Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

koda baya nan zata ri'ke mishi kanta, duk da yana fama da so da kuma burin kasancewa da ita, yayi hakan ne danya gwadata kuma Alhmdlh taci jarabawan

Domin inda ta yarda batai k'okarin hanashi ba, zaiji tsoran auranta domin zaiga bazata iya ri'ke mishi kanta ba, toh yanzu Alhmdlh gashi harda kuka takeyi danya Mata kiss Wanda shi d'aya yayi mata bata maida mishi martani ba, sai k'okarin cire bakinta daka nashi da tai tayi

A hankali ibtisam ta janye jikinta daka nashi tare da saka hannunta Tana share hawayenta

Mi'ka mata tissue yayi

K'in amsa tayi tare da fad'in plz ka bud'emin kofar Ina son shiga gida

Kabir yace ibtisam wai wannan fushin da kikeyi na miye? Karki manta nine Zan aureki nan da kwana biyar za'a d'aura auranmu, toh miye dan nayi kissing d'inki is nothing b....

Ibtisam ta Katseshi tare da fad'in may be Kai a wajanka ba wani abu bane, kabir ina son.... Murmushin da kabir yayi shine yasa tayi shuru ba tare data fad'i abunda tayi niya ba

Kabir murmushi yayi domin jin ta kira sunanshi Kai tsaye abunda bata tabayi ba kenan,

Kabir yace ina son ki sani ibtisam ni kabir nine mijinki insha Allah, Ina son ki fahimci wani abu, wlh ibtisam ina sonki dagaske ban taba tunanin koda da minti d'aya bane ni in cutar dake ba, so ina son ki sani sonki a jinina yake, nayi miki kiss just to know who you are, in zakiyi min adalci how many month na sanki, but ban taba attempting na in taba koda hannunki ba.

Ibtisam shuru tayi tana jinshi lallai abunda kabir ya fad'a hakane, bai taba tabah mata jiki ba sai yau, ido ta lumshe cikin jin kunya wannan ne rana ta farko dana miji yayi kissing d'inta, gaba d'aya jikinta wani iri yake mata, damma anyi bada son ranta ba hhhhh

Kabir yace my ibti plz forgive me

ibtisam cikin murya wacce tayi kuka, tace ina son hakan Karta kuma faruwa, plz karka manta Idan mace dana miji suka kebe na ukunsu shaidan ne, ina jin tsoran karmu aikata abunda zai haramta auranmu, ko kuma muyi abunda za muyi dana sani, ban taba fad'a maka wannan Abun ba but yau zan fad'a maka, "bazan iya juran in rasaka ba, ni nasan Sonka a jini na yake, ban San ya kakeji a tare dani ba, but ni Ina jinka duka ilahirin jiki na, nasan abunda nake fad'a mata bako wace mace zata iya fad'ama namiji gaba da gaba ba, ina fad'a maka hakan ne domin kasan irin sonda nake maka, sannan kuma karka k'ara aikata abunda kamin yau, domin bazan iya juran rasaka a rayuwa ta ba,"ban taba son wani namiji ba sai kai, ban San so ba sai a kanka, Dan Allah Ina son karmu aikata abunda za muyi dana sani, wlh Ina jin tsoran abunda zai rabamu sai kuma ta saki kuka mai sauti

Gaba d'aya KABIR rudewa yayi tare da rungumo ta jikinshi yana fad'in ibtisam ni nasan abunda nayi miki Allah shine shaida na bada wani mugun abu nayi miki ba, sannan ina son ki sani bazamu aikata abunda za muyi dana sani ba, "ibti Kece mace ta farko Nima dana Fara so, duk da y'an mata da dama sunce suna sona, amma Kece naji Ina So, kuma nake burin aure, ban taba tunanin inyi wani abun da zai zama Abun kunya gareni ni dake ba, yau Ina cikin farin ciki my ibti ta fad'amin irin sonda take min am so happy

Da sauri ta janye jikinta daka nashi, wani irin kunya taji ta kamata lokaci d'aya, tare da fad'in maina aikata, hannu tasa ta rufe fuskanta cikin jin kunya

Kabir kam dariya yayi tare da canza firar tasu dan yaga yanda taji kunya akan abunda yace, dan haka saiya canza firan da fad'in ibtisam kinga kayan lefenki kuwa?..

Kaita girgiza alaman a'a

Yace Mai yasa ko kayan ne basuyi miki ba?

Tace a'a haka kawai

Kallonta yayi tare da kura mata ido, yace ibti are you happy with this marriage kuwa?

Da sauri ta kalleshi ido cikin ido domin ita yake kallo, tace am happy with it mana, "maika gani??

Kabir yace naga kince baki ga kayan lefenki ba, naso in miki yafi haka, in miki guda 24, but banda enough kud'i gidanki ya cinye kud'in

Ibtisam tace ko d'aya wlh, abunda kayi yayi fatana shine Allah yasa ma auren albarka, sannan abunda yasa ban gani ba saboda ina jin kunya, bazan iya zuwa ince zan kalla ba, gasu ummi a gidan,"kaji wannan shine dalili na, nak'in kallon kayan

Kabir yayi murmushi tare da fad'in yayi kyau, hakan yayi my shy ibti

Dariya tayi

Yace Bari inzo in gudu yunwa nakeji Sosai

Ibtisam tace ko in kawo maka abinci

Kabir yace a'a, Bari inje kawai

Ibtisam tace plz muje kaci, kaga in....

Yace ya kikai shuru

Tace ba komai, muje kaci a nan.

Yace no my ibti

Ibtisam tace Bari in kawo maka snack Toh, bud'e kofar tayi amma taji a rufe kallonshi tayi alaman ya d'aga mata

Murmushi yayi tare da d'aga mata sannan ta fita

Tayi wajan 5mnt sai gata da cooler guda uku a cikin basket dasu wasu Abu a plate guda biyu ansa full paper an rufe, bayan motar ta bud'e tare da ajiye Mai sannan ta rufe kofar

Bud'e gaban motar tayi wanda ta tsaya a tsaye ba tare data shiga ba, tace gashi saida safe koh

Kabir murmushi yayi tare da fad'in wannan ne snack din koh?

Dariya tayi tare da fad'in Toh naga kaki yarda in kawo ma, kuma Nasan in ba'ayi wasa ba, sai dai kasha tea

Dariya yayi yace tunda shine abincin gauraye koh

Ido ta lumshe tana murmushi

Sallama yayi mata tare da fad'in sai munyi waya yayi gaba

Cikin gida ibtisam ta shiga, kai tsaye d'akinsu ta shiga inda ta iske Granny da Zarah suna fira

Granny tace Sai yanzu kabirun ya tafi?

Ibtisam eh kawai tace tare da kwanciya tayi ruf da ciki Tana tunani, wanda ba tunanin komai take ba saina abunda ya faru tsakaninta da kabir, ido ta lumshe wani irin son kabir Mai tsafta takeji yana k'ara shigarta, lallai ina son kabir, sonshi ya kamani da yawa.

Allah na gode maka daka bani shi a matsayin miji, Allah ka bamu zaman lafiya, tare da hakuri da junanmu da kuma son juna.....

Zarah ce ta katse mata tunani da fad'in ibtisam Yadai naga kinyi shuru?..

Granny tace uhm ai tayi shuru tunda ansha kalaman soyayya

Dariya ibtisam tayi tare da tashi ta zauna tana kallon Granny tace Wlh Granny kina da abun dariya

Granny tace ahaf ai Nasan komai, domin wannan shurun bana banza ba

Ibtisam sai taji ta tsargu tana tunanin kodai Granny taga sanda kabir ya mata kiss ne?

Wanda hakan yasa ta kame bakinta tayi shuru ba tare data k'ara cewa komai ba

Granny tace uhm bari dai inje in watsa ruwa inyi bacci

Ibtisam kam gaba d'aya ranan sai juyi take tana tunanin abunda ya faru tsakaninta da kabir

Haka shima ta gefen KABIR din, wani irin sonta yakeji yana k'ara fusganshi, lallai yana son ibtisam da yawa, wanda ya tabbata sonta a jininshi yake.

Hidima ake Sosai na bikin ibtisam anje anyi mata danki a dangareren gidanta ginin gidan sama, sama akwai d'aki uku, k'asa kuma akwai d'aki biyu, ansa Mata gado a d'aki uku, sannan anyi mata jeran falo, gaskiya Abba yayi k'okari Sosai domin ya kashe dukiya Sosai akan wannan hidiman bikin, sannan ya fitar da y'arshi kunya, dan yayi mata kayan d'aki masu kyau masu tsada kuma, sai dai ayi musu fatan samun zaman lafiya da zuri'a dayyiba

Biki Wan shagali, yau za'ayi bridal shower inda aka kayata a hall, Mata ne zallah kawai a wajan inda Amarya tayi dressing cikin wata arniyar gown, Wanda yayi mata mugun kyau, ibtisam ba'a Mata wani makeup Sosai ba, Zarah ce tama shafa mata powder domin sunce kwalliya sai ranan dinner, Anci ansha anyi rawa kowa ya watse

Ranan da za'ayi dinner Mum tazo Kano Wanda ranan bikin saura kwana uku

Masu makeup aka kawo inda suka tsara ma Amarya kwalliya na Kece raini, gaba d'aya ban gane ibtisam ba, domin tayi wani irin mugun kyau, lallai ibtisam kyakyawa ce, shi kanshi kabir daya ganta ranan saida yayi mamaki, domin ita ba ma'abociyar yin kwalliya bace, lallai yayi Sa'a daya samu ibtisam a matsayin mata, wajan zaman amarya da ango su biyu inda sukai bala'in kyau, gaba d'aya iyayen amarya da ango sun hallari dinner din, inda Zarah ta bada kad'an daka tarihin Amarya, Tahir kuma ya bada na ango, ranan anyi B'ari da kud'i wajan lik'i, kabir sai kafu kafu yake da ibti d'inshi

Anci ansha sannan aka fara tafiya, ango da kanshi ya dawo da Amaryanshi gida, koda suka faka motar a kofar gidansu ibtisam, kallonta yayi tare da fad'in Amarya bakya laifi, koda kin kashe dan masu gida

Ibtisam tayi dariya tare da fad'in kai dako an d'aureni, in kashe d'an masu gida Kut

Shima dariyan yayi tare da fad'in babu Mai d'aureni karki manta kefa amaryan barrister Kabir ce, Kinga kuwa babu Mai d'aure min ke

Dariya tayi Sosai ba tare da tace komai ba

Yace Kinga yanda kikai kyau kuwa? Kai dama haka kike dakyau ban sani ba? Gaskiya am lucky

Ibtisam tace uhm.

Kabir ido ya k'ura Mata yana kallonta.

Ibtisam da kanta ke k'asa jin yayi shuru yasa jikinta ya bata kaman yana kallonta ne, A hankali ta d'ago kanta Aiko caraf idonta ya sauka a nashi, da sauri ta kauda kanta gefe tare da fad'in ina jin bacci Zan shiga gida

Kabir murmushi yayi tare da kamo hannunta ya ri'ke yace kin gaji da ganina ne??

Kaita girgiza alaman a'a tana kuma k'okarin kwace hannunta daka nashi

Ganin tana son ta janye hannunta daka nashi yasa ya k'ara ri'ke hannun Nata dakyau, tare da fad'in tunda dai bakya son ganina let me go

Tace a'a kawai na gaji ne Sosai

Kabir yace OK saida safe

Da sauri tace Allah ya kaimu, domin ita burinta ya sakar mata hannu daka ri'kon da yayi mata

Shiko kabir bai sakar mata hannun ba, sannan bai bud'e motar ba,dan yayi luck d'inshi

A hankali tace let go of my hand, I need to go and sleep plz

Sakar mata hannun yayi tare da fad'in take care

Tace I will sannan yayi unlock din motar ta fita

Cikin gida ta shiga wanda yake makil da mutane, kai tsaye d'akinsu ta nufa wanda babu wani ba'kon daya sauka a d'akinsu

Zarah tace ina kuka je keda angon naki?

Ibtisam tace muna waje tun d'azu

Zarah tace nasha ko AI kun biya wata duniyar ne

Uhm kawai ibtisam tace tare da kwanciya akan gadon d'akin Tana fad'in Kai na gaji Wlh, Bari in huta kad'an, in tashi inje in wanke wannan makeup din

Zarah tace aiki ja, wlh kinyi kyau Sosai, sun iya makeup

Ibtisam tace Sosai kuwa.

Zarah tace nifa ina son saki a status Amma saboda karsu Aisha su gani na kasa saki

Ibtisam tace in banda abunki kiyi Hiding nasu su daina kallon miki status mana

Zarah ta saki dariya tare da fad'in hakane fah, kai Bari inyi yanzu in saka

Washe gari Thursday kuma ranan za'ayi kamu, A ranan Ahmad brother d'in ibtisam yazo, shida Dad, ita dama Mum a hotel ta sauka, domin tace bata iya kwana cikin mutane

Ibtisam tayi murnan ganin Ahmad Sosai

Anyi ma ibtisam makeup inda aka tafi wajan kamu, shima kamun an k'ayata shi Sosai, inda ango da abokanan ango suka zo suka musu lik'i tare da d'aukan amarya da ango hoto, suka dan zauna na wani lokaci wanda bai wuce minti 30 ba, sannan suka wuce.

Hall din da akai kamu din yayi matukar tsaruwa, da had'uwa, komai dai gwanin burgewa da sha'awa, abun ba'a cewa komai

Anci ansha Anata son Barka Kafin kowa ya watse daka wajan

Koda suka koma Gida, ibtisam wanka tayi tare dayin sallah sannan ta kwanta danta huta, domin gaba d'aya tunda aka fara wannan hidiman bikin bata samun hutu

Tana kwance tana tuna ranan da Kabir yayi kissing d'inta, ido ta lumshe tare da furta Anya zai barni kuwa har in kammala karatu na kuwa?  Uhm naga yanda yake ta zakewa uhm..... K'aran wayarta ne ya  Katse Mata tunani

D'auka tayi taga kabir dinne, sawa tayi a kunne tare da fad'in hello

Kabir yace my ibti kinyi bacci ne?

,
Tace a'a, nadai kwanta Ina shirin inyi

Yace OK, yau fah kinyi kyau Sosai gaskiya

Tace uhm nagode

Yace gobe zani Abuja, gaba d'aya na manta muna da zama a court wlh, gashi gobe Friday

Ibtisam tace toh fah, yanzu inka tafi goben sai yaushe kenan?

Kabir yace goben zan dawo, zan tafi da sassafe, coz 10 zamu zauna, shap na manta wlh gaba d'aya

Ibtisam tace Allah ya kaimu, Allah ya kaika lafiya ya dawo mun dakai lafiya

Ya amsa da Ameen my ibti

Sun taba fira Sosai inda yayi mata sallama

Washe gari tun 6 kabir ya kama hanyar zuwa Abuja

Masu iya magana dai sukace rana bata k'arya sai dai Uwar d'iya taji kunya, A yau juma'atu babban rana a garin Kano Bayan an idar da sallah juma'a aka fara maganan daurin auren ibtisam da Kabir Wanda Dad ne wakilin ibtisam

Ana faman son a d'aura aure sai ga wani ya shigo cikin masallacin da sauri yana fad'in ku dakata, inada magana

Nan kowa hankalinsa yayi kanshi..

Mutumin ya kalli Abba, tare da fad'in karka yarda ka aura ma kabir y'arka, domin yana da cutar nan Mai karya garkuwan d'an Adam, wato HIV aid

Gaba d'aya aka saki salati, d'aya daka cikin dangin kabir ya tashi cikin zafin rai, tare da fad'in amma kam bawan Allah wannan wani irin kazafi ne?

Mutumin idonshi nakan Abba yace, bawan Allah gaskiya na fad'a, amma idan zaku cuci yarinyar shikenan, ni Nayi gaba, in kuna tantama ku gwada

Abba kam shuru yayi yana nazari, gaba d'aya kanshi ya kulle

Dad ne yayi karfin halin yin magana tare da kallon iyayen Kabir, yace inaga Ayi gwajin HIV, Kafin Ayi bikin

Nan k'anin mahaifin Kabir yace wannan ai cin fuska ne, kenan Sun yarda da abunda wannan Makaryacin yace?

Dad yace ko d'aya, amma domin a kauda tantama ko zargi inaga Ayi gwajin

Nan k'anin mahaifin Kabir yace tunda suna zargin kabir su ri'ke y'arsu, basa son auren

Wani aminin mahaifin Kabir yace gaskiya ne, dama su Dad sun tarasu ne dan suci musu zarafi

Dad abun dariya ma ya bashi, shidai baiga Abun fad'a ba, kojin zafi, kenan dagaske yana da HIV, din tunda suka d'auka da zafi

Dad yace kuyi hakuri, dukanmu ba yara bane, ina son ku sani mu iyayen yarinya bazamu Jefa rayuwarta cikin hatsari ba S....

Nan abokin baban kabir yace babu damuwa mun gode, amma ina son ku sani yanda aka tara mutane a nan, toh sai anyi wannan aure, ni naba ma kabir auran y'ata, ku kuma saiku aurar da y'arku mu gani

Dad murmushi yayi tare da fad'in shikenan, itama yanzu za'a aura Nata auran a gabanku, tunda baku da adalci...

Nan Dad ya ciro kud'i ya mi'ka ma Abba d'aya sannan yaba iyayen Kabir masu, ya kalli Abba yace ina nema ma Najeeb auren ibtisam

Nan Abba ya girgiza kai tare da fad'in ni zan bada sadaki domin d'ana ne NAJEEB,

Nan take Abba ya ciro dubu d'ari aka d'aura auren Najeeb da ibtisam

Suma aka d'aura auren kabir da Hafsat

Toh kabir dai yana hanyar dawowa kaduna, koya zaiji wannan Abun inya dawo?

Sannan ga ibtisam da aka d'aura mata aure da babban enemy d'inta, itama koya zata ji wannan Abun?

Toh Uwar Gayya NAJEEB, Zaima yarda da wannan auren kuwa? Musamman yanda baya shakkan kowa, yaga an d'aura mai ibtisam yarinyar da yake fad'in bata da kunya, sannan bata da komai.....  Yanzu aka fara muje zuwa......









Read and leave it, dnt share to anyone

*IDAN KIKA KARANTA BAKI BIYA BA INA BINKI BASHI, KUMA NAUYI NE A KANKI*

*WACCE TAKE SON BIYA ZATA TURA 200 TA ACCOUNT NUMBËR DINNAN*

3138831065 Firstbank Maryam Alhassan

*SAI A TURO SHAIDAN BIYA TANAN 08060860886 IDAN KUMA KATI NE MTN SHIMA TA NUMBER DIN ZAKI TURA 200 NAIRA ONLY*

*KARKI MANTA KINYI ALKAWARI, BAZAKI FITAR MIN DA NOVEL BA, IDAN KIKA FITAR DASHI KEDA ALLAH, KUMA KINA D'AYA DAKA CIKIN MUNAFUKAI, DOMIN ALAMAN MUNAFUKI GUDA UKU NE, 1 IDAN ZAIYI MAGANA YAYI K'ARYA 2 IDAN AKA AMINCE MASA YAYI HA'INCI 3 IN YAYI ALKAWARI YA SABA, KIN DAI JI, KINCE KIN MIN ALKAWARI, IDAN KIKA SABA KIN ZAMA MUNAFUKA, KUMA WUTAR MUNAFUKI DABAN TAKE, IDAN KIKA FITAR KINMA KANKI*

Bayan an d'aura auren ibtisam da Najeeb, nan take aka d'aura na hafsat da kabir suma. Inda dubban mutane suka shaida wannan auren

Bayan mutane sun Fara fita, daka family din ibtisam saina KABIR cikin masallacin

Abokin mahaifin Kabir yace kayan da kuka saka a gidan nawa kuka kashe?

Abba shuru yayi ba tare da yace komai ba, domin ya Lura kaman y'an uwan kabir sun d'auki abunda zafi, wanda shi baiyi zaton haka daka garesu ba, ko kad'an, dan yasan y'an gidan mutunci ne

K'anin mahaifin Kabir yace ku Fada nawa kuka kashe, dan Inaga tunda Abun ya zama haka gwara a baku kud'in kayan tunda ankai an kuma jera

Dad yace hakane, sai dai ina son ku sani, mun bar ma kabir kayan da duk mukasa a cikin gidan, koba komai ya nuna mana k'auna domin na tabbata inda ya.....

Mahaifin hafsat ya dakatar da Dad tare da fad'in kayi hakuri amma maganan gaskiya bazamu amshi wannan kyautar ba, domin y'atace zata zauna a gidan, kuma a matsayina na mahaifinta inada burin yi mata komai in zatayi aure Dan haka ku fad'i abunda kuka kashe

Dad ya kalli Abba tare da fad'in ya fad'a abunda ya kashe tunda yace haka

Nan Abba ya fad'a, tare da fad'in wasu ya manta

Mahaifin hafsat check ya rubuta tare daba wani yace yaje banki yanzu da sauri inya Kawo kud'in saiya kaima mahaifin ibtisam gida

Abba da Dad tashi sukayi suka tafi, harda Allah Abba baiyi zaton haka daka family din KABIR ba, koda yake ya gode Allah da hakan ta faru Koba komai y'arshi ta tsira daka wannan mugun cutar Mai Karya garkuwan jikin d'an Adam, toh Ina ma mutumin da yazo ya fad'a? Koma wanene Allah ya biyashi, "lallai aure Kafin gwaji yanada matukar amfani Sosai ya kamata a dinga yin gwaji Kafin Ayi aure domin gudun dana sani nan gaba

Nan su Dad da Abba suka shiga mota Bayan sun gama gaisawa da mutane Wanda suka zo ko ince suka tsaya aka d'aura aure Bayan an idar da sallah

Kai tsaye gida suka nufa inda taron mata ne makil a ciki, amma haka Abba ya shiga bayan yakai Dad falon ba'ki ya zauna wanda babu kowa a ciki.

Gidan cike yake da mutane y'an biki, Zarah dake zaune a falo tana ganin Abba tasan an d'aura aure dan haka da sauri ta shiga inda ibtisam take tana waya da kabir kwace wayar Zarah tayi a hannun ibtisam tare da fad'in kai wannan angon ai sai kayi hakuri tunda an d'aura aure ka barta taji da mutane Wanda suka zo dan tayaku murna, waya tun d'azu

Kabir yayi dariya tare da fad'in ayi mana hakuri, Nima tun dazu aketa kirana amma na'ki kashe wayar inata ganin calls Nasan duk y'an tayamu murna ne

Zarah tace toh gaskiya ka d'auka kabar ibtisam taji da mutane, anjima fah za'a kawo maka ita

Kabir dariya yayi cikin jin dad'i tare da fad'in insha Allah, Nima na shigo Kano yanzu plz ki kulan min da my wife

Zarah tace an gama barrister Kabir tare da kashe wayan

Kallon ibtisam tayi dake zaune tana dariya, Zarah tace congratulations burinku ya cika yanzu Naga Abba ya shigo Nasan har an d'aura auren

Ibtisam tace uhm

Dukan wasa zarah takai Mata tare da fad'in ya kika ji?

Ibtisam tace Zarah gabana yana fad'i, wlh yanzu naji gabana ya fara fad'i,kodan an d'aura auren ne yasa nake jin haka??

Zarah tayi dariya tare da fad'in ina tunanin hakane amma ki dinga furta Kalman Innalillahi'wa inna ilaihirajiun.

Ibtisam tashi tayi daka k'asa tahau gadon d'akin ta kwanta tare da fad'in Innalillahi'wa inna ilaihirajiun, tana ta nanata wa, lokaci d'aya kuma ta lumshe ido

Tayi wajan 5mnt sannan ta bud'e idon tare da kallon Zarah wacce ita din ita take kallo

Ibtisam tace Zarah har yanzu gabana yana fad'i plz bani wayana in kira kabir

Zarah tace ki kira kabir kuma? Ba yanzu kuka Gama waya ba? Kai Wlh ban taba ganin amarya da ango masu zumudi ba irinku,saurin Mai kukeyi ne? Anjima fah kad'an za'a kaiki

Ibtisam tace uhm wlh ko d'aya kawai gabana ne ke fad'i, sai yasa nake son ji ko KABIR ya isa Gida, kin San yana hanya ne

Zarah tace kwantar da hankalinki dazu dana amshi wayar yace Min ya shigo Kano, may be yanzu yana gida ma

Ibtisam tace nidai plz bani waya ta, inyi magana dashi

Mi'ka mata zarah tayi ganin yanda ta damu, kiran Layin KABIR tayi taji call waiting alaman yana waya, dan haka ta kashe dan tasan inya gama zai kirata

Aiko ko 1 mnt ba'ayi ba sai gashi ya kirata, d'auka tayi da sauri tare da fad'in ka isa Gida?

Kabir yace ibtisam maike faruwa ne wai?

Tace Dame?..

Yace waya nakeyi yanzu haka Ina kan Layin gidanmu ne, ance an samu matsala wajan auren kuma sunki fad'amin wai saina k'araso

Ibtisam tace matsala kuma? Kai Anya kuwa

Yace zan kiraki Ltr Bari in shiga inji

Tace OK tare da kashe wayar ta tashi tsaye....  Dai dai lokacin Ummi ta shigo d'akin Tana fad'in ibtisam abbanki yana kira

Tace ummi yana ina

Ummi tace yana falonshi na ba'ki

Ibtisam gyalenta ta d'auka tare da yafawa tabi bayan Ummi suka shiga har falon ba'kin, inda taga su mum da Dad da Abba da Granny

Granny tace ku fad'amin maiya faru mana, tun dazu sai jira muke gata tazo AI

Ibtisam zama tayi a k'asa tare da gaida Dad wanda ya amsa

Lokaci d'aya Dad ya fara magana kaman haka, an samu matsala wajan daurin auren ibtisam da Kabir

Dam ibtisam taji gabanta ya yanke ya fad'i

Dad ya zayyano musu abunda ya faru har d'aura auren najeeb da ibtisam da akayi da kuma auren da akayi ma kabir din

Ibtisam tashi tayi tana hawaye tare da fad'in Wlh sharri akayi masa, wlh k'arya akayi masa, ni na yarda koda yana da HIV Wlh zan aureshi a haka, dan Allah Abba kar a fasa wannan auren na ro'keka Abba cikin kuka mai ban tausayi....

Abba yace rufemin baki mara hankali, baki ji abunda akace ba, an d'aura miki aure keda Najeeb b....

Wani irin ihu ta saki Wanda ita sai yanzu taji hakan, domin sanda Dad na bayani tunda taji ance an fasa aurenta da Kabir saboda yana da HIV gaba d'aya taji kunnenta ya toshe bata ji

Tace Wlh Abba bana son wannan auren, kabir.....  Lokaci d'aya jiri ya d'auketa tayi k'asa luuuuuuu..

Da sauri mum ta ri'keta tare da kiran sunanta ibtisam ibtisam, amma ina ko gezau batayi ba

Granny ce ta kawo ruwa aka yayyafa Mata ta Farfado aiko tana farfadowa tare da fad'in Wlh kabir nake so Dan Allah karku rabamu sai kuma ta saki kuka mai ban tausayi Tana fad'in na shiga uku

Abba ranshi ya baci da abunda ibtisam din take fad'i dan haka cikin bacin rai yace in batayi shuru ba saiya karyata

Dad yace a'a akan wani dalili, taya zaice mata haka, Aiko dan abunda ya sameta dole tayi shock, in baka lallabata ba ai baka Mata fad'a ba, abun saiya mata yawa

Abba kallon Ummi yayi tare da fad'in ku tashi ku shiga ciki da ita.

Tashi sukayi harda Granny akai ciki, ibtisam na ri'ke jikin Mum Kai tsaye d'akin su ibtisam din suka shiga, inda suka iske Zarah

Zarah ganin ibtisam na kuka yasa ta d'auka ko anyi mata irin nasihan da akema amare ne yasa take kuka

Mum tace ibtisam kiyi hakuri, ki d'auki hakan a matsayin kaddara, Allah yasa kabir bashi bane mijinki K....

Please Login or Register in order to submit comment