Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

wani abun mamaki ta kasa fad'ama kowa, daga tazo fad'a saita fasa, ta rasa dalili, ita dai ranta yana bata ta rufa Mai asiri.....

Hawaye take da yake ba kuka bane, kuma akwai huta ga k'aran fanka yasa su Aisha basu San mai takeyi ba, balle su Fara mata tambaya ko lafiya

Ido ta lumshe tana ganin yanda najeeb din ke fucking din Najwa, da sauri ta bud'e ido tare da tashi ta zauna tana sauke wani nishi, sama sama, lokaci d'aya kuma ta fita taje ta dauraye fuskanta, inda ta hango zarah Tana waya

Bayan ta dauraye fuskan Nata, ciki ta koma inda tahau gado ta kwanta, still tunanin nedai ya kuma dawo mata, duk yanda takai danta cire Abun a rai ta kasa gaba d'aya tunanin abun ne a ranta

Haka taita juyi akan gadon har zarah ta shigo d'akin Itama ta kwanta, ibtisam ta kasa bacci har su Aisha masu fira suma sukai bacci

Washe gari ibtisam idonta duk ya kumbura ga ciwon kai, domin batai bacci ba, ga exam 8 haka ta shirya ta nufi exam, Bayan sun fito daga exam dinne ta dawo dak'i inda ta samu kubra na zaune ta manne waje d'aya alaman zazzabi ke damunta

Ibtisam tace kubra bakya jin dad'i ne??

Kubra tace eh wlh fever ke damuna Sosai, plz ki bani paracetamol insha, ko zanji dama dama

Ibtisam tace Kai Wlh banda paracetamol, amma inaga ki tashi muje hspt sai a dubaki, a baki magani, Kinga is very risk kisha magani baki San maike damunki ba

Kubra tace hakane, bari muje, tashi kubra tayi ta d'auki babban hijab tasa suka fita ita da ibtisam, inda sukai cikin Shika domin taga Dr

Bayan taga Dr inda aka bata gwaji inda aka ga Malaria ne, nan aka rubuta Mata magani, suka biyo ta wajan emergency, inda suna tsaye domin wata mota ta wuce, aka faka wata mota kusa dasu, nan aka bud'e wani matashi ne wanda kallo d'aya zaka mishi kace lafiyanshi kalau, domin ko motsi bayayi amma sai wanda suka kawo shi sukace bazai iya tafiya ba, nan aka d'auko Keken guragu domin a sashi, nurse din na tabashi tace ai ya rasu......

Kubra wani irin ihu tasa yanda kuka san ta san yaron, kuka take tana fad'in ibtisam kalla kiga, wlh kaman kice ya tashi, kalla kiga ikon Allah Innalillahi'wa inna ilaihirajiun, wayyo kai Allah yaji k'anka

Nan y'an uwan yaron suka bita da ido, domin ganin yanda ta nuna damuwa akan dan uwan nasu

Nan ibtisam ta jata sukai gaba

Kubra na hawaye tana fad'in ibtisam wannan kukan Inayi ne tare da tausaya ma kaina, wlh ibtisam tunani Nayi inda nice na mutu, mai zance ma Allah?? Gaba d'aya na bata rayuwa ta, na bijire ma Abun da ubangiji yace Ayi, nabi hudubar shaidan, amma yanzu na gode Allah daya ganar dani tun lokaci bai k'ure Ba, wlh gaba d'aya komai na duniya ya fitar min a kai, ina matukar jin tsoran in aikata Sabo yanzu, lallai ibtisam idan kana son ka k'ara jin tsoran Allah imani ya Kama ka kazo asibti ziyara, na tabbata inda mun shiga accident and emergency da munga abubuwa wanda tayu wani in muka gani bazamu iya bacci ba, saboda tausayi, ibtisam kalla wannan saurayin, jikinshi fresh kaman bai mutu ba, kaman kice Mai ya tashi, ya kuma tashi din, lallai duniya ba komai bace

Ibtisam tace hakane nima mutuwar shi ta tsaya min a rai tasa gaba d'aya jikina yayi sanyi..... Allah yaji k'anshi tare da sauran musulmai

Kubra ta amsa da Ameen, tare da fad'in Wlh ibtisam ke Kinji dad'i kina da aure, rayuwarki Abun sha'awa, baki da wani fargaba, amma mu gashi babu aure ga sabon Allah, gashi karatun bama bashi muhimmanci tunda yawon mu kawai muke, in mun dawo mubi lecturer su kwanta damu, dan karsu fadar damu, kai Wlh babu komai cikin raina sai tarin dana sani, gobe zan koma Gida tunda na Gama paper, ina son koda na koma Kafin hutu ya Kare zamu dinga waya ina tambayarki abunda ya shige min duhu

Ibtisam tace karki damu kubra, insha Allah, duk sanda kike da tambaya ki kirani kawai

Nan sukai gaba, inda suka koma cikin skul

Koda suka shiga d'akinsu a kwance suka tarar da zarah

Ganin Sun shigo yasa Zarah fad'in Ina kukayi

Ibtisam tace hspt na raka kubra ganin Dr, ya paper din??

Zarah tace hmm, Alhmdlh, tare da kallon kubra tace bakya jin dad'i ne? Ko duk maganan mutumin nan ne??  Kubra tace a'a kawai zazzabi naji Inayi

Zarah tace Allah ya sawake

Washe gari duka suka watse sukai gida, Zarah taso ibtisam ta bita suyi abuja amma ta'ki, dole ta hakura ta tafi abuja ibtisam tayi Kano

Ibtisam ta isa Gida wajan 1 Tana shiga ta iske Ummi bata nan sai granny dake sallah, Dan haka itama alwala taje tayi inda ta Fara sallah

Bayan ta idar, ta kalli Granny dake zaune tace ina ummi??

Granny tace ta tafi anguwa, ya naga kin dawo, ko baki da lafiya ne? Naga duk kin rame

Ibtisam tace Hmmm granny ba dole ba, exam babu dad'i Wlh, munyi hutu ne sai yasa na dawo

Granny tace auwo tare da gatsan goranta tana ci tana gurus gurus

Ibtisam tace wai ba zaki daina cin wannan goran ba??  An fad'a miki yana da Illa, Amma kin k'i, wlh Granny ki shafa mana lafiya ki daina, kar kije kici abunda zaisa Musha wuya, gwara ki mutu cikin salama ba tare da wahalan jinya ba......

Granny tace dallah Rufamin baki, AI sai a kasheni, naga bakan mutum nake ba, in naci goro ya kashe ni, jiki na ko naki, haba yara sai iyayi komai ace yana da Illa shi kenan mutum kar yaji dad'in rayuwa, haba ni ban taba jin inda akace goro nada Illa ba

Ibtisam tace ai sai kiyi taci tunda an fad'a miki kin dage, nidai in ciwo ya kama ki bazanyi jinya ba, tunda na fad'a

Granny ta tsuke baki tare da fad'in shirmen banza da hofi, dama wake bukatar ki? AI na tabbata babu abun arzikin da zaki iya, Aini da kiyi jinyata gwara in zauna ni d'aya yafi min, wannan ba'kar zuciya taki, gashi mijin naki kin kasa hakuri dashi.....

Granny jin ibtisam tayi shuru yasa ta kalleta, ganinta tayi tana hawaye....

Granny tace miye haka kuma?? Haba takwarata maiya faru? cikin sigar rarrashi take tambayarta

Ibtisam kallon Granny tayi tare da fad'in yanzu Granny komai najeeb yayi ba'a ga laifinshi ba sai nawa???

Granny tace ba haka nake nufi ba, abunda nake nufi kin kasa hakuri dashi.....

Ibtisam tace taya zanyi hakuri dashi?? Granny karki manta ni mace ce, an d'aura min najeeb ba tare da sanina ba, infact ma ban taba tunanin zan aureshi ba, gaba d'aya nasa rai za muyi aure da kabir sai naji an d'aura da wani, yau najeeb Koba dan uwana bane shi, dole yanda naji babu dad'i hakan zanyi, anyi min wannan a matsayina na mace, wanda ya zama dole in hakura in zauna dashi, Wanda nasan igiyar auren shine keda ikon tsinkata, sannan shi namiji ne, Ance in za suyi adalci su Fara daga Biyu.....

Kinga Mata biyu akace ba d'aya ba, kinga yana da ikon k'ara auren wacce yake so, amma nifa??  Bani dashi, dole shi dinnan dai zan zauna mawa, ba wani ba, granny inda kin San zafin rabuwa da wanda kake so da ance Nayi hakuri, da yawa mutane basa gane wani abu, yau Indai Abu ba'a kansu yake ba, koya fad'a musu ba, toh basa gane irin zafin abun da kuma rad'adinsa

Nasan ni mace ce, kuma Aljanna ta tana k'asan kafar mijina, Nasan dole nayi masa biyayya, dole nayi masa abunda yayi umarni da inyi masa Indai bai saba ma sha'ria ba......

Duk Nasan wannan, toh amma shi najeeb din yana bin abunda ubangiji yace??

Baya bi, mutumin daya kauce ma mahaliccin shi taya wani zai bishi.....

Kuka ta saki mai cin rai sannan tace Granny, Koba alakan aure najeeb jinina ne, duk da tun Farko bama jituwa haka koda mukai aure babu wata magana Mai dad'i data taba shiga tsakanin mu, yau Koba najeeb dake jinina ba, ko wani naga yana shan giya Wlh zan tsaneshi, amma da yake najeeb akwai ala'kan jini sannan aure ya had'amu dole haka na hakura, kuma na tabbata inda najeeb ba jinina bane kuda kanku zaku ce saiya rabu dani, tun a lokacin da yayi min sharri yace wannan cikin ba nasa bane

Ya kamata inda kuna sona a lokacin da kun raba wannan auren, amma daga karshe sai kuka barni a wajansa, duk da ya nuna baya bukatar in zauna a tafi dani amma sai lokacin kika ce dole in zauna,  haka kuka tafi kuka barni dashi

Granny Kun San irin abunda naji??  Kun san irin kuncin da naji??  Duk baku Sani ba, ku burinku in zauna dole a gidan miji, tunda ni mace ce banda wani zabi face inyi hakuri da duk irin abunda miji zaimin, ku matsalanku kar ace y'arku ta zama bazawara koh??  Koba shi bane matsalan??

Granny da yawa a k'asar Hausa Anfi samun irin wannan matsalan, kiga namiji shine dukan mace, cin zarafin ta, ya hanata haiyuwa, saboda baya bukata, ya tauye Mata hakkinta, etc

Kinga duk irin wannan matsalolin ba zasu gyaru ba, har sai iyaye sun daina jin tsoran kar y'ay'ansu su dawo gida su Zame musu nauyi ko kuma kar ace suna da bazawara

Granny shifa aure sunna ne, ba farillah bane, sannan shi aure daka ranan da mace tayi komai kikayi lada ake baki, bauta ne

Ni a nawa ganin Nasan duk abunda akace bauta ne sai an jure, amma da mace ta zauna miji ya dinga kuntata Mata, ita kuma tana masa abunda zaiji baya so, gwara a raba auren, domin anyi aure Dan samun lada sannan yakai mutum da Aljanna, amma babu farin ciki kuna kai kanku hanyar halaka, ku jefa kanku wuta, Indai irin wannan ne miye amfanin auren??  Kinga babu shi

Namiji zai bugi mace, ya mata mummunan duka, inta dawo gida sai a bata hakuri ace ta koma aure d'an hakuri ne shi dama bauta sai an jure, aita bata hakuri ana fad'in kiyi ta hakuri wata rana sai labari.....

Toh Kunga tun daga nan kun ba mijin daman ci gaba da dukanta kenan, domin yaga yayi na Farko ba'a d'auki mataki ba, an k'ara tura mishi ita, kinga zaiga baki da wani gata, wani namijin ma sai yaga kaman Turaki akeyi wajansa, kinga ba'a Fata a haka sai kiji ana fad'in ya kasheta wata rana, ko ita ta kashe shi, domin ita zuciya bata da k'ashi. Bawai Ina nufin Idan namiji ya bugi mace a raba auren bane a'a, but ya kamata a nemo shi aji dalili da zai bugeta, in Abun ta Kama a nemo har waliyansa ayi magana akan Karya k'ara dukanta, in Abun bazaiyi ba ko babu Mai fad'a mishi yaji zaku iya zuwa kotu, alkali ya bashi takarda yayi signing akan inya K'ara dukanki akwai hukunci akansa.

Indai aka d'auki wannan matakin bazai k'ara ba, shine ake kira da kwatan y'anci

Idan ana haka za'a rage irin abubuwan dake faruwa a gidajan aure musamman......

Granny ta dakatar da ita da fad'in ya isa haka ibtisam, na fahimta, amma ina son ki sani, shi aure dace ne, kuma ko wace mace tana da nata jarabawan, Mai hakuri yana tare da Allah, eh abunda kika fad'a gaskiya ne, yana dakyau a kwatan ma mutum yancinshi , amma ina son ki san wani abu guda d'aya akan najeeb, sannan ina son ki sama ranki wani abu, ki d'auka duk abunda yayi miki yayi miki ne cikin rashin sani, ba tare da yasan yayi ba...... Ibtisam na k'okarin magana Granny ta Katseta da fad'in kiyi shuru in Gama magana sai kiyi

Granny taci gaba da fad'in yanzu kinga NAJEEB yana Abu ne ba tare da sanin ilimin addini ba, kinga baiyi karatun addini ba, duk wasu abu da zaki ga yanayi Ina son ki d'auka cewa bai sani bane, abunda muke k'okarin yanzu mu d'aura shi a hanya kenan, muna son yasan addini ta yanda zai bauta ma mahaliccin sa, duk wannan Abun laifin mahaifinshi ne daya fifita boko akan karatun addini, wanda shi yake d'auka yama d'ansa gata ne, bai san ba gata ya masa ba, domin inda yana sonsa yana son nuna mishi gata shine ya koya Mai ilimin addini, wanda shine zai kaishi ga tsira ranan lahira,.

Granny kamo hannun ibtisam tayi tana fad'in dan Allah takwara ta, Ina son ki zauna da najeeb, ki ceto Dan uwanki daga fad'awa halaka, ina son ki zauna dashi matsayin mata Mai biyayya, domin ke y'ar uwarsa ce, Kece zaki fi kowa sanin darajansa, Koba dangantakar aure akwai na jini, ina son ki duba girman Allah kiyi hakuri ki koma wajan mijinki..........

Ibtisam kuka ya kubce mata sosai gaba d'aya ta kasa magana, ta rasa mai yasa Granny take ganin kaman itace take gudun zama dashi, shine fah yace ya saketa, Bayan haka kuma ance Mai sakin baiyi ba, amma ya tafi ba tare da yace komai ba, sannan tunda ya tafi bai kuma waiwayo waba, amma granny tazo tana d'aura mata laifi........






Read and leave it, dnt share to anyone*IDAN KIKA KARANTA BAKI BIYA BA INA BINKI BASHI, KUMA NAUYI NE A KANKI*

*WACCE TAKE SON BIYA ZATA TURA 200 TA ACCOUNT NUMBËR DINNAN*

3138831065 Firstbank Maryam Alhassan

*SAI A TURO SHAIDAN BIYA TANAN 08060860886 IDAN KUMA KATI NE MTN SHIMA TA NUMBER DIN ZAKI TURA 200 NAIRA ONLY*

*KARKI MANTA KINYI ALKAWARI, BAZAKI FITAR MIN DA NOVEL BA, IDAN KIKA FITAR DASHI KEDA ALLAH, KUMA KINA D'AYA DAKA CIKIN MUNAFUKAI, DOMIN ALAMAN MUNAFUKI GUDA UKU NE, 1 IDAN ZAIYI MAGANA YAYI K'ARYA 2 IDAN AKA AMINCE MASA YAYI HA'INCI 3 IN YAYI ALKAWARI YA SABA, KIN DAI JI, KINCE KIN MIN ALKAWARI, IDAN KIKA SABA KIN ZAMA MUNAFUKA, KUMA WUTAR MUNAFUKI DABAN TAKE, IDAN KIKA FITAR KINMA KANKI*






Kaman granny tasan abunda ibtisam ke tunani, tace ibtisam zaki ga kaman bana goyan bayanki, ba haka bane, yanzu duniya ta canza, komai ya canza, idan mace batai hakuri gidan mijinta ba inta fita bata san wanda zata aura ba, kinga gwara tayi hakuri ta zauna da Wanda tasan halinsa, saita dinga kiyaye wa, amma yanzu in mace ta nemi saki , inhar mijinta ya saketa bata san wa zata fad'a mawa ba, sai yasa ake cewa hakuri shine gaba da komai, kuma Mai hakuri yana tare da Allah, wlh ibtisam ban taba ganin laifinki ba gaba d'aya na najeeb ne, domin ke aka cuta amma gashi ina rokanki akan kiyi hakuri wata rana insha Allah za kiyi dariya

Ibtisam nidai burina in ganku tare har abada, shine Fata na, indai kukai haka zan mutu cikin salama......

Da sauri ibtisam ta rungume Granny tana kuka tare da fad'in insha Allah bazaki mutu ba Granny

Granny tayi murmushi tare da fad'in ai mutuwa ta zama dole ibtisam, lokaci kawai ake jira, amma dole ce ko Ana so ko ba'a so

Ibtisam tace toh nidai Granny abar maganan mutuwar nan dan Wlh ba son jinta nake ba, gaba d'aya

Granny tace Indai kam baki Sonta saiki koma ma mijinki, yanda zaki sani farin ciki

Ibtisam tace Granny ni Kinga Wlh yunwa ma nake ji, Sosai mai kuka dafa ne Inci

Granny tace ja'ira wato canza firan zakiyi koh??  Yayi miki kyau ai

Ibtisam tashi tayi ta nufi kitchen inda ta dibo abinci domin taci, tana cikin ci sai ga Ummi ta shigo cikin d'akin tana fad'in ah Ashe y'an karanta an dawo

Ibtisam cikin fara'a da murna take fad'in eh Ummi tun dazu na dawo bakya nan

Ummi tace Mun fita da Maman fati ne, ya karatun an Gama jarabawan kenan?

Ibtisam tace eh mun gama zamu sha hutu Mai tsawo harna wata d'aya da sati Biyu

Ummi tace Kai Aiko zaku dad'e a gida Sosai Allah ya taimaka bari inje in watsa ruwa duk na kwaso rana, Ummi ciki tayi tabar ibtisam da Granny





*AMERICA*

najeeb ne zaune yana karanta al'qur'ani domin gaba d'aya yanzu ya iya had'a ba'ki, abun har mamaki yaba malamin yanda yayi saurin iyawa, gashi najeeb baya dad'ewa ya gane Abu, wanda yawanci tun a k'aramin shekaru mutum yake saurin haddace Abu haka, amma sai gashi Abun mamaki shi najeeb da girmansa yana haddace Abu da wuri

Malamin ne yazo inda najeeb yake yana fad'in gaskiya najeeb ka gode Allah, wlh komai naka Abun sha'awa babu wuya ka haddace Abu, nan da nan wlh kana da kwakwalwa sosai

Najeeb saida yakai karshen Aya sannan ya kalli malamin Bayan ya ajiye al'qur'ani yace malam ba komai bane yasa kaga Ina saurin haddacewa ba sai Dan Ina son in koya wanda Allah yaga zuciya ta, duk abunda nake da Wlh Ina aikatawa ne ba tare da sani na ba, sannan yanzu dana gane nake son in koya in iya dole in dage, aikina gaba d'aya na dau hutu dan in nemi ilimin addini, inta Kama ma Wlh ajiye aikin zanyi, duk da nayi yunkurin yin hakan amma suka d'age akan bazan ajiye ba, inje inyi hutu, shine nace na d'auki hutun 5mnt

Malamin yace hakan ma yayi tunda gashi yanzu ko wata biyu bamu yiba amma harka iya abubuwa da dama, ko a haka ka tsaya aika gode Allah, domin wani wanda ya taso tun yana yaro yayi karatun ban tunanin zaiyi aiki dashi akan Kai yanda kake aiki dashi, yanzu nima tafiya ta Kama ni dole zan tafi saudiya, domin mahaifina baida lafiya, Kaga bazan zauna ba har inyi wata ukun da Nayi alkawari ko a haka na Barka Alhmdlh Nasan ka koya abubuwa da yawa

Amma idan naje naga yanayin jikin nasa inda hali zan dawo.....

Najeeb yace a'a karka damu, nida kaina zan biyo ka saudiya, zanje Nigeria insha Allah daga nan Zanzo harda iyayena domin su ganka, ku gaisa

Malamin yace haka yayi, tare dayi MA NAJEEB addu'an samun nasara a rayuwa

Najeeb Bayan ya koma gidansa gaba d'aya baya son zama shi d'aya sai yaji gidan yayi masa girma, kwanciya yayi akan kujeran falon inda ya lumshe ido, lallai sai yanzu yasan yana rayuwa, a da yana rayuwa ne amma kaman matacce, domin bai San yanda zai bauta ma Allah ba, gaba d'aya wannan canjin daya samu ya sameshi ne ta sanadin rayuwarshi da ibtisam ta shigo

Ya fara tunanin yasan mai yasa shan giya ya zama haramun da zina, lokacin da tace mishi duk manyan laifin da Allah ya hana kana aikatawa, tun daga ranan ya fara tunanin sanin Mai yasa ya zama laifi har yakai shi ga kiran malam, wanda gashi yanzu gaba d'aya rayuwarshi ta canza, sai dai abu d'aya da yake fatan shima ya canza

Lokaci d'aya ya tashi ya nufi bedroom d'inshi inda ya fad'a toilet yayi wanka ya fito daga shi sai boxer da singlet Kai tsaye kitchen ya nufa inda ya Tarar damai mishi aiki yace ta Kawo mai coffee, yana fad'in haka ya juya falon ya zauna yana danna wayarshi dake hannunsa

Bayan Mai aikin ta kawo mai coffee ta ajiye Mai akan center table har zata wuce najeeb yace ta tsaya tare da fad'in gobe zani Nigeria so zaki iya d'aukan hutu, but amma ki dinga zuwa kina duba gidan coz ban son in dawo inga datti ko k'ura

Ta amsa da OK sir

Najeeb d'aukan coffee din yayi inda ya fara sha.....

Washe gari kaman yanda yace hakan ko ta faru domin kuwa jirgin k'arfe 10 yabi inda ya tafi Nigeria Kai tsaye a abuja ya sauka inda aka turo mai driver yazo ya d'auko shi,.

Bayan sun k'arasa gida, Zarah da saurinta ta nufeshi tana fad'in Wlcm bros

Murmushi ya sakar mata tare da kallonta yace ya gida da skul?  Yana ganki a gida??

Tace lafiya bros munyi hutu ne

Yace OK

Nan suka shiga ciki abunda najeeb bai taba yiba yau yayi gaida iyayenshi cikin girmamawa, gaba d'aya daga Dad har Mum sunyi mamaki tare da kallon juna

Najeeb ya lura da hakan sai yayi murmushi tare da fad'in kai am so tired I need to rest hope d'aki na a gyare yake??

Mum tayi murmushi tare da fad'in eh my only son, a gyare yake, AI ban barin dakinka da datti, domin Nasan yaron nawa baya son kazanta, amma before ka huta Aida kaci abinci koh

Yace Mum bari in huta na gaji Sosai wlh, nayi missing food d'inki amma tunda kika ga na kasa ci, toh na gaji ne

Tace OK a huta dakyau

Yayi murmushi tare da shiga d'akin nashi wanda yana shiga ya fad'a gado ya kwanta sai bacci

Mum da Dad sukam zama sukayi inda Dad yake fad'in kinga yanda yake gaidamu cikin girmamawa, gaba d'aya harta magananshi ya canza kaman bashi ba

Mum tace Wlh kuwa abun ya bani mamaki, bari dai ya tashi muji ya akayi





Ibtisam ce zaune tana ta wanke underwear d'inta, a wajan fanfo din dake waje, a tsakar gidan

Granny ta fito tana fad'in in banda kazanta mutum saiya tara su wando da skirt da yawa Kafin ya wanke, ai wannan kazanta ne

Ibtisam tace kazanta?? Lallai Granny Wlh kina shiga sabga ta da yawa, d'ago wani pant d'inta tayi tare da nuna mata da tace ina kika ga alaman kazanta a nan??  Kuma pant d'in ga sunan gudu biyar ne duka amma kina wani kiramun kazanta, salan wani yaji kisa a d'auka haka nake

Granny tace toh aji mana, AI gaskiya na fad'a Inba Kazami ba, taya mutum zai dinga tara pant da yawa haka babu wanki, ko ni da nake tsohuwa bana irin haka saike yarinya karama saboda lalaci.

Ibtisam tashi tayi tana d'iban kayan domin ta gama zata toilet ta shanya tace Kedai kika sani, nidai banda lokacin wannan surutun dake inada abunyi da yawa

Granny tace ai kyace haka mana t.....  Wani irin K'ara ta saki tare da yin k'asa, da sauri ibtisam ta saki roban dake hannunta ta nufi Granny tana fad'in Granny lafiya kuwa? Maiya sameki tana tambayar Granny tana kuka

Ganin granny bata ko motsi yasa ta nufi d'akin ummi dake bacci da gudu tana fad'in ummi Ummi kizo mukai Granny asibti na shiga uku Granny ta fad'i k'asa

Ummi dake bacci sai taji kaman tana mafarki da sauri ta tashi amma sai taji ba mafarki bane domin dai dai lokacin ibtisam ta shigo d'akin Tana fad'in ummi Granny ta fad'i muna cikin magana Dan Allah mu kaita asibti ki kira abba

Da sauri Ummi ta tashi tare dasa hijab tana fad'in maiya faru da ita?? Kai tsaye waje suka nufa inda suka tarar har yanzu tana nan kwance a k'asa tana nishi sama sama

Nan Ummi tace maza su kamata su kaita asibiti, hakan ko sukayi ibtisam ta fita ta kira Mai adai daita sahu inda suka Kama Granny ita da Ummi sukai motar da ita, direct asibiti suka nufa da ita inda aka amsheta akai emergency da ita domin a duba lafiyarta

Ibtisam kuka take Sosai, domin a duniya Tana son Granny, ko kad'an bata son taga wani abu ya sameta

Ummi sai a sannan ta kira abba Inda ta fad'a mishi halin da ake ciki, ko minti 30 baiyi ba ya garzayo asibitin Kai tsaye inda ya Tarar dasu suna zaune ibtisam nata faman kuka

Abba yace maiya sameta?? Nan ibtisam ta Fara fad'a mishi Abba muna fira na tashi inje inyi shanya tasa ihu tare da faduwa

Abba yace Toh ya isa mana kibar wannan kukan Mai Dr yace ??

Ummi tace baice komai ba, har yanzu Dr bai fito ba

Nan Abba ya zauna suna jiran fitowan Dr din

Wayar abba ce tayi K'ara d'auka yayi yaga Dad ne Bayan sun gaisa Dad yake cema Abba d'anka ya dawo yau

Abba yace a Barka da fatan ya dawo lafiya

Dad yace lafiya

Abba yace gamu a asibiti Mama bata da lafiya

Nan Dad yace Subhanallah maiya sameta??

Abba yace gamu nan dai har yanzu Dr bai fito ba

Nan Dad yace bari yanzu mu kamo hanya

Abba yace kai yamma yayi fah

Dad yace ya zamuyi dole mu tawo

Nan Bayan sun kashe wayan Dad ya kalli Mum yace mama bata

Please Login or Register in order to submit comment