Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
yanzu saiki bar fushi tunda mijinki ya kawo miki abunda kike son kije ki gani Murmushi ibtisam tayi Ahamd yace ina Abba da ummi, da y'ar tsohuwa mai jaraba Ibtisam kuka ta saki tare da fad'in Ahmad Granny ta rasu...... Ahmad gaba d'aya shuru yayi yana jin wani abu yana mishi yawo a Kai..... Yayi wajan 5 mnt a haka sannan ya saki dariya yana fad'in granny din kike ma fatan mutuwa?? Wlh Bari ta jiki zaki sani shine harda wani kuka koh?? Toh ai ba first April bane balle ace April Fool ..... Ibtisam tace Ahmad dagaske Granny ta rasu jibi ne zata cika kwana 7 Tashi yayi da sauri ya fita ganin haka Zarah da ibtisam suka bishi Direct part din najeeb ya shiga inda ya Tarar dashi daga shi sai boxer da singlet Najeeb yace Ahmad lafiya kuwa?? Dai dai lokacin ibtisam ta shigo ita da Zarah Najeeb idonshi ya sauka akan na ibtisam dake kuka Nufan Ahmad tayi ta rungumeshi tana fad'in Ahmad dagaske nake maka.... Ahmad yace Ban yarda ba, kallon najeeb yayi tare da fad'in bros dagaske abunda take fad'a gaskiya ne Granny ta rasu.... Najeeb yace eh dagaske ne ta rasu.... Ahmad wani irin kuka yasa Mai ban tausayi, tare da fad'in shine babu wanda ya fad'amin sai yanzu, wayyo Granny, kuka yake Sosai Najeeb gaba d'aya sun Fara juyar Mai dakai ga ibtisam na kuka wanda yake jin kukan nata har cikin ranshi, ga Ahmad shima yana kukan Karfin hali yayi inda ya kalli Ahmad yace haba Ahmad karka manta addu'a take bukata ba kuka ba, kaifa namiji ne, taya zaka dinga kuka irin haka?? Namiji an sanshi da dauriya Nan Ahmad ya share hawayen idonshi tare da fad'in hakane, addu'a take bukata ba kuka ba, rayuwa kenan, Allah yaji k'anki Granny yasa kin huta. Zarah da najeeb suka amsa da Ameen Ganin Ahmad yayi shuru yasa najeeb nufan ibtisam tare da ru'ko hannunta.... Ganin haka yasa Ahmad da zarah suka fita daga d'akin Najeeb d'ayan hannunshi yasa yana share mata hawayen idonta tare da fad'in plz ki daina wannan kukan, kalla yanda gaba d'aya kika saka kanki cikin damuwa duk kin rame, karki manta duk wani mai mai mamaci ne, dole mai rai saiya mutu komin dad'ewa, sannan ita Granny addu'a take bukata ba kuka ba..... Cikin kuka tace kasan zafin rabuwa da wanda kake so a rayuwa kuwa?? Sai yanzu nake yarda da abunda ake fada ba mutuwa akema kuka ba sabo ne, d'aki d'aya nake kwana da Granny, gado d'aya, koda tafiya zatayi yawanci tare mukeyi, sabo dani yasa ko tafiya bata son yi, sanda zan tafi skul babu yanda batayi ba akan in fasa tun Tana fad'in bata so harta dawo tana fad'in in zauna a Kano inyi kar inje wani gari, kasan mai yasa take fad'in haka?? Duka saboda Sabo ne, ta saba dani, bata son inyi nesa da ita, gashi yau na wayi gari gaba d'aya babu ita a cikin wannan duniyar, dole inyi kuka, kukan ne kad'ai zaisa in rage abunda nake ji, kaf duniya bana tunanin akwai wanda ya shaku da Granny sama dani, a gaban idona ta fad'i ta Fara jinyar kwana biyu, haka a gaban idona ta mutu, wannan abubuwan gaba d'aya sun kasa goguwa a idona Najeeb matseta yayi a jikinsa tare da fad'in daga ranan da mutum ya rasu, a lokacin baya son komai sai addu'a, domin wannan addu'a ita yafi bukata, ita kad'ai ce mutum Zaima mutum ka nuna mishi gata Nasan yanda sabo yake, lallai nasan dole ki shiga cikin wani hali, but Ina son kiyi hakuri a duk sanda kika tuna ta kiyi mata addu'a, kinji Ta tsagaita da kukan amma bata bashi amsa ba, tana nan dai manne a jikinsa Najeeb ganin haka yasa ya dan cireta a jikinsa, yaja hannunta yai gadon d'akin da ita tare da zaunar da ita akai Shima zama yayi a kusa da ita, ya kura mata ido, abubuwa da yawa yake ji a game da ita, wanda bazai iya misalta yanda yake jiba, gaba d'aya baya Son ya ganta cikin damuwa Ibtisam kam lokaci d'aya ta tashi tare da fara tafiya Tana son barin d'akin Najeeb rukota yayi tare da rungumeta yana fad'in ibtisam, sanda Granny zata rasu ta ro'ki alfarma akan mu kasance tare har abada, wannan shine magananta na karshe...... Ibtisam a hankali tace ina sane ban manta ba, amma ina son ka sani zan zauna dakai domin haka Granny take Fata, amma badan ina so ba, najeeb gaba d'aya har yanzu na kasa manta abun da..... Sai kuma ta saki kuka tare da k'okarin jan jikinta daga nashi Shi kam najeeb ido ya lumshe jin tana k'okarin kwatan jikinta daga nashi yasa ya saketa tun Kafin ta fad'a mishi Kalman da yafi tsana a duniya Fita tayi da sauri Tana kuka Najeeb idonshi ne ya canza launi, Lokaci d'aya ya lumshe ido, tare da zama a kujeran dake kusa dashi wanda yake cikin bedroom din nashi Ibtisam kam daki ta shiga inda ta tadda babu kowa kwanciya tayi akan gadon d'akin tana kuka, ba komai take tunawa ba sai yanda taga najeeb da Najwa, duk yanda taso ta manta da abun amma saita kasa, Abun yana damunta sosai, tana jin Abun Sosai a cikin ranta, ko tayi niyan sakewa dashi saita kasa inta tuna abun , taci kuka Sosai har bacci yayi gaba da ita Washe gari da safe suna zaune a dinning suna breakfast saiga najeeb yazo inda ya gaida iyayenshi cikin girmamawa Dad amsawa yayi tare da fad'in an tashi lafiya?? Yace lafiya kalau.. Ahmad da Zarah gaida najeeb sukayi wanda yasa itama ibtisam ta gaidashi Amsawa yayi ba tare daya kalleta ba.. Dad yace ma najeeb anjima kaida mamana ku shirya kuje kuga wani gida dana siya nasa an saka komai, saiku koma can, inda akwai abunda kuke bukata saiku k'ara da kanku Mum tayi dariya tare da fad'in Aikam, yauwa ba yanzu zata koma ba, sai anyi Mata kayan akwati gaskiya, domin ba'ayi mata ba, naso inyi tafiya inje in had'a mata Toh ban samu naje ba, abubuwa nata taso wa Najeeb yace Mum zamu saudiya cikin week dinnan, domin ina son muje mu duba mahaifin malami na, sannan kuyi mishi godiya daya koyar dani Mum tace hakan yayi. Wajan k'arfe biyar NAJEEB ya kira Zarah tare da fad'in ta turo Mai ibtisam tazo ta sameshi a mota Fad'ama ibtisam abunda najeeb yace tayi har zata ce basai taje ba, ta tuna da abunda abba yace, tashi tayi tasa after dress akan kayan dake jikinta ta fesa turare sannan ta kalli Zarah tace kizo muje tare mana Zarah tace wa?? Sai dai kun dawo, ban zuwa gayyan sodi muje in rakaki Mota dai Fita sukayi najeeb tunda ta fito ya kura mata ido, har suka k'araso zarah ta bud'e Mata Bayan motar inda najeeb ke zaune ta shiga driver yaja Har suka k'arasa gidan babu wanda yama dan uwansa magana Bayan sun k'arasa fita yayi itama ganin haka yasa ta fita suka nufi cikin gidan, wanda NAJEEB ya bud'e wow Masha Allah, falon babba ne yayi mugun tsaruwa ga kyau, gidan d'aki d'aya a k'asa da falo sai kitchen sannan d'aki hud'u a sama da falo Ko wani d'aki ansa kayan furniture Gidan yayi mugun tsaruwa, kallonta najeeb yayi tare da fad'in mai kike bukata a saka a ciki?? A hankali tace babu komai Yace ok, fita sukayi inda ya amshi ke din motar yace driver ya koma Gida bayan ya bashi kud'i, kallon ibtisam yayi yace shiga gaba muje Bata Musa mishi ba, domin a yanzu tayi aniyar bin umarninshi duk da bawai tana sonshi bane, zata bishi tunda shine a saman ta, uwa uba tana tuna abunda Granny tace sannan da abunda mahaifinta shima yace Mata Tuk'i yake basu tsaya ko ina ba, sai wajan saida waya inda yace ta fito suje, Bayan sun shiga yace a bashi latest iPhone inda aka d'auko Mai iPhone 11 ya amsa tare da tambayar Kudin aka fada mishi, ATM d'inshi ya bada aka cira cikin POS sannan suka fita kai tsaye mtn office suka nufa yace a bashi sim card, shi yayi register da sunanshi da komai nashi Bayan sun koma Mota ne yace ta bashi duka iPhone d'inta Kallonshi tayi alaman akan wani dalili?? Ganin bata da niyan bashi yasa ya d'auki wayar duka a gabanta ya goge komai na ciki, tare da kallonta Wanda itama shi take kallo yace ba bincike zanyi miki a waya ba, gashi na goge komai, ciro sim d'inta yayi a gabanta ya karya sim din guda biyu, ya jefar tare da mi'ka mata wayar daya siya da sim din, yace bana bukatar kiyi amfani da abunda bani na siya ba...... Yana fad'in haka ya tada motar sukai gaba Ita ibtisam mamaki abun yake bata, Toh miye na karya mata sim, tare da ri'ke Mata wayoyi, Indai haka yake ji basai ya siya mata sim kawai ba Shi kam NAJEEB ganin wayoyin hannunta yasa yake zargin kabir ne ya bata, wanda ya tambayi Zarah tace kabir ne ya bata wannan shine dalilin da yasa baya son ganin wayoyin a hannunta, domin kwata kwata baya bukatar abunda ya shafi kabir a wajan ibtisam din....... Hmmm ikon Allah toh wannan idan yaji kabir din yabar mata kayan akwati ya zaiyi???? Read and leave it, dnt share to anyone*IDAN KIKA KARANTA BAKI BIYA BA INA BINKI BASHI, KUMA NAUYI NE A KANKI* *WACCE TAKE SON BIYA ZATA TURA 200 TA ACCOUNT NUMBËR DINNAN* 3138831065 Firstbank Maryam Alhassan *SAI A TURO SHAIDAN BIYA TANAN 08060860886 IDAN KUMA KATI NE MTN SHIMA TA NUMBER DIN ZAKI TURA 200 NAIRA ONLY* *KARKI MANTA KINYI ALKAWARI, BAZAKI FITAR MIN DA NOVEL BA, IDAN KIKA FITAR DASHI KEDA ALLAH, KUMA KINA D'AYA DAKA CIKIN MUNAFUKAI, DOMIN ALAMAN MUNAFUKI GUDA UKU NE, 1 IDAN ZAIYI MAGANA YAYI K'ARYA 2 IDAN AKA AMINCE MASA YAYI HA'INCI 3 IN YAYI ALKAWARI YA SABA, KIN DAI JI, KINCE KIN MIN ALKAWARI, IDAN KIKA SABA KIN ZAMA MUNAFUKA, KUMA WUTAR MUNAFUKI DABAN TAKE, IDAN KIKA FITAR KINMA KANKI* Bayan sun isa Gida ibtisam tana ganin ya faka motar ta fita tayi cikin Gida da ledan wayar daya siya mata, koda ta shiga ciki babu kowa a falon d'akinsu ta tafi Kai tsaye inda ta iske Zarah zauna tana danna waya, ajiye ledan wayar tayi akan gadon d'akin Zarah d'auka tayi tana bud'ewa lokaci d'aya tace wow latest iPhone, waya baki?? Ibtisam tace wa kike tunani zai bani Dariya zarah tayi tare da fad'in your darling hubby Ibtisam Hararanta tayi tare da fad'in kyaji dashi dai Zarah tashi tayi tare da saka wayar a caji tana fad'in, ni kam so nake inga camera din wayar nan, da suka saka har guda uku, bari yayi caji in gani Ibtisam tace uhm aiki ja Najeeb ganin ta fita yasa ya girgiza Kai tare da fitowa shima yayi cikin gidan inda yayi d'akinshi direct Ibtisam bayan sun fito yin dinner inda Mum take tambayanta gidan yayi Tace eh mum cikin jin kunya Dad yace ina najeeb din yake ma?? Mum tace yana d'akinsa Nasan Dad bayan ya gama cin abinci tashi yayi yana fad'in yau a gajiye yake, kai tsaye bedroom yayi domin yana bukatar ya kwanta ya huta Mum tashi tayi itama tabi bayan mijinta inda ya rage daga Zarah sai ibtisam Ahmad ya koma skul Zarah sai faman d'aukan hoto take da wayan ibtisam din, ita kam ibtisam abinci take ci abunta Najeeb ne ya fito inda yazo ya zauna a kujeran dake kallon na ibtisam Zarah tace bros shine ni baka siyo min wayar ba, nima in fito gari ba Kallon ibtisam yayi wacce akai Sa'a itama shi take kallo gira ya d'aga Mata alaman Yadai Da sauri ta juyar da kanta tare da ajiye spoon din abincin da takeci Najeeb ganin haka yasa yayi murmushi, lokaci d'aya kuma ya kalli Zarah tare da fad'in, wace waya kike ri'kewa?? Tace Bros iPhone 7 cefa Yace ok saiki bari in munje saudiya in siyan miki Tace Bros plz kaban kud'in gobe muje mu siya mana.. Yace ke dawa zaki goben??.. Tace ni da ibtisam, ta k'arasa maganan cikin dariya Najeeb yace ashe ba zaki ba, ni daga yanzu babu inda zata dinga zuwa Kallon ibtisam yayi da take sauraransu yace plz yunwa nakeji bani abinci Inci Ibtisam kallonshi tayi cikin ranta tace Wlh wannan ya iya abu, kalla yanda yake wani abu kaman irin mun saba dinnan, tashi tayi tare da d'aukan plate ta zuba Mai sannan ta kai mishi gabanshi ta ajiye Gaba tayi zata wuce yace heey come back Ina zaki?? Ibtisam tsayawa tayi cak, ta kasa magana bata ma san mai zata ce mishi ba Janyo mata hannu yayi tare da janyota ta fad'o ya ri'keta tayi jikinsa.....  Ganin haka zarah yasa ta tashi tabar wajan tana murmushi cikin ranta tana fad'in sai aukin fad'in basa son juna..... Ibtisam data tsorata domin sai taga kaman zata fad'i ta lumshe ido da sauri, jin bata fad'i ba yasa ta bud'e ido wanda suka sauka akan na najeeb, gaba d'aya kallon idon juna suke..... Sunyi wajan minti biyu a haka ibtisam ta rufe ido domin bazata iya juran kallon idon nashi ba, dan wani abu takeji tun daga kafarta har tsakiyar kanta Najeeb ganin haka yasa ya kura ma fuskanta ido yana kallonta, lokaci d'aya ya d'agota tare da tashi daga kan kujeran ya mi'ke tsaye, hannunshi yasa a kugunta ya ri'ke mata su, lokaci d'aya ya janyota ya matseta da jikinsa, yana son kamshin jikinta, gaba d'aya najeeb wani irin mugun sha'awa yakeji sosai, ido ya lumshe yana shafa mata baya Ibtisam kam gaba d'aya gabanta sai faman dukan uku uku yake, ga zuciyarta dake faman bugawa da karfi fat fat Sun d'auki lokaci a haka Kafin ta Fara k'okarin ta kwaci jikinta...... A hankali yace don't move..... Kaman ya danna remote haka ta tsaya ta daina kokarin fita daga jikin nasa Sakinta yayi tare da juyata ta baya ya kama kugunta ya matse tare da fad'in did you miss me??? Ibtisam data juya Mai baya taji tambayar tashi tazo Mata a bazata, tare kuma dajin mamakin tambayar tashi da yayi mata..... Katse mata tunani yayi da fad'in answer me? Did you miss me??  Tunda na tafi kin taba tunani na koda sau d'aya?? Ibtisam hannunta tasa a nashi Tana k'okarin cirewa daga kugunta da yasa nashi Ganin tana son cire Mai hannu yasa ya k'ara matseta Sosai a jikinsa tare da fad'in idan kina tare dani ki daina k'okarin cewa zaki kwata kanki, domin.....  Juyo da ita yayi yanda zai dinga kallon fuskanta ganin haka yasa ta rufe ido da sauri Murmushi yayi tare da hura Mata iska akan fuskanta, K'ara matse idonta tayi Ganin haka yasa yaci gaba da fad'in ko da yaushe Indai kika bari na ri'keki kaman haka, just surrender ur self.... Bud'e ido tayi a hankali ya sauka akan nashi inda shima ya kura mata ido, a hankali ta Fara zame jikinta Lokaci d'aya taja da karfi tayi baya...... Dariya tayi wanda bata san tayi ba, sannan tace gashi na kwaci kaina.....  Tana fad'in haka tayi gaba da sauri Najeeb kam idonshi na kanta harta bace yana murmushi ganin ta bace yasa ya lumshe ido tare da K'ara sakin wani murmushin Zama yayi amma yau najeeb ya kasa cin abinci domin gaba d'aya ji yayi bazai iya ci ba, dan sai yaji ya gundureshi, dan gajeran tsaki yayi tare da tashi yayi d'akinsa inda yayi toilet yayi wanka sannan yazo ya kwanta..... Ibtisam kam bayan ta shiga dak'i Zarah tace har an Gama soyewa? Ibtisam tace uhm Kedai kika sani Zarah tace a'a kudai kuka sani keda bros, gaba d'aya ku dukanku babu komai a idonku sai Son junanku..... Ibtisam dariya ta saki tare da fad'in ki daina wannan maganan, na tabbata abunda yasa kika ga najeeb na haka saboda abunda Granny tace ne, hawaye ne ya zubo mata a ido tare da fad'in nima inayi ne saboda ita, Allah sarki Granny Allah yaji k'anki inama kina Raye Zarah tayi dan murmushi tare da fad'in rayuwa kenan, Allah yasa mu cika da imani Ibtisam ta amsa da Ameen Zarah tace Wlh Ina tuna irin abubuwan da akayi da Granny, abun ban dariya koda yaushe burinta taga kowa cikin farin ciki, kai duniya kenan, gashi yanzu bata cikin ta Ibtisam hawaye ya silalo mata tare da fad'in Wlh kuwa, koda yaushe da tunaninta nake kwana nake tashi, yanda naji mutuwar Granny banji ko Ummi ce ta rasu zanji irin yanda naji, Wlh nafi shakuwa da Granny akan ummi data haifeni Zarah tace hakane, Nima Nasan haka, yanzu abu d'aya za kiyi ki nuna kina son Granny dagaske..... Ibtisam ta katse zarah da fad'in Mai kenan?? Zarah tace Kibi magananta na karshe, ki kama mijinki hannu bibbiyu, wlh Granny na matukar son ku tare, ki duba shine magananta na karshe, ibtisam wannan shine za kiyi ki tabbatar kina Sonta dagaske Ibtisam kuka mai sauti tasa tare da fad'in Zarah Wlh Ina k'okarin yin hakan amma daga naga najeeb abunda ya aikata wanda har yau na kasa fad'ama kowa shike dawo min ciwo cikin rai, na kasa mantawa.... Zarah tace ibtisam kiyi hakuri, Nima bance ki fad'amin ba, ina so kiyi hakuri, ki cire komai a ranki, kiba mijinki second chance, wlh najeeb ya canza sosai, ki mishi uzuri ki d'auka komai yayi miki a baya rashin sani ne, yanzu Alhmdlh ibtisam najeeb ya fara karatun addini, idan kika lura ya canza ba kaman da ba, ko ta yanda yake magana dasu Mum zaki fahimci hakan yanzu.....  Shuru Zarah tayi na wani lokaci sannan taci gaba da fad'in "ibtisam Wlh najeeb yana sonki, koda bai furta miki ba ni naga sonki a cikin idonsa..... Ibtisam tace zarah kenan Wlh najeeb baya so na, kawai yana zama danine badan so ba, kaman yanda nima bana sonshi..... Zarah murmushi tayi tare da fad'in aiko k'arya kikeyi, domin kaman yanda najeeb ke sonki haka kema kike son sa, ibtisam Wlh kina son najeeb amma zan iya cewa baki gane cewa kina son shiba, domin har yanzu kina d'auka son kabir shine a ranki, which kin dad'e da daina son kabir ko ince da ba so kikayi ba, duba da yanda kabir shine kika fara soyayya dashi amma baki aureshi ba..... Na tabbata Idan kika zauna kikai nazari ki tuna da Idan kinga KABIR ya kikeji?? Sannan Idan kinga najeeb ya kikeji??  A nan ne zaki gane wa kike so..... Ibtisam wani kukan tasa Tana fad'in Zarah ban sani ba, nidai abunda na sani shine bana jin kabir kaman da, kwata kwata yanzu bana tunaninsa har sai najeeb yayi min wani abu da naji haushi, sai in tuna dashi ..... Zarah tace kinga alaman so na Farko kenan, karki manta kince sai najeeb yayi miki Abu kike tunawa da kabir, kenan in najeeb bai baki haushi ba bazaki tuna dashi ba??  Ibtisam son najeeb ya kamaki amma kin kasa fahimta, nidai shawarata shine ki ri'ke mijinki hannu bibbiyu ki manta da komai, ki d'auka kaman ba'ayi ba Ibtisam shuru tayi tana nazarin maganan zarah Wanda ita da kanta tasan gaskiya ne, ido ta lumshe tana tunanin maganan Granny da sukai baya akan tayi hakuri da mijinta, domin in kince zaki kashe auren baki San wanda zaki aura ba..... Da sauri ta bud'e ido tana hawaye, tabbas hakane Allah ka bani ikon yimai biyayya Tashi tayi Kai tsaye tayi toilet wanka tayi ta fito d'aure da towel, kayanta ta bud'e ta d'auko rigan bacci tasa ta kwanta Gaba d'aya suna shirin tafiya saudiya, Mum tana ta gyara ibtisam Sosai Ibtisam da zarah na zaune a bukka suna firan skul, ibtisam tace ni bani number din kubra bani da number din kowa a waya na yanzu Zarah tace bani da number d'inta sai dai in tambayi aysha ta turomin Tsaki ibtisam tayi tare da fad'in batta Dan Allah ni banson hulda dasu balle har ki tambayeta Abu Dariya Zarah tayi tare da fad'in akan wani dalili?? Maita miki?? Ibtisam tace hakanan kawai ni haushi take bani Zarah tace kodan tana son najeeb ne?? Ibtisam tace ina ruwa na taita sonshi mana, nidai kawai bana sonta batai min ba kawai naji bana son hulda da ita ne Zarah tace kawar taki?? Kawai kice yanda take kuzanta mijinki ne bakya so. Ibtisam tace koma dai Mai nene ke kika sani, tare da fad'in mubar maganan plz Zarah dariya ta saki tare da fad'in najeeb Dai ya gama da zuciyarki Kafin ibtisam tayi magana suka ji muryan najeeb na fad'in naji Ana kiran sunana.... Idonshi nakan ibtisam dake kwance a k'asa kanta Nakan tum tum Da sauri ta tashi tare da zama Zarah tace yauwa bros zo kaji wani abu Ibtisam hararan Zarah tayi alaman tayi shuru Zarah ganin haka yasa ta kwashe da dariya, najeeb zama yayi kusa da ibtisam a k'asa tare da kallon zarah yace inaji Zarah ta kuma sakin dariya tare da fusge wayar dake hannun ibtisam ta Fara d'aukansu hoto tana fad'in Kai nice couple, najeeb d'aura hannunshi yayi akan kafad'an ibtisam tare da janyota kusa dashi Sosai..... Da sauri ta kalleshi ido daya ya kashe mata tare da fad'in camera zaki kalla not me Da sauri ta juyar da kanta tare dajin wani irin kunya sosai Zarah tace smile ibtisam Ibtisam hararan Zarah tayi Shi kam najeeb sai wani manneta yake a jikinsa Najeeb ya kalli Zarah tare da fad'in muga pic din Mi'ka Mai wayar tayi najeeb yace wow tare da nuna ma ibtisam yace wa yafi kyau?? Kallonshi tayi alaman ban sani ba..... Yace bani zaki kalla ba, d phone Ido ta lumshe tare da k'okarin tashi Janyota yayi ta zauna akan kafarshi yana fad'in Ina zaki Zarah tashi tayi tare da barin wajan tana fad'in naga in Abun ya tashi basa tuna akwai mutane a wajan, nima Allah ya bani Wanda nake so Ibtisam k'okarin tashi take amma Najeeb ya ri'keta dakyau, tare da fad'in na fad'a miki indai kika zo inda nake harna ri'keki just surrender kawai domin bazaki iya escaping ba Ibtisam jin dagaske bazata iya kwatan kanta ba yasa ta nutsu, matso ta yayi Sosai ya k'ara manneta a jikinshi, lokaci d'aya yasa hannunshi ya cire mata k'aramin hijab din dake jikinta, gaba d'aya gashin kanta ya bayyana wanda yake a tsefe D'agota yayi suka mi'ke tsaye yasa ido ya kura mata yana kallonta, ita kam kanta na k'asa domin bazata iya kallonsa ba, wani irin Abu takeji Idan ta kalli idonshi Lokaci d'aya ya janyota jikinshi tare da d'aura hannunshi akan west d'inta tare da manna kanshi akan fuskanta, ibtisam idonta a lumshe yake gaba d'aya hancinsu a had'e yake suna shak'an numfashin juna Dukansu biyun wani irin yanayi suka shiga wanda ko wannansu bazai iya misaltashi ba, lokaci d'aya ya saka bakinshi cikin Nata ya fara kissing d'inta tare da tsotsan k'asan lips d'inta yana saki tare da kamo harshenta..... Gaba d'aya ibtisam jikinta ya mutu ji tayi ta kasa ri'ke kafarta, tana k'okarin tayi k'asa ta fad'i..... Da sauri ya ri'keta tare da saka hannunshi biyu ta bayanta ya ri'keta dakyau tsam a jikinsa yana kissing d'inta Yayi wajan 8 minute yana haka, Kafin ya barta yana kallonta Ibtisam idonta a lumshe yake..... Najeeb ya kira sunanta da ibtisam..... A hankali ta bud'e ido tana kallonsa ganin yana kallonta yasa ta kuma rufe ido, Ganin haka yasa yayi murmushi tare da fad'in I miss your lips alot..... Jin abunda yace yasa ta bud'e idonta da sauri Tana kallonsa Hancinta yaja yana fad'in Did you miss me??? Kawar da kanta gefe tayi Ya saka hannunshi ya juyo Mata da kanta yace answer me?? A hankali tace ina son in shiga ciki.... Murmushi yayi tare da fad'in mijinki na nan Mai zakiyi a ciki?? Am hare in front of you..... Ido ya kuma k'ura mata wani irin Abu yake ji gashi yana matukar bukata, domin a matse yake Sosai dan an dad'e ba'a had'u ba...... Ibtisam k'okarin jan jikinta tayi ya kuma matsota jikinsa tare da fad'in fad'amin kinyi kewa na???.. Kai ta girgiza mishi alaman a'ah Dan sakinta

Chapter 41 of 46