dubi aljani
Maraful Dauwas a wannan lokaci ole ne ka
zubar masa da hawaye.
A ranar da aka daura auren Gimbiya Rashmin
da dan sarkin aljanu na birnin Misra ne, to a
ranar ne wannan asiri da aka yi mata na juyar
da ?wa?walwarta ya karye, kuma a daidai
lokacin da ango ya shigo dakin amaryarsa, koda
amarya ta dago da kai taga ba Maraful Dauwas
bane sai ta kwala uban ihu, kuma ta dauki wata
wuka dake ajiye a bisa tebur bisa faratin yayan
itatuwa ta soka wa kanta a ciki, nan take ta
sulale kasa matacciya.
Nan fa ango ya dimauce har bai san sa'adda ya
fice waje da gudu ba.
233
TASKARNOVELS.COM.NG
Lokacin da labari ya iski sarki cewa ai Gimbiya
Rashmin ta kasshe kanta sai ya kmau da
tsananin bakin ciki, nan take ya hadiyi zuciya
shima ya mutu.
Shiko aljani Maraful Dauwas sai da ya shekara
dari biyu a cikin wannan kurkukun a tsare, ba a
kuma sake shi ba sai bayan da mahaifiyar
Gimbiya Rashmin ta mutu, aka nada sabon sarki
a garin.
Koda aka saki Aljani Maraful Dauwas daga
kurkuku aai yaji gabadaya ya tsani kansa kuma
ya tsani duniyar, dama tun yana kurkukun
labari ya riske shi cewa Gimbiya Rashmin ta
kashe kanta, dan haka shim aai ya fara kokarin
kashe kan nasa, ammab sai dakarun dake
tsaronsa suka sa ido soaai a kansa dare da rana
bisa dole ya hakura da batun kashe kansa.
Lokacin da Aljani Maraful Dauwas ya fice daga
kurkukun kuma yajinya tsani duniya da duk
abinda ke cikinta sai ya yanke shawarar ya kai
kansa inda b zai sake ganin mutane ko aljanu ba,
domin ya karasa sauran rayuwarsa ta duniya,
bisa wannan dalili ne ya tafi can karshen birnin
sin ya shiga cikin kogon darul ikisina ya rufe
234
TASKARNOVELS.COM.NG
kansa a ciki har zuwa tsawon shekaru dubu
biyu da dari biyu bai fito ba balle yaga koda
hasken rana, dama can shi kogon darul ikisina
kogo ne da yayi kaurin suna a duniya kuma
babu mai iya shigarsa face wand ya san wasu
dalasuman sihiri wadanda na musamman ne
guda bakwai, sai mutum ya karanta wadannan
dalasuman n tsafi a fili sannan kofar kogon zata
bude, idan kuwa yayi kuskure a wajen karanta
dalasiman sau daya to shikenan har abada kofar
ba zata bude ba, koda kuwa zai sake karantawa
sau dubu.
Shi kansa Aljani Maraful Dauwas ya gaji wannan
dalasuman ne a wajen kakansa na dari da
ashirin da biyu, kuma ba a rubuce suke ba a
cikin kundi ko littafi, akan cinyarsa ta hagu aka
rubuta su da wata wuka ta sihiri yadda har
abada babu wani abu da zai iya goge su koda
kuwa wuta ce.
Lokacin da boka Muzafar Ibn Mauzar ya zo nan
a labarinsa sai sarki Lafaru ya vika da tsananin
mamaki kuma hankalinsa ya dugunzuma
sadoda tunanin gagarumin aikin dake gabansa
da daharinsa gamj da wahalar dake cikinsa yafi
dukkanin dadin da zai biyo baya. Bayan sarki
235
TASKARNOVELS.COM.NG
Lafaru yayi dan nazari sai ya dubi boka Muzafar
cikin nutsuwa ya ce Ya kai wannan babban
bako, ina da tambayoyi kwarara a gareka;
tambaya ta farko ita ce shin kaima kana da
wadannan dalasumai na tsafi ne guda bakwai
wadanda za'a karantasu kofar kogon darul
ikisina ta bude ne, tambaya ta biyu ta yaya kake
ganin cewa aljanu Maraful Dauwas zai amince
ya fito daga cikin kogon darul ikisina har yaje
fadar sarki Nashmir ya sato mana gimbiya
Ramlatus siyam alhalin ya tsani duniya da duk
abinda ke cikinta, tambaya ta uku ita ce me yasa
aljani Maraful Dauwas baiyi tawaye ba a lokacin
da mahaifin gimbiya Rashmin yasa aka yi masa
dukan kawo wuka har aka kaishi kurkuku,
bayan aljanin ya kasance gawurtaccen jarumi
mai tarwatsa maza a filin daga.
Sa'adda boka Muzafar ya ji wadannan
tambayoyi guda uku sai ya bushw da dariya
sannan ya ce Ya kai wannan sarki k yi sani cewa
makaho baya cewa ayi wasan jifa face ya
tabbatar da cewa ya taka hoge, kamar yadda
aljani Maraful Dauwas ya gaji wadannan
dalasiman tsafin haka nima na gajesu a wajen
kakana na uku, kuma duk duniya mutum hudu
ne masu wannan dalasuman tsafin sai kuma
236
TASKARNOVELS.COM.NG
aljanu uku, a cikin mutane saura mutum biyu jal
a raye daga nk sai sarkin birnin Hindu wato
mahaifin gimbiya Ramlatus siyam, a cikin aljanu
kuwa saura aljani Maraful Dauwas kawai.
Dangane da tambaya ta biyu kuwa hakika babu
kalaman da zamu fadawa aljani Maraful Dauwas
ya amince yayi mana wannan aiki domin dukiya
ko mulki basa gabansa, abu daya ne zamu je
masa da shi idan muka yi sa'a ya amince, kayi
sani cewa a yamma da birnin Misra bayan
mutuwar Gimbiya Rashmin da shekaru hamsin
an haifi wata kyakkyawar budurwa mai
tsananin kama da gimbiya Rashmin tamkar an
tsaga kara harma ta fi Rashmin kyawun sura,
kai inda za a hada Rashmin da budurwarnan
mai suna Rahila da sai mutum yayi tsammanin
cewa tagwaye ne, zamu dauki Rahila mu tafi da
ita can cikin kogon darul ikisina domin aljani
Maraful Dauwas ya ganta da idanunsa, tabbas
idan yayi arba da ita zai cika da mamaki wata
kila ma yayi tunanin ko fatalwal masoyiyarsa ce
Rashmin, nan take sai muyi masa al?awari cewa
zamu bashi ita ya aura amman bisa sharadin zai
biya mana bukatarmu, ko shakka bana yi nasan
aljani Maraful Dauwas zai bari wannan tayi ya
wuce shi ba, game da tambayarka ta uku kuwa
237
TASKARNOVELS.COM.NG
dalilin da yasa aljani Maraful Dauwas bai yi wa
sarki tawaye ba shine akwai alkawari mai karfi
da mahaifinsa ya dauka kan cewa har abada
shida zuri'arsa baza su taba yi wa sarkk tawaye
daga yin bauta ba, face shi da kansa ya daina
bukatarsu. Ya kai wannan sarki ka yi sani cewa
yanzu take ba tare da bata wani lokaci ba zan
daukeka mu aiwatar da wannan gagarumin
aikin da ke gabanmu, amman kafin mu tafi sai
na kirkiri mai irin kamanninka sak kuma na
kwantar da shi bisa gadonka, ya cigaba da
rashin lafiya hadimnaka na ci gabada yi masa
hidima har izuwa lokacin da zamu dawo saboda
mu bagarar da matarka sharlis, domin idan taga
baka nan na san tabbas sai ta yi kyakkyawan
shiri, kuma muddin ta gano zata iya tarwatsa
shirin namu dan dukkanin wani sihirin tsafi da
nake takama da shi itama tana da shi, da abu
daya kacal na fita, wannan abu ba komai bane
face wayo gami da hangen nesa, kasan ance duk
wanda ya rigaka kwana dole ne ya rigaka tashi.
Koda jin wadannan batutuwa sai sarki Lafaru ya
dubi bboka Muzafar cikin tsananin farin ciki ya
ce ai nima wayo ne ya ceceni yanzu nayi kamar
bani da lafiya har nazo na sameka.
238
TASKARNOVELS.COM.NG
Muzafar yayi murmushi yace ai koda baka yi
wannan wayo ba, lallai sai na zo gareka a
sirrance tunda nayi bincike naga amfaninka a
cikar burin rayuwata.
Sarki Lafaru ya yi murmushi sannan ya ce da
boka Muzafar na rokeka daka gaggauta dauke ni
daga cikin wannan gida domin mu tafi biyan
bukatar abinda ke gabanmu, ahalin yanzu ji
nake kamar akan kaya nake.
Kafin sarki Lafaru ya gama rufe bakinsa tuni
boka Muzafar ya shafi jikinsa da hannunsa na
hagu, kawai sai yaga Husaininsa ya fito daga
cikin jikinsa, hatta kayan da ke jikin Husaini iri
daya ne babu banbanci ko kadan, kawai sai
Husaini ya je ya kwanta akan gadon sarki, boka
Muzafar ya sake dafa kafadar Sarki Lafaru nan
take suka bace gaba dayansu, basu bayyana a ko
ina ba sai a birnin Kufa a gaban wani narkeken
aljani mai matukar girma gami da ban tsoro,
kuma muninsa ya wuce ayi misali idan mutum
ya kalli fuskar aljanin zai iya haukacewa nan
take, amman da yake sarki Lafaru ya saba gamo
da ire-irensu a baya kafin alkadarinsa ya karye
sai bai tsorata ba ainun.
239
TASKARNOVELS.COM.NG
Ba tare da bata lokaci ba boka Muzafar ya kama
hannun Sarki lafaru ya jashi suka hau kan
wannan narkeken aljani sannan Muzafar ya ce
Ya kai Marhabul Zaurus maza ka kaimu can
yammacin birnin Damaskas a ajiye mu a garin
su kyakkyawa Rahila.
Da jin wannan umarni sai Aljani Marhabul
Zaurus yayi murmushi mai kama da gurnanin
zaki ya ce an gama ya shugabana, nan take
nakeken aljanin ya bude fukafukansa ya tashi
tre da lulawa cikin gajimare yana mai keta gizagizai tamkar tauraruwa mai wutsiya
Tafiyar da suka yi bata kai ta rabin sa'a ba suka
iso yammacin birnin Damaskas, aljani Marhabul
Zaurus ya sakko kasa ya dira bisa turba a bakin
kofar wani babban birni wanda suka iske kofar
a rufe, dakarun yaki kimanin su dubu suna
tsaitsaye a bakin kofar rike da muggan makamai
suna gadi.
Ba tare da boka Muzafar ya ce da sarki Lafaru
wani abu ba sai kawai ya sauka daga kan aljani
Marhabul Zaurus ya nufi wajen masu gadin
kofar kai tsaye. Koda ganin haka sai Sarki Lafaru
ya sauko da sauri ya bishi a baya cikin sauri240
TASKARNOVELS.COM.NG
sauri gudu-gudu har ya tarar da hi suka kasara
wajen masu gadin kofar a tare. Da zuwansu sai
Boka Muzafar ya dubi shugaban dakarun ya
daka mashi tsawa sannan ya ce, Ya kai wannan
bawan sarki maza ka ruga wajen sarkinku ka
fada masa cewa ni boka Muzafar ibn Mauzur
gani na dura a kasarsa kuma ina son ya bani
aron yarsa Rahila zan dawo da ita bayan
kwanaki sittin da biyar.
Koda jin wannan batu sai gabadaya dakarun
suka kyalkkyale da dariya, haka suka yita yi
kamar ba zasu daina ba, daga can sai shugaban
nasu ya dubi boka Muzafar ya ce Kai ko wane
irin mahaukaci ne, kuma a ina ka taba ganin uba
ya bada aron yarsa budurwa balle kyakkyawa
kamar Rahila, wai shin zautuwa k yi ko kuma
basirarka ce ta toshe?
Koda jin haka sai zuciyar boka Muzafar ta kama
tafarfasa tamkar zata kone daga can kuma sai ya
daga hannu ya sharara wa shugaban dakarun
mari, sabida zafin marin sai da yayi katantanwa
sau uku kuma yaga taurarin wuya. Boka
Muzafar ya dubeahi a fusace tare da cewa
ubanka ne ya zautu amman ba ni ba, kuma mai
tosashiyar ?wa?walwa...
241
TASKARNOVELS.COM.NG
Kafin Muzafar ya gama rufe bakinsa tuni
shugaban dakarun da sauran yaransa sun zare
makamansu tare da yi masa kawanya, koda
ganin haka sai shima boka Muzafar ya zare nasa
takobin suka kacame da azababben yaki, shi
kuwa sarki Lafaru sai ya buta a bayan wata
bishiya yana mai leken abinda ke faruwa.
Kaico! Hakika maza sun fadi, lokacin da Sarki
Lafaru aga ana wannan gumurzu tsakanin boka
Muzafar da dakarun nan sai yaga boka Muzafar
ya zame masu alakakai, amman shi gashi a labe
ya kasa kai masa dauki sai hawayen takaici ya
zubo masa, saboda tunow da cewa da fa shi
Gwarzon Sadauki ne mai tarwatsa gungun maza
kuma komai yawansu a filin daga, amman yanzu
ko mutum daya ba zai iya gwabza yaki da shi ba,
domin yana jin rashin karfi a jikin nasa yadda ko
takobi ba zai iya dagawa ba.
Lokacin da boka Muzafar yaga wannan dakarun
yakin su dubu ya zame masu alakakai yana ta
kashesu tamkar guguwar annoba ce ta sauka a
wannan birni, su kuma sun kasa koda lakutar
jikinsa, sai ya raina jarumtarsu, dan haka sai ya
maida takobinsa cikin kufe ya ci gaba da
gumurzu da su babu makami a hannunsa. Duk
242
TASKARNOVELS.COM.NG
wanda ya kawo masa sara ko suka sai ya kauce
ya gabza masa naushi daya take zai baje a kasa
sumamme.
Koda sarki Lafaru ya hango irin wannan
tsananin gagarumar jarumtaka da boka Muzafar
ke yi, sai ya cika da tsananin mamaki domin ko
shi kansa sa'ar da yake da karfin damatsensa
bai yi tsammanin ya taba jarumtakar da ta kai
irin wannan ba, kuma a cikin tsananin zafin
nama kamar haka.
Cikin abinda bai wuce dakika hamshin ba, boka
Muzafar ya bazar da dukkanin dakarun su dubu
a kasa, daga sumammu sai karyayyu babu
wanda zai iya mikewa tsaye a cikinsu.
Koda ganin haka sai boka Muzafar yasa kafarsa
ta dama da doki kofar shiga garin wacce aka yita
da zallar bakin karfe, mulmulalle mai tsawon
kamu dari gami da fadin kamu saba'in. Nan take
kofar ta jijjege daga jikin katangar ta fadi kasa
rikica! Karar katuwar kofar ce ta cika garin
gabadaya, ta dugunzuma hankalin dukkan
mutanen garin har suka fara tsammanin cewa
rundunar yaki ce ta kawo masu harin sumame.
243
TASKARNOVELS.COM.NG
Nan da nan Sarkin garin da kuma hadimai suka
debo makan yki sama da su dubu dari uku suka
yi hawa Bisa dawakan tare da sukwanosu zuwa
bakin kofar birnin domin su tari Abokan gaba.
Da isowar sarki da dakarunsa sai suka cika da
tsananin mamaki da suka ga mutum biyu jal sun
tunkaresu.
Sarkinsu ya dubi boka Muzafar da sarki Lafaru
ya daka masu tsawa ya ce Ina sauran dakarun
naku suka buya, shin kunzo da wani sabon salon
yaki ne da kuke ganin zaku iya cutar da mu da
shi ne?
Koda jin wannan tambaya sai boka Muzafar ya
dubi sarki sannan ya ce mu ba yaki ne ya
kawomu ba, ba kuma mu biyu muka zo ba,
wadannan masu gadi naku da kuke gani a kasa
tamkar tsommokara taurin kai suka yi mana,
suka ki isar da sakonmu a gareka, bisa wannan
dalili ne na fusata n banke kofar wannan birni
naku na shigo. B wani abu ne ya kawo mu ba
face mun so ka bamu aron yarka dan tayi mana
wani aiki na kwana sittin da biyar kacal, ina mai
tabbatar maka da cewa zamu dawo maka da ita
244
TASKARNOVELS.COM.NG
cikin aminci da salama kamar yadda muka
karbeta daga hannunka.
Lokacin da boka Muzafar ya zo nan a zancensa
sai sarki da dukkanin dakurunsa suka bushe da
dariya, kamar yadda masu gadin kofar suka yi a
karon farko, lokaci daya kuma suka tsuke
bakinsu suka yi tsit tamkar mutuwa ta gifta ta
tsakaninsu. Sarki ya dubi wasu zakwakurarun
dakarunsa mutum hudu ya ce da su maza ku
kama wannan baki ku kaisu kurkuku ku kullesu,
lallai ba kalau suke ba aljanu ne suka shafesu.
Gama fadin hakan da wuya sai wadannan
dakaru hudun suka tasarwa su Lafaru. Da zuwa
sai suka kai hannu zasu cafkesu, cikin matukar
zafin nama na gaban kwatance boka Muzafar ya
cafi hannun nasu su hudun a kuma lokaci guda
ya kakkarya su, tamkar ya karya sillen kara.
Dakarun suka rusa ihu tare da gaduwa kasa, kaji
aikin sadaukai maganin maza.
Koda sarki da sauran dakarunsa suka ga abinda
ya faru sai duk suka zare makamansu uka afka
wa su boka Muzafar, kawai sai lafaru ya ruga
izuwa maboyarsa ya labe, shiko boka Muzafar
sai ya tari rundunar shi kadai aka kacame da
245
TASKARNOVELS.COM.NG
mummunan yaki. Nan fa boka Muzafar ya
gagaresu kuma ya addabesu ya zamana cewa
baya saransu da takobinsa sai dai ya kare
dukkanin harinsu, sannan ya riga gabza masu
naushi da hannu da kafa, komai girman kato
idan boka Muzafar ya yi masa naushi daya sai ya
kife kasa kuma ba zai sake mikewa ba. Boka
Muzafar ya rinka tsale a saman dakarun nan
yana shawagi tamkar tsuntsu mai fuka-fukai,
yayi tq zubar da su kasa yana masu sarkiya ya
hana dawa tsayuwa, kafin rabin sa'a ta cika ya
bazar da mutum dari a kasa.
Koda sauran dakarun nan suka ga abinda ke
faruwa sai suka zubar da makamansu suka mika
wuya, sarkinsu ne kawai ya ki mika wuya, kawai
sai ya sakko daga kan dokinsa ya gyara
tsayiwarsa kuma ya rike takobinsa da hannu
biyu ya tsaya cak a waje daya.
Koda ganin haka sai boka Muzafar ya dubeshi
saman yayi murmushi ya ce Ya kai wannan sarki
mene ne dalilin da yasa ba zaka mika wuya a
gareni ba, alhalin kasan cewa ba zaka iya samun
snasara a kaina ba?
246
TASKARNOVELS.COM.NG
Koda jin wannan tambaya sai sarkin yayi ajiyar
zuciya cikin alamun takaici ya ce Ya kai wannan
Sadauki mai jarumtaka ta ban al'ajabi yi sani
cewa har abada sarki sarki ne, bazai taba mika
wuya a rabashi da mulkinsa, dukiyarsa ko kuma
yayansa ba face bisa dole idan ya ga ya kasa
kare kayansa, ya za a yi n dauki yata ta cikin
kuma da hannuna na baka ita aro bansan me
zaku yi da ita ba, kuma ma bn san ka ba, ai sai
dai ku fara kasheni sannan kuje ku dauketa.
Da jin wannan batu sai boka Muzafar ya risina
ga sarki ikin girmamawa ya kai gaisuwa tare da
cewa Ni din nan ba sarki bane na kasance boka
ne, amman ina girmama sarauta, ya kai wannan
sarki hakika ka burgeni da ka zama mai kishin
jama'arka, mulkinka gami da iyalanka. Nikam.ba
zan kasheka hakazalika bazan kashe kowa a
cikin garin nan ba domin kawai nazo daukar
yarka, amman fa duk wanda yayi gigin hanani
daukarta to fa lallai ne zai rasa hanaye gami da
kafafu, idan har baka son wannan birni naka ya
zama na nakasassu ina mai shawartarka daka
bani Gimbiya Rahila salin alin na tafi da ita.
Da jin hka sai sarki ya daka wa boka Muzafar
tsawa ya ce da shi Bafa zai yuwuba, idan har
247
TASKARNOVELS.COM.NG
kaga ka tafi da ita totabbas sai dai idan bana
numfashi.
Lokacin da boka Muzafar ya ji wannan batu sai
ya fisata ainun ya zare takobinsa ya ruga izuwa
kn sarki, shima sarkin sai ya daga takobinsa
sama ya ruga gareshi, saura kiris su hadu sai
kawai sukaga gimbiya Rahila ta dako wawan
tsalle tare da dura a gabansu, duk su biyu sia
suka ja da baya suka yi cirko-cirko kamar
zakaru suna masu kallonta cikin mamaki bisa
yadda akayi ta bayyana tsulum a gabansu.
Gimbiya Rahila ta kalli mahaifinta a lokacin da
idanunta suka ciko taf da kwalla, suka fara
zubar da hawaye ta ce Haba ya abbana yanzu
akna rayuwata kadai sai ka bari a maishe da
jama'arka nakasassu, ka tuna cewa a garin nan
akwai iyayenka, kakanninka gami da yan
uwanka, kuma su ka fara samu kafin ka sameni,
kada ka manta ni ya mace nake, mokai daran
daewa dole ne muyi aure mu rabu ko da kuwa
wani bai zo ya rabani da kai da karfin tsiya ba,
ina mai rokonka da ka hakura ka bayar da ni ga
wadannan mutanen domin naje nayi masu irin
aikin da nake so, sabida bana son mutum daya
ya jara cituwa a wannan birni bisa sanadiyyata,
248
TASKARNOVELS.COM.NG
daga kjarshe idan da rabon sake saduwa
sainkaga na dawo gida, idan kuma na mutu acan
sai ka rungumi kaddara domin ita rayuwa tana
da lokacinta, idan babu mutuwa ai akwai tsufa
da rashin lfiya.
Lokacin da Gimbiya Rahila ta zo nan a zancenta
sai jikin sarki yayi sanyi, kawai sai ya karasa
gareta ya rungumeta suka gashe da kuka tare
domin tunda aka haifi Gimbiya Rahila bata taba
rabuwa da mahaufinta ba daidai da rana daya,
dare da rana suna tare har ta girma ta cika
budurwa face makwanci idan dare yayi.
Ko da ganin yadda sarki da Rahila ke kuka
rabuwa da juna sai tausayinsu ya kama boka
Muzafar da sarki Lafaru har basu san sa'adda
idanunsu suka cika da kwalla ba.
Nan take boka Muzafar ya ji yayi nadama bisa
wannan babban buri da yasa a gabashi, tunda ga
shi a sanadinyyar haka ya zama bakin takobi
mai raba mai masoya. Boka Muzafar ya tuna
cewa shifa a yanzu bashi da kowa a duniya
iyayensa sun mutu tun yana yaro dan shekara 6
matarsa ta mutu a lokacin da ta zo haihuwar
fari, dan cikin nata ma sai ya zo a mace, to tun
249
TASKARNOVELS.COM.NG
daga sannan bai sake marmarin yin aure ba,
bugu da kari tun yana karami aka kmashi a
matsayin bawa, aka daukeshi daga garinsu na
asali aka tafi da shi can wata nahiyar da ban da
shi da dangin iya balle na baba.
A lokacin ne aka siyar da shi ga wani
shahararren boka wanda yayita bauta a gareshi
har ya shekara ashirin da biyar, a sannan ne mai
gidan nasa ya mutu ya gaji sirrinkan tsafinsa
saboda tsananin biyayyar da yayi wa mai gidan
nasa.
Koda boka Muzafar ya tuna cewa shifa yanzu
bama zai tuno asalin inane mahaifarsa ba, balle
ya tuno da danginsa ba, sai ya koma can gefe
daya ya hada kai da gwiywa ya kama kuka. Yana
cikin wannan hali ne yaji an dafa kafadarsa,
koda ya dago kainsai yaga ashe sarki Lafaru ne
tsaye a kansa, koda Lafaru yaga hawaye a cikin
idanun boka Muzafar sai jikinsa yayi sanyi
sannan ya ce da shi Y kai wannan shu'umin
boka kuma sadaukin boye ina dalilin wannan
kuka naka alhalin ga shi bukatarmu ta biya,
mahaifinta ya hakura zai bamu Gimbiya Rahila.
250
TASKARNOVELS.COM.NG
Koda jin wannan tambaya sai boka Muzafar ya
yi ajiyar zuciya sannan ya share hawayensa ya
ce Ya kai abokin tafiyata, ka sani cewa duniya
babu ranar bakin ciki kamar ranar rabuwa da
masoyi, hakika na kamu matuka da tausayin
wannan sarki da yarsa, bisa yadda zasu yi
rabuwar dole ba a son ransu ba, kuma hakan ne
ya tuno mani da asalina na kasancewata
maraya, wanda ma ba zai iya tuno mahaifarsa
ba bare danginsa, hakika kaddara ta yanke mani
kauna da farin cikin rayuwa wanda har abada
bazan samesu ba domin kowa ya bar gida gid ya
barshi.
Yayin da sarki Lafaru ya ji haka sai shima ya
tuna cewa shima fa yanzu bashi da kowa face
mulkinsa sai kuma dukiyarsa da ya baro a
birnin Kufa, nan take ya sake tunawa yau fa
saura kwanaki arba'in yayi yaki da sarki
Nurwas na birnin Zaruk kuma ga shi gashi
yanzu ya bar kasar, to wai shin yanzu za a yi
wannan yakin ko kuma ba za a yi ba? Idan kuma
aka yi yakin suwa za su samu nasara?
Shin wannan halifa nasa wanda boka Muzafar
ya kirkira zai iya kare birnin daga sharrin sarrki
Nurwas da dakarunsa? Shin da gaske ne idan
251
TASKARNOVELS.COM.NG
basu samu nasara ba bisa abinda suka fito nema
ba shida boka Muzafar dansa Shaddad zai girma
ya zama babban makiyinsa har kuma ya
kasheshi?
Sarki Lafaru yana cikin wannan tunani ne
Gimbiya Rahila da mahaifinta suka zo kansa
suka tsaya, cikin hanzari boka Muzafar da sarki
Lafaru suka mike tsaye suna masu fuskantarsu.
Sarkin ya dubi boka ya ce ya kai wannan
Sadauki mai jarumtaka ta al'ajabi, kayi sani
cewa ban kasance boka ba, dan haka ban san
irin aikin da yata zata yi maku ba? Amman da
ganin fuskokinku baku yi kama da makaryata ba
kuma ba zaku kasance masu kin cika alkawari
ba, abu daya nake zargi akanku bai wuce rashin
aldalci ba ga duk wanda ke karkashinku sannan
zaku iya yin komai dan ganin bukatarku ta biya.
Ni dai yanzu ga yata nan na damkata amana a
hannunku bana bukatar na ji abinda zaku yi da
ita, amman ina son ku kasance masu rike
alkawari ku dawo mani da ita lafiya kamar
yadda kuka yi alkawari da farko. Idan kuwa
kuka ci amanata to kuma amana zata ci ku.
252
TASKARNOVELS.COM.NG
Koda gama fadin haka sai sarki ya sake
rungume Gimbiya Rahila a kirjinsa tare da
fashewa da matsanancin kuka itama kawai ai ta
kama kukan, da kyar suka kasi juna kana daga
bisani suka yi bankwana. Daga nan sarki da
dakarunsa suka juya suka shige cikin birnin na
su.
Sarki na waigen yarsa gimbiya Rahila yana mai
zubar da hawaye, haka itama, haka dai suka ci
gaba da daga wa juna annuwa har suka kule.
Ba tare da wani bata lokaci ba, boka Muzafar
sarki Lafaru da gimbiya Rahila suka fito daga
cikin wannan birni inda suka iske aljani Maraful
Dauwas a zaune yana jiransu. Nan take duk su
ukun suka haye bayan aljani Marhabul Zaurus
shi kuwa sai ya bude fuka-fukansa ya tashi sama
ya luluka a cikin gajimare sannan ya tsaya cak a
cikin iska.
Koda ganin haka sai boka Muzafar ya daka masa
tsawa tare da cewa Me kake nufine da zaka
tsayar da mu cak a sararin samaniya?
Cikin razana da biyayya aljani Marhabul Zaurus
ya rusuna ya ce Ya shugabana ai baka fada mani
inda zamu je ba, umarninka nake jira?
253
TASKARNOVELS.COM.NG
Koda jin haka sai boka Muzafar yayi ajiyar
zuciya sannan ya ce Yanzu mun hau mataki na
farko a wannan gagarumar tafiya da ke
gabanmu, saura mataki na biyu wanda shine
tafiya zuwa dauko abokan tafiyarmu. Ya kai
Marhabul Zaurus na umarceka daka kaimu
birnin Misra domin mu sadu da sadauki
Haiman, kafin Boka Muzafar ya gama rufe
bakinsa tuni aljani Marhabul Zaurus ya dubi
bangaren kudu ya falfala da matsanancin gudu
cikin gajimare tamkar tauraruwa mai wutsiya.
Tunda aka fara wannan tafiya hira ta barke
tsakanin sarki Lafaru da boka Muzafar, ita kuwa
gimbiya Rahila sai tayi shiru kawai ta kishingida
kamar tana yin bacci idanunta a lumshe bata
tanka masu ba.
Sarki Lafaru ne ya fara yin gyaran murya
sannan ya dubi boka Muzafar ya bushe da
dariya, al'amari da ya baiwa boka Muzafar
mamaki da haushi kenan, ya dubeshi a fusace ya
ce ina dalilin wannan dariyar ta ka?
Sarki Lafaru ya hadiye rai sannan ya ce Gani
nayi ni da kai duk mun kai shekaru dari a
duniya amman hr yanzu bamu da kwanciyar
254
TASKARNOVELS.COM.NG
hankali, sannan muna da buri mai tsauri a cikin
zukatanmu, kamata yayi ace a yanzu muna cikin
rayuwar farin ciki da nutsuwa tare da iyalanmu.
Da jin wannan batu sai boka Muzafar ayi
murmushi sannan ya ce Ai shi rai da kake
ganinsa baya rabuwa da buri, daga lokacin da
mutum yayi aure babu abinda zai fara tunani
sama da haihuwa. Idan ya samu haihuwar sai
kuma ya fara tunanin tara dukiyar da zai baiwa
dansa, idan tafiya tayi tafiya aka tara abin
duniya ya taru sosai sai a fara hangen mulki,
idan mulkin ya samu sai a fara hangen daukaka,
a lokacin da daukakar ta samu zaka ga tsufa ya
fara zuwa, to a Sannan ne lafiya zata yi karanci
dan haka sai kaga kullum a cikin neman lafiya
ake, wani har ya mutu ba zai samu lafiyar ba,
wani kuma sai kaga yau da lafiyar gobe kuma
babu, haka dai rayuwa zata kare amman buri
bai kare ba walau yaro matashi ko tsoho.
Koda boka Muzafar ya zo nan a jawabinsa sai
Gimbiya Rahila ta yi caraf ta tari numfashinsa
tare da cewa Wanne abu mutum zai yi domin ya
iya sarrafa zuciyarsa da kwadayin burika?
255
TASKARNOVELS.COM.NG
Boka muzafar ya amsa mata da cewa babu wani
abu mai kore burika daga cikin zuciya face ya
dauki hakuri, kuma ya rike gaskiya da amana,
idan har yayi hak to samu da rashi ba zasu
dameshi ba.
Rahila tayi murmushi ta ce nda kunyi aiki da
wannan maganar da ka fada yanzu da bazaka
rabani da mahaifina ba domin kuje ku bayar da
ni ga aljani Maraful Dauwas na maye gurbin
masoyiyarsa gimbiya Rashmin.
Koda jin wannan batu sai boka Muzafar da sarki
Lafaru suka zazzaro idanu cikin tsananin
mamaki suka kasa cewa komai, tsawon yan
dakiku su dukansu sunyi shiru daga can sai
boka Muzafar yayi ajiyar zuciya ya ce Yake
Gimbiya Rahila ya akayi kika san wannan
al'amari namu alhalin baki kasance matsafiya
ba, haka shima mahaifinki bai kasance matsafi
ba?
Rahila ta girgiza kanta cikin alamun takaici
sannan ta ce Ashe baku yi mamaki ba lokacin da
na bayyana tsulum a tsakiyarku ba sa'adda kai
da mahaifina kuke shirin kaurewa da yaki, a
cikinku babu wanda yaga ta inda na fito kawai
256
TASKARNOVELS.COM.NG
nasan kun ganni ne tsulum a tsakiyarku, to ka
sani
All Chapters
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 11 Chapter of 14