Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
dubi aljani Maraful Dauwas a wannan lokaci ole ne ka zubar masa da hawaye. A ranar da aka daura auren Gimbiya Rashmin da dan sarkin aljanu na birnin Misra ne, to a ranar ne wannan asiri da aka yi mata na juyar da ?wa?walwarta ya karye, kuma a daidai lokacin da ango ya shigo dakin amaryarsa, koda amarya ta dago da kai taga ba Maraful Dauwas bane sai ta kwala uban ihu, kuma ta dauki wata wuka dake ajiye a bisa tebur bisa faratin yayan itatuwa ta soka wa kanta a ciki, nan take ta sulale kasa matacciya. Nan fa ango ya dimauce har bai san sa'adda ya fice waje da gudu ba. 233 TASKARNOVELS.COM.NG Lokacin da labari ya iski sarki cewa ai Gimbiya Rashmin ta kasshe kanta sai ya kmau da tsananin bakin ciki, nan take ya hadiyi zuciya shima ya mutu. Shiko aljani Maraful Dauwas sai da ya shekara dari biyu a cikin wannan kurkukun a tsare, ba a kuma sake shi ba sai bayan da mahaifiyar Gimbiya Rashmin ta mutu, aka nada sabon sarki a garin. Koda aka saki Aljani Maraful Dauwas daga kurkuku aai yaji gabadaya ya tsani kansa kuma ya tsani duniyar, dama tun yana kurkukun labari ya riske shi cewa Gimbiya Rashmin ta kashe kanta, dan haka shim aai ya fara kokarin kashe kan nasa, ammab sai dakarun dake tsaronsa suka sa ido soaai a kansa dare da rana bisa dole ya hakura da batun kashe kansa. Lokacin da Aljani Maraful Dauwas ya fice daga kurkukun kuma yajinya tsani duniya da duk abinda ke cikinta sai ya yanke shawarar ya kai kansa inda b zai sake ganin mutane ko aljanu ba, domin ya karasa sauran rayuwarsa ta duniya, bisa wannan dalili ne ya tafi can karshen birnin sin ya shiga cikin kogon darul ikisina ya rufe 234 TASKARNOVELS.COM.NG kansa a ciki har zuwa tsawon shekaru dubu biyu da dari biyu bai fito ba balle yaga koda hasken rana, dama can shi kogon darul ikisina kogo ne da yayi kaurin suna a duniya kuma babu mai iya shigarsa face wand ya san wasu dalasuman sihiri wadanda na musamman ne guda bakwai, sai mutum ya karanta wadannan dalasuman n tsafi a fili sannan kofar kogon zata bude, idan kuwa yayi kuskure a wajen karanta dalasiman sau daya to shikenan har abada kofar ba zata bude ba, koda kuwa zai sake karantawa sau dubu. Shi kansa Aljani Maraful Dauwas ya gaji wannan dalasuman ne a wajen kakansa na dari da ashirin da biyu, kuma ba a rubuce suke ba a cikin kundi ko littafi, akan cinyarsa ta hagu aka rubuta su da wata wuka ta sihiri yadda har abada babu wani abu da zai iya goge su koda kuwa wuta ce. Lokacin da boka Muzafar Ibn Mauzar ya zo nan a labarinsa sai sarki Lafaru ya vika da tsananin mamaki kuma hankalinsa ya dugunzuma sadoda tunanin gagarumin aikin dake gabansa da daharinsa gamj da wahalar dake cikinsa yafi dukkanin dadin da zai biyo baya. Bayan sarki 235 TASKARNOVELS.COM.NG Lafaru yayi dan nazari sai ya dubi boka Muzafar cikin nutsuwa ya ce Ya kai wannan babban bako, ina da tambayoyi kwarara a gareka; tambaya ta farko ita ce shin kaima kana da wadannan dalasumai na tsafi ne guda bakwai wadanda za'a karantasu kofar kogon darul ikisina ta bude ne, tambaya ta biyu ta yaya kake ganin cewa aljanu Maraful Dauwas zai amince ya fito daga cikin kogon darul ikisina har yaje fadar sarki Nashmir ya sato mana gimbiya Ramlatus siyam alhalin ya tsani duniya da duk abinda ke cikinta, tambaya ta uku ita ce me yasa aljani Maraful Dauwas baiyi tawaye ba a lokacin da mahaifin gimbiya Rashmin yasa aka yi masa dukan kawo wuka har aka kaishi kurkuku, bayan aljanin ya kasance gawurtaccen jarumi mai tarwatsa maza a filin daga. Sa'adda boka Muzafar ya ji wadannan tambayoyi guda uku sai ya bushw da dariya sannan ya ce Ya kai wannan sarki k yi sani cewa makaho baya cewa ayi wasan jifa face ya tabbatar da cewa ya taka hoge, kamar yadda aljani Maraful Dauwas ya gaji wadannan dalasiman tsafin haka nima na gajesu a wajen kakana na uku, kuma duk duniya mutum hudu ne masu wannan dalasuman tsafin sai kuma 236 TASKARNOVELS.COM.NG aljanu uku, a cikin mutane saura mutum biyu jal a raye daga nk sai sarkin birnin Hindu wato mahaifin gimbiya Ramlatus siyam, a cikin aljanu kuwa saura aljani Maraful Dauwas kawai. Dangane da tambaya ta biyu kuwa hakika babu kalaman da zamu fadawa aljani Maraful Dauwas ya amince yayi mana wannan aiki domin dukiya ko mulki basa gabansa, abu daya ne zamu je masa da shi idan muka yi sa'a ya amince, kayi sani cewa a yamma da birnin Misra bayan mutuwar Gimbiya Rashmin da shekaru hamsin an haifi wata kyakkyawar budurwa mai tsananin kama da gimbiya Rashmin tamkar an tsaga kara harma ta fi Rashmin kyawun sura, kai inda za a hada Rashmin da budurwarnan mai suna Rahila da sai mutum yayi tsammanin cewa tagwaye ne, zamu dauki Rahila mu tafi da ita can cikin kogon darul ikisina domin aljani Maraful Dauwas ya ganta da idanunsa, tabbas idan yayi arba da ita zai cika da mamaki wata kila ma yayi tunanin ko fatalwal masoyiyarsa ce Rashmin, nan take sai muyi masa al?awari cewa zamu bashi ita ya aura amman bisa sharadin zai biya mana bukatarmu, ko shakka bana yi nasan aljani Maraful Dauwas zai bari wannan tayi ya wuce shi ba, game da tambayarka ta uku kuwa 237 TASKARNOVELS.COM.NG dalilin da yasa aljani Maraful Dauwas bai yi wa sarki tawaye ba shine akwai alkawari mai karfi da mahaifinsa ya dauka kan cewa har abada shida zuri'arsa baza su taba yi wa sarkk tawaye daga yin bauta ba, face shi da kansa ya daina bukatarsu. Ya kai wannan sarki ka yi sani cewa yanzu take ba tare da bata wani lokaci ba zan daukeka mu aiwatar da wannan gagarumin aikin da ke gabanmu, amman kafin mu tafi sai na kirkiri mai irin kamanninka sak kuma na kwantar da shi bisa gadonka, ya cigaba da rashin lafiya hadimnaka na ci gabada yi masa hidima har izuwa lokacin da zamu dawo saboda mu bagarar da matarka sharlis, domin idan taga baka nan na san tabbas sai ta yi kyakkyawan shiri, kuma muddin ta gano zata iya tarwatsa shirin namu dan dukkanin wani sihirin tsafi da nake takama da shi itama tana da shi, da abu daya kacal na fita, wannan abu ba komai bane face wayo gami da hangen nesa, kasan ance duk wanda ya rigaka kwana dole ne ya rigaka tashi. Koda jin wadannan batutuwa sai sarki Lafaru ya dubi bboka Muzafar cikin tsananin farin ciki ya ce ai nima wayo ne ya ceceni yanzu nayi kamar bani da lafiya har nazo na sameka. 238 TASKARNOVELS.COM.NG Muzafar yayi murmushi yace ai koda baka yi wannan wayo ba, lallai sai na zo gareka a sirrance tunda nayi bincike naga amfaninka a cikar burin rayuwata. Sarki Lafaru ya yi murmushi sannan ya ce da boka Muzafar na rokeka daka gaggauta dauke ni daga cikin wannan gida domin mu tafi biyan bukatar abinda ke gabanmu, ahalin yanzu ji nake kamar akan kaya nake. Kafin sarki Lafaru ya gama rufe bakinsa tuni boka Muzafar ya shafi jikinsa da hannunsa na hagu, kawai sai yaga Husaininsa ya fito daga cikin jikinsa, hatta kayan da ke jikin Husaini iri daya ne babu banbanci ko kadan, kawai sai Husaini ya je ya kwanta akan gadon sarki, boka Muzafar ya sake dafa kafadar Sarki Lafaru nan take suka bace gaba dayansu, basu bayyana a ko ina ba sai a birnin Kufa a gaban wani narkeken aljani mai matukar girma gami da ban tsoro, kuma muninsa ya wuce ayi misali idan mutum ya kalli fuskar aljanin zai iya haukacewa nan take, amman da yake sarki Lafaru ya saba gamo da ire-irensu a baya kafin alkadarinsa ya karye sai bai tsorata ba ainun. 239 TASKARNOVELS.COM.NG Ba tare da bata lokaci ba boka Muzafar ya kama hannun Sarki lafaru ya jashi suka hau kan wannan narkeken aljani sannan Muzafar ya ce Ya kai Marhabul Zaurus maza ka kaimu can yammacin birnin Damaskas a ajiye mu a garin su kyakkyawa Rahila. Da jin wannan umarni sai Aljani Marhabul Zaurus yayi murmushi mai kama da gurnanin zaki ya ce an gama ya shugabana, nan take nakeken aljanin ya bude fukafukansa ya tashi tre da lulawa cikin gajimare yana mai keta gizagizai tamkar tauraruwa mai wutsiya Tafiyar da suka yi bata kai ta rabin sa'a ba suka iso yammacin birnin Damaskas, aljani Marhabul Zaurus ya sakko kasa ya dira bisa turba a bakin kofar wani babban birni wanda suka iske kofar a rufe, dakarun yaki kimanin su dubu suna tsaitsaye a bakin kofar rike da muggan makamai suna gadi. Ba tare da boka Muzafar ya ce da sarki Lafaru wani abu ba sai kawai ya sauka daga kan aljani Marhabul Zaurus ya nufi wajen masu gadin kofar kai tsaye. Koda ganin haka sai Sarki Lafaru ya sauko da sauri ya bishi a baya cikin sauri240 TASKARNOVELS.COM.NG sauri gudu-gudu har ya tarar da hi suka kasara wajen masu gadin kofar a tare. Da zuwansu sai Boka Muzafar ya dubi shugaban dakarun ya daka mashi tsawa sannan ya ce, Ya kai wannan bawan sarki maza ka ruga wajen sarkinku ka fada masa cewa ni boka Muzafar ibn Mauzur gani na dura a kasarsa kuma ina son ya bani aron yarsa Rahila zan dawo da ita bayan kwanaki sittin da biyar. Koda jin wannan batu sai gabadaya dakarun suka kyalkkyale da dariya, haka suka yita yi kamar ba zasu daina ba, daga can sai shugaban nasu ya dubi boka Muzafar ya ce Kai ko wane irin mahaukaci ne, kuma a ina ka taba ganin uba ya bada aron yarsa budurwa balle kyakkyawa kamar Rahila, wai shin zautuwa k yi ko kuma basirarka ce ta toshe? Koda jin haka sai zuciyar boka Muzafar ta kama tafarfasa tamkar zata kone daga can kuma sai ya daga hannu ya sharara wa shugaban dakarun mari, sabida zafin marin sai da yayi katantanwa sau uku kuma yaga taurarin wuya. Boka Muzafar ya dubeahi a fusace tare da cewa ubanka ne ya zautu amman ba ni ba, kuma mai tosashiyar ?wa?walwa... 241 TASKARNOVELS.COM.NG Kafin Muzafar ya gama rufe bakinsa tuni shugaban dakarun da sauran yaransa sun zare makamansu tare da yi masa kawanya, koda ganin haka sai shima boka Muzafar ya zare nasa takobin suka kacame da azababben yaki, shi kuwa sarki Lafaru sai ya buta a bayan wata bishiya yana mai leken abinda ke faruwa. Kaico! Hakika maza sun fadi, lokacin da Sarki Lafaru aga ana wannan gumurzu tsakanin boka Muzafar da dakarun nan sai yaga boka Muzafar ya zame masu alakakai, amman shi gashi a labe ya kasa kai masa dauki sai hawayen takaici ya zubo masa, saboda tunow da cewa da fa shi Gwarzon Sadauki ne mai tarwatsa gungun maza kuma komai yawansu a filin daga, amman yanzu ko mutum daya ba zai iya gwabza yaki da shi ba, domin yana jin rashin karfi a jikin nasa yadda ko takobi ba zai iya dagawa ba. Lokacin da boka Muzafar yaga wannan dakarun yakin su dubu ya zame masu alakakai yana ta kashesu tamkar guguwar annoba ce ta sauka a wannan birni, su kuma sun kasa koda lakutar jikinsa, sai ya raina jarumtarsu, dan haka sai ya maida takobinsa cikin kufe ya ci gaba da gumurzu da su babu makami a hannunsa. Duk 242 TASKARNOVELS.COM.NG wanda ya kawo masa sara ko suka sai ya kauce ya gabza masa naushi daya take zai baje a kasa sumamme. Koda sarki Lafaru ya hango irin wannan tsananin gagarumar jarumtaka da boka Muzafar ke yi, sai ya cika da tsananin mamaki domin ko shi kansa sa'ar da yake da karfin damatsensa bai yi tsammanin ya taba jarumtakar da ta kai irin wannan ba, kuma a cikin tsananin zafin nama kamar haka. Cikin abinda bai wuce dakika hamshin ba, boka Muzafar ya bazar da dukkanin dakarun su dubu a kasa, daga sumammu sai karyayyu babu wanda zai iya mikewa tsaye a cikinsu. Koda ganin haka sai boka Muzafar yasa kafarsa ta dama da doki kofar shiga garin wacce aka yita da zallar bakin karfe, mulmulalle mai tsawon kamu dari gami da fadin kamu saba'in. Nan take kofar ta jijjege daga jikin katangar ta fadi kasa rikica! Karar katuwar kofar ce ta cika garin gabadaya, ta dugunzuma hankalin dukkan mutanen garin har suka fara tsammanin cewa rundunar yaki ce ta kawo masu harin sumame. 243 TASKARNOVELS.COM.NG Nan da nan Sarkin garin da kuma hadimai suka debo makan yki sama da su dubu dari uku suka yi hawa Bisa dawakan tare da sukwanosu zuwa bakin kofar birnin domin su tari Abokan gaba. Da isowar sarki da dakarunsa sai suka cika da tsananin mamaki da suka ga mutum biyu jal sun tunkaresu. Sarkinsu ya dubi boka Muzafar da sarki Lafaru ya daka masu tsawa ya ce Ina sauran dakarun naku suka buya, shin kunzo da wani sabon salon yaki ne da kuke ganin zaku iya cutar da mu da shi ne? Koda jin wannan tambaya sai boka Muzafar ya dubi sarki sannan ya ce mu ba yaki ne ya kawomu ba, ba kuma mu biyu muka zo ba, wadannan masu gadi naku da kuke gani a kasa tamkar tsommokara taurin kai suka yi mana, suka ki isar da sakonmu a gareka, bisa wannan dalili ne na fusata n banke kofar wannan birni naku na shigo. B wani abu ne ya kawo mu ba face mun so ka bamu aron yarka dan tayi mana wani aiki na kwana sittin da biyar kacal, ina mai tabbatar maka da cewa zamu dawo maka da ita 244 TASKARNOVELS.COM.NG cikin aminci da salama kamar yadda muka karbeta daga hannunka. Lokacin da boka Muzafar ya zo nan a zancensa sai sarki da dukkanin dakurunsa suka bushe da dariya, kamar yadda masu gadin kofar suka yi a karon farko, lokaci daya kuma suka tsuke bakinsu suka yi tsit tamkar mutuwa ta gifta ta tsakaninsu. Sarki ya dubi wasu zakwakurarun dakarunsa mutum hudu ya ce da su maza ku kama wannan baki ku kaisu kurkuku ku kullesu, lallai ba kalau suke ba aljanu ne suka shafesu. Gama fadin hakan da wuya sai wadannan dakaru hudun suka tasarwa su Lafaru. Da zuwa sai suka kai hannu zasu cafkesu, cikin matukar zafin nama na gaban kwatance boka Muzafar ya cafi hannun nasu su hudun a kuma lokaci guda ya kakkarya su, tamkar ya karya sillen kara. Dakarun suka rusa ihu tare da gaduwa kasa, kaji aikin sadaukai maganin maza. Koda sarki da sauran dakarunsa suka ga abinda ya faru sai duk suka zare makamansu uka afka wa su boka Muzafar, kawai sai lafaru ya ruga izuwa maboyarsa ya labe, shiko boka Muzafar sai ya tari rundunar shi kadai aka kacame da 245 TASKARNOVELS.COM.NG mummunan yaki. Nan fa boka Muzafar ya gagaresu kuma ya addabesu ya zamana cewa baya saransu da takobinsa sai dai ya kare dukkanin harinsu, sannan ya riga gabza masu naushi da hannu da kafa, komai girman kato idan boka Muzafar ya yi masa naushi daya sai ya kife kasa kuma ba zai sake mikewa ba. Boka Muzafar ya rinka tsale a saman dakarun nan yana shawagi tamkar tsuntsu mai fuka-fukai, yayi tq zubar da su kasa yana masu sarkiya ya hana dawa tsayuwa, kafin rabin sa'a ta cika ya bazar da mutum dari a kasa. Koda sauran dakarun nan suka ga abinda ke faruwa sai suka zubar da makamansu suka mika wuya, sarkinsu ne kawai ya ki mika wuya, kawai sai ya sakko daga kan dokinsa ya gyara tsayiwarsa kuma ya rike takobinsa da hannu biyu ya tsaya cak a waje daya. Koda ganin haka sai boka Muzafar ya dubeshi saman yayi murmushi ya ce Ya kai wannan sarki mene ne dalilin da yasa ba zaka mika wuya a gareni ba, alhalin kasan cewa ba zaka iya samun snasara a kaina ba? 246 TASKARNOVELS.COM.NG Koda jin wannan tambaya sai sarkin yayi ajiyar zuciya cikin alamun takaici ya ce Ya kai wannan Sadauki mai jarumtaka ta ban al'ajabi yi sani cewa har abada sarki sarki ne, bazai taba mika wuya a rabashi da mulkinsa, dukiyarsa ko kuma yayansa ba face bisa dole idan ya ga ya kasa kare kayansa, ya za a yi n dauki yata ta cikin kuma da hannuna na baka ita aro bansan me zaku yi da ita ba, kuma ma bn san ka ba, ai sai dai ku fara kasheni sannan kuje ku dauketa. Da jin wannan batu sai boka Muzafar ya risina ga sarki ikin girmamawa ya kai gaisuwa tare da cewa Ni din nan ba sarki bane na kasance boka ne, amman ina girmama sarauta, ya kai wannan sarki hakika ka burgeni da ka zama mai kishin jama'arka, mulkinka gami da iyalanka. Nikam.ba zan kasheka hakazalika bazan kashe kowa a cikin garin nan ba domin kawai nazo daukar yarka, amman fa duk wanda yayi gigin hanani daukarta to fa lallai ne zai rasa hanaye gami da kafafu, idan har baka son wannan birni naka ya zama na nakasassu ina mai shawartarka daka bani Gimbiya Rahila salin alin na tafi da ita. Da jin hka sai sarki ya daka wa boka Muzafar tsawa ya ce da shi Bafa zai yuwuba, idan har 247 TASKARNOVELS.COM.NG kaga ka tafi da ita totabbas sai dai idan bana numfashi. Lokacin da boka Muzafar ya ji wannan batu sai ya fisata ainun ya zare takobinsa ya ruga izuwa kn sarki, shima sarkin sai ya daga takobinsa sama ya ruga gareshi, saura kiris su hadu sai kawai sukaga gimbiya Rahila ta dako wawan tsalle tare da dura a gabansu, duk su biyu sia suka ja da baya suka yi cirko-cirko kamar zakaru suna masu kallonta cikin mamaki bisa yadda akayi ta bayyana tsulum a gabansu. Gimbiya Rahila ta kalli mahaifinta a lokacin da idanunta suka ciko taf da kwalla, suka fara zubar da hawaye ta ce Haba ya abbana yanzu akna rayuwata kadai sai ka bari a maishe da jama'arka nakasassu, ka tuna cewa a garin nan akwai iyayenka, kakanninka gami da yan uwanka, kuma su ka fara samu kafin ka sameni, kada ka manta ni ya mace nake, mokai daran daewa dole ne muyi aure mu rabu ko da kuwa wani bai zo ya rabani da kai da karfin tsiya ba, ina mai rokonka da ka hakura ka bayar da ni ga wadannan mutanen domin naje nayi masu irin aikin da nake so, sabida bana son mutum daya ya jara cituwa a wannan birni bisa sanadiyyata, 248 TASKARNOVELS.COM.NG daga kjarshe idan da rabon sake saduwa sainkaga na dawo gida, idan kuma na mutu acan sai ka rungumi kaddara domin ita rayuwa tana da lokacinta, idan babu mutuwa ai akwai tsufa da rashin lfiya. Lokacin da Gimbiya Rahila ta zo nan a zancenta sai jikin sarki yayi sanyi, kawai sai ya karasa gareta ya rungumeta suka gashe da kuka tare domin tunda aka haifi Gimbiya Rahila bata taba rabuwa da mahaufinta ba daidai da rana daya, dare da rana suna tare har ta girma ta cika budurwa face makwanci idan dare yayi. Ko da ganin yadda sarki da Rahila ke kuka rabuwa da juna sai tausayinsu ya kama boka Muzafar da sarki Lafaru har basu san sa'adda idanunsu suka cika da kwalla ba. Nan take boka Muzafar ya ji yayi nadama bisa wannan babban buri da yasa a gabashi, tunda ga shi a sanadinyyar haka ya zama bakin takobi mai raba mai masoya. Boka Muzafar ya tuna cewa shifa a yanzu bashi da kowa a duniya iyayensa sun mutu tun yana yaro dan shekara 6 matarsa ta mutu a lokacin da ta zo haihuwar fari, dan cikin nata ma sai ya zo a mace, to tun 249 TASKARNOVELS.COM.NG daga sannan bai sake marmarin yin aure ba, bugu da kari tun yana karami aka kmashi a matsayin bawa, aka daukeshi daga garinsu na asali aka tafi da shi can wata nahiyar da ban da shi da dangin iya balle na baba. A lokacin ne aka siyar da shi ga wani shahararren boka wanda yayita bauta a gareshi har ya shekara ashirin da biyar, a sannan ne mai gidan nasa ya mutu ya gaji sirrinkan tsafinsa saboda tsananin biyayyar da yayi wa mai gidan nasa. Koda boka Muzafar ya tuna cewa shifa yanzu bama zai tuno asalin inane mahaifarsa ba, balle ya tuno da danginsa ba, sai ya koma can gefe daya ya hada kai da gwiywa ya kama kuka. Yana cikin wannan hali ne yaji an dafa kafadarsa, koda ya dago kainsai yaga ashe sarki Lafaru ne tsaye a kansa, koda Lafaru yaga hawaye a cikin idanun boka Muzafar sai jikinsa yayi sanyi sannan ya ce da shi Y kai wannan shu'umin boka kuma sadaukin boye ina dalilin wannan kuka naka alhalin ga shi bukatarmu ta biya, mahaifinta ya hakura zai bamu Gimbiya Rahila. 250 TASKARNOVELS.COM.NG Koda jin wannan tambaya sai boka Muzafar ya yi ajiyar zuciya sannan ya share hawayensa ya ce Ya kai abokin tafiyata, ka sani cewa duniya babu ranar bakin ciki kamar ranar rabuwa da masoyi, hakika na kamu matuka da tausayin wannan sarki da yarsa, bisa yadda zasu yi rabuwar dole ba a son ransu ba, kuma hakan ne ya tuno mani da asalina na kasancewata maraya, wanda ma ba zai iya tuno mahaifarsa ba bare danginsa, hakika kaddara ta yanke mani kauna da farin cikin rayuwa wanda har abada bazan samesu ba domin kowa ya bar gida gid ya barshi. Yayin da sarki Lafaru ya ji haka sai shima ya tuna cewa shima fa yanzu bashi da kowa face mulkinsa sai kuma dukiyarsa da ya baro a birnin Kufa, nan take ya sake tunawa yau fa saura kwanaki arba'in yayi yaki da sarki Nurwas na birnin Zaruk kuma ga shi gashi yanzu ya bar kasar, to wai shin yanzu za a yi wannan yakin ko kuma ba za a yi ba? Idan kuma aka yi yakin suwa za su samu nasara? Shin wannan halifa nasa wanda boka Muzafar ya kirkira zai iya kare birnin daga sharrin sarrki Nurwas da dakarunsa? Shin da gaske ne idan 251 TASKARNOVELS.COM.NG basu samu nasara ba bisa abinda suka fito nema ba shida boka Muzafar dansa Shaddad zai girma ya zama babban makiyinsa har kuma ya kasheshi? Sarki Lafaru yana cikin wannan tunani ne Gimbiya Rahila da mahaifinta suka zo kansa suka tsaya, cikin hanzari boka Muzafar da sarki Lafaru suka mike tsaye suna masu fuskantarsu. Sarkin ya dubi boka ya ce ya kai wannan Sadauki mai jarumtaka ta al'ajabi, kayi sani cewa ban kasance boka ba, dan haka ban san irin aikin da yata zata yi maku ba? Amman da ganin fuskokinku baku yi kama da makaryata ba kuma ba zaku kasance masu kin cika alkawari ba, abu daya nake zargi akanku bai wuce rashin aldalci ba ga duk wanda ke karkashinku sannan zaku iya yin komai dan ganin bukatarku ta biya. Ni dai yanzu ga yata nan na damkata amana a hannunku bana bukatar na ji abinda zaku yi da ita, amman ina son ku kasance masu rike alkawari ku dawo mani da ita lafiya kamar yadda kuka yi alkawari da farko. Idan kuwa kuka ci amanata to kuma amana zata ci ku. 252 TASKARNOVELS.COM.NG Koda gama fadin haka sai sarki ya sake rungume Gimbiya Rahila a kirjinsa tare da fashewa da matsanancin kuka itama kawai ai ta kama kukan, da kyar suka kasi juna kana daga bisani suka yi bankwana. Daga nan sarki da dakarunsa suka juya suka shige cikin birnin na su. Sarki na waigen yarsa gimbiya Rahila yana mai zubar da hawaye, haka itama, haka dai suka ci gaba da daga wa juna annuwa har suka kule. Ba tare da wani bata lokaci ba, boka Muzafar sarki Lafaru da gimbiya Rahila suka fito daga cikin wannan birni inda suka iske aljani Maraful Dauwas a zaune yana jiransu. Nan take duk su ukun suka haye bayan aljani Marhabul Zaurus shi kuwa sai ya bude fuka-fukansa ya tashi sama ya luluka a cikin gajimare sannan ya tsaya cak a cikin iska. Koda ganin haka sai boka Muzafar ya daka masa tsawa tare da cewa Me kake nufine da zaka tsayar da mu cak a sararin samaniya? Cikin razana da biyayya aljani Marhabul Zaurus ya rusuna ya ce Ya shugabana ai baka fada mani inda zamu je ba, umarninka nake jira? 253 TASKARNOVELS.COM.NG Koda jin haka sai boka Muzafar yayi ajiyar zuciya sannan ya ce Yanzu mun hau mataki na farko a wannan gagarumar tafiya da ke gabanmu, saura mataki na biyu wanda shine tafiya zuwa dauko abokan tafiyarmu. Ya kai Marhabul Zaurus na umarceka daka kaimu birnin Misra domin mu sadu da sadauki Haiman, kafin Boka Muzafar ya gama rufe bakinsa tuni aljani Marhabul Zaurus ya dubi bangaren kudu ya falfala da matsanancin gudu cikin gajimare tamkar tauraruwa mai wutsiya. Tunda aka fara wannan tafiya hira ta barke tsakanin sarki Lafaru da boka Muzafar, ita kuwa gimbiya Rahila sai tayi shiru kawai ta kishingida kamar tana yin bacci idanunta a lumshe bata tanka masu ba. Sarki Lafaru ne ya fara yin gyaran murya sannan ya dubi boka Muzafar ya bushe da dariya, al'amari da ya baiwa boka Muzafar mamaki da haushi kenan, ya dubeshi a fusace ya ce ina dalilin wannan dariyar ta ka? Sarki Lafaru ya hadiye rai sannan ya ce Gani nayi ni da kai duk mun kai shekaru dari a duniya amman hr yanzu bamu da kwanciyar 254 TASKARNOVELS.COM.NG hankali, sannan muna da buri mai tsauri a cikin zukatanmu, kamata yayi ace a yanzu muna cikin rayuwar farin ciki da nutsuwa tare da iyalanmu. Da jin wannan batu sai boka Muzafar ayi murmushi sannan ya ce Ai shi rai da kake ganinsa baya rabuwa da buri, daga lokacin da mutum yayi aure babu abinda zai fara tunani sama da haihuwa. Idan ya samu haihuwar sai kuma ya fara tunanin tara dukiyar da zai baiwa dansa, idan tafiya tayi tafiya aka tara abin duniya ya taru sosai sai a fara hangen mulki, idan mulkin ya samu sai a fara hangen daukaka, a lokacin da daukakar ta samu zaka ga tsufa ya fara zuwa, to a Sannan ne lafiya zata yi karanci dan haka sai kaga kullum a cikin neman lafiya ake, wani har ya mutu ba zai samu lafiyar ba, wani kuma sai kaga yau da lafiyar gobe kuma babu, haka dai rayuwa zata kare amman buri bai kare ba walau yaro matashi ko tsoho. Koda boka Muzafar ya zo nan a jawabinsa sai Gimbiya Rahila ta yi caraf ta tari numfashinsa tare da cewa Wanne abu mutum zai yi domin ya iya sarrafa zuciyarsa da kwadayin burika? 255 TASKARNOVELS.COM.NG Boka muzafar ya amsa mata da cewa babu wani abu mai kore burika daga cikin zuciya face ya dauki hakuri, kuma ya rike gaskiya da amana, idan har yayi hak to samu da rashi ba zasu dameshi ba. Rahila tayi murmushi ta ce nda kunyi aiki da wannan maganar da ka fada yanzu da bazaka rabani da mahaifina ba domin kuje ku bayar da ni ga aljani Maraful Dauwas na maye gurbin masoyiyarsa gimbiya Rashmin. Koda jin wannan batu sai boka Muzafar da sarki Lafaru suka zazzaro idanu cikin tsananin mamaki suka kasa cewa komai, tsawon yan dakiku su dukansu sunyi shiru daga can sai boka Muzafar yayi ajiyar zuciya ya ce Yake Gimbiya Rahila ya akayi kika san wannan al'amari namu alhalin baki kasance matsafiya ba, haka shima mahaifinki bai kasance matsafi ba? Rahila ta girgiza kanta cikin alamun takaici sannan ta ce Ashe baku yi mamaki ba lokacin da na bayyana tsulum a tsakiyarku ba sa'adda kai da mahaifina kuke shirin kaurewa da yaki, a cikinku babu wanda yaga ta inda na fito kawai 256 TASKARNOVELS.COM.NG nasan kun ganni ne tsulum a tsakiyarku, to ka sani

Chapter 11 of 14