Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

what.

Bakinshi ya daura kan goshin yaron ya sumbaci yaron yana murmushi sanan yama yaron huduba ya karbi dabinon dasuka sayo da zasuzo yatauna yabama yaron yabashi ruwan zamzam, yadago kanshi ya kalli Mom yace "Mom sunan d'ana Arham Waleed Warbai" shiru Mom tayi tana kallon Waleed din for few seconds itama Ilham saida tabude ido gabanta nafaduwa ko Waleed yagane ne saisa yabama yaron sunan Arham sosai ta birkice saikuma cikeda siyasa tace "d'ana yawani kama yayi kama da abokin ka saikuma kawani bashi sunan shi" karban yaron Mom tayi tace "Allah ya rayaka Arham, daidai nan aka bude kofa Ammi ce ta shigo yar aikinta abayanta da direba rikeda basket din abinci, tace "ku yakuri ai danaji ya'ta ta haihu kitchen na koma da kaina namata abincin da maijego yakamata taci, sassanunku now ina Dr da nurses din dasuka karbi haihuwan jikana kuga" tawuce tafita waje tana kwalama nurses da Dr kira, duk wanda yazo bashi bandir din yan dari biyar guda take zukuga yanda aka cika Mummy sai murmushi take, saida ta rabar da kudin tass sanan ta shigo dakin ta kalli Mummy Ilham tace "bakin ciki kikemin ne aminiyata bazaki tashi akan kujera na zauna na dauki jikana ba"? Kwashewa da dariya akayi, Mummy ta tashi daga kujeran tace "maida wukan dadin abin nidai kafin nayi wanan jikan naki nayi wasu balle amin yanga" zama Ammi tayi tace "yanga yanzu kika fara gani" all this maganganun ko Waleed dake zaune bata kalla ba, saisa ma bataje gadon ta duba Ilham ba sabida yana wurin, ahankali Mom ta taho rikeda Arham junior sanan tamikama Ammi shi ahankali tace "ga Arham Waleed Warbai, Arham karami" Mom tai maganan tana kallon fuskarta kaman yanda itama Ammi tadago tana kallon fuskar Mom kafin ahankali tadaura fuskarta kan yaron, shiru tayi ganin yaron kaman Arham yay kaki, dudda yaron jariri ne but kamannin was so obvious da kana gani zaka gane da Arham yake kama, gabaki daya Ammi jitayi duk wanan farin cikin da murnan nan da rawan jikin datake yi na zatazo taga jikanta yakoma ciki, abinda ma yafi bata abin shine sunan dataji Waleed yasamai, kuma tai alkawari bazata sake shiga rayuwan shiba kaman yanda yafadi, so yasaka sunan abokinshi ma danshi danyaci mata mutunci itakuma bazata cemai komiba ya kyauta, murmushi kawai tayi tace "Allah rayaka Ar.....an jikalle" tafadi ahankali danta kasa kiran sunan Arham din, bude kofa akayi Baban Ilham ya shigo ciki yana ganin Waleed yace "assha, sannu son wanan daurin asibiti ai saikafi shekara baka warkewa tashi muje nakaika wajen wani mai dauri yana maka zaka warke cikin sati tashi muje" yay maganan yana kallon Waleed tashi yayi ahankali yabita gaban Ammi da kanta kekan jaririn, suka wuce suka fita, a mota baban Ilham ya daukeshi sai janshi yake da hira amman baya wani iya amsawa da kyau dan nauyin mutumin yakeji, agaban wani gida yaga sunyi parkin, fitowa sukayi baban Ilham yace "muje" shiga sukayi har wani dankareren falo inda wani mutumi ke zaune, Baban Ilham yace "Barka da rana malam, ga dana nan ya karye akafada munzo agyaramai" tashi baban yayi yazo yadaura hannunshi kan wajen saida Waleed ya yatsine fuska sabida zafi, Baban yace "ba karaya bace kashi ce ta goce ina gyarawa yanzu shikenan" da sauri Baban Ilham yace "kagani ko babu abinda asibiti suka iya indai kan dauri ne, yace Baba ayi mun gode" kwalama wasu maza kira Baba yayi, Waleed yaga wasu karfafan maza su kusan shidda sun shigo, hannu Baba yasa ya warware daurin sanan aka rike Waleed din, addu'a Baba yayi yatofa kan kafadar sanan yakai hannunshi kan wajen yafar kokarin saita kashin sosai Waleed yaso yadaure dayaga azaban ba nan bane yafara kokarin kwace kanshi amman ko motsi baya iyayi, da azaba yay azaba kuka yafara kaman zai mutu Baban Ilham sai sannu yakemai kusan awa daya aka dauka a hannun sanan baban ya gyara tsaf aka sakeshi da sauri yasa hannu yana share hawayen Baban Ilham sai sannu yakemai, magani Baba ya shafamai akafadar yace "ka warke baka bukatan wani dauri kuma angama" kudi Baban Ilham yaciro mai yawa yabiya mai sanan suka tafi.







Duk suna zaune adakin Dr ta shigo ta duba Ilham sanan tabasu sallama tawuce tafita, ahankali Mummy tace "aminiya natafi da ita gida tai jego ne?" ada Ammi tai alkawari bazata je jegon gidaba amman sai kawai taji gwara sun tafi, gyama Mummy kai tayi tace "eh kuwuce kuma a kulamin da matan d'a da jika da kyau, suna arba'in zanzo na kwashi abuna wlh" duk akai dariya Mummy tace "nina nafi kowa sanin bala'in ki ai bazanyi wasa ba yallabiya" tai maganan tana kallon kofa ganin anbude Baba ne da Waleed da idanunshi sukai jajir da sauri Mom tai wajen Waleed din tace "sannu Dan Yaro an gyara" gyadamata kai yayi, Baba yace "bama karaya bace ashe gocewar kashi ne yanzu an gyara an shafamai magani, Allah yabashi lpy" ahankali Mom tace "angode Alhaji" Mummy tace "Allah baka lpy" itadai Ammi tai kaman bataji su ba, Mummy ne tace "Alhaji an sallamemu mutafi dasu gida, agida zatai jego" da sauri Baba yace "to bari nakai kayan mota" daukan kaya yashiga yi Waleed yaje zai tayashi da sauri Baba yace "kaga jeka zauna kaida hannu ba lafiya ne zakadau abu jeka huta" yay maganan yana fita, ganin haka yasa Mom ta shiga tayashi suka kwashe komi sukakai mota, sanan Waleed yadau hijab yabama Ilham tasaka ahankali yace "test me all that you need zan aiko miki dashi" murmushi tayi ya gyadamai kai ganin yana wani ji da ita kodan ta haifamai d'a ne, kofa yabude mata tafita suka jera atare tana tafiya ahankali har motar Baba ta shiga ta zauna sanan ya matsa ganin Ammi tazo baby ta shiga ta bama Mummy sanan suka rufe musu motar suka tafi Ammi tajuya tai motar ta ta shige direba yajata banda Waleed daya tsaya chak awajen, ahankali Mom tace "mutafi" daga kafa yayi yawuce ya shiga motar ta suka tafi, gida sukaje yana fitowa flat dinshi yaje kwanciya kawai yayi, yaciro wayarshi number Arham yakira amman harta gama ringing bai dauka ba, 3 miss calls yamai ganin bai dauka ba yasa yamai message.

_"Hey blood, I called no answer I guess you are still angry with me, I called nafada maka Khadija ta haihu, an sami baby boy, yaron yay kama dakai sosai blood, and do you know what's even great? Yaci sunanka, sunanshi Arham Waleed Warbai, blood you mean alot to me, u make my life colourful, I am sorry idan maganan dana maka jiya kajita somehow I was just trying to know what you've been up to lately, and I am also sorry akan abinda Ammi na tamaka please forgive us, take care, anjima zan shigo_"

Yaturamai sakon tareda lumshe ido bacci na saceshi kafin baccin yay nasaran daukeshi.
[17/10, 18:47] Aishat Muhammad: 💫 _TWO DIFFERENT WORLD_ 💫





✍️ M SHAKUR





3️⃣2️⃣ & 3️⃣3️⃣





Wuraren karfe biyun rana ya farka, sosai yaji karfin jikinshi kawai gajiya yakeji bawani abuba, tashi yayi dagakan gadon yaje gaban madubi ya tsaya ya kalli kwayar idanunshi na dama ganin har yanzu akwai jini aciki yasa yabar gaban madubin yana tunanin inya fita anjima zai tsaya a pharmacy yasai maganin dazai saka jinin idanun ya washe, bathroom ya shiga, wanka yayi yasake yin brush sanan yafito, wardrobe dinshi yaje yadauko wasu native, farin yadi ne mai taushi da akamai jumper yasaka sanan yadau turare yafeshe kanshi dashi, dadduma yahau yay sallan azahar sanan ya zira takalmi bayan yadauki wallet dinshi yafito, side din Ammi yayi gabanshi nafaduwa, ahankali yabude kofar ya shiga hada ido yayi da Ammi dake zaune kan dogon kujera hannunta rikeda remote ko taji zai shigo ajikinta ne oho dayasa take kallon kofar oho, suna hada ido ta ijiye remote din ta tashi daga kan kujeran da sauri ya shigo dakin yamaida kofan yarufe yace "Ammi, Ammi please wait" sama Ammi tayi da sauri yabita kafin yakai harta shige dakinta tarufe da key dan bamata son ya shigo, tsayawa jikin kofar yayi yay shiru, yakai kusan 5min ahaka sanan yace "Ammi please listen to me, kiyakuri kinji please Ammi na" yay maganan ahankali yana knocking kofarta yakai kusan 10min ahaka awurn ganin bamata da niyyan bude kofan yasa yawuce ya sauka kasa, dinning yaje yazauna sabida shegen yunwa yakeji, warmer yabubbude, tuwon shinkafa yagani da vegetable soup, zubawa yayi baima wani iyaci da yawaba yasha ruwa yamike tsaye key motar Ammi dake kan centre table yadauka yawuce yafita, motar ta ya shiga ya zauna sanan yaciro wayarshi ganin har lokacin Arham baimai reply din message dinshi ba yasa yatada motar direba yabude mai yawuce yafita daga gidan.


Agaban gidansu Arham yay parking motarshi yabude yafito yatura gate ya shiga gidan, babu kowa a tsakar gidan, sallama yayi yabude kofa ya shiga falon Mama ce ta amsa mai ahankali, saikuma tasaki murmushi tace "Waleed kaida bakaji sauki bane ba kafito? Ya karfin jikin? Maman ka takirani ta sanar dani abin farin cikin daya samemu ubangiji Allah ya raya, ya dayyaba, ya sunan yaron ne"? Murmushi yayi yace "sunanshi Arham Mama" wani iri Mama taji jikinta yay sanyi, sanyin ma karara hakan yasa tama kasa magana, lurada yanayin ta yasa Waleed yace "Mama ina Arham yana nan"? Cikin dan fushi tace "ohon mai rabona dasa Arham a idanuna kwana uku kenan yau" mikewa da sauri Waleed yayi yay corridor falon shiga yayi direct yay gaban dakin Arham, knocking kofar yayi yakirashi. "blood" jin shiru yasa yatura kofar ahankali ya shiga cikin dakin, dakin babu haske sai uban duhu, ahankali yamika hannunshi ya kunna switch hakan yasa dakin yya haske, Arham ya hango kwance kan gado bai lulluba ba dagashi sai gajeren wando fuskarshi ta kumbura suntum tsabagen dukan dayaci, jikinshi duk tabon ciwo dawani irin sauri Waleed yay gadon yace "subhallahi blood who did this to you eh? Waya maka haka"? Yay maganan yana dago Arham zaune, tashi zaune Arham yayi yana wani irin kallon Waleed din da sauri Waleed ya sauka yay bayinshi, ruwan zafi ya dauko yajefa towel ciki yazo yazauna akan gadon cikeda tausayi ya matso towel din kaman zaiyi kuka yakai kan fuskarshi yana dannamai yace "blood am so sorry, am ashamed of abinda Ammi na tasa aka maka, look what they did to you, this people are heartless, sorry blood" yay maganan yana gaggasamai, ijiye ruwan akasa Waleed yayi bayan yagama yasauka daga kan gadon yanabin dakin dayay kacha kacha da kallo yace "kasha any medication, kaci abinci?" dudduba dakin yayi ganin baiga maganin anything ba yasa yadau ruwan yakai bayi yafito sanan yadawo kan gadon, hannunshi yadaura kan kafadar Arham yana kallonshi kaman yanda Arham din ke kallonshi, ahankali yace "talk to me blood meke maka ciwo eh? Sanan wani abinci zakaci let me go out and get it for you, kafada min please ina da ina ke maka ciwo mow"? Wani irin kallo Arham kemai kafin ahankali yakai hannunshi ya kabar da hannun Waleed daga kan kafadarshi yace "wato halinka Waleed naban mamaki" ahankali Waleed na kallonshi yace "halina blood kaman ya"? Dan murmushi Arham yayi yakai hannunshi ya share fuskarshi dahar lokacin lema leman ruwan da Waleed yagasamai jiki kekai yace "kaida uwarka kunsan polisawa sunzo sun kamani sunmin bugun mahangurba shine yanzu zakaso kana wani rawan jiki kana bani kulawa kaman bakasan hakan yafaru ba" sassauta murya Waleed yayi ahankali yace "blood listen to me, I have no reasons to lie to you koda chan banmaka karyaba yanzu ne zan maka karya, believe me bansan Ammi tasa amaka abu makamancin hakaba, a lokacin danasani saida nasa aka janye aka sakeka, blood you are my only friend danai basing life dina dashi in this world, bazan taba hurting nakaba no matter what, besides you are morethan a friend to me, you are my blood Arham" tabe baki Arham yayi sanan ya nunashi da yatsa yace "ku masu kudin nan feels zaku iya duk yanda kukaga dama aduk lokacin dakuka so, zaku iya duk yanda kuka so aduk lokacin dakukaga dama, listen to me Waleed wlh zan gwadama aduniyan nan dudda uban kudinga, kadaiga mahaifinka nada kampany akasan waje dake gina boat dawasu kampanoni, mahaifiyarka nada kampany da business da dama ko, amman wlh zan nuna maka duk wayan nan kudin da dukiyan dakuka tara bazai taimakeka da komiba saika gane kurinka Waleed" shiru Waleed yayi yana kallon idanun Arham, all he could see was hatred, tsantsan tsana kawai yake gani a kwayar idanun Arham, wani iri yaji yanaji kaman zaiyi kuka saikuma yahana kanshi, ahankali yana kallon Arham din yace "Arham all wanan fadan da maganganun is it akan kawai natambayeka ina kake kai kudin ka? But why do I feel kaman there's more to this case, blood na kalli idanunka abu daya kawai nake gani shine tsantsan tsana ta, blood mena maka? Menataba maka? What have I done to you please kafadi mini watakila bansani ba please tell me kaji my friend" da sauri Arham yanuna kanshi yace "friend? Nine friend dinka Waleed? I can never be a friend to rich kids sabida all they know is sumaka ihu, suyi controlling naka, suyi matching naka and step your your neck aduk lokacin dasukaga dama, Waleed zaka iya tuna how many times kakemin ihu kakemin tsawa in your office kanamin fada"? Wani irin hawaye ne Waleed yaji sun gangaromai shaaarr, hannu Arham yanunamai yace "ba kuka nace kamin ba tambayanka nayi, kasan how many times kakemin ihu aka a office"? Girgiza mai kai Waleed yayi ahankali kafin yafuzar da iska yasa hannu ya share idanunshi tass sanan yanisa yace "I never meant all those shout, badan cin mutunci kowani abubane yasa nayi hakaba, Blood kasanni sama da kowa, and you know how passionate I am towards my work at the orphanage, idan yazo takan orphanage dina ne banson wasa kawai strictly work saisa I do all those to you sabida kai aikin da yakamata kayi, but tunda har ahaka kadauki abun ka fassara am sorry for that too I didn't do it because am rich or whatever I do it cus I feel is my own way of motivating my staff to do more, to perform better, idan akazo kan human resources management akwai two ways of motivating a staff, akwai positive motivation and negative motivation, I guess mine was the negative one but kayakuri" ya karashe maganan ahankali muryanshi tayi sanyi sosai, tabe baki Arham yayi yace "orphanage orphanage orphanage, staff, staff, staff, Mr, Dr. Waleed Warbai the chief CEO of Warbai orphanage home and home of the disables how does the name sound"? Yatambayi Waleed dake kallonshi cikin yanayi na isgilanci sanan yaydan murmushi yace "I will make you a promise yau dinan akuma gabanka, Waleed kome kaci sai Arham yaci! Waleed kome kasaka sai Arham yasaka! Waleed kome kahau sai Arham yahau! Waleed kowani matsayi ka taka sai Arham yataka shima! Sai last thing dazan fada maka is over between us" da sauri Waleed ya kallai, gyadamai kai Arham yayi yace "yes is over tsakanina dakai Dr Waleed Warbai, we should go our separate ways, yanzun haka danake maka magana my resignation letter na gidan marayun ka duk lokacin dakaje za'a baka, ka kama gabanka nakama gabana, daidai da silebiyar dinka karka sake bama Mahaifiyata, Arham bai sanka ba bai san dazaman kaba kaima do me a favour ka kwatanta hakan, is over we are not friends we are not friends, please katashi kafitar min daga daki kabar min gida and yau yakasance rana ta karshe dazaka kara zuwa gidanmu" kasa koda motsi Waleed yayi daga inda yake, hannu Arham yadaga yanuna mai kofar dakinshi yace "out, I said out" yadaka mai tsawa irin na cin mutuncin nan yace "indai kai ba maye bane katashi kafitar min daga daki mara zuciya kawai dolo" sosai Waleed ke kallonshi kafin ahankali yasauka daga kan gadon idanunshi sunyi ja mugun ja yabude kofa ahankali Mama yagani gaban kofan, murmushin dole ya kakalo yace "sai anjima Mama" baima jira amsanta ba yawuce yafita da sauri yya wajen gate yafita yabar gidan ya shiga motarshi yaja dawani irin gudu sanan yabar anguwan.



Bin bayan Waleed Mama tayi da kallo taji gabaki dayan maganan su sabida ita kanta tadamu tun ranan batada Arham a idoba sabida fushin datake yi dashi yasa taki zuwa tadubashi, hakan yasa Waleed na shiga dakin tabiyo bayanshi.







Tura kofan dakin tayi ta shiga, hada ido tayi da Arham da yana ganinta ya saukar da kanshi kasa, ahankali dawata irin murya dake rawa sosai Mama tace "Arham Waleed kama wanan cin mutuncin, Arham anya nina haifeka kuwa? Anya nonon nan nawa kasha"? Takama nonon ta tanunamai, saikuma tafashe da kuka sosai dan her heart is so heavy tace "wlh wlh da'ace a asibiti na haifeka Arham da na rantse maka da Allah dayau dinnan sainace bakaine danda nahaifa ba, anchanza mini kai a asibiti, amman agida na haifeka dagani sai unguwar zoma" tafashe da kuka sosai, sanan ta share idanunta tass da bakin zaninta tace "wlh albasa batai halin ruwa ba, babu ta inda ka gado malam mahaifinka, baban ka malami ne, wayan nan manya manyan malaman da ayau a Abuja dasu akeji duk ubanka ya koyarda su Arham, Arham ubanka malami ne, kakanka malami ne, amman kaiko Arham shaidanin yaro ne" tafadi haka tsabagen yanda zuciyarta ke tafarfasa, cikin ihu da fada da kunan rai tace "Arham wai shinko katuna waye Waleed koko kamanta ne?" tamai tambayan tana kallonshi sanan tace "Arham kanajin tsoron Allah kuwa? Arham kana kokarin ka tabbatar da cewan mutane kadau mutum daga rana ka maidashi inuwa shi saiya maida kai rana, Arham kai butulu ne eh? Yanzu inda ace zaka tashi kaje sip dinan naka zan rantse da Allah nakuma kara idan akwai kayanka daka saya da kudinka basu wuce kala biyu, Arham gabaki dayan sitiranka Waleed kisiya maka, Arham yaron nan nasonka har kuka naji yana maka kanamai ihu kana cewa ba kuka kace yamaka ba, matarshi ta haihu yarada ma danshi sunanka Arham duk baka ganin abubuwan nan? Da ace Waleed bai tsamoka daga talauci dahar yau ayaba kake saidawa, Arham Arham Arham" Mama tama rasa maizata cemai saikuma tafashe da kuka tace "kaga yanda idanun yaron nan suka taru da jini dukan dakamai? Amman bai rikeka ba ya tattako yazo wajenka, bari kaji bazan taba bari ka wulakanta mai sonka ba wlh, bazan taba bari ka wulakanta wanda ya chanza mana nidakai rayuwa ba, Arham bazan taba bari ka wulakanta Waleed ba domin ka wulakanta yaron nan kadauka nika wulakanta aduniyan nan, dan haka dau wayar ka ka kirashi agabana kasa handsfree dan naji, kabashi hakuri sanan kafadimai duk abubuwan daka fadamishi wasa kake kanajina "! Mama ta dakamai tsawa, dago idanunshi Arham yayi ya kalli Mama yace "Mama kiyakuri amman wlh ni bazan kirashi ba, kuma kidena cewa ya taimake mu babu abinda Waleed yamana Allah ne yataimake mu kuma shine yamana komi wlh, daman shi Allah haka yake abinshi inya tashi taimaka maka saiya nemo wani ya taimaka maka ya hanyar shi, tunda ai shi Allah bazai sakko kasa yamika maka kudi da hannunshi ba yace gashi Arham saidai yay amfani dawani, dan haka wlh Mama ni Allah ne yamin komi babu wani mahaluki daya isa yataimaken, Shidin banzan shi, kudin shi na banza meyake dashi, shi idan ma yaga asalin masu kudi guduwa zaiyi yaboye wlh irinsu Otedola, Zuckerberg da sauransu, shidin me shidin banzan shi, dan ubanshi nada kampani a kasan waje yake mana kapapa yana daga mana kafada wlh bazan kirashi ba" yay maganan ranshi duk abace, rungume hannu Mama tai aciki tana kallon Arham kaman tasami TV, ahankali Mama tace "Arham Annabi yace a kullum mudinga kallon nakasa damu bana sama damu ba hakan zaisa mungode ma Allah da kyau, Arham batun yau nake karantan wani abu tattare dakaiba amman yau Allah ya bayyanamjn abin gabaki dayanta Hassada kakema Waleed" da sauri Arham yana daga murya yace "shi awa zan tsaya inamai hassada Mama? Ubanme yakeda shi? Allah ya kyauta kafin na ganshi naga masu kudi dubu ni mama kima dena min maganan wani Waleed banson jinta, dashi da wanan matsiyaciyar uwarnan nas...." bai karasa maganan ba Mama taxuba ma bakinshi mari, sanan tacire slippas din kafarta tahau dukanshi ta ko'ina tace "Arham kaci uwaka, bani na haifeka ba, wanan bakin halin naka da bakar zuciya uwarka da ubanka basu dashi, wayanda suka taimake ka kake zagi eh, kai wani irin butulu ne, Arham ni kake so kabama kunya aduniyan nan" dudda dukanshi take bakinshi kin mutuwa yayi yace "ki kasheni Mama, dama batun yau nasan kinfison Waleed kan danda kika haifa ba, Waleed nada kudi, yasai miki gida da mota, gaki da generator ga solar, ga kayan abinci ga kudin kashe wa ba dole ba, Mama ki kasheni sabida Waleed, badai danni banda kudiba banda gidan marayu ba saisa bakisona nima ba zakiga abinda zai faru Mama kicigaba da dukana har saina daina numfashi, badai kowa dukana yake akan Waleed dan gata ba, ajebota kucigaba nikuma namuku alkawarin sainaima Waleed abinda dukanku bazaku iya taimakon shiba wlh, wlh kuwan, kiyita dukan" yakara mika mata kanshi dantaji dadin duka, dukanshi Mama tayi har saida Sadiya taji ta shigo da gudu taja Mama baya dake haki kaman zata mutu tace "sadiya kibarni na kashe yaron nan nahuta dan ba da'na bane, Sadiya kibarni, Arham nason yacimin mutunci, Sadiya Arham nason ya kunyatani aduniya, dawani idanu yakeson na kalli mutanen nan dasuka mana komi a rayuwa eh" tafashe da kuka, rungumeta sadiya tayi itama tahau kuka tace "Mama yakuri kidena kuka dan Allah" cikin wani irin fushi Arham ya tashi ya finciki key motarshi yafita daga dakin ya barsu awajen idanunshi sunyi jajir.








Waleed rasa inda zashima yaji dadi aranshi yayi kirjinshi sai wani irin mugun tafarfasa yake, baisan ya akayi ba yadaiga yazo gidan marayun shi, parking motarshi yayi yafito sai gaisheshi ake yama kasa amsasu da sauri da sauri yake tafiya har zuwa cikin asibitin shi, direct ward din da Widad ke kwance yake, bude kofar ahankali Ya shiga maida kofar yayi yarufe yana kallonta ganin bacci take, direct yawuce gadon da sauri zama yayi kan plastic chair gaban gadon kawai yakifa kanshi kan gadon kukan dake cinshi tun adakin Arham ya shiga sakinshi awajen ahankali yana shesheka, maganganun Arham gets to him sosai, sun shigeshi was he that bad kaman yanda Arham ya suffanta shi? Was he?.

Kaman amafarki taji kaman ana kuka ahankali wanda sautinshi ke kaiwa har kokon kirjinta, bude idanunta tayi kaman wacce ta firgita ta kalli ko'ina kafin ta kalli gefenta, kan mutum tagani kife kan gadon, gashin kan nawani irin shining sunyi sili sili tsabagen gyara dasuka ji, dudda bataga fuskarshi ba amman tagane mutumin nanne bargon jikinta tayaye da sauri taja jikinta ahankali ta tashi tazauna tana kallonshi tai raurau da ido, ahankali tadaga hannunta ahankali tadaura akanshi, jin soft hannu dake dauke da dan danshi danshin zufa akan sumanshi yasa yadago kanshi ya kalleta da jajayen idanunshi da hawaye yacikasu sosai, wani irin kallonshi take hankalinta yatashi sosai ganin yana kuka ahankali yakai hannunta kan fuskarshi sharemai hawayen tayi da sauri tana girgizamai kai, jiyayi zuciyarsshi tawani irin tsinke baisan lokacin daya tashi daga kan kujeran yazauna abakin gadon ya rungume cikinta tsam ba, fuskarshi nakan cikinta yasaki kuka ahankali cikin harshen turenci yace "Saheeba baki sanni ba, dudda duka yanzu 10month kikayi da sanina, dan zaman dakikayi tareda ni please ki gayamin am I a bad person? I know I makes different decisions, but kowani decision zan dauka abune dazai kawo cigaba dakuma raya wanan gidan marayun, you know ana yawan cewa breakup masoya ne kawai irin couples haka ke breakup ba'asan cewa akwai friendship breakup ba and the shit hurts badly" yasaki kuka sosai akan cikinta dayasa tahau girgiza mai kai tana bubbuga kanshi alamun yay shiru tana kokarin magana takasa but kana ganinta kasan ta mugun damu,

Please Login or Register in order to submit comment