sharadi don ceton rayuwar
sarki? Baka tsoron cewa idan dabararmu ta yi
nasara sarki ya kubuta fishinsa zai iya tabbata
akanka?". Koda jin wannan batu sai Shurkaib ya
bushe da dariya, sannan ya ce, "Ku a tunaninku
ni ina tsoron mutuwa ne? Ku tuna cewa
shekaruna sun haura casa'in a duniya,
na haifi ya'ya, ya'yanma sun haihu, nayi yakeyake da dama ba adadi. Babu irin masifar da
ban gani ba a duniya, kuma babu wani buri da
ban cika ba face guda daya, kuma yanzu ne na
samu damar da zan cika wannan buri nawa bisa
wannan uzuri da ke gabanmu. Inaa tabbatar
muku da cewa duk dabarar da za ku kawo
domin a kubutar da rayuwar sarki ba za a yi
nasara ba.
Tawa dabarar ce kadai za a bi a samu nasara.
Yanzu na baku dama ku fara gabatar da taku
dabarar idan ba a dace ba sai na fadi tawa, idan
har sarki ya amince da sharadina". Sa'adda
Karbuza da Barsuma suka ji wannan batu, sai
suka fara cika da mamakin Shurkaib suka
tabbatar da cewa da gaske yake. Karbuza ya ce,
"Shi ke nan ai yanzu sai ka zo mu je wajen sarki
domin mu gaggauta yin abin da ya kamata mu
24
TASKARNOVELS.COM.NG
yi domin bata lokacinmuu cikin wannan daji
tamkar baiwa abokan gaba dama ne su rigamu
zuwa inda takobin Saiful Lujara take." Koda jin
haka sai Basuma da Shurkaib suka ce a cikin
hadin baki, "Zancenka dutse ne". Nan take su
ukun suka dawo inda sarki Dujalu ke kwance a
karkashin gawar wannan halitta.
Duk su ukun suka durkusa a gabansa. A
wannan lokaci Hursiya ta tallafo kan sarki
Dujalu ta dura masa ruwa a baki. ya sha. Gama
shan ruwan nasa ke da wuya ya yi arba da su
Karbuza tsugunne a gabansa sai ya fusata ya ce,
"Me kuke jirane har yanzu baku yi tunanin
dabarar da za ku yi ba ta ceto rayuwata?"
Kurbazu ya numfasa ya ce, "Ya shugabana ai
abin da muka je muka tattauna ke nan, kuma
kowannenmu yana da tasa dabarar dabam.
Zamu fara jarraba tawa dabarar, in yaso a
jarraba ta Barmusa, idan tawa ba tai nasara ba,
idan shima tasa bata yi ba sai a jarraba dabarar
Shurkaib.
" Sarki Dujalu ya ce, "Na umarceku da ku aikata
hakan cikin gaggawa domin idan muka kara
kwana hudu anan cikin wannan daji rundunar
Su sarki Maharaz za ta zo ta riskemu. Ni kuwa a
25
TASKARNOVELS.COM.NG
shirina shi ne mu rigasu zuwa tekun bahar
Sufiya ya zamana cewa kafin su isa tuni mun
danko takobin Saiful Lujara." Karbuza ya dubi
dukkanin dakarun aljanun da ke wajen ya ce,
"Na umarceku da ku ruga izuwa cikin wannan
daji ku tsunko murtuka murtukan jijiyoyin
bishiyoyi dogaye ku zo da su yanzu.
Kafin Karbuza ya gama rufe bakinsa tuni gabe
dayan dakarun aljanun sun bace bat! Kafin
cikar dakika sittin sai gasu sun dawo dauke da
dogayen jijiyoyin murtuka-murtukan bishiyoyi
masu yawan gaske tamkar za su yiwa dajin gaba
daya rufi da su. Ba tare da bata lokaci ba
Karbuza ya umarcesu da su kukkulla jijiyoyin
wasu jikin wasu. Nan da nan aka samar da
dogayen igiyoyi na jjiya barkatai.
Karbuza ya saké bada umarnin a daura jijiyoyin
a jikin gawar katuwar halittar. Kowacce
doguwar jijiya daya aka sa kartin aljanu majiya
karfi guda dubu suka riketa. A kalla an sami
sama da aljanu miliyan daya. nan take aka basu
umarni da su ja igiyar sama a lokaci guda,
domin su daga gawar sama daga kan sarki
Dujalu domin sami damar zareshi. Aljanun gaba
dayansu suka tattaro karfin daratsensu suna jan
26
TASKARNOVELS.COM.NG
jijiyoyin a lokaci guda. Maimakon gawar
halittar ta rabu da kasa, sai gaba dayan
jijiyoyinPartFaka daura a jikinta suka tsittsinke,
aljanun suka fado kasa gaba dayansu Al'amarin
da ya baiwa kowa mamaki ke nan a wajen,
kuma hankalisu ya dugunzuma. Sarki Dujalu ya
juyo da wuyansa da kyar ya dubi Barsuma cikin
alamun karayar zuciya ya ce,
"Ya kai Barsuma babban gwarzo, NAMIJIN
DUNIYA, mai dakawa maza gumba a hannu, ka
ga yadda dabarar Karbuza ta kare, kai kuma
wacce dabara ke gareka?" Barsuma yai gyaran
murya sannan ya ce, Ina son aje a nemo mini
giwaye adadin ninkin wannan aljanu sau dari.
Ma'ana kowanne aljani guda giwa dari ce za ta
wakilceshi, sanann a nemo mini dogayen
sarkoki murtuka-murtuka na karfe a daura a
jikin gawar wannan halitta sannan a daura a
jikin giwayen domin su ja sarkar su janye
gawar".
Koda jin hake sai dakarun miliyan dubu daga
cikin aljanun sulka 6ace bat a lokaci guda. Kafin
kiftawar ido sai gasu sun dawo tare da
wadannan giwaye da sarkokin karfe. Kamar
yadda Barmusa ya bada umarni haka aka yi,
27
TASKARNOVELS.COM.NG
amma koda giwayen suka yunkura suka ja
sarkokin karfen, sai sarkokin suka tsittsinike
saboda tsananin nauyin katuwar halittar sai
gani aka y giwayen na faduwa wasu na danne
wasu. Nan fa hankali ya kara dugunzuma fiye
da ko a yaushe, zuciyar sarki Dujalu ta kara
karaya ya fitar da rai ga cikar burin rayuwarsa
ya fara tunanin cewa tabbas ajalinsa ya gabato.
Duk da sanin hakan sai ya yi ta maza ya dubi
Shurkaib ya ce,
"Ya kai tsoho mai dabara, ya kai tudu mai nisan
da yaro ba zai hango ba. Ya kai masanin jiya,
kuma masanin gobe, ka ga yadda dabarun yan
uwanka suka kasan ce. Ka sani cewa karfin
tsafina da karfin damtsena ba za su ceceni ba
daga cikin wannan hali da na shiga ba, wacce
dabara ce da kai wadda in dai aka yi ta zan tsira
da rayuwata?
Na yi maka alkawari idan har ka ceci rayuwata
duk abin da kake bukata zan baka shi in dai
akwai shi anan duniya domin rayuwata ta fishi
daraja a idanuna". Sa'adda tsoho Shurkaib yaji
wannan batu na sarki Dujalu sai ya cika da
tsananin farin ciki bai san sa'adda ya saki
murmushi ba sannan ya dubi Dujalu cikin
28
TASKARNOVELS.COM.NG
nutsuwa ya ce, "Ya shugabana idan na fadi
dabarata ba a cimma nasara ba na yarda kasa a
kasheni a take a wannan wuri. To amma ka sani
cewa ba zan fadi dabarata ba face ka dada
jaddada alkawarin da ka furta yanzu kuma ka
rubutashi a rubuce tare da sa a buga hatiminka".
Koda jin haka sai sarki Dujalu ya girgiza kai
yana mai nuna alamar cewa ya aminta da hakan.
Nan take ya sa aka kawo masa tauwada da
alkalami gami da fatan rubutu.
Har ya dangwalo tawada zai yi rubutun bisa
fatar sai Hursiya ta yi sauri ta rike hannunsa a
lokacin da hawaye ke zuba daga idanunta ta ce,
"Haba ya dan uwana ina amfanin rayuwa idan
buri bai cika ba? Yanzu idan Shurkaib ya ce
abin da muka fito nema ya ke so fa". Koda jin
haka sai kowa da ke wajen yai tsuru-tsuru har
shi kansa sariki Dujalu kuwa.
Shi kuwa tsoho Shurkaib sai ya yi murmushi ya
ce "Ko kadan bani da muradin kayan yakin
MAZAN JIYA" Da jin hake sai sarki Dujalu yai
mumushi, nan take ya yi rubutun yarjejeniya
cewa ya amince duk abin da Shurkaib ya furta
yana so zi bashi bayan dabararsa ta cimma ga
ci. Bayan ya gama rabutawar ne aka kawo
29
TASKARNOVELS.COM.NG
hatimi ya buga, kuma ya mikawa Shurkaib bada
shakkar komaiba. Shurkaib ya karbi fatar
yarjejeniyar ya sanyata cikin aljihunsa sannan
ya dubi gaba dayan aljanun da ke wajen ya
ce,"A cikinku wane ne mafi sanin sirrin hakan
kasa?", Koda jin haka sai wani tsamurmurin
aljani ya daga hannu ya ce, "Yau shekarata dubu
saba'in ina sh akin hakan kabari a garinmu"
Shurkaib ya dubeshi yai murmushi ya ce,
"Matso nan kusa da inda sarki yake. Ina son ka
haka rami karami dai-dai fadin gangar jikin
sarki a farkashinsa yadda zai fada cikin ramin
ba tare da kasa ta zabtare ba gawar wannan
katuwar halitta ta sake danne shi ba". Nan take
kuwa wannan aljani ya bi wannan umarni ya
kama aikinsa. Ko sa'a daya bata cika ba sai ya
kammala aka ga sarki ya fado cikin ramin daga
karkashin katuwar gawar halittar.
Cikin matukar zafin nama akayi sauri ake zare
sarki Dujalu daga cikin ramin. Ai kuwa ana
gama zareshi ke nan sai kasar wajen ta rusa
saboda nauyin gawar halittar, gawar ta lume a
cikin ramin, dajin gaba daya ya kama girgiza
saboda gawar halittar, ta ci gaba da nutsewa
izuwa cikin karkashin kasa. Ba shiri kowa da
30
TASKARNOVELS.COM.NG
kowa ya kama gudu. Sai da aka yi gudu na sa'a
shida sannan aka isa inda kasa bata girgiza
sannan aka tsaya ana haki. Daga inda aka
tsaitsaya ana iya hango yadda komai na
wancana dajin ya nutse izawa cikin farkashin
asa ya zamans cewa ba sauran bishiyoyi da
duwatsu wadanda ake iya hangowa.
A wannan lokaci ne kowa hankalinsa ya dawo
jikinsa. Bayan an nutsu sai sarki Dujalu ya tako
da kafafunsa yazo gaban Shurkaib ya tsaya daf
da shi yadda har suna iya jin numfashin
junansu. Sarki Dujalu ya dubeshi cikin
murmushi ya ce, "Yanzu sai ka fadi muradinka
naji domin na cika alkawarina". Koda jin haka
sai kowa ya yi tsit! Dajin gaba daya yai shiru
tamkar mutuwa ta gifta,
kamar suma sauran halittun da ke dajin sun yi
shiru suna sauraron munafunci. Tsoho
Shurkaib yai gyaran murya ya ce, "Ba wani abu
nake so ka bani ba face auren yar uwarka
gimbiya Hursiya, kuma ba nine mijinta ba, dana
za ka aurawa". Koda sarki Dujalu yaji wamnan
batu sai gaba dayan jiikinsa ya kama karikarwa
saboda tsananin bakin ciki, zuciyarsa ta kama
tafarfasa kamar za ta kone. Nan nan Dujalu yaji
31
TASKARNOVELS.COM.NG
nadama tazo masa bisa alkawarin da ya dauka,
saboda wasu babban siri da ya 6oye a cikin
zuciyarsa wanda duk duniya babu wanda ya
sanshi face shi kadai. Inda sarki Dujalu ya san
cewa abinda Shurkaib zai bukata ke nan da ya
zabi a barshi a cikin halin da yake ciki ya rasa
rayuwarsa,
burinsa ya rushe in yaso gimbiya Hursiya ta
koma gida ta ci gaba da sarauta. Kawai sai aka
ga idanun sarki Dujalu sun kada sun yi jawur
tamkar an gasa danbuda a wuta. Cikin sanyin
jiki ya sunkui da kansa kas ya ce,Lallai zan zamo
mai cika alkawari a gareka bayan mun samo
abin da muka fito nema" Koda gama fadin haka
sai sarki Dujalu ya tafi izuwa gaban wata
korama ya zauna ya kurawa ruwan koramar
idanu yana zubda hawaye.
Ya yin da Hursiya ta ga hakan sai itama ta nufi
inda yake. Koda sarki Dujalu ya waigo ya ga ita
ce ke tahowa gareshi sai yai sauri ya goge
hawayensa. Hursiya tazo ta zauna daf da shi
sannan ta dubeshi cikin murmushi ta ce, ya kai
dan uwana ina dalilin da yasa na ka ga shiga
cikin halin damuwa bisa jin bukatar tsoho
Shurkaib? Shin baka son na auri dansa ne
32
TASKARNOVELS.COM.NG
saboda bai kasance jininmu ba?". Lokacin da
sarki Dujalu yaji wannan tambaya sai ya dubeta
ya maida mata da martanin murmushin cikin
yake sanann ya ce, Ya ke 'yar uwata kiyi sani
cewa bukatar Shurkaib tazo mini da shammace,
ban taba tsammanin cewa kece muradinsa ba
ga dansa. Ki tuna cewa a tarihin
zuri'armu babu wani jininmu da ya taba auren
bare, yanzu gashi Shurkaib zai karya mana
wannan tarihi. Bugu da Kari, ina bakin ciki ace
ranar da babu ni, mulkinmu da dukiyarmu da
duk wannan daukaka da nake nema mana a
yanzu Za ta koma wajen zuri'ar tsoho Shurkaib,
domin idan kika auri dansa tamkar hakan ta
tabbatu ne."
Lokacin da Dujalu yazo nan a zancensa sai
tausayinsa ya kama Hursiya ta rungumeshi ta
fashe da kuka. Shi kuwa sai ya cika da tsananin
farin ciki a cikin zuciyarsa. Hakika rashin sani
yagi dare duhu. Inda Hursiyya ta san sirrin da
sarki Dujalu ya boye ma ta da taji ta tsaneshi
fiye da yadda ta tsani mutuwarta Haka dai
Hursiya da sarki Dujalu suka ci gaba da hira a
nan bakin koramar har izuwa lokaci mai dan
tsawo. Da fatan an tashi lafiya, sannan duk
33
TASKARNOVELS.COM.NG
wanda yake son complete zai iya tuntubata ta
wannan number 08138873799 kira ko
whatsapp. MAZAN JIYA Littafi na biyu 2 Part
C Na Abdulaziz Sani m gini Typing Abubakar
Saleh AlQuyraemey Daga can sai Hursiya ta
dago kai ta dubeshi ta ce, "Ya ki ?an uwana kayi
sani cewa zuciyata ta kasa samun sukuni saboda
rashin jin ci gaban labarin sadauki Hantaru.
Lallai ina son naji yadda karshen rayuwarsa ta
kasance".
Sa'adda sarki Dujalu yaji wannan batu sai ya yi
mrumushi sannan ya ce, "Ya ke yar uwata dama
na san cewa kina cikin kaguwa bisa son jin ci
gaban wannan labari, saboda haka Zan yi iyakar
kofarina na kammala miki wannan labari kafin
wayewar gari, domin so nake gobe da sassafe
mu ci gaba da tafiya domin mu isa tekun bahar
Sufiya akan lokaci, kafn su sarki Maharaz su zo
su riskemu".
Ya yin da Hursiya tajii wannan batu, sai ta cika
da farin ciki ta nutsu tana mai kurawa sarki
Dujalu idanu, shi kuwa sai ya yi gyarsn murya
ya cigaba da ba ta labari kamar haka. Lokacin
da hantaru ya zama katon dutse wannan
jibgegegiyar Micijiyar ta hadiyesthi, sai
34
TASKARNOVELS.COM.NG
macijiyar ta shiga cikin wani irin mugun hali
domin dutsen ya zame ma ta masifa a cikin
cikinta, yai ma ta nauyi, ya ZAmana cewa da
kyar ta ke iya motsawa. Koda taji dutsen na
damunta sai ta fara kokarin ta sake yin amansa
waje da karfin taiya. Idan ta turo dutsen izuwa
makogwaronta sai dutsen ya koma da baya,
wato ya ki yarda ya ito.
Nan fa Macijiyar ta kama tumuwa da kasa, tana
dukan kowacce kusurwa ta kogon da
kawunanta, al'amarin da ya sa gaba dayan
kogon ya ragurguje ke nan ya kama girgiza. A
duk sa'adda micijiyar ta tumu da kasa sai
dutsen cikin cikin nata yaji kamar zai tarwatse
don haka bisa dole dutsen ya taho da kansa
izuwa makogwaronta.
Koda jin hakan sai Macijiyar ta wangame
bakinta wanda dutsen ke ciki, sannan ta sake
wangame wani bakin dabam ta sokashi a cikin
wancan domin ta zaro dutsen. Koda dutsen ya
ga haka sai ya rikide ya zama wuta. Ai kuwa
Macijiyar na hadiye dutsen wutar sai tayi
bindiga ta tarwatse, sassan jiikinta ya yi flla-flla
a kasa tamkar an yankashi gutsun- gutsun, sai
ga dutsen wutar ya gangara Can gefe daya. Nan
35
TASKARNOVELS.COM.NG
take dutsen ya rikida ya zama sadauki Hantaru
kwance kasa, duk jikinsa yai kaca-kaca da
raunika, jini na zuba yana numfashi da kyar
kamar ransa zai fita. A Sannan ne nadama tazo
masa, ya tabbatar da cewa abune mawuyaci ya
sami nasarar daukar takobin daraja a cikin
wannan kogo,
musamman da ya dubi ragowar rijiyoyin da bai
bude ba guda ?ari tara da casa 'in da tara.
Babban abin tsoroa gareshi shi ne, rashin sanin
rijiyar da takobin Saiful Lujara ke ciki, ko
shakka babu kowacce rijiya ba Za a rasa mugun
abu ba a ciki. ldan ya bude wadda ya gamu da
abin da zai hallakashi a ciki shi ke nan burinsa
ya yanke, kuma dak wahalar da ya sha a baya ta
zAma a banza.
Hantaru ya tuno da batun mahaifiyarsa Salimat
wadda ba ita ce ta haifeshi ba amma kuma yana
kaunarta fiye da kowaa rayuwarsa sai kuma
gimbiya Larziya wadda a halin yanzu ya kamu
da tsananin begenta har ya amince ya sallama
rayuwarsa domin ya mallaketa. Hantaru ya
tuno da batun cin amanar da mahaifiyarsa ta
jini ta yiwa sarki Kusaidu ita da boka Ardusa.
Lallai yana son ya koma birnin Kisra domin ya
36
TASKARNOVELS.COM.NG
yiwa Farzira da boka Ardusa hukunci bisa
wannan cin amana, kuma ya sadu da sarki
Kusaidu wanda ke matukar kaunarsa a
matsayin dan cikinsa. To amma ai Salimat ta
gargadeshi akan kada ya taba lafiyar Zarifa. Abu
na biyu da ya fadowa Hantaru a rai shi ne, batun
alkawarin da ya ?
aukarwa gimbiya Lazirina cewar duk wuya duk
rintsi ba za su rabu ba, kuma duk bukatar da
tazo masa da ita zai biya ma ta ita. Koda
Hantaru yazo nan a tunaninsa sai zuciyarsa ta
karaya, ya fara tunanin hanyar da zai bi ya yi
jinyar jikinshi sannan ya ci gaba da bude
ragowar rijiyoyin guda dari tara da casa'in da
tara har ya sami wadda takobin Saifal Lujara ke
ciki. Hantaru ya tambayi kansa a cikin ziciyarsa
ya ce, "Yanzu ta ya ya zan reyu a cikin wannan
kogon dutse babu ruwa babu abinci?" Koda
aiyana hakan,
sai idanunsa suka kai kan sassan jikin
Macijiyar da ya kashe da kuma jinin jikinta da ya
malala ya cika kasan kogon wanda za a iya yin
wanka a cikinsa. Hantaru ta daga kansa sama ya
yi arba da wasu tsirarun ciyayi da kananan
bishiyoyi da tsirai da suka tofo a cikin dutsen,
37
TASKARNOVELS.COM.NG
sai farin cilki ya kama shi, don ya fahimci cewa
zai iya rayuwa a cikin kogon izuwa tsawon
kwanaki kadan. Hantaru ta daga kansa sama ya
yi arba da wasu tsirarun ciyayi da kananan
bishiyoyi da tsirai da suka tofo a cikin dutsen,
sai farin cilki ya kamna shi, don ya fahimci cewa
zai iya rayuwa a cikin kogon izuwa tsawon
kwanaki kadan.
Hantaru ya fara da tunanin abinda ya kamata ya
fara yi a yanzu tun da gashi har jiri ya fara
dibarsa sakamakon jinin da ke zuba daga
raunikan jikinsa Lallai ya zama dole ya yi
tunanin abin da zai ya tsaida jinin. Cikin
matukar karfin hali ya mike tsaye yana tangadi
ya kama hawa kan duwatsun dake cikin kogon
yana dogarawa ya isa inda ya hango wata
bishiya mai faffadan ganye.
Sai da ya rage saura baifi taku uku be ya isa inda
bishiyar take sai ya zame ya fado kasa Haka dai
ya daure ya sake tashi ya hau kan ?utse. A karo
na biyu ma bai nasara ba sai ya fado. A karo na
uku ne ya samu dama da kyar ya tsinko ganyen
ya fado kasa a matukar galabaice. Da jen ciki
yaje inda wata busasshiyar karamar bishiya
take ya karyo kirare a jikinta, ya sake dawowa
38
TASKARNOVELS.COM.NG
da baya ya dauki duwatsun wuta biyu ya dinga
gogasu akan wadannan kirare har wuta ta
kama A haka ne ya dinga narka ganyan wannan
bishiya da ya karyo yana mannashi a jikin
raunikan jikinsa. Duk sa'adda ya manna ganyen
sai yaji kamar ya kurrma ihu saboda tsananin
zafi da zogin da ke shigarsa.
Har wani irin gumi da haweyen azaba ne ke
zubo masa. Bayan ya gama sa maganin a jikin
dukkanin raunikan jikinsa ne ya kwanta ya huta
tsawon rabin saa a sannan ne jini ya daina zuba
daga jikinsa ya dawo cikin haiyacinsa sosai. Nan
take Hantaru ya mike zaune ya tsinto sassan
jikin Macijiyar nan ya soka a jikin itace ya gasa,
wato yai tsire.
Haka ya ci gaba da gasa naman Macijiyar har ya
gasa mai yawa ya zamana Cewa naman ya gasu
sosai yadda zai kwana biyu bai lalace ba. Daga
wannan rana Hantaru ya ci gaba da rayuwaa
cikin wannan kogo yana mai ci gaba da jinyar
jikinsa domin ba zai iya ci gaba da bude Sauran
rijiyoyin ba, ya zamana cewa bashi da abinci sai
wannan gasasshen naman Macijiyar, kuma
bashi da ruwan sha sai jininta da ya malala a
kasa. Har sai da jinin Macijiyar ya daskare ya
39
TASKARNOVELS.COM.NG
ZAmana cewa sai ya sareshi da takobi yake sha.
Wannan gasashen naman kuwa sai ya lalace ya
rube har ma ya fara tsutsa, amma a hakan yake
cinsa domin ya rayu kada yunwa ta kashe shi.
Hantaru dai bai samu cikakkiyar lafiya ba sai
bayan kwana goma sha uku. ranar kwana na
goma sha ukun ne Hantaru ya je gaban rijiya ta
biyu ya tsaya yana shawara da zuciyarsa akan
ya budeta ko kada ya bude.
Da zarar ya kai hannu da nufin zai sare mukullin
rijiyar sai hannunsa ya kama karkarwa ya kasa
saboda tsoron kada ya budo abin da yafi na
rijiyar farko balai wanda ka iya zama sanadin
ajalinsa gaba daya. Sai da Hantaru ya jarraba
hakan sai ya kasa sare mukulin, Nan take
Hantaru ya tuno da irin gwagwarmayar da ya
sha a baya da lamarin da ke gabansa na auren
gimbiya Larziya da batun komawa birnin Sin,
sei kawai yi kanin tsoro ya kau dagA zaciyaraa
Nan take ya daga takobinsa sama yana kurma
ihu ya sare makullin.
Nen take murfin rijiyar ya fadi cen gefe daya.
Bisa mamaki sei baiga komai ba Hantaru ya
sake rike takobinasa da kyau ya gyara tsayuwa
ya jiran yaga abinda da zai fito daga cikin rijiyar.
40
TASKARNOVELS.COM.NG
koda ya ji shiru sai ya matsa gaba da nufin ya
wuce kan rijiya ta uku itama ya budeta. Yana
gifta wennan rijiya ta kwatsam sai ya jiyo wani
irin gurnani irin wanda bai ta6a ji ba da huci na
busowa. Cikin razAni Hantaru ya ja aa beya ya
sake gyara tsayuwa Wani irin dogon hannun
bil'adama ne lafcece ya fara lekowa daga cikin
rijiyar,
sannan hannu na biyu ya leko. Daga can kuma
sai ga mutum ya taso sama a hankali gama
mikewa gaba daya. A sannAn ne Hantaru ya gA
she maridi ne. Tun da Hantaru yazo duniya bai
taba ganin bil'adama mai tsananin tsawo da
kauri ba tamkar wannan maridi, domin ita dai
rijiyar zurfinta ya kai kamu dubu, amma gashi
ta yiwa maridin kadan, tsugunnawa ma yai a
cikinta.
Fadinta ya kai kamu arba'in, amma da kyar
maridin ya fito daga cikinta, sai da ya muskuta
kirjinsa sannan ya sami damar fitowa. Hantaru
ya karewa wannan maridi kallo daga sama har
kasa sai zuciyarsa ta karaya ya tabbatar da
Cewa rayuwarsa na tsakanin RAI DA MUTUWA.
Kawai sai yaja da baya ya takure a jikin bangon
kogon, amman bai yar da takobinsa ba. Maridin
41
TASKARNOVELS.COM.NG
ya wangame katon bakinsa ya kurma wani ihu,
wanda ya haddasa girgizar kogon gaba ?aya har
duwatsu kanana suka rinka zubowa kasa. Karar
ihun tasa Hantaru ya yarda takobinsa ya rufe
kunnuwansa har ya tsugunna kasSa yana
neman maboya, domin ji ya yi kamar dodon
kunnensa zai fado kasa. Nan take maridin ya
shako wuyan Hantaru ta baya da
'yan yatsun hannunsa biyu ya ?aga sama
tamkar ya dauki fara, sai ga kafafun Hantaru na
wutsi-wutsil, gaba daya jikinsa na reto. Maridin
ya tsaya yana tunanin irin kisan da ya kamata ya
yiwa Hantaru. Da farko sai ya dunkule hannu ya
kai masa wawan naushi a fuska. Duk da cewa
yana ruke da wuyan Hantaru gam- sai da
Hantaru yi waf ya zunguri idon maridin da f
kafa, domin ya tabbatar da cewa idan maridin
ya gabza masa
Wannan naushi, sai ya tatitse fatarsa tamkar an
taka ayaba akan dutse. Tsokanewar idon da
Hantaru ya yiwa maridin ne yasa ya dimauce ya
saki wuyan Hantaru ya fado kasa, amma huk da
haka sai da hannun Maridin ya nutse a cikin
bangon kogon dutsen tamkar ansa diga da
guduma an buga a cikin bengo sai gashi ya
42
TASKARNOVELS.COM.NG
haddasa wawakeken rami ajikin bangon, amma
bai ji zafin komai ba a hannunsa tamkar ma
takarda ya huda. A fusece maridin ya juyo ya
?aga kafarsa pa y kawowa Hantaru mugun taku.
Cikin matukar zafin nama Hantaru ya goce ya
bar inda yake. Sai ga kafar Maridin ta lume a
cikin kasa iya kaurin gwiwarsa.
De ya zare kafarsa kuwa sai ga rami zururu
wanda za a iya saka mutum uku a ciki a
binnesu. Nan fa aka fara guje guje tsankanin
Hantaru da Maridin a cikin kogon, yana kai
masa wawan naushi da bugu da hannu da kafa
shi kuma yana gOcewa da zallewa. Dak inda
maridin ya gabza sai ya haddasa mugun rami,
walau bango ko kan kasa. Al'amarin da ya janyo
gaba dayan kogon ya
kama rugujewa. Sai ga kafar Maridin ta lume a
cikin kasa iya kaurin gwiwarsa. De ya zare
kafarsa kuwa sai ga rami zururu wanda za a iya
saka mutum uku a ciki a binnesu. Nan fa aka
fara guje guje tsankanin Hantaru da Maridin a
cikin kogon, yana kai masa wawan naushi da
bugu da hannu da kafa shi kuma yana gOcewa
da zallewa. Dak inda maridin ya gabza sai ya
haddasa mugun rami, walau bango ko kan kasa.
43
TASKARNOVELS.COM.NG
Al'amarin da ya janyo gaba dayan kogon ya
kama rugujewa ke nan, ya zamana cewa shi
kansa maridin hankalinsa ya tashi, don haka sai
ya koma gefe daya ya tsaya cak Yana hanki suka
kara kallon- kallo tsakaninsa da Hantaru.
Babban abin da ya fi tayarwa da Hantaru
hankali shi ne, kofar kogon ta rufe ruf, babu ta
inda ma zai iya fita bare ya nemi hanyar gudu
sakamakon rugujewar da kogon ya yi, manyan
duwatsu suka rikito kasa.
Nan fa Hantaru ya aiyana a ransa cewa bashi da
wata mafita face ya tunkari wannan maridi ya
San dabarar da zai bullo masa ya kashe shi.
Dole ne ayi daya cikin biyu, ko shi maridin ya
sami nasara ko shi Hantaru ya samu.
44
TASKARNOVELS.COM.NG
Kamar hadin baki sai maridin da Hantara suka
wangame baki a lokaci guda kowannensu y
kama kwarara ihu.
Abin da ya ?aurewa maridin kai kenan, domin a
wannan karon ihun maridin bai ruda Hantaru
ba, bare ya dimauce har ya toshe kunnuwansa.
Tun da wannan maridi ya wanzu a cikin wannan
kogo tsawon daruruwan shekaru bai ta6a ihu ba
ga duk abin da ya shigo abin ya iya jurewa ba.
Kai bama mutum ba hatta aljan idan yana
Wannan ihu nasa firgicewa suke, wasu su kama
gudawa, Wasu ma sanadiyyar kurmancewarsu
ke nAn.
Idan kuwa mutane ne ma take suke haukacewa,
amma yanzu sai gashi Hantaru ya jure masifar
ihun nasa harma yanA mai da martani da Dasa
ihun.
45
TASKARNOVELS.COM.NG
A zahirin gaskiya Hantaru bu karamar juriya ya
yi ba a wannan karon, domin gaba dayan jikinsa
ya kama tsuma da karkarwa domin ji yake
kamar an dura masa kwari masu yawa ba adadi
a cikin kunnuwansa, suna tsinttsinka jijiyoyin
kunnen, kuma yana jin kamar ana tsotse jinin
jikinsa.
Bayan kowannensu ya yi ihu da kururuwa har
gabadaya kogon ya gama rugujewa, duwatsun
suma suka rikito kasa, al'amarin da ya janyo
Hantaru ya sami sababbin raunika ke nan a
sassan jikinsa, in banda ma yana gocewa da tuni
manyan duwatsu sun danneshi. Shi kansa
Hantaru ya san cewa tsananin sa'a ne kawai ya
ceceshi a cikin wannan kogo, sa'adda yake
rugujewar amma ba zafin namansa ba.
Koda gama rugujewar kogon sai Maridin ya
falfalo da gudu yana take duwatsu suna
rumurmushewa, ya yiwo kan Hantaru gadangadan. Koda Hantaru ya ga mutuwa ta
durfafoshi sai shima ya yi ta maza ya ruga izuwa
kan maridin Shima yana mai ci gaba da kwarara
46
TASKARNOVELS.COM.NG
ihu shima, maridin yana nasa ihun, kowannensu
tafe yake cikin mugun nufi, kai da gani ka san
cewa idan akayi wannan gamo dole ne mutuwa
ta sami rabonta Sai da ya rage bafisaura taku
daya ba A tsakaninsu ba sai Hantaru ya yi sufa a
kasa tamkar akan kankara mai santsi yake ya
shiga karkashin Maridin ya takarkare iya
karfinsa ya gabza masa naushi da hannaye biyu
a marainansa.
Take maridin ya yi suman tsaye ya kame kamar
ya zamo gunki. Cikin zafin nama Hantaru ya
mike zumbur ta bayan maridin yasa guiwar
hannunsa ya doki tsakiyar hannun maridin na
hagu. Take hannun ya karye ya yi kara kas!
Maridin ya kurma ihu ya juyo a fusace ya
kawowa Hantaru mangari da daya hannun nasa.
Cikin sa'a kuwa ya sami Hantaru a kirji. Karfin
mangarin ne yasa Hantaru yai sama ya fado
kasa kan dutse ya baje a sume.
Maridin ya yunkura da kyar
All Chapters
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 2 Chapter of 14