fita ba daga cikin gidansu domin dare da
rana babu abin da take so face ta Zauna a cikin
lambun gidansu tana kallon tsuntsaye da
kananan dabbobin daji. Idan ka ga ta fita daga
cikin wannan lambu sai idan lokacin barcinta
ya yi" Koda Sulbaini ya zo nan a ZAncensa sai ya
fiddo madubin tsafinsa ya ajiye a gabansu
99
TASKARNOVELS.COM.NG
waziri kuma ya shafeshi da hannun dama. Take
fuskar Mafira ta baiyana akan madubin da
kuma dukkan surar jikinta. Koda ganinta sai
waziri da sauran wadannan bokaye hudu suka
rude fiye da lokacin da suka ga Zarifa domin a
zahirin gaskiya Mafira ta fi Zarifa tsawo da
yalwal gashi. Boka Sulbaini ya ci gaba da bayani
ya ce, "ldan har sarkinmu ya sami nasarar auro
Mafira za shirya gasar kamo barewa tsakanin
zuri'ar makera da zuriar mafarauta na wannan
birni kamar yadda aka saba yi a kowacce
shekara domin a taya sarki murnar wannan
biki nasa. Da jin wannan batu sai waziri ya sake
rudewa ya rasa hukuncin da zai yanke akan
budurwar da sariki ya kamata ya zaba tsakanin
Zarifa da Mafira. Baban Rabbasu ya murtuke
fuskarsa zuciyarsa ta kama tafarfasa saboda
kishi da bakin ciki akan boka Sulbaini ya zo da
abin da ya zama kishiyar nasa. Lokacin da boka
Sulbaini ya ga baban Rabbasu na kumburekumbure da bata rai sai shima ya murtuke
fuskarsa kamar an aiko masa da sakon mutuwa,
har ma jikinsa ya kama tsuma, al'amarin da ya
firgita waziri ke nan da sauran wadannan
bokaye hudu domin sun san cewa idan
wadannan hamshakan bokaye biyu suka
100
TASKARNOVELS.COM.NG
kacame da fada ba karamin bala'i ne zai faru ba,
wata kila ma sai gidan gaba daya ya rushe ko
kuma ya kama da wuta. Koda waziri ya fahimci
haka sai ya mike zumbur ya dubi boka Sulbaini
da Baban Rabbasu ya ce, "Yanzu ina son gobe da
safe ku hallara a fada, domin kowannenku ya
nunawa sarki fuskar budurwar da ya zaba masa
in ya so sai sarki ya Zabi wacce ya fi So da
kansa." Koda jin haka sai boka Sulbaini da boka
Zaharu suka mike tsaye suka tafi ko sallama
babu. Kashe gari kuwa da sassafe sai ga boka
Sulbaini da boka Zaharu a fada, sun hallara.
Bayan sun zube kasa gaban sarki sun kwashi
gaisuwa sai waziri ya maida bayani bisa duk
abin da ya faru jiya a gidansa tsakanin sa da su
boka Zaharu. Sa'adda Sarki ya ji wanann bata'u
sai ya cika da matukar farin ciki yai shiru yana
tunani har tsawon 'yan dakiku. Daga can sai ya
yi gyaran murya ya ce, "Ya ku wadannan
manyan bokaye na birnina abin takama a
gareni, ku yi sani cewa bana bukatar ku nuna
mini fuskokin wadannan yan mata guda biyu.
Abin da nake so da ku shi ne, ku yi shiri ni da ku
da waziri da kuma wasu tsirararun dakaruna za
mu yi tafiya izuwa birnin Kisra. Ina son
kowannenku ya yi amfani da iya karfin sihirinsa
101
TASKARNOVELS.COM.NG
domin na sami nasarar auro budurwar da ya
za6a mini. Duk wanda ya bani sa'ar dana auri
Zabinsa lallai zan yi masa kyauta ta musamman
kuma Zan bashi girma na musamman a cikin
masarautata. Ina so ku gane cewa a cikinku bani
da gwani ko abin so sai wanda kokarinsa ya sa
na auro budurwar da ya zaba mini. Da wannan
furuci nake sallamarku domin ku je gida ku yi
duk shirin da ya kamata. Lallai i yanzu ZA mu
kasance masu jiranku anan fada". Koda Sarki
ya gama wannan jawabi sai ya mike tsaye ya
shiga cikin gidan. A sannan ne boka Zaharu da
boka Sulbaini suka kalli juna cikin harara a
lokacin da idanuwansu suka kada suka yi jawur
kamar an gasa dan buda a wuta. Daga can sai
kowannensu jikinsu ya kama tsuma kamar za su
kaure da fada har wani irin tiririn hayaki ne ke
fita daga cikin kunnuwansu, baminsa da
hancinsu. Koda ganin wannan al'amari sai
hankalin gaba ?ayan jama'ar da ke fadar ya
dugunzuma aka fara mimewa ana ficewa da
sauri. Shi kuwa waziri sai yai sauri ya kama
hannun boka Sulbaini ya jashi suka fice daga
cikin fadar yana jansa da hira cikin lafazi mai
taushi domin ya sanyaya masa zuciya. Nan take
waziri ya sa aka kawo keken dokinsa suka shiga
102
TASKARNOVELS.COM.NG
ciki tare suka ZAuna sannan aka ja suka tafi. Sai
da waziri ya kai boka Sulbaini har kofar gidansa
yana tausar zuciyarsa akan kada ya daka ta
boka Zaharu su yi fada tun da idan suka yi fada
sai sun dagula hankalin kowa a garin kuma sai
kwanciyar hankali da zaman lafiya ya yi
karanci. Sa'adda boko Sulbaini ya ji wannan
batu sai ya yi murmushi ya ce, "Ya kai waziri
kayi sani cewa kiyayyar da ke tsakanina da
boka Zaharu ta gado ce domin tasowa muka yi
muka ga iyayenmu da kakanninmu na yinta. Ina
tabbatar maka da cewa har abada ba zamu
daina wannan gaba ba face dayanmu ya ga
bayan ?aya ko kuma idan mun yi RAGAS. Bugu
da kari ka sani cewa ni daga zuri'ar Makera na
fito shi kuwa daga zuri'ar mafarauta yake, gabar
da ke tsakanin wannan Zuri'a biyu ta fi shekara
dari ana yinta kuma har duniya ta nade ba za
daina ba. Ni kam zan yi iya kokarina na ga cewa
ba mu yi rigima ba ni da shi a cikin wannan
birni namu face idan ta kure babu yadda zan yi"
Nan dai Waziri ya yiwa boka Sulbaini sallama ya
tafi gida. A daren Wannan rana babu wani
mahaluki da ya yi barci a cikin birnin Darul
Mahabul saboda wata irin tsawa mai firgitarwa
aka rinka kwadawa a Sararin samaniya har
103
TASKARNOVELS.COM.NG
tartsatsin wuta yana zubowa kasa. Duk wata
dabba mai rai ko shuka idan wannan tartsatsin
wuta ya fado ma ta, nan take take konewa
kurmus. Duk wani mai tsautsayi da ya sake ya
fito waje kuwaa wannan dare sunansa gawa.
Kai ba ma mutane ba hatta Aljanun da ke ZAune
a birnin saida suka yi hijirar dole a wannan
dare suka bar cikin garin suka koma can nesa
da gari cikin dazuzzuka basu dawo ba sai da
gari ya waye. Ba komai ne ya haddasa duk
wannan bala'i ba face fishin da su boka Sulbaini
suka yi da juna. Wato a cikin daren ne suka
rinka aikawa junansu da masifu iri- iri amma
maimakon masifar ta sauka a kansu sai ta rinka
kwamarzuwa da yar uwarta a sama cikin
sararin samaniya tana zubowa kasa kan mai
uwa da wabi. Kashe gari kuwa da safe, Sarki,
Waziri da Dakarun rakiya mutum dubu biyu
suka yi hawa cikin shigar yaki mai kwarjini da
ban sha'awa Sannan aka tanaji guzuri mai yawa
bisa kan rakumi dari biyu sanann aka kimtsa
wadansu kuyangi guda goma wadanda za su yi
wa sarki hidima a cikin tafiyar. Sarki bai fito ba
daga cikin gida sai da boka Sulbaini da boka
Zaharu suka iso.
MAZAN JIYA Littafi na biyu
2 Part G Na Abdulaziz Sani m gini Typing
104
TASKARNOVELS.COM.NG
Abubakar Saleh AlQuyraemey Ciki na sani
kuma na zo ne domin na taimakeki na biya miki
bukatarki". Koda jin wannan batu sai mamaki
ya kama Zarifa kuma ta cika da dumbin farin
ciki. Ba tareda fargabar komai ba Zarifa ta
zauna daf da boka Ardusa ta kura masa idanu
tana mai sauraron abinda zai fada ma ta. Boka
Ardusa yai murmushi gami da gyaran murya
sannan ya ce, "Ya ke ma'abociyar
kyawu,tauraruwar kyawawa, ina son ki sani
cewa na san baki da wani buri wanda ya fi ki
daukaka a duniya fiye da dukkan sauran mata,
kuma kina son kimallaki dukiyar da babu mai
kamarta. Tabbas idan kika yi abubuwan da zan
umarceki sai bukatarki tabiya. Yanzu nazo
gareki a sirrance lallai ki rike sirrin kada ki
kuskura ki gayawa wani wannan sirri na
zuwana wajenki koda bukatarki ta biyane idan
kuwa kika fadi sai dan da za ki haifa yazamo?
sanadin ajalinki". Koda jin haka sai Zarifa ta ja
dogon numfashi ta ce,'Ai kuwa ba zan taba
gayawa wani wannan sirri ba". Boka Ardusa ya
ce,' Na san kin yi mamakin yadda aka yi na
kawo kaina wajenki, to amma ba abin mamaki
bane idan kika yi la'akari da matsayina a yanzu
na bokan da yafi dukkan bokayen duniyar nan
105
TASKARNOVELS.COM.NG
karfin sihiri, amma kuma ina daga cikin
talakawan bokayen. Yau shekarata ashirin da
biyar ina bauta a karkashin wannan masarauta
ta birnin Kisra kuma akwai alkawari mai nauyi
tsakanina da dangin su Sarki Kusaidu cewar ba
zan daina bauta a garesu ba sai bayan shekara
hamsin, kin ga ke nan a gaba akwai shekaru
ashirin da biyar. A ka'idar wannan alkawari ban
isa na yiwa wani aiki ba face su idankuwa na
kuskura na yiwa wani aiki mutuwa zan yi domin
an yi alkawarin ne a cikin sihirin tsafi bisa
amincewar mahaifina da mahaifin sarki
Kusaidu. Yanzu na zo wajenki ba aiki zan yi
miki ba kawai zan gaya miki abubuwan da za ki
yi ne a kanki domin bukatarki ta biya, ladana a
wajenki abubiyu ne rak. Abu na farko,bayan
bukatarki ta biya za kibani kanki na sanki 'ya
mace domin a rayuwata nayi alkawarin ba zan
ta6a kwanciya da wata 'yamace ba sai wadda
take da tsananin kyawu nagaban kwatance,
kuma wadda ta kasance 'yar attajirin da babu
kamarsa a wannan nahiya gabadaya,gashi kuma
na yi dace na sameki. dace na sameki. Ladana
na biyu shi ne, za ki raba dukiyarki gida biyu ki
bani rabi bayan mutuwar 'yar uwarki Marifa
domin a sannan ne za a baki gaba dayan
106
TASKARNOVELS.COM.NG
dukiyar da mahaifinki ya bari. ldan kin amince
da wannan sharadi yanzu take zan gaya miki
abubuwan da za ki yi ki samu cikar burinki.
Sa'adda boka Ardusa ya zo nan a zancensa sai
hankalin Zarifa ya dugunzuma ainun ta rasa
abin da ke ma ta dadi a duniya ta mike tsaye
dagakan gadonta ta kama kaikawo da tunani
bisa hukuncin da ya kamata ta yanke akan ta
yarda dashi. Abin da ya fara fado ma ta a rai shi
ne ya za ayi ta bayar da wannan kyakkyawan
jiki na ta ga boka Ardusa tsohon da ya kai sa'an
ubanta alhalin tana takama da tsananin kyawun
da babu mai tabata face babban Basarake ko
mashahurin attajiri. Abu na biyu da ya fado ma
ta a rai shi ne, yaza a yi ta raba wannan dukiya
ta ta mai tsananin yawa ta baiwa wani rabi,
wacce ta ishi mutum rayuwa a duniya koda zai
shekara dubu Lokacin da boka Ardusa ya ga
Zarifa ta shiga halin rudewa da wasi-wasi sai ya
mike tsaye yadubeta ya ce, "Wai shin kin manta
ne da abin da bokaye da dama suka gaya miki
cewa babu mai iya biya miki bukatarki face ni.
Idan zuciyarki bata gamsu da al'amarina ba shi
ke nan ni zan yi tafiyata na barki da wayonki".
Koda jin haka sai Zarifa ta yi sauri ta shagaban
boka Ardusa ta ce, "Ya kai wannan sakin
107
TASKARNOVELS.COM.NG
bokaye ka yi sani cewa jikina da dukiyata ba
abakin komai suke ba muddin zan sami biyan
bukata Lallai na amince da dukka wanann
sharadi naka don haka kayi sauri ka sanar da ni
abubuwanda zan yi domin bukata ta biya".
Koda jin haka sai boka Ardusa ya yi murmushi
ya ce, "Kafin nayi miki bayanin abubuwan da za
ki yi kuma kika yi su kika sami nasara sannan
daga baya kika yi min butulci, ma'ana kika ki
cika mini alkawari, lallai zaki mutu a cikin
kwanaki talatin cicif bayan yin aurenki. Haka
kuma dole ne ki ci gaba da bani kanki a duk
sa'adda na bukace ki, idan kuwa kikaki asirinki
zai tonu kuma ki rasa abin da kika samu a
rayuwa. Yanzu sai ki saurareni da kyau domin
kiji duk abubuwan da zan gaya miki wadanda za
kiyi su bukatarki ta biya. Abu na farko da za ki
yi shi ne, dole ne ki fada mini tambayoyi guda
uku wadanda mahaifinki ya fada miki ki
tambayi masu neman aurenki gami da
amsoshinsu domin nasanar da sarki Kusaidu su
ya sami damar aurenki.Kin ga idan kika auri
sarki Kusaidu za ki sami damar da babu wata
mace da ta samu a duniya domin shi ne sarkin
da a tarihi sarakan duniya babu masarautar da
ta fi tashi tsohon tarihi da daukaka da karfin
108
TASKARNOVELS.COM.NG
mulki. Duk sarkin da ya yi zamaninsa har bayan
shudewarsa ba a mancewada shi da matansa
domin har a fadar sarkin Aljanun duniya ana
rubuta tarihinsu a ajiye, atakaice dai sai sunanki
ya bazu ko ina a duniya kinga ke nan ko ta nan
kin yiwa 'yar uwarki Marifa fintinkau. Abu na
biyu da za ki yi shi ne, ki samo kasko i yi fitsaria
cikinsa sannan ki diga digon jininki a ciki, sai ki
kira sunan 'yar uwarki sau uku ki tofa a ciki
sannan ki wanke idanunki da shi amma a ranar
da za a yi gasar neman aurenku. Dazarar 'yar
uwarki Marifa ta hada idanu da ke awannan
rana ba za ta yi wata goma sha uku ba aduniya
za ta mutu, idan kuwa baki hada idanu daita ba
to kece za ki mutu a cikin wata goma sha ukun.
Wannan shi ne iyakar abin da za ki yi. dukkan
burinki ya cika..Da wannan furuci nake miki
sallama sai mun hadu a ranar gasa." Kafin
Zarifa ta bude baki ta ce wani abu tuni boka
Ardusa ya yi girgiza ya bace 6at. Al'amarinda ya
matukar baiwa Zarifa mamaki ke anan domin
ya tafi ba tare da ta fada masa wannan
tambayoyi uku ba, wadanda zai sanar da sarki
Kusaidu gamida amsoshinsu. Zarifa ta koma
kan gadonta zuciyarta cike da sake-sake da
tunani bisa wannan abu da ya faru tsakaninta da
109
TASKARNOVELS.COM.NG
boka Ardusa. Ba wani abu take tunani da wasiwasi ba face hadarin da ke cikin aikin da boka
Ardusa ya sa ta. Koda takwanta akan gadonta
domin ta mike kafafunta tayibarci sai kawai
tayi arba da wata takarda akangadon. Al'amarin
da ya matukar ba ta tsoro damamaki ke nan
domin a saninta babu wata takarda& cikin
turakar ta ta koda guda daya kuma babu yadda
za a yi a shigo da wani abu ba tare da saninta
ba.Hannun Zarifa na karkarwa ta sa
hannayenta biyu ta dauki takardar wacce ta
kasance fara kal babu zanen komai a kanta.Koda
ta dubi takardar sai ga hoton fuskar boka
Ardusa ta baiyana akai yana mai murmushi a
gareta sannan ya ce"Maza kifadi wadannan
tambayoyi uku gami da amsoshinsu." Koda jin
haka sai Zarifa ta karanto tambayoyin gami da
amsoshinsu. Bisa mamaki sai Zarifa ta ga an
rubuta duk abin da ta fada akan wannan
takarda ba tare da ta ga mai rubutun ba ko
alkalamin da ke yin rubutun. Nan take takardar
ta6ace 6at tamkar bata taba wanzuwa ba a
wajen. Koda ganin haka sai Zarifa tayi
murmushi sannanta kwanta. Kwanciyarta ke da
wuya sai barci yasace ta,bata sani ba. Abin da
bata sani ba shi ne, kafin boka Ardusa ya bace
110
TASKARNOVELS.COM.NG
daga cikin turakar ya busa mata hodar banju ta
shaka, shi ya sa nan da nan barci yakamata in
ba don haka be da ba za ta iya barcin basaboda
tunanin gagarumin aikin da ke gabanta dakuma
sharadin da ke tsakaninta da boka Ardusa. DA
RANAR gasa tazo sai fadar birnin Kisra ta cika ta
batse da mutane duk inda mutum ya duba
gabas da yamma, kudu da arewa sai dai ya ga
kawunan bil'adama fululu babu masakar tsinke.
A tsakiyar fadar ne jaruman gasa suka taru
wadanda gaba dayansu sun kasance sarakai da
attajirai da ma manyan bokaye daga kowanne
bangare a kasashen da ke nahiyar. Sarki
Kusaidu da sarkin Darul Mahabul ne suka shigo
a karshe,bokayensu na take musu baya.
Maimakon su sarki Kusaidu su tafi izuwa inda
karagar mulki take sai suma suka shiga tsakiyar
fadar inda sauran jaruman gasar suke. Saboda
shakkar wanman gasa gaba dayan jaruman da
suka tsaya a tsakiyar fadar su goma ne kacal su
sarki Kusaidu ne suka zamo cikon na shabiyun.
Ba wani abu bane ya janyo hakan ba face
sauran jama'ar da suke son su shiga gasar
wadanda adadinsu ya fi dubu dari bokayensu
sun tabbatarmusu da cewa 6ata lokacinsu za su
yi ba za su iyacin nasara ba. Shi kuwa Sarkin
111
TASKARNOVELS.COM.NG
Darul Mahabul ana i gobe za ayi gasar ne ya
sami f kwarin guiwar fitow awanann gasar
bayan boka Sulbaini da boka Zaharu sun
hakura da kiyayyar da ke tsakaninsu sun hada
karfi da karfe sun binciki amsar tambayar da za
ayi masa ya iya amsawa. Kuma a binciken da
suka yi sai suka kasa gano tambayoyin da Zarifa
za ta yi sai na Marifa suka gani. Koda suka ga
tambayoyin sai suka kasa fahimtar amsoshinsu
har sai da suka tara gaba dayan hadiman
aljanunsu suka bazamasu ?zuwa cikin duniya
wajen tsofafin mutane da aljanu masana ilimin
tarihi. Da Kyar da sidin goshi aljanun suka samo
amsar tarabayoyi biyu. Amsar tambaya ta uku
kuwa ba a sameta ba sai a lokacim da suka fito
filin gasar sannan wani hadimin boka Sulbaimi
yazo da ita. Ai kuwa cikin gaggawa ya radawa
sarki amsar a kunnensa.Koda jin amsar sai
sarki ya cika da farin ciki kuma ya sami
nutsuwar shigar gasar. Jim kadan de shigar su
sarki Kusaidu cikin jaruman gasa sai ga Zarifa
da Marifa suka shigo cikin filin fadar.Kowacce
daga cikinsu ta caba ado na ban mamnaki kuma
na kure adaka,kuyanginta na biye da ita gaba da
baya suna watsa furanni masu kamshi akan
hanyar takawarta. Kamshin turaren da su
112
TASKARNOVELS.COM.NG
Zarifa suka sanya a jikinsu ne ya fara dukan
hancin kowa a fadar.Koda jama'a suka ji
wannan kamshi sai suka waigo suka dubi masu
shigowar,wohoho! Nan fa maza suka rude suka
dimauce, wasu suka kama dalalar da yawu,
basu sani ba wasu kuwa sai suka kama yanke
jiki suna faduwa kasa sumammu saboda sun ga
abin da kwakwalwarsu ba za ta iya dauka
ba.Masu Karfin hali ne suka rinka kuka suna
zubar de hawaye saboda takaici bisa sanin
cewa ba za su taba mallakar wadannan
kyawawan 'yan mata biyu. Tun kafn su Zarifa
su shigo cikin fadar sai Zarifa ta ga Marifa ta sha
lullu6i kuma ta sunku da kanta kas idanunta
basa kallon komai face kasa inda take takawa.
Alamarin da ya dugunzuma hankalin Zarifa ke
nan domin ta san cewa idan har basu hada ido
ba ita da Marifa kashinta ya bushe kuma ba za ta
taba cika burinta ba. Nan fa Zarifa ta fara
tunanin abin de za ta yi domin ta tabbatar cewa
ta hada idanu da Marifa. Inda matsalar take shi.
ne akwai tazara tsakaninta da Marifa kuma
akwai kuyangin Marifa a tsakaninsu. Koda
Zarifa ta ga fuskar Marifa a rufe take sai itama
ta janyo mayafinta tayi lullu6i kuma ta sunkui
da kanta kas amma zuciyarta sai bugawa take
113
TASKARNOVELS.COM.NG
da karfi cikin tsananin tsoro. Zarifa da Marifa
suka ci gaba da tafiya suka nufi inda aka
tanadar musu su zauna amma Zarifa na daga kai
tana satar kallon Marifa ko za ta ga itama ta
dago kai domin su hada idanu, amma bata dago
din ba. Zarifa na cikin wannan satar kallo ne ta
hada ido da boka Ardusa,nan take ya yi ma ta
nuni da idanunsa cewa lallai tayi duk iyakar
kokarinta ta hada idanu da Marifa kafin su isa
inda kujerun zamansu suke. Koda ganin
wannan inkiya sai hankalin Zarifa ya kara
dugunzuma ta shiga tunanin abin da za ta yi ya
zamana cewa lallai ta hada idanu da Marifa
kafin su kai mazauninsu. Sai da ya rage saura
baifi taku goma ba su isa mazaunin nasu
sannan dabara ta fado ma ta. Kawai sai tayi
kamar tayi tuntu6e, cikin shammace ta tafi tagataga ta fadi a gaban Marifa.Cikin mamaki da
kaduwa Marifa ta sunkuya ta dubi Zarifa suka
hada idanu. Suna hada idon sai Marifa taji wani
abu ya soketa a kirji tamker an tsira ma ta
mashi. Saura kiris tayi ihu kuma ta fadi kasa,
amma sai ta daure ta mike ta ci gaba da tafiya. A
sannan ne ta ga Zarifa ta dubeta tayi ma ta wani
irin murmushi na mugunta. Nan take Marifa ta
tsergu da cewa tabbas 'yar uwarta Zarifa tayi
114
TASKARNOVELS.COM.NG
ma ta wani mugun asirin. Zarifa da Marifa sun
dade suna yiwa junansu mugun jifa na sihiri
amma sihirin yaki ya yi tasiri akan kowannensu
kuma duk wajen bokan da suka je yana gaya
musu cewa sai dai su yi hakuri babu wani sihiri
da zai iya huda jikinsu a yanzu,domin
mahaifinsu ya yi musu tsari na musamman babu
wanda zai iya karya wannan sihirin face bokan
da ya yishi kuma ba wani bane face boka
Ardusa. Cikin tashin hankali da mamaki Marifa
ta karasa zuwa kan kujerar da aka tanadar ma
ta ta zauna,itama Zarifa sai taje ta zauna akan ta
ta kujerar fuskarta cike da murmushi,zuciyarta
ta cika makil da farin ciki. Zamansu ke da wuya
sai Alkalan gasar suka fara zartar da aikinsu
aka ware jaruman da ke son Marifa da wadanda
ke son Zarifa. A zaton sarki Kusaidu Sarkin
Darul Mahabul zai shiga cikin sahun masu son
Zarifa amma sai ya ga ya shiga cikin sahun
masu son Marifa. Nan take Sarki Kusaidu ya hau
kan layin masu son Zarife ya tsaya daga Kanhe.
Masu son Zarifa mutum bakwai ne, masu son
Marifa kuwa mutun uku ne,sarkin Darul
Mahabul ya zamo na hudunsu. Saboda haka
sarki Kusaidu ne na takwas a cikin sahun masu
son Zarifa. Be wani abu bane ya sa masoyan
115
TASKARNOVELS.COM.NG
Zarifa suka hi yawa ba face its Zurifa ta baiyana
fuskarta an gani tun kafin a fara gasar don haka
jaruman gasar sun dauka tafi 'yar uwarta kyau
sai da Marifa ta yaye lullubinta gaba daya aka
ga kyawunta de kyawun surar jikinta wanda har
yafi na Zarifa sannan aka dimauce. Shi kuwa
sarki Kusaidu ya zabi Zarifa ne saboda boka
Ardusa ya gaya masa cewa na ta tambayoyin
kadai ya sani amma bai san na Marifa ba.Wani
abin mamaki shi ne duk da cewa Marifa tafi
Zarifa kyau sai sarki Kusaidu yaji yafi son Zarifa
kuma nan take ya kamu da tsananin begenta a
Zuciyarsa. Ba tare da 6ata lokaci ba Alkalan
gasa suka umarci Zarifa da ta mike tsaye ta
karanto tambayoyinta guda uku ga jaruman
gasarta mutum takwas bisa sharadin cewa duk
wanda ya amsa tambayar dai-dai shi ne zai
zamo mijin da za ta aura. Cikin mumushi gami
da takama Zarifa ta mike tsaye ta fuskanci
miliyoyin jama'ar da ke cikin fadara lokacin da
aka yi tsit! Tamkar mutuwa ta gifta. Zarifa ta
bude baki cikin muryarta mai zaki tamkar
sarewa ta ce tambayoyina gareku masoyana su
ne kamar haka. Tambaya ta farko, a duniya
wane abu ne mafi tsananin karfi, karfin da yafi
na radadin mutuwa ciwo kuma yafi karfin
116
TASKARNOVELS.COM.NG
wadatacciyar lafiya dadi a zuciyar bil'adama da
aljanu? Tambaya ta biyu ita ce, "Wacce halittace
me rai tana ci kuma tana sha amma bata kashi
da fitsari?. Tambaya ta uku ita ce"Wane abu ne
wanda idan ya baiyana yana firgita mutane da
aljanu a duk inda suke, idan (kuma kishiyarsa
ya baiyana sai su sami nutsuwa da kwanciyar
hankali?" Sa'adda Zarifa ta gama fadin
wadannan. tambayoyi guda uku sai ta zauna
akan kujerarta takasa kunne tana sauraron
amsae da jarumin farkozai bayar.Gaba dayan
fadar sai ta sake yin tsit! Mutane suka shiga
zancen zuci suna maimaita tambayoyin uku a
cikin zukatansu suna kokarin amsawa. Nan take
jarumin farko ya mike tsaye yace'Amsar
tambaya ta farko ita ce,soyayya,domin karfin
soa cikin zuciya yafi komai tunda mutum ko
aljan zai iya sallama rayuwarsa don yamallaki
masoyinsa haka kuma idan mutum yamallaki
masoyinsa yana jin tsananin farin ciki
azuciyarsa fiye da a bashi komai na rayuwa.
Amsar tambaya ta biyu ita ce babu wata halitta
wacce tana ci kuma tana sha amma bata fitsari
da kashi face shuka, domin taki ne abincinta,
kuma ana zuba ma ta ruwa ta tsotse.Har abada
shuka ba ta fitar da takin da ta tsotse daga
117
TASKARNOVELS.COM.NG
jikinta kuma ba ta fitar da ruwan da ta tsotse a
matsayin bashi da amfani a jikinta. Game da
tambaya ta uku kuwa babu abin dake firgita
mutane da aljanu idan ya baiyana face yaki,
kishiyarsa kuwa shi ne zaman lafiya" Ya yin da
wannan jarumi na farko yazo nan ajawabinsa
sai Zarifa tayi murmushi ta ce"Ya kai wannan
masoyi nawa hakika kayi matukar kokari
domin ka amsa tambaya ta farko da ta biyu daidai amma tambaya ta uku ba daidai bace don
haka sai ka koma gefe daya ka baiwa wanda ke
bayanka wuri ya jarraba sa'arsa ko zai iya amsa
tambaya ta ukun". Koda jin haka sai wannan
jarumi ya kamu da tsananin bakin ciki, nan take
zuciyarsa ta buga ya Sulale Kasa matacce. Cikin
hanzari dakaru suke ruga suka dauke gawarsa
aka yi wajen fadar da shi. Jarumi na biyu ya
matso gaba a lokacin da gaba dayan jikinsa ya
kama karkarwa tamkar an tsamoshi a cikin
ruwan Kankara a lokacin da ake hunturun
sanyi. Jarumin ya yi shiru yana tunani da nazari
a cikin Kwakwalwarsa ya tuna irin nisan tafiyar
da ya sha daga garinsu zuwa wannan birni na
Kisra da kuma ya tuno da miliyoyin darhaman
da ya kashe kafin ya sami damar shiga wannan
gasa. Jarumin ya dada tunawa cewa shi fa dan
118
TASKARNOVELS.COM.NG
sarkin garinsu ne kuma shi kadai ne da namiji a
wajen ubansa mai gadon sarauta. Da ya
tabbatar da cewa bai san amsar wannan
tambaya ta ukun ba, sai ya koma gefe daya yana
mai nuna alamar cewa ya gaza. Nan take fadar
ta rude da ihu har wasu ma na jifansa suna
cewa ya yi abin kunya. Sai da Dakaru suka yi
tsawa sannan mutane suka daina jifan da ihun,
sannan jaruman gasar suka ci gaba da amsa
tambaya ta uku. Har aka zo kan jarumi na
bakwai ba a sami wanda ya amsa dai-dai ba.
Koda aka zo kan Sarki K s?idu s?i fadar ta sake
rudewa da shewa da tafi gami da jinjina.
Maroka suka kama yiwa sarki Kusaidu
kirari,makada kuwa suka kama buga ganguna
da tambura. Sai da Sarki y tsaya a inda zai
amsa tumbayar sannan fadar tayi tsit ya
zamana ba a jin komai face numfashin jama'a. A
wannan lokaci Zarifa ta murtuke fuskarta tana
kallon sarki K s?idu kuma ta kura masa idanu.
Dama haka ta rinka yi duk sa'adda masu gasar
ke amsa tambayoyin sai idan ta ga mutum ya
amsa dai-dai sannan tayi murmushi tayi
bayanin ko ya yi dai-dai. Sarki Kusaidu ya yi
gyaran murya sannan ya yi murmushi ya ce,
"Amsar tambayarki ta uku ita ce, "Haske da
119
TASKARNOVELS.COM.NG
duhu ba wai ya ki da zaman lafiya ba. Dalili
kuwa shi ne, komai jarumtakar mutum ko aljan
idan ya tsinci kansa a cikin matsanaicin duhu
wanda baya iya ganin komai dole ne hankalinsa
ya dugunzuma ya firgice domin bai san abin da
zai faru gareshi ba. Haka kuma idan haske ya
baiyana gareshi ya sami nutsuwa da kwanciyar
hankali tun da zai iya ganin kowacce irin masifa
da za ta tunkaroshi kuma zai yi tunanin hanyar
da zai bullowa masifar ya iya tararta." Koda
sarki Kusaidu yazo nan a zancensa sai fuskar
Zarifo ya fadada da murmaushi ta ce,' Tabbas
kai ne mijina domin ka amsa wannan tamabaya
dai-dai, haske da duhu su ne
All Chapters
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 5 Chapter of 14