shi ta tsinci
knta a cikin kogin soyayya tsundum, kuma ga
dukkan alamu wanda take so din shi baya sonta.
Abinda bata sani ba shine shim ya kamu da
tsananin kaunarta amman daya tuno da
alkawarin da ya daukar wa mahaifiyarsa sai
yaga ya zama dole ya cire sonta dgaa cikin
zuciyarsa.
Sai da suka shafe sa'a bakwai suna tafiya a cikin
sararin samaniya bisa aljani Marhabul Zaurus
sannnan suka iso birni Farisa, take kuwa suka
sauka a cikin wani kayataccen gidan sarauta.
Koda ganin wannan gidab sarautar sai su sarki
Lafaru suka cika da tsananin mamaki, suka
kama kalle kalle da waige waige tamkar
mutanen kauye domin ko a labari basu taba jin
ginin mai girma da kawatuwa kamar wannan
ba, ginin fadar gaba daya anyishine da tubalun
lu'u lu'u, ba a dora komai ba, kuma duk inda
280
TASKARNOVELS.COM.NG
mutum zai taka a cikin gidan sai dai ya taka
yakutu babu inda wani wuri mai kasa, komai ka
gani na amfani hatta kayan dawakai da zinare
aka yi su, duk inda mutum ya duba a cikin gidan
sai dai yaga barori da kuyangi sunata kai kawo
da hidima a cikin gidan, kafin su sarki Lafaru su
sauka daga kan aljani Marhabul Zaurus sai
kawai suka hango sarkin farisa da yar uwarsa
Gimbiya Zarina sun taho garesu cikin tsala ado
na gaban kwatance, suna sanye da wadansu
kurayen tufafi iri daya, abinda ya fara daure wa
su jarumi Imran kai shine ganin yadda sarkin
Farisa da yar uwarsa Gimbiya Zarina suke
matukar kama da juna, inba dan Sarkin Farisa
ya kasance d namiji ba da sai mutum yace
hasana d husaina ne. Sarkin Farisa da gimbiya
Zarina suka tunkaro inda su jarumi Imran suke
fuskokinsu cike da annuri suna t murmushi
kamar wadnda aka yiwa bushara da samun
mulkin duniya. Tsananin kyawun Gimbiya
Zarina ne ya fara dimauta Sarki Lafaru, yayi
ajiyar zuciya sannan ya cw a cikin zuciyarsa, Oh
hakika duniya da fadi take, kuma abin cikinta
yawa gareshi, tabbas wanda baiyi tafiya ba bai
more kallo ba, unda muka fara wannan tafiya
duk inda muka riski mace mai kyau da mun
281
TASKARNOVELS.COM.NG
kara gaba sai mug wacce ta fita kyau, to wai shin
ya kyawun Gimbiya Ramlatus siyam zai kasance
akan kyawun wadannan mata da nake haduwa
da su yanzu, ashe kuwa idan har na auri
Gimbiya Ramlatus siyam nasan sai nafi kowa
samun matsayi a duniya, a daidai lokacin da
sarki Lafaru ke wannan zancen zuci ne su
gimbiya zarina suka iso daf da su. Koda Zarina
ta hada ido da jarumi Imran sai taji zuciyarta ta
buga da karfi saboda kwarjininsa da kuma
kyawunsa, dan hkaa sai ta yi sauri ta kauda
kanta ga barin kallonsa, ta dubi jaruma Shadira
da Lumaira matar Sadauki Haiman,bisa mamaki
sai ta ji ta kamu da kishi akansu, duk da cewar
tasan ta fisu kyau nesa ba kusa ba, cikin
matukar farin ciki Zarina ta yi wa boka Muzafar
barka da zuwa ta ce Lale marhabun da babban
boka mai share mana hawayenmu kayi sani
cewa tun jiya nida dan uwana ba mu rintsa ba,
saboda farin ciki da dokin zuwanku bisa
wannan gagarumar tafiya dake gabanmu, dan
haka yanzu mun gama kintsawa ssi tafiya kawai.
Cikin murmushi boka Muzafar ya dubi Gimbiya
Zarina ya ce an gaisheki ya mai ilimin daji, kece
kika san dabbobin daji da sharrinsu, kuma kece
sarauniyar mafarauta ta duniya, ina mai sanar
282
TASKARNOVELS.COM.NG
dake cewa abokan tafiya sun hadu, saura
mutum daya jal kuma ba wani bane face
sadauki Shaharan bn Lauwal na birnin
Hairussalas shine ma'abocin gudu, yanzu sai
kuyi harama mu tafi domin isa can birnin
Hairussalas kafin dare yayi mana.
Da jin haka sai kowa ya hau kan aljani Marhabul
Zaurus ya zauna shikuwa sai ya bude fukafukansa yayi sama yana mai tsala azababben
gudu cikin gajimare yana keta giza-gizai tamkar
gudun tauraruwa mai wutsiya. Aikuwa a cikin
sa'a uku kacal suka iso birnin Hairussalas suka
tsaya a kofar gidan sadauki Shaharan, da
saukarsarsu sai suka ga sadauki Shaharan a
gaban dokinsa wanda yake gasar gudu da shi,
dokin na durkushe bisa kafafunsa. Koda sadauki
Shaharan yayi arba da su boka Muzafar sai ya
cika da tsananin farin ciki, ya ruga da sauri ya
tarbi boka Muzafar suka rungume juna,
Shaharan ya janye jikinsa daga jikin na boka
Muzafar sannan ya dubi su sarki Lafaru dake
zaune a bisa aljani Marhabul Zaurus nan take
kuma ya ha?a idanu da Gimbiya Zarina, kawai
sai yaji zuciyarsa ta buga da karfi, har bai san
sa'ad da yayi mata murmushi ba, ita kuwa sai ta
hade fuska ta kauda kai ga barin kallonsa, ta
283
TASKARNOVELS.COM.NG
dubi jarumi Imran shima sai ya hade mata fuska
kuma ya sunkuyar da kansa kasa.
Shaharan ya juyo ya fuskanci boka Muzafar ya
ce ga dukkan alamu naga abokan tafiya sun
gama haduwa?
Boka Muzafar yayi murmushi ya ce kwarai
kuwa daman kai kadaine ka rage dan haka sai
ka taho mu tafi.
Shaharan ya dubi boka Muzafar cikin damuwa
Sannan yayi nuni izuwa dokinsa ya ce yanzu ya
zamu yi da wannan doki nawa har mu dauke shi
mu dirashi akan wannan aljanin?
Koda jin wannan tambaya sai boka Muzafar
yayi murmushi ba tare da yakara cewa komai
ba, sai kawai ya nufi inda dokin ya ke da zuwa
sai ya sa hannayensa biyu ya ciccibo dokin
tamkar ya dauki buhun harawa, yaje ya dorashi
akan aljani Marhabul Zaurus sannan shima ya
zauna.
Koda ganin irin sadaukantaka ta boka Muzafar
sai kow ya cika da mamaki, bisa ganin cewa yayi
amfani ne da tsagwaron karfin damtsensa ba
wai karfin sihirinsa ba, ba tare da bata lokaci ba
284
TASKARNOVELS.COM.NG
shima sadauki Shaharan ya zauna akan aljani
Marhabul Zaurus. Nan take ya sake bude fukafukansa ya tashi sama ya luluka a cikin gajimare,
babu abinda zai baiwa mutum mamaki face
yadda aljanin ya iya dauke mutane har kusan
goma sha daya da kuma doki guda daya akansa,
amman kamar bai dauki komai ba yake jin
kansa, saboda girmansa da kuma karfin
damtsensa, sai da suka shafe sa'a hudu suna
tafiya a sararin samaniya dayansu baice uffan
ba, a wannan lokacin Lumaira ta dora kanta a
saman cinyar mijinta Sadauki Haiman suna yi
wa junansu wasa da gashin kai, Shadira na
rungume da dan uwanta yaro Masnur yana
shinfide a bisa cinyarta ta kura masa idanu
kawai tana murmushi, shikuwa jarumi imran
yana kwance akan kafadar mahaifiyarsa tana
gyara masa dogon gashin kansa tana daure
masa a baya sabida yawansa da kuma santsinsa.
Gimbiya Zarina da dan uwanta Sarkin Farisa
kuwa sun lulluba a cikin mayafi guda
sakamakon iskar dake kada suturun jikinsu
marasa nauyi kamar ana hura balo. Shiko
sadauki Shaharan yana zaune daf da dokinsa
yana shafa wuyan dokin kuma yana satar kallon
285
TASKARNOVELS.COM.NG
Gimbiya Zarina, da yaga zata juyo su hada ido
sai yayi saurin kawar da idanunsa.
Ana cikin wannan hali ne kwatsam sai hadari ya
taso aka fara wata irin iska mai sanyi sosai
gamk da walkiya da tsawa mai furgitarwa,
wacce tasa yaro Masnur ya farka a firgice.
Koda ganin haka sai boka Muzafar ace da aljani
Marhabul Zaurus yayi masu rumfa. Nan take
aljani Marhabul Zaurus ya lullube su da biyu
Daga cikin fuka-fukansa tamakar an kifa kwarya
akansu, nan take suka daina jin sanyi kuma suka
tsira daga barazanar sakkowar ruwan sama da
ta tsawa wacce ka iya masu lahani, duk da cewa
Aljani Marhabul Zaurus ya kifesu da fukafukansa basu tsinci kansu a cikin duhu ba,
domin boka Muzafar ya samar masu da haske ta
hanyar tsafi. Sarki Lafaru na zaune gefe daya
kusa da boka Muzafar ya yi tagumi yana mai
tunani gami da zulumi.
Koda boka Muzafar ya ganshi a cikin wannan
hali sai ta kamu da tsananin tausayinsa saboda
haka sia ya matso kusa da shi ya zauna suka
fuskanci juna, boka Muzafar ya dubi Lafaru ya
286
TASKARNOVELS.COM.NG
ce Ya kai wannan sarki wai shin tunanin me
kake yi ne haka mai zurfi?
Sa'adda sarki Lafaru ya ji wannan tambaya sai
ya kawo gwauron numfashi ya ajiye sannan ya
ce Ya kai wannan sadaukin boka mai ban
al'ajabi, kayi sani cewa a halin yanzu babu
abinda nake tunani da zulumi face halin da birni
na ke ciki, da kuma abinda zai faru nan gaba
idan kwanaki arba'in suka cika idan sarki
Nurwas ya zo da dakarunsa na yaki da nufin ya
rushe mulkina ya haye kan karagata.
Koda jin wannan batu sai boka Muzafar ya
bushe da dariya sannan ya ce Ya kai Lafaru ka
kwantar da hankalinka tunda kana tare da ni,
nayi maka alkawari har muje kogon darul
ikisina mu dawo babau abinda zai taba
mulkinka da dukiyarka daja baro acan birninka,
domin wannan halifa naka d muka bari zai iya
tafuyar da kowa da komai hatta matarka sharlis
wacce ke kokarin ganin bayanka ita da dan da ta
haufa maka, yanzu bari na nuna maja halin da
birninka ke ciki.
Nan take boka Muzafar ya zura hannu a cikin
rigarsa ya dauko madubin tsafinsa ya shafeshi
287
TASKARNOVELS.COM.NG
da hannun hagu, sai ga hoton birnin Kufa ya
bayyana, aka nuno sarki Lafaru na zaune bisa
karagar mulki, fadawansa sun kewayeshi ana
tafiyar da harkokin mulkin, suna mamakin
yadda aka yi sarki ya samu lafiya, har ma yana
masu karyar cewa wai daya daga cikin
likitocinsa ne ya bashi wani magani mai kyau,
yana shan maganin kuma ya samu sauki nan
take.
Koda ganin wannan al'amari sai Sarki Lafaru ya
cika da tsananin mamaki irin karfin sihirin boka
Muzafar, domin shi dai gashi tare d boka
Muzafar amman kuma gashi can a birnin kufa
tare da fadawansa tamkar shi din ne ba wani ba.
Boka Muzafar ya sake shafar madubin tsafinsa
da hannun hagu take hoton komai ya bace ya
mayar da madubin cikin aljihun rigarsa, sannan
ya dafa kafadar sarki Lafaru ya ce Ka saki ranka
tamkar tsumma a randa, nan da cikar kwanaki
arba'in zan nuna maka yadda za a fafata a yakin
da za a yi tsakanin tsakanin jama'arka da na
sarki Nurwas, kuma ina mai tabbatar maka d
cewa halifanka ba zai bka kunya ba.
288
TASKARNOVELS.COM.NG
Koda jin wannan batu sai hankalin sarki lafaru
ya kwanta, har fuskarsa ta fadada da murmushi
ya dubi boka Muzafar yayi masa godiya.
Boka Muzafar ya dubeshi yace akan me zaka yi
mani godiya, bayan nine da babban riba idan
muka samu nasara bisa abinda muka fito nema.
Koda jin wannan batu sai sarki Lafaru ya ji
zuciyarsa ta karaya, kawai sai ya dubi boka
Muzafar cikin yanayin damuwa ya ce Ya kai
wannan boka maganar da Gimbiya ta fada mana
kan batun Aljani Maraful Dauwas ta jefa ni cikin
tashin hankali da wasi wasi, ka fa tsaya kayi
naxari akan al'amarin sosai, masoyiyar aljani
maruful dauwa ita kuma gimbiya Rahila mutum
ce kawai dai kammaninsu ne yazo iri daya, babu
yadda za'a yi gimbiya Rahila ta debe wa Aljani
Maraful Dauwas kewar Gimbiya Rashmin
wanda babu aure a tsakanin mutum da Aljan,
shin kayi tunanin sabuwar maganar da zamu je
wa da aljani Maraful Dauwas da ita? Domin ya
amince da bukatarmu har ya yarda ya sati mana
gimbiya Ramlatus siyam.
Yayin da boka Muzafar ya ji wannan tambaya
sai hankalinsa ya tashi, yayi shiru bai ce komai
289
TASKARNOVELS.COM.NG
ba har zuwa tsawon yan dakiku, can ya dubi
inda gimbiya Rahila ta ke sharar baccinta kmaar
ma bata da abinda ke damunta, daman tunda
aka fara wannan tafiya da ita bata da wani aiki
sai bacci, kuma bata fira da kowa ba, sannan ko
yaushe tana rufe da jikinta da kuma fuskarta da
mayafi. Wasu ma daga cikin abokan tafiyar tata
basu ga fuskarta ba, kuma basu san amfaninta
ba a wannan tafiyar. Su boka Muzafar da sarki
Lafaru ne kadai suka san amfaninta a wannan
tafiya.
Lokacin da sarki lafaru ya ga boka Muzafar yayi
shiru ya shiga tunani mai zurfi kamar ba zai
daina ba, sai ya dafa kafadarsa, boka Muzafar ya
dago da sauri kuma a razane kamar wanda ya
farka daga mummunan mafarki, sannan ya dubi
sarki Lafaru cikin matukar damuwa ya ce ya kai
Lafaru ka yi sani cewa har a yanzu banyi
tunanin wata sabuwar magana ba da zamuje da
itq wajen Aljani Maraful Dauwas ba, amman
nayi bincike a hallarar tsafina naga cewa Bamu
da wani zabi face mu nemi taimakon gimbiya
Rahila, domin tabbas tana da magana sahihiya
wacce zata iya gamsar da aljani Maraful Dauwas
har ya amince ya fito daga cikin kogon darul
ikisina, har yaje ya sato mana gimbiya Ramlatus
290
TASKARNOVELS.COM.NG
siyam, inda matsalar take shine bamu san irin
sharadin da gimbiya Rahila zata shinfida mana
ba.
Kafin sarki Lafaru yace wani abu sai kawai suka
ga Gimbiya Rahila ta mike zaune ta yaye
mayafin data rufe fuskarta da shi, kawai sai ta
dubi boka Muzafar tayi masa murmushi mai
kama dana mugunta sai ta koma ta kwanta ta
sake lullube jikinta gabadaya ta kwanta ta ci
gaba da baccinta.
Boka Muzafar ya gyada kai sannan ya dubi
Lafaru ce wannan yarinyar ba karamar
hatsabibiya bace, ya zama dole muyi hankali da
ita.
Haka dai su boka Muzafar ssuka ci gaba da
tafiya a bisa aljani Marhabul Zaurus dare da
rana har suka shafe kwanaki 16, sannan boka
Muzafar ya umarci aljani Marhabul Zaurus da ya
sauko kasa domin a yada zango a huta, ba tare
da gardamar komai ba kowa aljani Marhabul
Zaurus ya saki fukafukansa ya yowa kasa ya
sauka a cikin wani katon daji mai yawan
duhuwa, duk inda mutum ya kalla sai dai yaga
kyawawan koramai, bishiyu da manyan
291
TASKARNOVELS.COM.NG
duwatsu ababan sha'awa, sannan ga tsutsaye iri
iri suna kuka mai dadi irin wanda ke tausasa
zuciya ya gusar mata da dukkanin wata
damuwa, cikin tsananin farin ciki gabadayansu
suka sauka daga kan aljani Marhabul Zaurus,
suka kama tattaki domin su wasa kafafunsu,
kumq su huce gajiyar zaman da suka yi a waje
daya.
Koda boka Muzafar yaga wasu daga cikinsu na
kokarin nausawa cikin wannan daji, sai ya
kwala masu kira, gaba dayansu suka dawo
gabansa suka tsaitsaya. Muzafar ya dubesu daya
bayan daya ya ce Ya ku abokan tafiya kuyi sani
cewa wannan daji da muke ciki shine dajin
karshe wanda daga shi sai wandannan
dazuzzuka guda 5 masu mugun hadari. Shi
kanshi wannan daji abin tsoro ne domin akwai
mugayen aljanu a cikinsa rukuni uku.
Rukuni na farko sun kasance yan fashi masu
tare mutane da aljanu su kwace masu dukkanin
dukiyarsu, sannan su rabasu da dukkanin
matansu, basa yin kisa amman kum sai sun
nakasta mazajen gabadaya, sun maishe su
guragu ko makafi ta hanyar gutsure masu kafafu
da kuma kwakule masu idanu. Karfin sihirin
292
TASKARNOVELS.COM.NG
tsafi ba zai kwacemu ba a hannunsu face
tsagwaron karfin damtse, zafin nama da karfin
gudu da jarumta.
Rukuni na biyu kuwa wadansu masifaffun
aljanu ne wadanda suka ksance dangin mayu, da
farko idan suka kama mutane suna shanye jinin
jikinsu ne, sannan sai su rinka cinye sassan
jikinsu da kadan kadan, gaba bayan gaba.
Rukuni na uku kuwa wadansu zakwakurarun
mayakan aljanu ne kimanin su miliyan arba'in
da uku dauke da muggan makaman yaki, su dai
wadannan aljanu babu wani makami da zai iya
tasiri a jikinsu har yayi masu rauni ko kuma ya
sokesu su mutu, sannan kuma idan zasu
shekara suna yaki ba zasu gaji ba, idan mutum
yana so ya tsira daga sharrinsu sai dai ya ratsa
ta cikinsu da zababben gudu yana bankesu da
karfin tsiya, kuma yana kare harin da zasu dinga
kawo masa, har sai ya isa karshen dajin sannan
za su rabu da shi. Kuyi sani cewa ba zamu iya
ketare wannan daji ta sama ba, dole sai dai mu
ketareshi ta kasa tare da aljnai Marhabul
Zaurus, domin duk abinda ya keta tq sama take
yake konewa ya murmushe ko mene ne shi.
Idan har muna son tsura da rayuwarmu yayin
293
TASKARNOVELS.COM.NG
ratsawa ta wannan mugun dajin sai dai mu hada
karfi da karfe mu yaki wadannan mugayen
aljanu, ya zamana cewa mun taimaki juna
tamkar uwa daya uba daya muke. Amman fa
duk da haka bani da tabbacin cewa duk da haka
zamu fita daga wannan daji a raye ko kuma
cikin koshin lafiya, domin komai zai iya faruwa
ga kowannenmu, yanzu babu abinda ya
kamacemu face mu kafa tantuna mu kwana
anan tunda duhu ya soma, zai fi kyau mu shiga
cikin wannan daji ido na ganin ido, domin
wadannan mugayen aljanu sunfi gani da
daddare.
Koda jin wannan jawabi sai kowa ya shiga
taitayinsa aka shiga zulumi gami da fargaba,
musamman wadanda suka kasnce ba jarumai ba
kamar mahaifiyar sadauki Imran, yaro Masnur,
Lumaira, sarkin Farisa da sarki Lafaru. Su kuwa
sauran jaruman sun saurari bayanin sarki lafaru
ne kawai, amman gani suke kamar zasu iya
ratsa dajin ba tare da sun sha wata muguwar
wahala ba. Kamar yadda Muzafar yake bayani,
Kasancewar sun halarci yakuna da dama a
rayuwarsu, abinda suka manta shine wadannan
aljanu da suke cikin wannan daji ba irin aljanun
da suka saba gumurzu da su bane, wadannan
294
TASKARNOVELS.COM.NG
aljanu ne na musamman masu sadaukartaka da
karfi na ban al'ajabi gami da mugun naci.
Ba tare da bata lokaci ba aka kafa tanti kuwa ya
shiga nasa tantin shida dan uwansa, Gimbiya
Rahila kadai ta shiga nata tantin ita kadai,
amman boka Muzafar da Sarki Lafaru ma a cikin
tanti daya suka zauna. Muzafar da Lafaru na
cikin cin abinci kenan sai kawai Gimbiya Rahila
ta fito daga nata tantin ta nufi tantin nasu inda
taga aljani Marhabul Zaurus yana rangadi a
tsakanin tantinan nasu dan tabbatar da tsaro.
Kai tsaye gimbiya Rahila ta kutsa kai zuwa cikin
tantin su sarki Lafaru, koda ganinta sai suka
cika da tsananin mamaki, boka Muzafar ya
dubeta ya ce Ya ke Rahila ene ne ya kawo ki
cikin tantinmu a wannan lokaci?
Sa'adda Gimbiya ta ji wannan tambayar sai ta yi
murmushi sannan ta cire mayafin da ke jikinta
da farin kyallen data rufe fuskarta da shi, nan
take kyakkyawar fuskarta da kuma surar jikinta
suka bayyana a fili karara.
Boka Muzafar da sarki Lafaru suka bude baki
suka kame, kuma suka kura mata idanu ashe
ganin farko da suka yi mata ganin tsoro ne
295
TASKARNOVELS.COM.NG
kuma tana lullube da fuskarta da jikinta shiyasa
basu ga bauwar da Allah yayi mata ba, yanzu ne
suka tabbatar da cewa Gimbiya Rahila ta fi gaba
daya yan matan da suke tare da su kyua, domin
bambancinta da su kamar fari da baki ne.
Gimbiya Rahila ta samu guri ta zauna nesa
kadan da inda su boka Muzafar suke zaune, ta
fuskancesu sannan ta dubesu a nutse ta ce, Ba
wani abu ne ya kawoni wajenku ba, sai domin
mu gama maganarmu tun kafin mu isa can
kogon darul ikisina, yanzu zan fada maku
sharadin da zan gindaya maku tun kafin na
taimka maku a wajen aljani Maraful Dauwas har
ya amince ya biya maku bukatarku. Ina so ku
saurara da kyau kuji bayanin da zanyi maku,
domin ku fahimci manufata da kuma burina.
Rahila tayi gyaran murya sannan ta ci gaba da
magana da cewa Tun sa'adda mahaifiyata ke
dauke da cika sai ta kasance mai tsananin farin
ciki gami da doki bisa son ganin ranar da zata
haihu, ba komai ne ya haddasa mata hakan ba
face wata rana ta fito waje tana tsefe gashin
kanta, a lokacin babu komai a jikinta sai wani
guntun mayafi data daura iya girjinta zuwa
gwiywoyinta, kamar yadda kuka ganni da
296
TASKARNOVELS.COM.NG
tsananin kyau to haka mahaifiyata take, dan
haka ita na yo gado.
Ba zato ba tsammani sai ga wani jibgegen aljani
ma'abocin kyau ya bayyana tsulum a gabanta,
cikin razana da firgici ta bude baki zata kwala
ihu sai taji muryarta ta dishe a lokacin da ta ji
jikinta ya mutu kuma ya kama karkarwa sabida
tsananin tsoro, kuma gashi ta kasa guduwa tana
tsaye cak waje guda, kawai sai wannan aljani ya
dubeta yayi murmushi har kyawawan
hakoransa suka bayyana da wushirya guda biyu
a jikinsu sama da kasa, wadanda suka kara wa
hakoran nasa kyau.
Aljanin ya dubeta ya ce kada kiji tsorona yake
sarauniyar kyawawa, banzo fomin na tsorataki
b sai domin yi maki albishir, ina mai sanar dake
cewa wannan ciki da kike dauke da shi zaki
haifeshi nan da cikar kwanaki goma sha tara,
kuma abinda zaki haifa wata kyakkyawar
jaririya ce wacce duk duniya ba za a samu mai
kyawunta ba, face wata jariri da za'a haifa a
gidan sarki Nashmir na birnin hindu. Rana daya
za a haifi wadannan jarirai yarki da yar sarki
Nashmir, kuma kyawunsu zai zamo daidai wato
kunnen doki, idan har kina son wannan ya da
297
TASKARNOVELS.COM.NG
zaki haifa tayi nisan kwana a duniya kuma ta
kubuta daga sharrin aljanu wadanda za su yi
sha'awar shiga jikinta dole ne ki dinga boye
fuskarta da dukkan ilahirin jikinta har izuwa
sa'ar da zata zama budurwa, idan kuma ba haka
ba kuwa to ba zata yi tsawon rai ba, kuma
sannan aljanu zasu rinka shiga jikinta suna
lalata mata rayuwa har ta haukace ko ta hallaka
sabida tsananin kyawunta.
Bugu da kari idan har kina son wannan ya taki
ta samu daukaka da matsayi babba a duniya,
dole ne ki aura mata mijin wannan yarinya yar
sarkin birnin hindu zata aura.
Yake wannan matar sarki kiyi sani cewa Ni suna
na aljani sautul baharu, kuma tun kina jaririya
na kamu da tsananin kaunarki, amma saboda
bana son na cutar da ke shiyasa ban shiga
jikinki ba, domin idan har masoyi yana kaunar
masoyinsa bil'adama ba zai iya cutar da shi ba,
na kasance babban da a wajen sarkin bokayen
aljanu na duniya, saboda haka duk wani sihiri
na tsafi na duniya na gajeshi, kuma komai naake
so a duniyar nan zan iya mallakarsa, amman
bana son komai face na mutu da soyayyarki a
zuciyata da kuma jin kyawawan kalamai daga
298
TASKARNOVELS.COM.NG
bakinki, na sani cewa bai kamata aljani ya auri
mutun ba, tabbatas inda ace ina da ikon sauya
halitta daga aljan zuwa mutum da tuntuni nayi
domin na samu damar aurenki, tun a ranar da
mahaifiyarki ta haifeni na gani a wata rana da
kika fito yawon shan iska, a wannan lokaci an
shifideki akan gado kina cikin turaka, sai na
tsaya daf dake na kura maki idanu, na dinga
maki murmushi kema sai naga kina maida mani
da martanin murmushin kin ta dariya.
Mahaifiyarki na can nesa kadan da ke, koda ta
hango abinda kike yi sai ta cika da mamaki
domin babu kowa a kusa da ke, abinda bata sani
ba shine kina ganina ina ganinki ita ce dai bata
iya ganina, daga wannan rana kullum sai na
ziyarceki sau bakwai domin kuwa sai na kalleki
nake jin dadi a cikin zuciyata, duk ranar da ban
ganki ba kuwa sai na yi zazzabi gami da ciwon
kai, hakika so cuta ne domin tsananin kaunar da
nake maki take take jefani a cikin wannan hali,
haka dai na kasance a tare da ke dare da rana na
zamo kamar mai tsaron lafiyarki, sau tari
iyyaenki sun sha ganin abubuwan mamaki da
dama, domin duk irin abin tashin hankalin daya
durfafo gidanku sai aga an kawar da shi, kuma a
rasa wanda ya kawar da shi din?
299
TASKARNOVELS.COM.NG
Haka dai kika fara girma har kika zama yar
shekara bakwai, a sannan ne kyawunki ya kara
fitowa karara, har mutane suka fara tsammanin
ke ba mutum bace aljana ce, aljanu kuwa sai
suka rinka kawo maki hari ni kuwa sai na rinka
fatartakarsu na hanasu shiga jikinki, bisa
wannan daliline na kulla gaba mai tsanani da
sarkin sadaukan aljanu na duniya, wani aljani
da ake kira da Barzuma ibn Kalsawar. Sai da
muka kwana arba'in muna yaki ni da shi ya
zamana cewa dukkaninmu mun suma sau
saba'in da bakwai jikin mu yayi fatafata da
raunika muka zube muna nufashi da kyar, anan
take aljani Barzuma ya tunkuyi kasa ni kuwa sai
nayi sa'a yan uwana sun zo giftawa suka ganni,
cikin dimauta suka daukeni suka tafi da ni gida
domin ayi jinyata, duk da ina cikin halin jinya
amman ban fasa zuwa wajenki ba kullum sau
bakwai nake zuwa gareki, ina tsaron lafiyarki
dan kada wasu aljanun ko kuma mutane su
cutar da ke. Ko sau daya ban taba bayyana a
gareki ba dan haka kika girma kika yi aure kawo
izuwa yanzu baki taba ganina ba, sai yanzu da
nake maki wannan bayani. Kiyi sani cewa a
ranar da aka daura aurenki da sarki sai da na
suma sau uku saboda bakin ciki, kuma na kwana
300
TASKARNOVELS.COM.NG
arba'in ina kuka da takaici ba ci ba sha, yanzu da
naga zaki haihuwa sai naji soyayyar da nake
maki ta tashi daga kanki ta koma kan yarki da
zaki haifa, nayi alkawari zan ci gaba da tsaron
lafiyar wannan ya da zaki haifa har izuwa
karshen rayuwata, amman ina mai dada yi maki
tuni da cewar lallai ki tabbar yarki ta auri mijin
da yr sarki Nashmir zata aura anan gaba koda
kuwa bakya raye, bani da wata bukata a wajenki
face ki furta mani kalmar karshe ta kauna muyi
bankwana domin ba zan sake bayyana ba a
gareki, amman alkawarin dana dauka akan
yarki lallai zan cika shi, kuma zan dinga bayyana
a gareta ina taimakonta bisa dukkan abinda
take son yi face wanda yafi karfina, wannan
shine kalami na karshe a gareki yake abar
kaunata, wadda nake kwana na tashi da
begenta.
Koda Aljani Sautul Baharu yazo nan a zancensa
sai idanunsa suka ciko da kwalla ya fara zubar
da hawaye. Al'amarin daya karya zuciyar
mahaifiyata kenan, nan take itama ta kamu da
tsananin tausayinsa, ta zubar da hawaye sannan
ta ce Ya kai babban masoyina hakika kaunar da
ka nuna mani ba karama bace, tunda ga shi ka
sallama rayuwarka domin tawa, inda da
301
TASKARNOVELS.COM.NG
tsautsayi da tuni ka mutu sakamakon fafatawar
da kayi da sarkin sadaukan aljanu wato
Barzuma ibn Kalsawar, haka kuma gashi ka
shekara ashirin da biyar kana kaunata da
begena a cikin zuciyarka da karfin tsiya bata
bari ta zugaka ka kashe mijin ba, ko kuma tasa
ka saceni ka kaini can inda babu mai iya zuwa,
lalla? kai masoyina ne na kwarai wanda har
abada bazan taba mantawa da shi ba, na rantse
da darajar iyayena ind ina da ikon suya halittata
daga mutum zuwa aljana da nayi domin na
aureka, na zama abokinyar rayuwarka ta har
abada.
D jin wannan batu sai hawayen farin ciki ya
zubo wa Aljani Sautul Baharu yace yi shiru haka
ya masoyiyata hakika babu wata sauran kalma
mai dadi da zaki furta mani wacce ta fi wannan,
gama fadin hakan keda wuya sai aljani sautul
baharu ya bace bat! Mahaifiyata ta neme shi
sama ko kasa ta rasa, nan fa ta rude ta kama
guje-guje a cikin gidan tana mai kiran sunansa,
amman har ta gaji da yawonta ta hakura. Daga
wannan rana mahaifiyata bata sake ganin aljani
sautul baharu ba har ta bar duniya.
302
TASKARNOVELS.COM.NG
Ni ko tun ina da shekara tara a duniya na saba
da shi, ya zamana cewa dare da rana muna tare,
bamu taba rabuw ba, kuma duk abinda zanyi
shine yake bani shawara, ban taba kaucewa
maganarsa ba. Wata rana ina zaune ni kadai a
cikin turakata sai kawai naga aljani Sautul
Baharu ya bayyana a gabana cikin mugun
yanayi, domin duk jikinsa sarane da takobi jini
na kwarara daga jikin nasa, cikin firgici da
dimauta na mike tsaye na rungumo shi alokacin
daya yanke jiki yana shirin faduwa kasa, nna
take fashe da kuka a lokacin da nake
tambayarsa wanda yayi masa wannan mugun
aikin.
Aljani Sautul Baharu ya bude baki da
All Chapters
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 13 Chapter of 14