Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
/>
turowa.
“Aki

waɗannan

fa?

Ko

tsofi ne?”
Ta

tambaya

da

ɗan
ƙarfi,
dan ta

ji

ya

kunna

ruwa,

alamun

wanka

zai

yi.
“Satin

da

ya

wuce

aka

aiko

da

su!”
Shi

ma

ya

bata

amsa

daga

cikin

bayin, Gulzar

ta

buɗe

ɗaya

daga

ciki,

sannan ta

fara

karantawa a

bayya

ne.
“Zuwa

ga

kyakkyawan

tauraron

wasan

fencing da

babu

kamarsa

a

MK

fencing

acadamy.

Haƙiƙa

ka

iya

sarrafa

takobi

cikin ƙwarewa, kana

bawa

takobi

umarni

cikin

iko

da burgewa,

ka

haɗu

sosai

Arman!...”
Gulzar

ta

zaro

ido

tana
rufe

bakinta.
“Aki

ai

wanna

'yar

makarantarku

ce”
Tana

jiyowa

dariyarsa

a

cikin

bayin,

kafin

taji

ya
bata

amsa

da.
“Ba

ɗaliba

ba

ce,

malama

ce!”
Ita

ma

Gulzar

ɗin

kwashewa

ta

yi

da

dariya,

sannan ta

aje

wadda

ke

hannunta

ta

ɗauko

wata

ta

shiga

karantawa,

har

Armaan

ya

fito

daga

bathroom ɗin

sanye

cikin

blue

polo

shirt

da

baƙin

cargo

trouser.

Ya

tsaya

a

jikin

dressing

mirror

yana

busar

da

sumarsa

da

ya

jiƙa

yayin

wankan

da

ya

yi.
“Ke

dan

Allah

ki

aje

wannan

wasiƙun

da

ba

ƙarewa

suke

ba”
Gulzar

ta

kalle

shi

ta

cikin

madubin

da

yake

tsaye

a

gabansa, sannan

ta

aje

wasiƙun

agefe,

ta

saka

hannunta a

cikin

jakar,

ta

fito

da

tikitin Coca-cola

Arena

da

suka

siya

ɗazu.

Ta

karanta

tikitin,

sannan ta

kalli

Arman

tana

faɗin.
“Wai

yau Chris Brown ya

yi

live

performance

kuma

ka

je

amma ba

ka

faɗa

min

ba?”
Ta

tambaya
tana sauƙa

daga

kan

gadonsa,
Arman

ya

aje

dryer dake

hannunsa,

sannan

ya

juyo

ya

kalleta.
“To

ai

abin

ne

ya

zo

a

ƙurace!”
Gulzar

ta

iyo
kansa da

gudu

tana

faɗin.
“Ai

ka

iya

ɗaukan

abokanka

zuwa

wurin!

Ni

kuma

ka

barni

a

nan”
Shi
ma
gudun

ya

saka

ya

fice

daga

ɗakin,
tana biye

da

shi

har

zuwa

saman

gidan,

dake

ɗauke

da

sitting areas,

daku ma

runfunan

shaƙatawa.

Masu

aikin

gidan

kuma
ma

aikin

tsaftace

wurin,
Arman

ya

zauna

a

kan

kujera

yana

kallonta.
“Ki

yi

hakuri

mana

me

gashi”
Gulzar

da

take

a

fusace,

ta

sa

hannu

ta

mayar

da

gashinta

da ya

suƙo

mata kan

fuska

zuwa

baya

tana

huci, sannan

ta

zauna

kusa

da

shi

tana

ture

shi.
“Ni

dai
ka cuceni”
Ta

faɗa

tana

sake

ture

shi, hakan

ya

sa

glasses

ɗin

dake

idonsa

ya

faɗi

ƙasa,

duhu

ya

mamaye

sashin

ganinsa,

dan

daga

zarar

ya

rabu

da

glasses

ɗin

babu

abin

da

yake

gani

face

duhu.

Cak

ya

tsaya

yana

motsa

idonsa

da

babu

abin

da

yake

gani

da

shi,

hannunsa

ya

miƙa

kan

inda

yake zaune,

yana

laluben

glasses

ɗin

nasa,

dan

ko

tafin

hannunsa

ba

ya iya

gani, ita
ma Gulzar

ɗin

sai

a

lokacin

ta

lura

da

shi.
“Ya

Ilahi

ana

asfe

aki”

(Wayyo

Allahana

ka

yi

haƙuri

Yayana)
Ta

faɗa

tana

ɗaukan

glasses

ɗin

nasa

da

ya

faɗi

ƙasa,

ta

goge

shi

a

jikin

rigarta,

sannan ta

saka

masa

shi.

Glasses

ɗin

na

hawa

kan

fuskarsa

ya
fara gani,

sai

ya

raintse

idonsa,

sannan ya

buɗe.
“Mein

bahut

off-sori

hoon

bhradaar,

mein

iss

ka

matlab

nahin

tha...”
(Ka

yi

haƙuri

Yayana,

ba

da

niyya

na

maka

hakan

ba)
Ta

faɗi

cikin

harshen

Urdu

tana

dafa

kafaɗunsa,

sai

ya

riƙe

hannunta yana

girgiza

mata

kai.
“Ma

fi

shi, insi

halla

(Ba

komai

fa, ki

manta

kawai)”
Gulzar

ta

jinjina

kanta,

sannan ta

miƙa

hannu

ta

ɗauki
Hummus
daga

cikin

kayan

maƙulashen

dake

kan

teburin

kusa

da

su,

ta

miƙa

masa.
“Za

ka

ci?”
Ya

ɗan

yi

murmushi

yana

gyara

zaman

glasses

ɗinsa,

sannan

ya

karɓa

daga

hannunta, ita
ma

ta

ɗauki

wani

bowl

ɗin

suka

fara

ci

tare.
“Yau

mun

haɗu

da

Faisal

a

Coca-cola

Arena”
Arman

ya

faɗa

yana

kallonta, ita
ma sai

ta

kalle

shi

tana

gyara

zama.
“Ya

faɗa

maka

wani

abin

ko?...

Kuma

me ka

masa?”
Ta

jero

masa

tambayoyin, sai

ya
yi dariya

yana

shafa

sumarsa

dake

cikin

askin

curly

top,

dan

har

sauƙowa

take

kan

goshinsa.
“Ban

masa

komai

ba,

kuma

ban

ce
masa komai

ba,

Ivana

ma

da

ta

yi

ƙoƙarin

ce
masa wani

abin

hanata

na

yi”
Gulzar

ta

harare

shi.
“Shi

ya sa

gaba

ɗaya

ya

bi
ya rainaka,

ba

finka

ya

yi

a

haife

ba

amma

kullum

gainka

yake

kamar

ƙaninsa.

Ni

ba

za

ka

burgeni ba

sai

ka

yarda

ka karɓi

shugabancin
Alhadi.

Ba

ma

ni

kaɗai

ba

daga

lokacin

za

ka

bawa

kowa

na

ahalin

nan

mamaki”
Arman

ya

ɗaga

kansa

sama

yana

kallon

taurarin

dake

ko

ina

a

sararin

samaniya.
“Shugabancin

babban

kamfani

kamar
Alhadi Group of Companies ya

fi

ƙarfin

makaho

kamar

Arman,

bara

a

gefen

hanya

ita

ce

tafi

dacewa

da

shi!”
Gul
ta

ja

tsaki

tana

aje

bowl

ɗin

hannunta.
“Wannan ra'yin wasu mutane ne da ban, kuma idan har ka ci gaba da faɗin haka kana

nufin shugabancin ya

fi

dacewa

da

shashashan
mutum

kamar

Faisal?”
Armaan

ya

kalleta

yana

ɗage

kafaɗunsa.
“Ban

sani

ba!”
Gulzar ta
ɗauke

ka
tana

juya

idonta, kuma

idon

nata

bai

sauƙa

a

ko

ina

ba

sai

a

kan

saman

gidan

su

Faisal

dake ɗan

gaba

da

nasu.

Daga

nan

inda

suke

tana

iya

hango

Faisal

da

ƙanwarsa Sakina

zaune

a

saman

nasu

gidan,

masu

aikin

gidan

zaune

a

wurinsu

suna

musu

hidima.
“Kalli

can”
Arman

ya

kalli inda

take

kallo.
“Yanda

Sakina

take

ji

da

kanta

kai
kace ita

matar

sarkin

Dubai

ce.

Ko

a

makaranta

ba

ta

da

ƙawaye

sai

'ya'yan

masu

kuɗi.

Kullum

jin

kanta

take

kamar

wata

sarauniya,

tana

kashe

kuɗi

ta

yi

yanda

ranta

yake

so.

Shi

kuma

Faisal,
lalataccen

ɗan
da
babu

uban
da

zai yi

alfahari
da

shi,

a

ƙalla

'yan

matansa

sun

kai

sha

bakwai,

babu

hotel

ɗin

da bai
taɓa

zuwa

ba

a

Dubhai,

har

ɗaki

yake da

shi

a

Burj Khalifa,

yanda yake

wadaƙa

da

kuɗi

za

ka

ɗauka

cewa

babansa
ne

a

kan
kujerar

shugabancin Majmu'at Shirkat Alhadi, daga

an
taɓasu

za

su

ce

su

ne

Faisak (FAISAL AND SAKINA)!

Humm!

Abin

haushi”

Ta

ƙarashe

tana

mayar

da

gashinta

dake

kan

kafaɗunta

zuwa

bayanta,
Arman

ya

yi

dariya.
“Komai

lokaci

ne

Gul, ki

ƙara

haƙuri”
Ta

masa

wani

irin

kallo,

sannan

ta

ɗauke

kai.
“Lokacin

ba

zai
ƙare

ba

har
sai
ka karɓi

shugabancin Alhadi.”
“Wannan

lokacin

ba

zai

taɓa

zuwa

ba”
Arman

ya

bata

amsa

zuciyarsa

ɗaya.

Da

Gulzar

ta

ga

takaicin

ɗan

uwan

nata

na

neman

kasheta

sai
ta

miƙe

ta

bar

shi

a

wurin.
“Gobe

laraba,

ka

shirya

zan

rakaka

wurin Doctor

Ƙuraishi”
Ta

faɗa

tana

barin

wurin,

Armaan

ya

yi

dariya,
Dr
Kuraishi

shi

ne

likitan

idon

da

yake

duba

shi

tun

yana

ƙarami.
*House

No.

34,

Street

12,

Al

Mankhool,

Bur,

Abu

Dabhi,

Dubai.*
ADAM POV.
A razane ya kalli tvn da Maama ta ƙure Volume ɗinta, razannaniyyar ƙarar da ta fito daga cikin tvn ce take naiman sawa ya saki fitsari yana zane.
“Maama dan Allah ki rage Volume ɗin nan”
Ya faɗa yana marairaicewa, kuma cikin harshen hausa, dan a gida sam ba ya larabci ko wani yaren da ba hausa ba, sai idan ya shiga cikin abokansa ne yake magana da wani harshen, tun da su larabawa ne, saɓanin shi da ya kasance ɗan bahaushe.
Maama ta yi tsaki, sannan ta kashe kayan kallon gaba ɗaya, ta dawo ta zauna kusa da shi kan sofa, inda yake zaune a tsorace yana cin abinci, Maama ta dungure kansa tana faɗin.
“Kai dai ka ji jiki. Na rasa a ina ka kwaso wannan shegen tsoron, kai ba mace ba, amma tsoro kamar farar kura, na rasa yaushe za ka daina wannan tsoron, ni dai ina jiye maka ranar da tsoron nan naka zai kasheka kana tsaye.”
Ya ƙifƙifta idonsa yana haɗiyar abincin dake bakinsa.
“Ya kamata gobe ka je wurin aiki, tun da yau ba ka je ba”
Ya jinjina kansa, dan har yanzu a dame yake.
“Akwai sauran wani aiki da shugabanmu ya bani. Ina so na ƙarasa kafin gobe”
Maama ta ɗauki wayarta, sannan ta miƙe tana faɗin.
“Ya kamata dai, kuma saura ka sake kallon wani film ɗin ban tsoron, wallahi ko ta kanka ba zan bi ba”
Sai ya ɗan yi murmushi yana kallonta, har ta bar shi nan zane a falon, a ƙalla yanzu kimanin shekaru biyar ke nan da rasuwar mahaifinsa. Kuma tun bayan lokacin ya rage daga shi sai Maama ne kaɗai suke rayuwa a gidansu. Mahaifinsa yana aiki a wata asibiti dake nan Dubai, kuma aikin shi ne abin da ya rabo shi da mahaifarsa wato Zamfara Nigeria. Dan shi kansa Adam ɗin ma a nan Dubai aka haife shi, kuma har bayan rasuwar Mahaifinsa ba su koma Nigeria ba, saboda shi ma yana aiki a nan.
Salma Ahmad Isah ✍️
_Har yanzu somin taɓi ne, domin muna duba da rayuwar jaruman namu ne, kafin mu tsunduma cikin labarin... Ku fai kada ku gajiya, ku biyoni domin jin yanda za ta kaya..._
°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°
. 🪄
...JUYIN

KWAƊO...
🪄
©️Salma Ahmad Isah
SalmaAhmadIsah

@ArewaBooks
SalmaAhmadIsah

@Wattpad
Page-3
*Moorfields Eye Hospital, 20 street Al Razi Building 64, Block E, floor 3, Dubai.*
ARMAN POV.
“Buɗe idon a hankali”
Dr Ƙuraishi ya bawa Arman umarnin yayin da ya gama duba masa idonsa. Arman ya buɗe idonsa a cikin hasken da Dr Ƙuraishi yake haska idonsa. Amma babu abin da yake gani face duhun da ya saba gani, saboda shi bai san banbancin da yake tsakanin idonsa na a rufe ko a buɗe ba, tun da duka biyun abu ɗaya yake gani.
“Kana iya ganin wannan hasken?”
Dr Ƙuraishi ya tambaya.
“Ba na ganin komai Dr babu komai sai duhu”
Dr Ƙuraishi ya kashe fitilar da ya haska idon nasa, sannan ya ɗauki glasses ɗinsa dake aje a gefe, ya mayar masa shi idonsa yana faɗin.
“Za ka iya sauƙowa”
Arman ya gyara zaman glashin, sannan ya sauƙe ƙafafunsa ƙasa, ya ɗauki canvas ɗinsa dake aje a ƙasa, ya saka a ƙafarsa, sannan ya dawo cikin main office ɗin Dr Ƙuraishi, inda Gulazar ke zaune tana jiransu.
“Babu wani ci gaba!”
Dr Ƙuraishi ya faɗa yana miƙawa Gulzar takardun lafiyar idon Arman ɗin. Gulzar ta karɓa, sannan ta kalli ɗan uwanta da shi ma yake kallonta.
“Za mu iya tafiya?”
Ya tambaya yana murmushi, shi sam bai ga wani abin shiga damuwa ba, dan ya san sam babu ci gaba a lafiyar idon nasa, ba dan Gulzar ɗin ta takura masa ba ma da ba zai zo ba, dan tun daren jiya ta yi booking appointment. Gulzar da gaba ɗaya take a dame ta miƙe, sannan ta ɗauki bag ɗinta ta rataya a kafaɗarta, ta bi bayansa suka bar office ɗin.
Suna tafiya a hanya ya dafa kafaɗarta yana bata haƙuri, kamar ita ce marar lafiyar ba shi ba. Har suka shiga mota suka nufi hanyar gida Gulzar ba ta sauƙo ba. Sai da suka kusa kaiwa unguwarsu kiran PAn Abby ya shigo wayar Gulzar.
“Alo Falak ya kike?”
Ta faɗa bayan ta ɗaga kiran, daga ɗayan ɓangaren Falak ta amsa, sannan ta faɗi dalilin kiran nata.
“Agha (Honorable person) Iƙlab ne yake son ganinki yanzu a kamfani”
Ta tattare girarta tana ɗagawa Arman hannu alamun ya dakata, ya dakatar da motar yana kallonta.
“Lafiya yake naimana?”
“Eh yace yana son ganinki ne”
“Ɗayib jaye! (Okay gani nan zuwa)”
Ta sauƙe wayar tana kallon Arman.
“Abby yana son ganina a kamfani, dan Allah ka kaini can”
Ba tare da yace komai ba ya jinjina kansa yana gyara zaman glashin dake idonsa, sannan ya ja mota ya juya akalar tuƙin nasa zuwa Alhadi Group of Companies. Duk kuwa da ya jima rabon da ya je kamfanin, amma tun da ta buƙata ba zai ƙi kaita ba.
*Majmu'at Shirkat Alhadi, Al Saaha street, Lobby C, Downtown Burj Khalifa, Abu Dhabi, Dubai.*
“Jininka ya hau da yawa Sayid Iƙbal (Mr Iƙbal). Ya kamata ka riƙa sauƙaƙawa kanka”
Faɗin likitan Sayid Iƙbal, yayin da yake tattare blood pressure monitor ɗin da ta yi amfani da shi wurin duba hawan jinin nasa, saboda haka kawai ɗazu ya yanke jiki ya faɗi ba gaira ba dalili. Zaune yake a kan wata boudoir chair, yayin da suit ɗin da ya cire daga jikinsa ke rataye a jikin chair ɗin. Ya lumshe idonsa yana shafa damtsen hannunsa da aka cire abin blood pressure monitor ɗin a jiki. PAnsa na tsaye a gefe, haka ma babban abokinsa Sayid Nusayr (Mr Nusayr), duka sauna cikin karafaren office ɗinsa dake ma'aikatar ne.
“Ni zan wuce”
Cewar Dr, yayin da ya gama haɗa kayan gwajinsa, sai a lokacin Sayid Iƙbal ya buɗe idonsa, sannan da ido ya yi wa Falak alama da ta raka Dr, ta jinjina kanta tana nunawa Dr hanya.
“Mu je na rakaka Dr”
Daga haka suka fice daga office ɗin. Suna fita Sayid Nusayr ya zauna kusa da Abby yana masa sannu.
“Bai

Chapter 4 of 13