dasa mini a
zuciyata. Ka yi sani cewa a lokacin da
dakarunka suka je kamoni a can kauyenmu na
Bairul sai da suka kashe iyayena da duk
179
TASKARNOVELS.COM.NG
mutanen gidanmu sannan suka bunkawa
gidanmu wuta kuma suka kwashe duk dukiyar
gidan saboda kawai mahaifina ya ce ba zai
bayar da ni ba. Ka sani cewa yau shekarata
goma sha takwas a duniya kuma tun da aka
haifeni ban taba fita ko ina ba daga cikin
gidanmu kai asalima ban taba ganin wani da
namiji ba face mahaifina domin babu maza a
gidanmu sai mata. A ranar da dakarunka suka
kawo mana farmaki ne na ga maza a rayuwata.
Kaine namijin farko da ya sanni 'ya mace kuma
kaine za ka zamo na karshe domin bokan
mahaifina ya tabbatar
mini da haka. Ya kai wannan sarki kayi sani
cewa tun da aka
haifeni mahaifina ke 6oyeni saboda tsoron kada
na fado
hannunka bisa muguwar dabi'arka da ka saba yi
akan
kyawawan mata, ashe shuka ya yi a idon
makwarwa.
Kuyangar mahaifina ce wacce ya aminta...
180
TASKARNOVELS.COM.NG
ashe shuka yayi a idon makwarwa domin
kuyangar mahaifinace wacce ya aminta da ita
fiye da kowa a duniya kuma itace wadda ta
reneni har na girma taci amanarsa saboda
kwadayin abin duniya ta labartawa dalkarunka
batuna.Tabbas bukatarta ta biya ta sami dukiya
mai yawan gaske ta siyar da mutuncina
gareka.To kasani cewa sakamakon wannan cin
zarafi dakayi mini daga yau burinka ya rushe
lallai sai na haifa maka magaji,daga yau sai
rayuwarka gaba daya ta sauya kai da samun
cikakkiyar lafiya har abada,jarumtakar dakake
takama da ita ta dakushe,duk dukiyar daka tara
ta zalunci sai ta kare,sai ya zamana cewa babu
mai fada aji a garin nan face ni Kafin sharlis ta
gama rufe bakinta tuni sarki lafaru ya kai mata
wawan sara da nufin ya cire mata kai.Bisa
mamaki sai yaga takobin ta wuce ta cikin jikinta
kamar ratsawar ba.
Gaskiya wannan zalunci yayi yawa kuma ni dai
bana goyon bayan sa.
MAZAN JIYA
181
TASKARNOVELS.COM.NG
Littafi na biyu 2
Part L
Na Abdulaziz Sani m gini
Typing Abubakar Saleh AlQuyraemey
Koda ganin haka sai sharlis ta bushe da dariya
sannan tace,"Ai tuni alkadarinka ya karye tun
sa'adda ka kasa sumar dani lokacin dazaka tara
dani.Bazaka iya kasheniba kuma bazaka iya
cutar daniba domin daga yau tsafi yafara tasiri
ajikinka.Abinda nakeso dakai kawai shine,ka
rufawa kanka asiri kabar komai a zuciyarka bisa
abinda yafaru yanzu tsakanina dakai.zaifi kyau
kasa a kebeni a gidan sarautar nan inda babu
mai ganina har izuwa lokacin dazan haife maka
danka.Idan ka bini kamar yadda nakeso zan iya
dawomaka da duk abinda karasa amma sai
bayan dana yagirma ya gajeka,idan kuwa kayi
mini taurin kai haka zan barka cikin takaici har
izuwa karshen rayuwarka kuma ina tabbatar
maka cewa bazaka maimaita shekarunka ba a
182
TASKARNOVELS.COM.NG
duniya.wato bazaka shekara tamanin ba a
duniya tunda yanzu ka cika arba'in daidai.Wannan shine furucina na karshe gareka
yanzu saika sanya akaini bangaren dazan zauna
acikin wannan gida naka. Lokacin da sharlis
tazo nan a jawabinta sai sarki lafaru ya fusata
ainun yarufeta da duka.Bisa mamaki saiyaji
ashe iska kawai yaketa duka kawai,gata dai
tsaye a gabansa tana tayi masa dariya amma ya
kasa taba jikinta.Koda ganin haka sai sarki
lafaru yakamu da tsananin bakin ciki yafashe da
kukan takaici.Babu abinda yafiyi masa ciwo face
ganin yadda 'ya mace ta gagareshi alhalin
manyan mazaje ma yazame musu GUGUWAR
ANNOBA,yazamo tamkar dodo a nahiyar gaba
daya har anayi masa kirarida KURA MAI
TARWATSA GARI!Yau gashi kura ta zama akuya
domin bazata iya tsorata kowaba.Sai da sarki
lafaru yadade a tsaye yana kukan takaici sannan
sharlis ta daka masa tsawa tace,"zakayi abinda
na umurceka dayine kokuwa sai na tara
fadawanka da jama'ar gari na tozartaka
agabansu kowa ya san cewa yanzu kai ba kura
bane akuyace. Koda jin haka sai sarki lafaru ya
kwalawa sarkin gida kira.Nan take sarkin gida
yashigo da gudu yafadi gaban sarki lafaru
183
TASKARNOVELS.COM.NG
yadubi sarkin gida yace"maza ka yiwa gimbiya
jagora izuwa bangaren nan daba'a taba
budeshiba
Sarki lafaru yace ina son yanzu-yanzu a bata
bayin dazasu dinga yimata hidima kuma kada
kowa ya kusanci inda take face kuyangin
nata,Koda jin wannan umarni sai sarkin gida ya
cika da tsananin mamaki bisa jin wannan sabon
umarni wanda ya saba da al'adar iyaye da
kakannin sarki. A tarihin gidan sarautar babu
wani sarki da ya taba ajiye mace acikin gidan sai
dai a wajen gidan sarautar amma yau sai gashi
sarki lafaru yakarya wannan ka'ida.Bisa wannan
daliline sarkin gida yatsaya nuku-nuku ya ki bin
umarni.Aikuwa sai sarki lafaru yadaka masa
tsawa,cikin rawar jiki sarkin gida yamike tsaye
zumbur yayiwa sharlis jagora izuwa cikin gidan
sarautar,sharlis ta waigo tayiwa sarki lafaru
murmushin mugunta.Nan take sarki lafaru
yafadi kasa yasake fashewa da kukan zuci don
kada hadiman gidan sujiyo sautin kukansa. Daga
wannan rana komai na rayuwar sarki lafaru ya
sauya,kuma al'amura suka sauya gaba daya
birnin ya zamana cewa matsafa sun sami yancin
kansu suna iya yin harkokinsu a ko'ina kuma
koyaushe sabanin da can da idan aka kamasu
184
TASKARNOVELS.COM.NG
ana kashesu.Mutane suka rinka yin addinai iriiri.a duk bayan kwana talatin
All Chapters
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 8 Chapter of 14