da fatan wayar gari lafiya.
MAMLAKATUL JIYAD.
Cike da ƙasaita, izza da isa wani basaraken matashi ke tafiya, kamar wanda ba ya son taka ƙasa, hannayensa goye a baya, yayin da masu gadinsa ke take masa baya. Wasu irin kayan sarakunan da ne a jikinsa, wanda kai daga ganinsu ka san sun amsa sunansu kayan alfarma.
Sai da suka kai ƙarshen dogon falon dake ƙarshen sashen sarki, sannan ya dakata, hakan ya sa su ma dakarun dake take masa baya suka dakata, cike da izza ya daga hannayensa, ba sa jira ko buƙatar ya furta musu abin da yake buƙata, cikin hanzari mutum biyu dake cikinsu, suka ƙara matsawa kusa da shi, sannan suka kama rigar sarautar dake saman kayan nasa da za'a iya kira da alkyabba.
Suka sauƙeta daga kan kafaɗunsa, sannan suka ja da baya a tare suna riƙe da rigar tasa, sai da suka ja da baya, sannan mutum biyun dake jikin wata ƙofa da aka ƙera da zallar baƙin ƙarfe suka buɗeta, hakan ya bayyanar da doguwar matakalar da ta yi ƙasa zuwa harabar fadar. Kuma daga ƙarshen matattakalar akwai wani keken doki da matuƙinsa, wanda ke jiran fitowar sarki.
Cikin wannan takun nasa na izza ya soma tafiya, har ya kai ƙarshen matattakalar, matuƙin keken dokin ne ya sauƙa daga wurin da aka tanada dominsa, ya buɗe gidan baya na keken, inda aka tanada domin zaman mai martaba, sai da ya shiga ciki ya zauna, sannan matuƙin ya rufe ƙofar keken dokin.
Kana ya koma wurin zamansa, ya fara sarrafa dokuna biyun dake jan keken, suka bar ginin fadar, suka hau wata hanya ɗoɗar, wadda za ta sadasu da hanyar barin gari, da yake kowa ya san keken dokin sarki masu yasa gadi ba su yi ƙoƙarin dakatar da su ba, suka yi saurin wangale maƙareriyar ƙofar ganuwar masarautar.
Ko da suka bar fadar dajin dake kusa da masarautar suka kutsa, dokunan na gudu a cikin dajin, yayin da Sarki Cangaz dake keken dokin ya matsu da su kai ga ƙarasawa fadar bokansa. Domin a daren jiya ya samu saƙo daga wurin bokan nasa, kan yana son ganinsa a safiyar yau, hakan ya sa ya yi sammakon tashi.
A lokacin da ya ji dokunan tare da keken sun tsaya cak, matsuwa tare da zaƙuwarsa na son ganin bokan ta ninku, ta yanda bai jira matuƙin ya buɗe masa ƙofar ba, da kansa ya buɗe ya fita, duk wata izza da isa da yake nunawa a masarauta a cikin dajin bai yi ta ba. Hasalima sauri ya yi ya faɗa wani gida dake jikin bishiya a cikin ƙungurmin dajin.
Yana buɗe ƙofar ya kutsa kai cikin gidan, babban boka Jalis dake durƙushe a gaban wani maƙareren allo ya ɗaga kai ya kalli Cangaz kammaninsa suke a na matashi, domin akwai wani sabon tsafi da boka Jalis ɗin ya haɗa masa a kwana nan, wanda yake sawa kamanin matashin kan yi tsawon kwanaki a jikinsa har na kimanin mako biyu, durƙushewa ya yi a gaban bokan, yayin da Boka Jalis ke ƙare masa kallo, fuskarsa ɗauke da murmushi.
“Ka yi kira na amsa Jalis, da fatan da wani labari me daɗi ka zo min”
Muryarsa me ɗauke da izza da ƙasaita ta furta suna duban juna shi da Boka Jalis.
“Ƙwarai kuwa shugaban talakawa. Mafarkin da ka daɗe kana yi na tsawon kwanaki ne ya zama gaskiya...”
“Ka yi saurin sanar da ni abin da yake faruwa”
Ya yi saurin katse shi, dan sam ba ya son wani tambihi, boka Jalis ya girgiza kai yana murmushi, sannan a hankali ya juyawa Malik Cangaz fuskar allon dake aje a gabansa, Malik Cangaz ya kalli allon dake ɗauke da hoton wasu matasa uku, waɗan da sam kammaninsu da kuma shigarsu ba ta yi kama da ta mutanen duniyarsu ba, cike da kokwanto ya kalli boka.
“Baƙi aka yi daga wata duniyar?”
Boka Jalis ya girgiza kai.
“Ba za mu iya kiransu da baƙi daga wata duniyar ba kai tsaye, amma za mu iya kiransu da baƙin sa'a, masu tafe da cikar mafarkinka... Kalli ka ga”
Ya ƙarashe yana nunawa Malik sarƙar wuyan Arman.
“Wannan shi ne makullin ƙofar da muke ta naiman mabuɗinta... Wannan makullin shi ne ƙarshen abin da zai sa ka ci gaba da zama a matashi har duniya ta naɗe”
Lokaci guda Malik Cangaz ya saki wani ƙassaitaccen murmushi, suka haɗa ido da Boka Jalis.
“Shin a ina waɗannan matasan suke? Domin ba na so na ƙara ko da sa'a guda ba tare da na buɗe ƙofar nan ba”
“Ai ba'a nan gizo yake saƙar ba Shugabana, waɗannan matasan uku da kake gani, sam ba mutanen wannan zamanin namu ba ne, ƙaddara ce ta yi JUYIN KWAƊO da rayuwarsu zuwa wannan zamanin namu. Kuma a halin da ake ciki su ma suna fafutukar yanda za'a yi su koma zamaninsu. Sannan an sanar da su cewa wannan ƙofar taka ita ce ƙofar da za ta mayar da su zamaninsu, dan haka su ma kansu suna tunkararka ne, ba kai ne kaɗai kake naimansu ba...”
Malik Cangaz ya miƙe tsaye, ya yi taku uku tare da juyawa boka Jalis baya.
“Ai ko ba za su taɓa komawa zamaninsu ba, domin ba zan taɓa bari su kai ga ganin ƙofar nan ba, ballantana har ta kai ga sun samu damar shiga cikinta... Zan sa a naimo min su duk inda suke a duniyar nan, domin a karɓo min makullin da suke tare da shi, saboda na buɗe ƙofar nan na cika burina!...”
Ya ƙarashe yana bushewa da dariya, shi dai Boka Jalis bakinsa ya ja ya yi shiru, dan ba zai sake cewa komai ba, shi ya san abin da ya gani kawai, domin Malik Cangaz farkon yaƙin ya sani kawai, bai san ya ƙarshen yaƙin zai kasance ba, kuma shi ɗin ma da ya sani ba zai faɗa masa ba domin tsira da rayuwarsa...
Malik Cangaz ya juyo tare da duban Boka Jalis.
“Haƙiƙa yau ka sanar da ni labarin da ya fi ko wanne daɗi a duniyar nan, dan haka dole na maka gagarumar kyauta, sannan ina gayyatarka zuwa wurin ganawa da yariman masarautar Azad, wanda zai zo tare da mahaifinsa a kan maganar auren Gimbiya Iqrah, da fatan za ka zo?”
Boka ya jinjina kai yana murmushin ɓoye sirrin zuciyarsa.
“Ƙwarai kuwa shugabana, zan kasance a wurin a lokacin da ake buƙata!”
DANEEN IQRAH.
Yalwataccen hasken rana da ya fara ratsowa cikin masarautar ne ya samu damar shiga ɗakinta ta hanyar ƙatuwar tagar dake saman ɗakin. Hasken ranar ya samu nasarar sauƙa a kan wata kyakkyawar hallita dake kwance a kan katafaren gadon dake tsakiyar ɗakin.
Kyakkyawan dogon gashin idonta na sama ne ya ɗaga zuwa sama, farin idonta dake ɗauke da ƙwaya kalar (brown) ya bayyana, sake rufe idon nata ta yi, sannan ta sake buɗe shi a karo na biyu, ta saka dogayen fararen yatsun hannunta, ta murza idonta, sannan a hankali ta saka hannunta ta yaye mayafin da ta lulluɓa da shi, ta tashi zaune, yayin da gashin kanta me tsayi ya lulluɓe kafaɗunta da kuma gadon bayanta.
Lokacin da ta yi miƙa tare da hamma kuyangu da bayin da suka saba mata hidima a kullum rana suka fara shigowa ɗakin ɗaya bayan ɗaya, kowanne ya shigo ɗakin sai ya miƙa mata gaisuwa, sannan zai fara aikinsa na kullum. Yayin da ita kuma ta nufi bayin dake cikin ɗakin, wasu kuyangu biyu suka rakata zuwa bayin, domin tayata tsaftace jikinta.
Lokacin da suka dawo ɗakin har an gama tsaftace ko mai da ko ina, a kan wata kujera ta zauna, kuyangun da aikinsu shi ne shirya gimbiya suka kewayeta, kowa da aikin da yake, wasu na gyara mata gashi, wasu na aikin gyara mata fata, yayin da wasu na taimakawa wurin saka mata tufafi.
Sai da suka ƙawata sarauniyar da ado irin wanda ya dace da duk wata 'yar sarki me jin isa da iko a wannan zamanin, sannan suka koma gefe, masu aikin kawowa sarauniya shayinta na safe suka matso, aka bata shayin ta sha, sannan ta tashi domin zuwa ɗakin karin kummalo da kowa ya saba halarta domin cin abinci. Sai da ta yi taku uku, sai kuma ta dakata, hakan ya sa su ma bayin da suka shirya domin take mata baya suka dakata. Cikin iko isa da izza ta kalle su da gefen ido.
“Ku bani wuri, akwai abin da zan gabatar cikin sirri”
Ta furta cikin muryarta me sanyi da zaƙin sauraro. Dukan ma'aikatan nata suka risina mata, alamun sun amsa saƙon nata, sannan suka soma barin ɗakin ɗaya bayan ɗaya. Sai da suka fita daga ɗakin gaba ɗayansu, ya rage sai amintacciyar hadimarta kaɗai a ɗakin, ta kalli hadimar da kanta yake a ƙasa.
“EID ya aiko da wani saƙo?”
Hadimar ta jinjina kanta dake ƙasa.
“Ƙwarai gimbiyar kyawawa...”
Daga haka ta nufi tagar ɗakin dake a bangon gabas, ta saka hannayenta ta buɗe ƙofar, hakan ya bawa mujiyar (owl) dake waje damar shigowa ciki, ta shiga kaɗa fuka-fukanta har ta isa kafaɗar gimbiya. Wani kyakkyawan murmushi ta yi tana kallon mujiyar, sannan ta saka hannunta ta ciro takardar dake riƙe a cikin ƙafafun mujiyar. Ta buɗe takardar ta soma karanta wasiƙar soyayyar da masoyinta SA'EID ya aiko kamar kullum.
Kan wata kujera ta koma ta zauna tana murmushi kamar wadda ta samu taɓin hankali, haka kalaman soyayyarsa ke ratsa mata zuciya, sai da ta gama karanta wasiƙar, sannan ta ɗauki wata takardar da alƙalami, ta rubuta nata kalaman, sannan ta saka a cikin ƙafar mujiyar, ta buɗe mata ƙofa ta turata zuwa waje ta tagar tana murmushi.
“Ina da wata magana idan har ba za ta ɓata miki rai ba ya shugabata!”
Gimbiya Iqra ta dubeta hadimarta Champa, murmushin dake kan fuskarta na samun kalaman masoyinta SA'EID ALI bai gushe ba ta furta.
“Ina jinki Champa”
“Ɗazu jakadan fada yake sanar da ni wani batu da nake da tabbacin ba ki san da shi ba...”
Murmushin fuskarta na shirin ɓacewa ta furta.
“Wani batu ne wannan?”
“A yau yarima Wajid ɗan sarkin Mamlakatul Azad zai zo tare da mahaifinsa a kan batun naiman aurenki?...”
Ɓat murmushin kan fuskarta ya ɓace a iska, wani abu me kama da ƙwai ya faɗo ya fashe a ƙirjinta. Sannan ta saki baki da hanci tana kallon Champa. Duk bayan tsawon lokacin da suka shafe suna soyayya da Eid masoyinta a rasa a gaɓar da za'a rabasu sai yanzu da soyayyarsu ta ɗauko daɗi?... Zuwan wani da ban fadar a kan maganar aurenta ba Eid ba na nufin za'a aura mata waninsa.
Kuma sam ita ba za ta lamunci hakan ba, ko da za ta gudu daga fadar ne za ta yi, domin tseratar da soyayyarta. Ta san ko da ta gabatar da Eid a gaban Malik Cangaz a matsayin mijin da take so ya aura mata ba zai amince ba, domin Eid ba shi da mulki, sannan ba shi da kuɗi ko wata dukiya da za ta siya masa mutunci a idon mahaifinta ballantana ta kai ga ya aura mata shi.
Salma
Ahmad
Isah
✍️
A zo a fara biyan kuɗin book, saboda book one ya ɗauko hanyar ƙarewa. If you wanna be part of the journey, pay ₦400 for nomarl group, and ₦800 for VIP group.
5487270431
Salma Isah
Monie point
Sai a tura shaidar biya ta 08130172702.
°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°
.
🪄
...JUYIN
KWAƊO...🪄
©️Salma
Ahmad
Isah
SalmaAhmadIsah
@ArewaBooks
SalmaAhmadIsah
@Wattpad
Page-10
ARMAN.
A rana ta gaba ma haka suka ci gaba da tafiya a cikin dajin, kasancewar suna duba taswirar da tsoho ya basu yasa ba su ɓata hanya ba ko sau ɗaya. Har rana ta biyu a tafiyar tasu ta ƙare babu wata matsala da ta samesu, ko wani baƙon abu da ya ziyarce su, sai a rana ta uku, ranar da suke hasashen iske ƙauyen Askar wani baƙon lamari ya riskesu a hanya.
Tun cikin daren ranar ake iska me ƙarfi, wadda take tafe da ƙura da kuma sanyi me shiga jiki, kuma tun a safiyar ranar iska ta ɗauke tentunan da suka kafa, lokacin da suka tafi naiman ruwan wanke jikunansu, sanda suka dawo suka iske babu tentin iska ta ɗauke.
Sa'arsu ɗaya, jakukkunansu ba su cikin tent ɗin lokacin da iska ta yi gaba da su, cike da salallamin rashin tent ɗin suka haɗa kayansu suka ci gaba da tafiya, dan yanzu abin ma ya fara zame musu jiki, har sun fara sabawa da yanayin tafiyar.
Suna tsaka da tafiya a tsakanin wasu bishiyoyi suka fara jin kuwwar wasu mutane, Adam ne ya fara jiyo kuwwar, hakan yasa ya ankarar da sauran, sai suka tsaya suna duba kewayen da suke, wai ko za su ga ta inda masu kuwwar za su ɓullo. Amma har bayan shuɗewar daƙiƙu biyu babu alamar komai. Sai da suka sakankance sannan suka ji faɗowar abu daga sama tim!.
Hakan ya sa suka ƙara razana, Arman ya turasu bayansa domin basu kariya, yayin da yake kallon ta inda abin ya faɗo, girman idonsa ya rage yana kallon mutumin dake tsaye a gabansu, alamun dai shi ne ya faɗo daga saman. Tun daga kan kwarjallen dake ƙugunsa zuwa rigar dake sanye a jikinsa duka na fata ne, kuma fuskarsa a rufe take, shi yasa ba su iya banbance kamarsa.
Kafin su yi wani yunƙuri wasu mutum uku dake sanye da kaya irin nasa suka sake dirowa daga saman bishiya, Arman ya sake kare Ivana da Adam da suke a matuƙar tsorace, shi ma kansa a tsorace yake, amma dole ya ɓoye tsoronsa domin kare abokansa.
Kallon-kallo aka tsaya yi, su suna karantar kama da kuma nau'in tufafin dake jikin mutanen huɗu, yayin da su ma suke kallonsu, dan za su iya cewa tun da suke fashi a hanyar, tsawon shekaru tara, ba su taɓa ganin mutane masu kama da waɗannan ba, bawai dan sun banbanta da mutane ba ne, a'a su ma kamar mutane suke, amma kalar tufafin jikinsu shi ne abin mamaki... Sai dai mamakin son sanin su wasu nau'in mutane ne ba shi zai hana su ƙwace duk wani abu da suke tafe da shi ba, dan haka wanda ya kasance shugansu ya miƙa musu hannunsa, cikin larabcinsa me kyau yace.
“Ku bamu kayanku!”
“Kaya?”
Adam ya maimata.
“Ku bamu kaya ko kuɗi, idan ba haka ba ku yi ta ranku!”
Dariya ta so kama Adam, dan shi ne ya fara fahimtar wasu irin mutane ne. Camera ɗinsa ya fitar ya shiga ɗaukansu a hoto. Yayin da su kuma suka shiga kare fuskokinsu saboda hasken flasher da Adam ke haskasu da ita.
“Adam me suke buƙata ne?”
Ivana ta tambaya tana kallonsa lokacin da ya gama ɗaukansu a hoto yana dariya.
“Wai 'yan fashi ne”
Ita kanta sai da abin ya so bata dariya. Ganin suna dariya ya harzuƙa 'yan fashin, ai rainin hankali ne ma, ya za'ayi su tambayesu kudi ko kayan kuɗi su zauna suna musu dariya. Hakan yasa suka fitar da makamansu masu firgita bil adama, suka yi kansu da shi. Amma Arman bai bari sun kai ga cutar da su ba, dan cikin azama shi ma ya fitar da nasa takobin ya nunasu da shi.
“Kada ku sake ko da taku ɗaya zuwa garemu, duk wanda ya sake kuma zan raba kansa da gangar jikinsa”
Ya faɗi a dake yana dubansu, juna suka kalla, dan ba sosai suka gane abin da yace ba. Ɗaya daga cikinsu ya sake yin wani takun zuwa gaba. Cikin ƙwarewa da iya sarrafa takobi, Arman ya juya takobin a hannunsa, sannan shi ma ya nufe shi, yana zuwa dab da shi ya kare farmakin da ɗan fashin ya kawo masa, sannan ya jujjuya takobin da hannunsa ɗaya, ya kai masa suka a gefen ciki, shi kansa bai ɗauka cewa zai iya samun wurin da ya hara ba. Domin bai taɓa amfani da takobin gaskiya ba, amma sai ga shi ya samu gefen cikin ɗan fashin.
Ya ƙwalla ƙara yana naiman ɗauki a wurin 'yan uwansa, su kuma kallon Arman kawai suka tsaya yi baki sake, dan a fashin da suka kwashi tsawon shekaru sun yi ba su taɓa haɗuwa da wanda ya mayar musu da martani ba sai yau. Arman ya zare takobin da ya sokawa ɗan fashin, sannan ya tura shi wurin 'yan uwansa. Da sauri suka ɗauki ɗan uwansu suka ruga cikin dajin da gudu.
“Hooooo! Abokina wai da ma haka ka iya sarrafa takobi!?”
Cewar Adam baki buɗe, dan bai taɓa ganin Arman ɗin na wasan takobi ba sai yau. Ita kuma Ivana takan je ta ga wasan nasa idan suna yi a Fencing Academy ɗinsu, amma duk da haka abin ya bata mamaki. Shi kansa Arman mamakin abin yake ji, takobin dake ɗigar jini ya ɗaga yana kallo, kafin ya mayar da shi cikin gidansa.
“Ya kamata mu yi saurin barin wurin nan, kafin wasu mugayen mutanen su zo”
Da wannan maganar tasa suka ci gaba da tafiya, kuma ba su yada zango ba har sai da suka fara hango gidan da tsoho yace musu shi za su fara gani kafin su kai ga shiga ƙauyen Askar. Duk da haka Arman bai tabbatar ba sai da ya buɗe taswirar da tsoho ya ba su, sannan ya ga waɗannan hasken ukun suna tsaye a kan ƙauyen Askar da aka masa alama, kansa ya ɗaga ya dubi su Adam.
“Wancan shi ne gidan da tsoho yace za mu fara gani kafin mu shiga ƙauyen Askar...”
Suka sake kallon gidan.
“To mu je mana”
Cewar Adam shi ne kan gaba, su ma bayansa suka bi zuwa gidan da aka gidan da ƙasa. Kasancewarsu 'ya'yan musulmai yasa sai da suka gabatar da sallama, kafin su kutsa kai gidan. Su ukun duka suka jeru a tsakar gidan. Suna kallon kallo da matar dake tsakar gidan.
Farar dattijuwa ce, wadda a ƙiyasin shekaru za ta kai hamsin da ɗori, sanye take da wasu tufafin da aka saƙa da zaren audiga, wanda aka rina shi zuwa kalar shuɗi. Ƙafafunta na cikin takalman fata irin na zamaninsu, hannunta riƙe da wata ƙwarya. Kamar yanda su ma suke kallonta, haka ita ma take kallonsu. Dan sam ba su mata kama da mutanen da ta sani ba.
“Barka! Mu baƙi ne a nan, akwai wani tsoho da ya ba mu wannan yace mu baki”
Cewar Arman yana nuna mata taswirar dake hannunsa. Nan take tsohuwar ta saki fuska, sannan ta musu alama da su shiga cikin ɗakinta.
“Anya za mu iya yarda da wannan tsohuwar me kamar yamusasshen ganye?”
Cewar Adam murya ƙasa yana duban abokansa. Arman ya bugi cikinsa da bayan hannunsa.
“Ka mana shiru, a wannan halin da muke ciki ba mu da ikon zargin kowa, mu dai kawai abin yin mu shi ne kare kai a lokacin da aka kawo mana farmaki”
Cewar Arman.
“Haka ne Adam, tun da har muka yarda da tsohon can ita ma babu dalilin da zai sa mu ƙi yarda da ita”
Cewar Ivana.
“Ku shiga mana”
Tsohuwar ta sake faɗa tana nuna musu ɗakinta da shi ma aka gina shi da ƙasa. Sai da suka gama ƙarewa gidan kallo, sannan suka shiga ɗakin nata da babu komai ciki sai wani gadon katako. Sai wasu jakukkunan fata dake gefe guda. A kan gadon dake ɗakin suka jeru su uku, Adam har da fitar da camera ya fara ɗaukan ɗakin a hoto.
A lokacin kuma matar ta shigo ɗakin, hannunta tiƙe da wani abu me kamar kofi, ta aje musu tana faɗin su sha abin ciki, dai suka girgiza mata kai a tare, alamun ba sa sha. Suna ganin sanda matar ta yi murmushi, sannan ta juya kanta tana kallon ƙofar ɗakin, cikin muryarta ta tsufa ta ƙwala ƙiran.
“UWAIS!”
Cikin abin da ya zarce mamaki Arman, Adam da Ivana suka dubi juna, sannan suka kalli farar dattijuwar, idan dai har ɗan rakiyar da za su tafi da shi ya kasance UWAIS ke nan wannan matar ita ce gimbiya FEROZA, wato mahaifiyar Amir UWAIS BIN DHAAKIR?.
_____•••____
UWAIS.
A hankali daddaɗar iskar dake busawa a dajin take kaɗa ganyayyakin bishiyun da suka ƙawata shi. Yayin da wani daddaɗan busar sarewa ke tashi a cikin dajin, da daɗin da yake naiman zarce na iskar da ake. Daga can kan reshen wata doguwar bishirya yake zaune, ya harɗe ƙafafunsa, yayin da iskar wurin ke ɗaga dogon gashin kansa, idanuwansa kuma a lumshe, domin shi kansa yana jin daɗin busar.
Sanye yake da Sirwal, wani nau'in tufafi irin na wancan zamanin, wanda ake yinsa da zare lilin. Takalman ƙafarsa na fata ne, wanda suke da zaren ɗauri, akwai ɗan siririn rawani a kansa, wanda bai ɓoye dogon gashin kansa ba. Wasu kyawawan tsuntsaye dake kan bishirya da yake zaune ne ke ta kukansu me daɗin saurare, waɗan da suka ƙarawa busar tasa ta yau armashi.
Cak busar sarewar ta tsaya, sannan a hankali ya buɗe kyawawan idanuwansa masu ɗauke da shuɗiyar ƙwaya. Ya motsa kunnensa na ɓarin hagu, domin jiyo abin da yake dajin dake gaban wanda yake ciki. Gurnanin damusa haɗi da kukan barewa ya jiyo lokaci guda.
Hakan tasa ya yi saurin miƙewa a kan reshen bishirya, sannan ya sofare zarewar hannunsa a cikin ma'ajiyarta dake saƙale a ƙugunsa. Tsalle ya daka ya iyo ƙasa, sai dai kafin ya kai ƙasa ya buɗe fukafukansa da ba su bayyana sai idan har shi ya bayyanar da su ya tashi sama. Cikin abin da bai fi ƙiftawar ido ba ya isa dajin dake kusa da wanda ya baro.
A kusa da inda yake jin gurnanin damusar ya sauƙa, kuma yana sauƙa ya sake ɓoye fukafukansa guda biyu, ya tsaya yana kallon wata baƙar damisa da take shirin farmakar wata barewa. A hankali ya miƙe tsaye, sannan ya zaro sarewarsa dake maƙale a ƙugunsa, ya juyata a hannunsa, nan take ta rikiɗa zuwa bakar da aka ƙera da ɗanyar azurfa, sannan a hankali ya riƙeta da hannunsa na hagu, ya ɗagata sama, tare da saitata a kan damisar, yatsun hannunsa na dama ya motsa, wata farar siririyar kibiya ta faɗo hannun nasa, a hankali ya saita kibiyar a jikin bakar, sannan ya sakata cikin yatsun hannunsa biyu.
Ya kanne idonsa tare da karkatar da kansa gefe, sai da ya saita damisar sosai, sannan ya saki kibiyar, babu kuskure ko kauce hanya kai tsaye kibiyar ta soki damisar a gefen cikinta, kukan da damisar ta saka ya sa barewar da take hari da farko ta razana ta falla cikin dajin da gudu.
Murmushi ya yi kawai, sannan ya juya bakar ta rikiɗe zuwa sarewa, ya sake saƙalata a cikin ma'ajiyarta me kama da gidan takobi, sannan ya yi wurin da damisar ta faɗi tana numfashi da ƙyar, tsuggunawa ya yi a kanta, ya kalli wurin da ya harbeta na ta zubar jini.
“Idan aka ce ku koma cin ciyawa ba iyawa za ku yi ba, kuma idan aka ce kada ku cutar da dabbobin da ba su ji ba ba su gani ba ƙi kuke, ya za mu yi da ku ne?”
Ya tambaya yana ɗora hannunsa a kan kibiyar, sannan a hankali ya zareta daga cikinta, ya shafa wurin da ya harbeta, sannan ya miƙe yana kallonta.
“Allah ya baki lafiya”
Yana gama faɗar hakan ya buɗe fukafukansa ya tashi sama. Yana shawagi a iska kiran mahaifiyarsa ya riske shi, hakan yasa bai sauƙa a ko ina ba sai a cikin gidansu.
IQRAH.
Ƙuri ta yi da ido tana bin yariman da aka ce shi ne wanda za'a aura mata da kallo, fuskar nan a haɗe, dan sam babu alamar fara'a a tattare da ita, ta cika ta yi fam, jira take a tsikareta ta fashe tau!. Ba sai an yi wani tone-tone ba, sam ita matashin bai mata ba. Ba wai dan ba shi da kyau ba, ba kuma dan ba shi da nasaba me kyau ba, sai dan kawai Eid shi ne a zuciyarta.
“... Yanzu amincewar Gimbiya kawai muke buƙata, daga zarar tace eh sai a
MAMLAKATUL JIYAD.
Cike da ƙasaita, izza da isa wani basaraken matashi ke tafiya, kamar wanda ba ya son taka ƙasa, hannayensa goye a baya, yayin da masu gadinsa ke take masa baya. Wasu irin kayan sarakunan da ne a jikinsa, wanda kai daga ganinsu ka san sun amsa sunansu kayan alfarma.
Sai da suka kai ƙarshen dogon falon dake ƙarshen sashen sarki, sannan ya dakata, hakan ya sa su ma dakarun dake take masa baya suka dakata, cike da izza ya daga hannayensa, ba sa jira ko buƙatar ya furta musu abin da yake buƙata, cikin hanzari mutum biyu dake cikinsu, suka ƙara matsawa kusa da shi, sannan suka kama rigar sarautar dake saman kayan nasa da za'a iya kira da alkyabba.
Suka sauƙeta daga kan kafaɗunsa, sannan suka ja da baya a tare suna riƙe da rigar tasa, sai da suka ja da baya, sannan mutum biyun dake jikin wata ƙofa da aka ƙera da zallar baƙin ƙarfe suka buɗeta, hakan ya bayyanar da doguwar matakalar da ta yi ƙasa zuwa harabar fadar. Kuma daga ƙarshen matattakalar akwai wani keken doki da matuƙinsa, wanda ke jiran fitowar sarki.
Cikin wannan takun nasa na izza ya soma tafiya, har ya kai ƙarshen matattakalar, matuƙin keken dokin ne ya sauƙa daga wurin da aka tanada dominsa, ya buɗe gidan baya na keken, inda aka tanada domin zaman mai martaba, sai da ya shiga ciki ya zauna, sannan matuƙin ya rufe ƙofar keken dokin.
Kana ya koma wurin zamansa, ya fara sarrafa dokuna biyun dake jan keken, suka bar ginin fadar, suka hau wata hanya ɗoɗar, wadda za ta sadasu da hanyar barin gari, da yake kowa ya san keken dokin sarki masu yasa gadi ba su yi ƙoƙarin dakatar da su ba, suka yi saurin wangale maƙareriyar ƙofar ganuwar masarautar.
Ko da suka bar fadar dajin dake kusa da masarautar suka kutsa, dokunan na gudu a cikin dajin, yayin da Sarki Cangaz dake keken dokin ya matsu da su kai ga ƙarasawa fadar bokansa. Domin a daren jiya ya samu saƙo daga wurin bokan nasa, kan yana son ganinsa a safiyar yau, hakan ya sa ya yi sammakon tashi.
A lokacin da ya ji dokunan tare da keken sun tsaya cak, matsuwa tare da zaƙuwarsa na son ganin bokan ta ninku, ta yanda bai jira matuƙin ya buɗe masa ƙofar ba, da kansa ya buɗe ya fita, duk wata izza da isa da yake nunawa a masarauta a cikin dajin bai yi ta ba. Hasalima sauri ya yi ya faɗa wani gida dake jikin bishiya a cikin ƙungurmin dajin.
Yana buɗe ƙofar ya kutsa kai cikin gidan, babban boka Jalis dake durƙushe a gaban wani maƙareren allo ya ɗaga kai ya kalli Cangaz kammaninsa suke a na matashi, domin akwai wani sabon tsafi da boka Jalis ɗin ya haɗa masa a kwana nan, wanda yake sawa kamanin matashin kan yi tsawon kwanaki a jikinsa har na kimanin mako biyu, durƙushewa ya yi a gaban bokan, yayin da Boka Jalis ke ƙare masa kallo, fuskarsa ɗauke da murmushi.
“Ka yi kira na amsa Jalis, da fatan da wani labari me daɗi ka zo min”
Muryarsa me ɗauke da izza da ƙasaita ta furta suna duban juna shi da Boka Jalis.
“Ƙwarai kuwa shugaban talakawa. Mafarkin da ka daɗe kana yi na tsawon kwanaki ne ya zama gaskiya...”
“Ka yi saurin sanar da ni abin da yake faruwa”
Ya yi saurin katse shi, dan sam ba ya son wani tambihi, boka Jalis ya girgiza kai yana murmushi, sannan a hankali ya juyawa Malik Cangaz fuskar allon dake aje a gabansa, Malik Cangaz ya kalli allon dake ɗauke da hoton wasu matasa uku, waɗan da sam kammaninsu da kuma shigarsu ba ta yi kama da ta mutanen duniyarsu ba, cike da kokwanto ya kalli boka.
“Baƙi aka yi daga wata duniyar?”
Boka Jalis ya girgiza kai.
“Ba za mu iya kiransu da baƙi daga wata duniyar ba kai tsaye, amma za mu iya kiransu da baƙin sa'a, masu tafe da cikar mafarkinka... Kalli ka ga”
Ya ƙarashe yana nunawa Malik sarƙar wuyan Arman.
“Wannan shi ne makullin ƙofar da muke ta naiman mabuɗinta... Wannan makullin shi ne ƙarshen abin da zai sa ka ci gaba da zama a matashi har duniya ta naɗe”
Lokaci guda Malik Cangaz ya saki wani ƙassaitaccen murmushi, suka haɗa ido da Boka Jalis.
“Shin a ina waɗannan matasan suke? Domin ba na so na ƙara ko da sa'a guda ba tare da na buɗe ƙofar nan ba”
“Ai ba'a nan gizo yake saƙar ba Shugabana, waɗannan matasan uku da kake gani, sam ba mutanen wannan zamanin namu ba ne, ƙaddara ce ta yi JUYIN KWAƊO da rayuwarsu zuwa wannan zamanin namu. Kuma a halin da ake ciki su ma suna fafutukar yanda za'a yi su koma zamaninsu. Sannan an sanar da su cewa wannan ƙofar taka ita ce ƙofar da za ta mayar da su zamaninsu, dan haka su ma kansu suna tunkararka ne, ba kai ne kaɗai kake naimansu ba...”
Malik Cangaz ya miƙe tsaye, ya yi taku uku tare da juyawa boka Jalis baya.
“Ai ko ba za su taɓa komawa zamaninsu ba, domin ba zan taɓa bari su kai ga ganin ƙofar nan ba, ballantana har ta kai ga sun samu damar shiga cikinta... Zan sa a naimo min su duk inda suke a duniyar nan, domin a karɓo min makullin da suke tare da shi, saboda na buɗe ƙofar nan na cika burina!...”
Ya ƙarashe yana bushewa da dariya, shi dai Boka Jalis bakinsa ya ja ya yi shiru, dan ba zai sake cewa komai ba, shi ya san abin da ya gani kawai, domin Malik Cangaz farkon yaƙin ya sani kawai, bai san ya ƙarshen yaƙin zai kasance ba, kuma shi ɗin ma da ya sani ba zai faɗa masa ba domin tsira da rayuwarsa...
Malik Cangaz ya juyo tare da duban Boka Jalis.
“Haƙiƙa yau ka sanar da ni labarin da ya fi ko wanne daɗi a duniyar nan, dan haka dole na maka gagarumar kyauta, sannan ina gayyatarka zuwa wurin ganawa da yariman masarautar Azad, wanda zai zo tare da mahaifinsa a kan maganar auren Gimbiya Iqrah, da fatan za ka zo?”
Boka ya jinjina kai yana murmushin ɓoye sirrin zuciyarsa.
“Ƙwarai kuwa shugabana, zan kasance a wurin a lokacin da ake buƙata!”
DANEEN IQRAH.
Yalwataccen hasken rana da ya fara ratsowa cikin masarautar ne ya samu damar shiga ɗakinta ta hanyar ƙatuwar tagar dake saman ɗakin. Hasken ranar ya samu nasarar sauƙa a kan wata kyakkyawar hallita dake kwance a kan katafaren gadon dake tsakiyar ɗakin.
Kyakkyawan dogon gashin idonta na sama ne ya ɗaga zuwa sama, farin idonta dake ɗauke da ƙwaya kalar (brown) ya bayyana, sake rufe idon nata ta yi, sannan ta sake buɗe shi a karo na biyu, ta saka dogayen fararen yatsun hannunta, ta murza idonta, sannan a hankali ta saka hannunta ta yaye mayafin da ta lulluɓa da shi, ta tashi zaune, yayin da gashin kanta me tsayi ya lulluɓe kafaɗunta da kuma gadon bayanta.
Lokacin da ta yi miƙa tare da hamma kuyangu da bayin da suka saba mata hidima a kullum rana suka fara shigowa ɗakin ɗaya bayan ɗaya, kowanne ya shigo ɗakin sai ya miƙa mata gaisuwa, sannan zai fara aikinsa na kullum. Yayin da ita kuma ta nufi bayin dake cikin ɗakin, wasu kuyangu biyu suka rakata zuwa bayin, domin tayata tsaftace jikinta.
Lokacin da suka dawo ɗakin har an gama tsaftace ko mai da ko ina, a kan wata kujera ta zauna, kuyangun da aikinsu shi ne shirya gimbiya suka kewayeta, kowa da aikin da yake, wasu na gyara mata gashi, wasu na aikin gyara mata fata, yayin da wasu na taimakawa wurin saka mata tufafi.
Sai da suka ƙawata sarauniyar da ado irin wanda ya dace da duk wata 'yar sarki me jin isa da iko a wannan zamanin, sannan suka koma gefe, masu aikin kawowa sarauniya shayinta na safe suka matso, aka bata shayin ta sha, sannan ta tashi domin zuwa ɗakin karin kummalo da kowa ya saba halarta domin cin abinci. Sai da ta yi taku uku, sai kuma ta dakata, hakan ya sa su ma bayin da suka shirya domin take mata baya suka dakata. Cikin iko isa da izza ta kalle su da gefen ido.
“Ku bani wuri, akwai abin da zan gabatar cikin sirri”
Ta furta cikin muryarta me sanyi da zaƙin sauraro. Dukan ma'aikatan nata suka risina mata, alamun sun amsa saƙon nata, sannan suka soma barin ɗakin ɗaya bayan ɗaya. Sai da suka fita daga ɗakin gaba ɗayansu, ya rage sai amintacciyar hadimarta kaɗai a ɗakin, ta kalli hadimar da kanta yake a ƙasa.
“EID ya aiko da wani saƙo?”
Hadimar ta jinjina kanta dake ƙasa.
“Ƙwarai gimbiyar kyawawa...”
Daga haka ta nufi tagar ɗakin dake a bangon gabas, ta saka hannayenta ta buɗe ƙofar, hakan ya bawa mujiyar (owl) dake waje damar shigowa ciki, ta shiga kaɗa fuka-fukanta har ta isa kafaɗar gimbiya. Wani kyakkyawan murmushi ta yi tana kallon mujiyar, sannan ta saka hannunta ta ciro takardar dake riƙe a cikin ƙafafun mujiyar. Ta buɗe takardar ta soma karanta wasiƙar soyayyar da masoyinta SA'EID ya aiko kamar kullum.
Kan wata kujera ta koma ta zauna tana murmushi kamar wadda ta samu taɓin hankali, haka kalaman soyayyarsa ke ratsa mata zuciya, sai da ta gama karanta wasiƙar, sannan ta ɗauki wata takardar da alƙalami, ta rubuta nata kalaman, sannan ta saka a cikin ƙafar mujiyar, ta buɗe mata ƙofa ta turata zuwa waje ta tagar tana murmushi.
“Ina da wata magana idan har ba za ta ɓata miki rai ba ya shugabata!”
Gimbiya Iqra ta dubeta hadimarta Champa, murmushin dake kan fuskarta na samun kalaman masoyinta SA'EID ALI bai gushe ba ta furta.
“Ina jinki Champa”
“Ɗazu jakadan fada yake sanar da ni wani batu da nake da tabbacin ba ki san da shi ba...”
Murmushin fuskarta na shirin ɓacewa ta furta.
“Wani batu ne wannan?”
“A yau yarima Wajid ɗan sarkin Mamlakatul Azad zai zo tare da mahaifinsa a kan batun naiman aurenki?...”
Ɓat murmushin kan fuskarta ya ɓace a iska, wani abu me kama da ƙwai ya faɗo ya fashe a ƙirjinta. Sannan ta saki baki da hanci tana kallon Champa. Duk bayan tsawon lokacin da suka shafe suna soyayya da Eid masoyinta a rasa a gaɓar da za'a rabasu sai yanzu da soyayyarsu ta ɗauko daɗi?... Zuwan wani da ban fadar a kan maganar aurenta ba Eid ba na nufin za'a aura mata waninsa.
Kuma sam ita ba za ta lamunci hakan ba, ko da za ta gudu daga fadar ne za ta yi, domin tseratar da soyayyarta. Ta san ko da ta gabatar da Eid a gaban Malik Cangaz a matsayin mijin da take so ya aura mata ba zai amince ba, domin Eid ba shi da mulki, sannan ba shi da kuɗi ko wata dukiya da za ta siya masa mutunci a idon mahaifinta ballantana ta kai ga ya aura mata shi.
Salma
Ahmad
Isah
✍️
A zo a fara biyan kuɗin book, saboda book one ya ɗauko hanyar ƙarewa. If you wanna be part of the journey, pay ₦400 for nomarl group, and ₦800 for VIP group.
5487270431
Salma Isah
Monie point
Sai a tura shaidar biya ta 08130172702.
°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°
.
🪄
...JUYIN
KWAƊO...🪄
©️Salma
Ahmad
Isah
SalmaAhmadIsah
@ArewaBooks
SalmaAhmadIsah
@Wattpad
Page-10
ARMAN.
A rana ta gaba ma haka suka ci gaba da tafiya a cikin dajin, kasancewar suna duba taswirar da tsoho ya basu yasa ba su ɓata hanya ba ko sau ɗaya. Har rana ta biyu a tafiyar tasu ta ƙare babu wata matsala da ta samesu, ko wani baƙon abu da ya ziyarce su, sai a rana ta uku, ranar da suke hasashen iske ƙauyen Askar wani baƙon lamari ya riskesu a hanya.
Tun cikin daren ranar ake iska me ƙarfi, wadda take tafe da ƙura da kuma sanyi me shiga jiki, kuma tun a safiyar ranar iska ta ɗauke tentunan da suka kafa, lokacin da suka tafi naiman ruwan wanke jikunansu, sanda suka dawo suka iske babu tentin iska ta ɗauke.
Sa'arsu ɗaya, jakukkunansu ba su cikin tent ɗin lokacin da iska ta yi gaba da su, cike da salallamin rashin tent ɗin suka haɗa kayansu suka ci gaba da tafiya, dan yanzu abin ma ya fara zame musu jiki, har sun fara sabawa da yanayin tafiyar.
Suna tsaka da tafiya a tsakanin wasu bishiyoyi suka fara jin kuwwar wasu mutane, Adam ne ya fara jiyo kuwwar, hakan yasa ya ankarar da sauran, sai suka tsaya suna duba kewayen da suke, wai ko za su ga ta inda masu kuwwar za su ɓullo. Amma har bayan shuɗewar daƙiƙu biyu babu alamar komai. Sai da suka sakankance sannan suka ji faɗowar abu daga sama tim!.
Hakan ya sa suka ƙara razana, Arman ya turasu bayansa domin basu kariya, yayin da yake kallon ta inda abin ya faɗo, girman idonsa ya rage yana kallon mutumin dake tsaye a gabansu, alamun dai shi ne ya faɗo daga saman. Tun daga kan kwarjallen dake ƙugunsa zuwa rigar dake sanye a jikinsa duka na fata ne, kuma fuskarsa a rufe take, shi yasa ba su iya banbance kamarsa.
Kafin su yi wani yunƙuri wasu mutum uku dake sanye da kaya irin nasa suka sake dirowa daga saman bishiya, Arman ya sake kare Ivana da Adam da suke a matuƙar tsorace, shi ma kansa a tsorace yake, amma dole ya ɓoye tsoronsa domin kare abokansa.
Kallon-kallo aka tsaya yi, su suna karantar kama da kuma nau'in tufafin dake jikin mutanen huɗu, yayin da su ma suke kallonsu, dan za su iya cewa tun da suke fashi a hanyar, tsawon shekaru tara, ba su taɓa ganin mutane masu kama da waɗannan ba, bawai dan sun banbanta da mutane ba ne, a'a su ma kamar mutane suke, amma kalar tufafin jikinsu shi ne abin mamaki... Sai dai mamakin son sanin su wasu nau'in mutane ne ba shi zai hana su ƙwace duk wani abu da suke tafe da shi ba, dan haka wanda ya kasance shugansu ya miƙa musu hannunsa, cikin larabcinsa me kyau yace.
“Ku bamu kayanku!”
“Kaya?”
Adam ya maimata.
“Ku bamu kaya ko kuɗi, idan ba haka ba ku yi ta ranku!”
Dariya ta so kama Adam, dan shi ne ya fara fahimtar wasu irin mutane ne. Camera ɗinsa ya fitar ya shiga ɗaukansu a hoto. Yayin da su kuma suka shiga kare fuskokinsu saboda hasken flasher da Adam ke haskasu da ita.
“Adam me suke buƙata ne?”
Ivana ta tambaya tana kallonsa lokacin da ya gama ɗaukansu a hoto yana dariya.
“Wai 'yan fashi ne”
Ita kanta sai da abin ya so bata dariya. Ganin suna dariya ya harzuƙa 'yan fashin, ai rainin hankali ne ma, ya za'ayi su tambayesu kudi ko kayan kuɗi su zauna suna musu dariya. Hakan yasa suka fitar da makamansu masu firgita bil adama, suka yi kansu da shi. Amma Arman bai bari sun kai ga cutar da su ba, dan cikin azama shi ma ya fitar da nasa takobin ya nunasu da shi.
“Kada ku sake ko da taku ɗaya zuwa garemu, duk wanda ya sake kuma zan raba kansa da gangar jikinsa”
Ya faɗi a dake yana dubansu, juna suka kalla, dan ba sosai suka gane abin da yace ba. Ɗaya daga cikinsu ya sake yin wani takun zuwa gaba. Cikin ƙwarewa da iya sarrafa takobi, Arman ya juya takobin a hannunsa, sannan shi ma ya nufe shi, yana zuwa dab da shi ya kare farmakin da ɗan fashin ya kawo masa, sannan ya jujjuya takobin da hannunsa ɗaya, ya kai masa suka a gefen ciki, shi kansa bai ɗauka cewa zai iya samun wurin da ya hara ba. Domin bai taɓa amfani da takobin gaskiya ba, amma sai ga shi ya samu gefen cikin ɗan fashin.
Ya ƙwalla ƙara yana naiman ɗauki a wurin 'yan uwansa, su kuma kallon Arman kawai suka tsaya yi baki sake, dan a fashin da suka kwashi tsawon shekaru sun yi ba su taɓa haɗuwa da wanda ya mayar musu da martani ba sai yau. Arman ya zare takobin da ya sokawa ɗan fashin, sannan ya tura shi wurin 'yan uwansa. Da sauri suka ɗauki ɗan uwansu suka ruga cikin dajin da gudu.
“Hooooo! Abokina wai da ma haka ka iya sarrafa takobi!?”
Cewar Adam baki buɗe, dan bai taɓa ganin Arman ɗin na wasan takobi ba sai yau. Ita kuma Ivana takan je ta ga wasan nasa idan suna yi a Fencing Academy ɗinsu, amma duk da haka abin ya bata mamaki. Shi kansa Arman mamakin abin yake ji, takobin dake ɗigar jini ya ɗaga yana kallo, kafin ya mayar da shi cikin gidansa.
“Ya kamata mu yi saurin barin wurin nan, kafin wasu mugayen mutanen su zo”
Da wannan maganar tasa suka ci gaba da tafiya, kuma ba su yada zango ba har sai da suka fara hango gidan da tsoho yace musu shi za su fara gani kafin su kai ga shiga ƙauyen Askar. Duk da haka Arman bai tabbatar ba sai da ya buɗe taswirar da tsoho ya ba su, sannan ya ga waɗannan hasken ukun suna tsaye a kan ƙauyen Askar da aka masa alama, kansa ya ɗaga ya dubi su Adam.
“Wancan shi ne gidan da tsoho yace za mu fara gani kafin mu shiga ƙauyen Askar...”
Suka sake kallon gidan.
“To mu je mana”
Cewar Adam shi ne kan gaba, su ma bayansa suka bi zuwa gidan da aka gidan da ƙasa. Kasancewarsu 'ya'yan musulmai yasa sai da suka gabatar da sallama, kafin su kutsa kai gidan. Su ukun duka suka jeru a tsakar gidan. Suna kallon kallo da matar dake tsakar gidan.
Farar dattijuwa ce, wadda a ƙiyasin shekaru za ta kai hamsin da ɗori, sanye take da wasu tufafin da aka saƙa da zaren audiga, wanda aka rina shi zuwa kalar shuɗi. Ƙafafunta na cikin takalman fata irin na zamaninsu, hannunta riƙe da wata ƙwarya. Kamar yanda su ma suke kallonta, haka ita ma take kallonsu. Dan sam ba su mata kama da mutanen da ta sani ba.
“Barka! Mu baƙi ne a nan, akwai wani tsoho da ya ba mu wannan yace mu baki”
Cewar Arman yana nuna mata taswirar dake hannunsa. Nan take tsohuwar ta saki fuska, sannan ta musu alama da su shiga cikin ɗakinta.
“Anya za mu iya yarda da wannan tsohuwar me kamar yamusasshen ganye?”
Cewar Adam murya ƙasa yana duban abokansa. Arman ya bugi cikinsa da bayan hannunsa.
“Ka mana shiru, a wannan halin da muke ciki ba mu da ikon zargin kowa, mu dai kawai abin yin mu shi ne kare kai a lokacin da aka kawo mana farmaki”
Cewar Arman.
“Haka ne Adam, tun da har muka yarda da tsohon can ita ma babu dalilin da zai sa mu ƙi yarda da ita”
Cewar Ivana.
“Ku shiga mana”
Tsohuwar ta sake faɗa tana nuna musu ɗakinta da shi ma aka gina shi da ƙasa. Sai da suka gama ƙarewa gidan kallo, sannan suka shiga ɗakin nata da babu komai ciki sai wani gadon katako. Sai wasu jakukkunan fata dake gefe guda. A kan gadon dake ɗakin suka jeru su uku, Adam har da fitar da camera ya fara ɗaukan ɗakin a hoto.
A lokacin kuma matar ta shigo ɗakin, hannunta tiƙe da wani abu me kamar kofi, ta aje musu tana faɗin su sha abin ciki, dai suka girgiza mata kai a tare, alamun ba sa sha. Suna ganin sanda matar ta yi murmushi, sannan ta juya kanta tana kallon ƙofar ɗakin, cikin muryarta ta tsufa ta ƙwala ƙiran.
“UWAIS!”
Cikin abin da ya zarce mamaki Arman, Adam da Ivana suka dubi juna, sannan suka kalli farar dattijuwar, idan dai har ɗan rakiyar da za su tafi da shi ya kasance UWAIS ke nan wannan matar ita ce gimbiya FEROZA, wato mahaifiyar Amir UWAIS BIN DHAAKIR?.
_____•••____
UWAIS.
A hankali daddaɗar iskar dake busawa a dajin take kaɗa ganyayyakin bishiyun da suka ƙawata shi. Yayin da wani daddaɗan busar sarewa ke tashi a cikin dajin, da daɗin da yake naiman zarce na iskar da ake. Daga can kan reshen wata doguwar bishirya yake zaune, ya harɗe ƙafafunsa, yayin da iskar wurin ke ɗaga dogon gashin kansa, idanuwansa kuma a lumshe, domin shi kansa yana jin daɗin busar.
Sanye yake da Sirwal, wani nau'in tufafi irin na wancan zamanin, wanda ake yinsa da zare lilin. Takalman ƙafarsa na fata ne, wanda suke da zaren ɗauri, akwai ɗan siririn rawani a kansa, wanda bai ɓoye dogon gashin kansa ba. Wasu kyawawan tsuntsaye dake kan bishirya da yake zaune ne ke ta kukansu me daɗin saurare, waɗan da suka ƙarawa busar tasa ta yau armashi.
Cak busar sarewar ta tsaya, sannan a hankali ya buɗe kyawawan idanuwansa masu ɗauke da shuɗiyar ƙwaya. Ya motsa kunnensa na ɓarin hagu, domin jiyo abin da yake dajin dake gaban wanda yake ciki. Gurnanin damusa haɗi da kukan barewa ya jiyo lokaci guda.
Hakan tasa ya yi saurin miƙewa a kan reshen bishirya, sannan ya sofare zarewar hannunsa a cikin ma'ajiyarta dake saƙale a ƙugunsa. Tsalle ya daka ya iyo ƙasa, sai dai kafin ya kai ƙasa ya buɗe fukafukansa da ba su bayyana sai idan har shi ya bayyanar da su ya tashi sama. Cikin abin da bai fi ƙiftawar ido ba ya isa dajin dake kusa da wanda ya baro.
A kusa da inda yake jin gurnanin damusar ya sauƙa, kuma yana sauƙa ya sake ɓoye fukafukansa guda biyu, ya tsaya yana kallon wata baƙar damisa da take shirin farmakar wata barewa. A hankali ya miƙe tsaye, sannan ya zaro sarewarsa dake maƙale a ƙugunsa, ya juyata a hannunsa, nan take ta rikiɗa zuwa bakar da aka ƙera da ɗanyar azurfa, sannan a hankali ya riƙeta da hannunsa na hagu, ya ɗagata sama, tare da saitata a kan damisar, yatsun hannunsa na dama ya motsa, wata farar siririyar kibiya ta faɗo hannun nasa, a hankali ya saita kibiyar a jikin bakar, sannan ya sakata cikin yatsun hannunsa biyu.
Ya kanne idonsa tare da karkatar da kansa gefe, sai da ya saita damisar sosai, sannan ya saki kibiyar, babu kuskure ko kauce hanya kai tsaye kibiyar ta soki damisar a gefen cikinta, kukan da damisar ta saka ya sa barewar da take hari da farko ta razana ta falla cikin dajin da gudu.
Murmushi ya yi kawai, sannan ya juya bakar ta rikiɗe zuwa sarewa, ya sake saƙalata a cikin ma'ajiyarta me kama da gidan takobi, sannan ya yi wurin da damisar ta faɗi tana numfashi da ƙyar, tsuggunawa ya yi a kanta, ya kalli wurin da ya harbeta na ta zubar jini.
“Idan aka ce ku koma cin ciyawa ba iyawa za ku yi ba, kuma idan aka ce kada ku cutar da dabbobin da ba su ji ba ba su gani ba ƙi kuke, ya za mu yi da ku ne?”
Ya tambaya yana ɗora hannunsa a kan kibiyar, sannan a hankali ya zareta daga cikinta, ya shafa wurin da ya harbeta, sannan ya miƙe yana kallonta.
“Allah ya baki lafiya”
Yana gama faɗar hakan ya buɗe fukafukansa ya tashi sama. Yana shawagi a iska kiran mahaifiyarsa ya riske shi, hakan yasa bai sauƙa a ko ina ba sai a cikin gidansu.
IQRAH.
Ƙuri ta yi da ido tana bin yariman da aka ce shi ne wanda za'a aura mata da kallo, fuskar nan a haɗe, dan sam babu alamar fara'a a tattare da ita, ta cika ta yi fam, jira take a tsikareta ta fashe tau!. Ba sai an yi wani tone-tone ba, sam ita matashin bai mata ba. Ba wai dan ba shi da kyau ba, ba kuma dan ba shi da nasaba me kyau ba, sai dan kawai Eid shi ne a zuciyarta.
“... Yanzu amincewar Gimbiya kawai muke buƙata, daga zarar tace eh sai a