Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
gimbiyoyin uku ba, kai kace wani yayansu ne.
“Horarwa na tafiya yanda ake so Asra!”
Cewar Malik cike da izza, Asra ta yi murmushi tana duban mahaifinta, sannan ta jinjina kanta a ladabce.
“Sosai ma kuwa Darvesh (Holy man)”
“Ko za mu iya ganawa na wasu daƙiƙu?”
Faɗin Malik Cangaz, Asra ta gyaɗa kai, a tare suka taka zuwa wata kusurwa dake cikin filin, wadda ta fitar da su (balcony) dake can saman fadar, daga wurin ma za ka iya hango gine-ginen gidaje masallatai da kuma kasuwar masarautar kaf.
“Zuwa yanzu kwanaki uku kacal suka rage a ɗaura auren Iqrah da yariman Azad... Duk wasu shirye-shirye mun kammalasu, ɓangaren tsaro ne ba mu yi komai ba, dan haka ina so a tabbatar da tsaro a masarautar nan, domin akwai tarin baƙin da za su zo daga baƙin masarautun da suke maƙotantaka da mu... Ba na son a samu wani kuskure!”
Asra ta jinjina kai tana saƙala gashin kanta a bayan kunnenta.
“Zan tabbatar da hakan Darvesh...”
“Zuwa gobe zan je kaiwa abokina sarkin Mamlakatul Dahi goron gayyata, domin ba na so na aika Manzo! Na fi so na je da kaina domin isar da saƙon... Dan haka ki shirya, ina so ki min rakiya!”
Asra ta risina cikin girmamawa.
“An gama Darvesh...”
“Na sallameki”
Da haka ta juya ta barshi tsaye a wurin yana kallon girman masarautarsa. Kafin kuma amintaccen hadiminsa ya shigo wurin a hanzarce.
“An kamo matasan da ake zargi da cin amanar ƙasarmu ta hanyar fitar da bayanan kasuwancinmu na sirri ya shugabana!”
Cewar hadimin, bayan ya kwashi gaisuwa. Malik ya dube shi cike da isa, sannan ya furta.
“A kai min su kurkukun cikin ƙasa, a gana musu azaba ta mako guda, kafin na kai ga zartar da hukuncin da ya dace a kansu, kafin su mutu ina so su ɗanɗana azabar da za ta bawa duk wani me sha'awar aikata laifi irin nasu tsoro!”
Hadimin ya risina cikin alamar dake nuna ya karɓi saƙon shugaban nasa.
“An gama ya kai wannan adalin sarki!”
Daga haka shi ma ya fita daga wurin ya barshi, tsaye cikin sallalamin jiran ranar da boka Jalis zai sake naimansa. Domin tun bayan ranar da suka haɗu a kan maganar gano matasan nan uku bai sake naimansa ba, kuma hakan na nuna cewa har yanzu boka bai gano inda suke ba. A tsarinsa shi kuma ba ya zuwa wurin bokan ba tare da bokan ya naime shi ba... Amma a wannan karon dole ya karya ƙa'idar, dole ya je ya ji yanda aka yi aka haihu a ragaya.
MAMLAKATUL AFSAH.
Cike da zaƙuwa Malik Safraz ya ɗaga kai ga tawagar ɓoyen da yakan aika domin bincike, ya ƙagu su sanar da shi inda takobin mulkinsa yake.
“Ya shuganmu, haƙiƙa takobinka ya bayyana a ban ƙasa, sai dai samunsa shi ne abu mai matuƙar wuya a gareka!”
Muryar ɗaya daga cikinsu ta furta, ba tare da ya bayyana ba, domin ko shi kansa ba ya iya ganinsu sai idan sun so hakan. Ya ɗaga kansa ya kalli saitin inda maganar ke tashi, sannan ya furta.
“Shin har akwai wani abu da zai gagareni samu a faɗin wannan duniyar?”
“Ƙwarai kuwa ya shugabanmu, kuma wannan takobi na ɗaya daga ciki!”
“Me nene dalilinku na faɗin hakan?”
“Wanda yake tare da takobin shi ne abin ji, domin ko da yankar naman jikinsa za'ayi a kan takobin nan sai dai a yi, amma ba zai taɓa bari a raba shi da wannan takobi ba...”
“Waye shi?”
Malik Safraz ya tambaya ransa na ɓaci.
“UWAIS!”
Muryoyi uku suka ba shi amsa take, a nan ne fa hantar cikinsa ta fara motsi, domin in har Uwais ko Feroza na raye a ban ƙasa mulkinsa na cikin haɗari!... Ke nan me ya kamata ya yi a wannan gaɓar!?... Tambayar ta tuno masa da wata hatsabibiya ɗaya da zai iya sawa wannan aikin hankali kwance. Lokaci guda ya yi murmushi, sai kuma ya haɗa da dariya yana jinjina kai, sannan laɓɓansa suka furta sunanta.
“NATILA!”
GARIN QUDWA, YANKIN GABASHIN SAHARAR SUBAH.
Hayaniyar jama'ar dake kaikawo a cikin 'yar ƙaramar kasuwar garin ce ta cika ko ina. Komai na kayan siye da siyarwa daga ƙasashen duniya akan kawosu kasuwar wannan gari na Qudwa. Domin garin ya kasance cibiyar kasuwanci, duk da garin bai cika girma ba.
Ko wani mutum dake cikin kasuwar za ka same shi sanye da shiga irin ta garinsu ko yankinsu, ko kuma masarautarsu. Yayin da ake hada-hadar cinnikayya a cikin kasuwar. Wata iska me ƙarfi ta taso daga cikin sahararar dake gabas da kasuwar, hakan yasa ƙura ta shiga bule mutanen cikin kasuwar. Kafin wata guguwa ta shigo cikin kasuwar, sannan ba ta sauƙa a ko ina ba sai kan rufin wani shago.
Kaɗan-kaɗan iskar ta fara raguwa, har ta ɗauke gaba ɗaya. Yayin da wannan guguwar ta rikiɗa zuwa wata doguwar budurwa. Sanye cikin baƙaƙen kaya, ta yi kitso guda biyu a kanta, tsayin jelar kitson har cinyoyinta. Fuskanta kuma a rufe yake, a hankali ta yi tsugunnon mage a kan rufin shagon, sannan ta shiga baza idonta a kan mutanen dake kai kawo...
Dan iskar da ta taso ba ta sa kasuwancin da ake gudanarwa ya dakata ba, sautin murmushin da ta yi ya fito tare da motswar ƙyallen da ta rufe fuskarta da shi, domin ta hango abin harinta, ci gaba ta yi da bin sawunsa, har ta ga sanda ya shiga wani loko da take da tabbacin babu kowa ciki.
Take ta ɓace daga saman shagon, kuma ba ta bayyana a ko ina ba sai a cikin lokon, sannan a gaban mutumin da take bibiya. Shi kansa mutumin da ya ganta sai da ya razana, hakan ya sa kayan dake hannunsa suka zube a ƙasa, ya ɗaga hannayensa sama kamar me laifi.
A wannan karon budurwar dariya ta yi, sannan ta buɗe fuskarta, kyakkyawar fuskarta ta bayyana gare shi, haƙika tana da kyau, amma kyawun ɗan maciji. Lokacin da ya ganeta bai san sanda ya saki fitsari a wando ba, jikinsa ya soma kyarma, domin ganin NATILA na dai-dai da ganin mutuwar mutum.
“Sannunmu da sake haɗuwa, Malam Ayyaz!”
Jikin Ayyaz na rawa ya shiga ja da baya yana son bata haƙuri, cikin wani irin sauri da ya ɗararma hankali ta isa gabansa, sannan ta saka hannayenta ta riƙe wuyansa.
“Dole na kasheka, sannan na ciro zuciyarka na kaiwa shugabana, na masa alƙawarin sadaukar masa da zuciyarka a daren yau!...”
Ta ƙarashe maganar wasu zaƙa-zaƙan fiƙoƙi na fitowa daga haƙwaranta na sama. Sannan ta kafasu a wuyansa, nan take Ayyaz ya fara shure-shure, amma Natila ba ta saki wuyansa ba sai da ta zuƙe fiye da rabin jinin jikinsa. Duk da haka ba ta ƙyale shi ba, da ta saki wuyan nasa ta ɗaga hannunta me yalwar dogayen farata, ta caka a ƙirjinsa, sannan ta ciro zuciyarsa, kana ta saki gangar jikinsa ta faɗi ƙasa.
Zuciyar dake riƙe a hannunta ta kalla, bakinta duk ya ɓaci da jinin jikinsa, ta sa bayan hannunta goge bakin nata, sannan ta sake rufe fuskarta, ta tsallake gawarsa ta ɓace a iska.
Salma Ahmad Isah ✍️
___________
_😳 Akwai matsala!_
_Ko su waye suka kama ADVENTURERS ɗinmu?. Shin ya za a yi su kuɓuta?_
_Batun wannan Natilar! Ya kuke ganin haɗuwarta da ADVENTURERS ɗinmu za ta kasance?._
_
Book 1 ya kusa ƙarewa, dan haka ya kamata a fara biyan kuɗin book 2 tun yanzu._
5487270431
Salma Isah
Monie point
Shaidar biya kuma ta 08130172704.
°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°

🪄

...JUYIN

KWAƊO...🪄
©️Salma

Ahmad

Isah

SalmaAhmadIsah

@ArewaBooks
SalmaAhmadIsah

@Wattpad
Page-13
ADVENTURERS.
Kukan Adam shi ne ya cika ɗan ƙaramin akurkin da aka cusasu ciki, dan duka su huɗun tare da wata mata da ba su santa ba na cikin wani abu me kamar keji, yayin da mutanen da suka kamosu ke zaune kusa da kejin, sun yi ayari suna gabatar da bautarsu zuwa ga wutar da suka hura, domin sun lura cewa mutanen wuta sukw bautawa.
Kuma bayan hasken wutar babu komai a wurin sai na farin wata da ya samu zarafin ratsowa ta jikin ganyen bishiyoyin da suke a ko ina na dajin, sai kuma na fitilun wayoyinsu da suka kunna. Tun bayan da mutanen suka kama su ba su musu komai ba, kuma ba su ce da su komai ba, sai kallonsu da suke ta yi tun ɗazu, kamar za su cinyesu.
“Mi shan Allah Adam skut! (Dan Allah Adam ka yi shiru!)”
Cewar Ivana cikin rarrashi, Adam ya goge hawayen da yake, yana duban Arman dake wurga masa harara, shi kuma Uwais kallonsu kawai yake yana murmushi, dan kukan da Adam ɗin ke yi dariya yake son ba shi.
“Ki bar ni na yi kuka, wata ƙila wannan shi ne kukana na ƙarshe, daga shi kuma ba zan sake ba!... Saboda waɗannan abubuwan yanka mu za su yi, ko su cinye, ko su bawa dabbobinsu!...”
Ya ƙarashe yana jingina kansa da jikin itatuwan da suka kafa kejin.
“Idan ba ka mana shiru ba sai na maka duka!”
Cewar Arman a ƙufule. Sannan ya ƙara da.
“Kalli Ivana, ko ita ba ta yi kuka ba sai kai, ƙaton banza kawai!”
Adam ya kame jikinsa yana ƙifƙita ido. A karo na barkatai, Arman ya sake haske matar da suka tarar a cikin kejin da fitilar wayarsa, amma har yanzu tana a yanda suka shigo kejin suka sameta. Dunƙule take a wuri guda, ta haɗa kai da gwiwa, kuma duka jikinta a rufe yake.
“Uwais ka tambaya mana wannan matar ko ta san abin da mutane nan suke so!...”
Cewar Arman yana gyara zaman glasses ɗinsa.
“Da ace za ta faɗa da ta faɗa tuntuni, tun yaushe nake mata magana? Amma ko tari ka ji ta yi?...”
Uwais ya ƙarashe da tambaya. Arman ya girgiza kansa yana ci gaba da haska matar, sannan ya ƙura mata ido. A hankali ya fara takawa zuwa inda matar take, yana daf da durƙusawa a kusa da ita, mutumin da suke sa ran shi ne shugaban mutanen da suka kamasu ya furta.
“Ku je ku fito da su yanzu mu sadaukar da su ga wutar bautarmu!”
Hakan ya sa Arman ya fasa durƙusawa, ya juyo ya kalli abokansa cikin tashin hankali, Ivana ta dubi Uwais, sannan ta dubi Arman, yayin da Adam ya ƙara fashewa da wani sabon kukan yana faɗin sun mutu.
Har zuwa lokacin da wasu mutum biyu suka buɗe ƙofar kejin da suke ciki ba su iya taɓuka komai ba, sai da aka gama fito da su daga cikin kejin, har da matar da a yanzu suka lura da cewa fuskarta a rufe take, aka jerasu a gaban wutar dake ciki.
“Dan Allah Arman ka yi wani abin!”
Cewar Adam cikin kuka. Arman ya lumshe idonsa, yayin da yake lalubo takobin da datijjo ya ba shi a cikin jakar dake bayansa. A lokacin da ya riƙo takobin ya buɗe idonsa, sannan cikin zafin nama ya miƙe tsaye, ya zare takobin yana nuni da shi ga mutanen da suke riƙe abokansa da wannan matar.
“Kada ku cutar da su! Ku ƙyalesu!”
Ya faɗa yana nuna musu takobin.
“Me kuke jira wai? Ku danna min kawunansu a cikin wuta!”
Shugaban mutanen ya basu umarni cike da isa, wanda yake riƙe da Adam ne ya riƙo gashin kansa, yana shirin danna kan Adam a cikin wutar Arman ya yi tsallen albarka, ya ɗaga takobin hannunsa ya datse hannun mutumin!.
Ƙarar da ya ƙwalla ce ta janyo hankalin sauran mutanen wurin. Sannan kuma ita ta razana sauran da suka ga faruwar lamarin. Sai suka yi saurin ja baya daga jikinsu Ivana, yayin da shi ma Uwais ya yi amfani da wannan dama wurin juya sarewarsa zuwa baka, sannan ya motsa hannunsa ya fito da kibiya, tare da sakata a jikin bakar, shi ma ya nuna mutanen da ita.
Adam da Ivana kuma suka yi saurin ɓuya a bayansu, su kuma suka musu garkuwa, amma wannan matar ta ɗazu har zuwa lokacin tana durƙushe a gaban wutar, ba ta motsa ba ballantana ta yi yunƙurin guduwa, kuma kanta a ƙasa, sannan fuskarta a rufe.
“Lalle kun aikata babban kuskure, tun da har kuka iya illata ɗaya daga cikinmu, kuma a sansaninmu... Ina me muku albishir da ba za ku bar nan da rai ba... Dakaru! Ku tabbatar da kun gama min da su yanzu...!”
Cewar shugaban dakarun, nan da suka yi kan Arman da Uwais, amma kuma sam ba su ba su damar cutar da ɗaya daga cikinsu ba, domin sun zage iya ƙarfinsu suna yaƙin kare kai. Ƙarshe ma shi Uwais fuka-fukansa ya buɗe ya tashi sama, daga saman yake harbin mutanen da kibiya, yayin da Arman ya bada himma wurin sarrafa takobi daga ƙasa.
Amma kamar ƙara musu yawa ake. A nan ne fa Arman ya fara gajiya, saboda sam shi bai saba ba, hakan ya sa ƙarfinsa ya fara gazawa, har ta kai ga an samu wani a cikin dakarun ya buga masa wani madoki. Da ya yi nasarar kai shi ƙasa, hakan ya jawo glasses ɗinsa suka faɗi ƙasa, duhu ya mamaye ganinsa, sannan takobin hannunsa ma ya faɗi gefe guda.
Dakaren da ya samu nasarar kai shi ƙasa ya tsaya a kansa yana dariyar cin nasara. Adam da Ivana kuwa na gefe suna ganin ikon me duka, duk yanda suke jin ana batun yaƙi a tarihi ne kawai, ashe akwai lokacin da za su tsinci kansu ana yaƙi a gabansu. Ita Ivana Uwais ma ya fi bata mamaki, dan su duka ba su taɓa sanin cewa yana da fuka-fuki ba.
Lokacin da Arman ya faɗi suka ankara, dan haka ita da Adam suka yi wurin domin ceton abokinsu dake laluben glasses ɗinsa a ƙasa, domin ba ya ganin komai, yayin da shi kuma mayaƙin dake kansa ya ɗaga mashi yana shirin soka masa...
“Kai!...”
Cewar Ivana hankali tashe, yayin da ta nufi wurin Arman da gudu, Adam na binta a baya. Sai dai kafin su ƙarasa wurin, wani takobi da aka cillo daya can baya ya caki mayaƙin a ciki... Hakan ya sa suka taka birki suna kallon mayaƙin, yayin da yake silalewa zuwa ƙasa.
Baki buɗe kuma dubansu ya zarce zuwa inda aka wullo takobin, ganin wannan matar ta ɗazu tsaye, kuma riƙe da takobi yasa suke san cewa ita ce wadda ta cillo takobin wannan takobin. Take mayaƙan da abin ya faru kan idonsu ita ma suka far mata, tsayuwarta ta gyara, tare da gyara riƙon takobinta, tana jiran isowarsu, kuma har zuwa lokacin fuskarta a rufe take.
Ai suna isa wurin da take aka fara yaƙin gaske, dan yanda suka baibayeta sai kace za su cinye namanta ɗanye, amma ba ka jin komai sai ƙaran takobinta, daga ta kai suka wuri za ka ga gawa na faɗuwa ƙasa timm. Nan fa wurin ya yamutse, gawawwakin mutanen nan ne kawai suke zuba.
A lokacin kuma Adam da Ivana suka samu isa wurin Arman dake yashe a ƙasa, suka samu suka ɗaga shi zaune, sannan Adam ya ɗaukar masa glasses ɗinsa da glass ɗin frame ɗaya ya fashe, amma duk da haka suka saka masa, domin ya samu ya ga wannan bidirin da ake a filin.
“Sannu Arman”
Cewar Adam yana miƙar da shi. Zaman glasses ɗin ya gyara, yayin da ya tsayar da dubansa a kan matar nan ta ɗazu dake ta'asa a filin wurin, hatta Uwais ɗan kallo ya koma... Domin yanda take sarrafa takobi a wurin ya matuƙar basu mamaki.
*
Arman ya sa hannu ya buɗe kit ɗin glasses ɗinsa, domin ɗaukar wanda ya rage masa, tun da wanda yake tare da shi ya fashe. Guntun glasses ɗin ya ɗauka, sannan ya sa hannu ya cire na idonsa, kana ya saka wanda ya ɗauka, ya maye wurin wanda ya ɗauka a cikin kit ɗin da wanda ya cire a idonsa.
Ya kuma gyara zaman glasses ɗin a idonsa, sannan ya saka yatsun hannunsa a cikin sumarsa da ta yamutse, yana ɗaga kansa, tare da kallon Ivana dake zaune kan sleeping bag ɗinta, dan bayan sun rasa tent ɗinsu a kan sleeping bag ɗin suke kwana. Yanayin zamanta kaɗai zai sa ka gane cewa a gajiye take, domin sai da ta jingina da bishiyar dake kusa da ita, tana bincika wani abu a cikin backpack ɗinta, yayin da suke magana da Uwais.
Ya juya kansa zuwa ɓarin damansa, inda Adam ke zaune a kan tasa sleeping bag ɗin, shi kuma lafiyar camera ɗinsa yake bincikawa saboda ɗazu ba a gama yaƙin nan ba sai da ya ɗaukeshi a hoto. Batun yaƙi da ya gifta a cikin kansa ya sa ya yi saurin kallon wannan budurwar ta ɗazu da ita kaɗai ɗinta ta ƙarar da mayaƙan ɗazu.
Tana zaune daga kan wani itace, ta saka wani ƙyalle tana goge jinin da ya ɓata takobinta mai tsananin kaifi, wanda ta yi ta'asa da shi ɗazu. Hankalinta kwance, kamar ba ita ce ta yi kashe-kashen ba. Har zuwa yanzu da suke zaune a wurin ba ta yi magana ba, hakan yasa suka fara zaton ko kurma ce. Shi kuma Uwais yana daga gefen Ivana, yayin da take masa bayani a kan chocolate ɗin da ta ba shi.
“Miye ma kika ce sunan shi?”
Ya tambayeta yana juya ledar chocolate ɗin. Ivana ta yi murmushi a gajiye, ita ba ita ta yi yaƙin ba, amma haka take jinta a gajiye. Ko wannan tafiyar ƙafan da suke ma ai dole ta gaji, tun da abu ne da ba ta saba ba.
“Shukulata, da turanci kuma Chocolate!”
Ya jinjina kansa yana taɓe baki, sannan ya kaita baki zai ci da ba tare da ya cire laidar ba, ta yi saurin dakatar da shi.
“A'a zai ka cire ledan fa”
Ta karɓa daga hannun shi, sannan ta buɗe masa ledan, shi dai kallonta kawai yake, ta sake miƙa masa.
“Mi ye shi ledan?”
Ta yi dariya.
“Ana sakawa ne domin ya bawa chocolate ɗin kariya daga datti ko cutuka kafin a ci, kuma yana ƙara tsayin daɗewar chocolate ɗin...”
Ya sake jinjina kansa.
“Kuma yana da daɗi?”
Ta gyaɗa masa kai tana nannaɗe gashinta cikin top knot bun. Uwais ya saka chocolate ɗin a baki, sannan a hankali ya gutsira, ya fara taunawa yana juya idonsa.
“Da akwai daɗi ba?”
Ivana ta tambaya.
“Akwai daɗi sosai”
Ya bata amsa yana murmushi. A dai-dai lokacin kuma Arman ya tambayi wannan matar.
“Wacece ke? Me ya sa waɗannan mutanen suka kama ki?”
Tambayar da ya mata ta jawo hankulan sauran. Suka dubeta, cak ta tsaya da goge jinin da take, sannan ta kallesu da idonta.
“SANA!”
Kawai suka ji ta furta, sannan ta sa hannu ta yaye ƙyallen da ta rufe fuskarta da shi, cikin su ukun babu wanda ya santa, amma shi Uwais ya san fuskarta, ba ma ita kaɗai ba, har ma da sauran 'yan uwanta uku babu wanda bai san kamarsa ba, duk da bai taɓa ganinsu ido da ido ba.
“DANEEN SANA BINT MALIK CANGAZ!?”
Shi ne kaɗai abin da Uwais ya samu furtawa.
IQRAH.
Zaune take a wani wuri da aka keɓe a fadar domin shaƙatawa. Akwai wani (Fountain) dake tsakiyar wurin, yayin da (grass carpet) ke zube a ko ina na wurin, sannan akwai iska me daɗi dake busawa a ko ina. Hadimanta na zaune a ƙasa, yayin da suke bata labaran nishaɗi, ita kuma sai murmushi take. Domin duka wasu tsare-tsare da suke ita da Eid na guduwarsu a ranar da za'a ɗaura aurenta ya kamalla, hatta da ƙauyen da za'a ɗaura musu aure Eid ya zaɓa musu.
Yanzu ranar ɗaurin auren kaɗai suke jira, domin sun yanke cewa ba za su gudu ba sai a ranar da za'a ɗaura auren. Buɗe ƙofar shiga sashen da aka yi ya sa hankulansu ya koma zuwa wurin, Asra tare da wasu bayi har uku ne suka shigo wurin. Ko wacce baiwa na ɗauke da wani (tray) da aka rufe da ƙyalle.
Asra na sanye da wata Thawb kalar ruwan zuma, ta ɗora Muƙawar a kanta, wanda bai ɓoye dogon gashin kanta ba, tana tafiyarta irin ta jarumai, dan sam ba ta tafiya irin ta sauran mata. Da hannu ta yi wa hadiman Iqrah alama da su basu wuri, hakan ya sa duk suka fice daga wurin, Iqrah ta miƙe tsaye tana kallon 'yar uwarta.
“Barka da zuwa Ukti!”
Cewar Iqrah tana murmushi. Ita kuma Asra sai ta murtuke fuska tana binta da kallon tuhuma, dan haka kawai take jin ba ta yarda da ita ba. Da farko tace mata ba ta son wannan haɗin auren, ya za'ayi yanzu kuma ta zo tana murmushi?... Dole dai da akwai abin da take ƙullawa.
“Sarƙoƙi ne Darvesh ya aikoni da su, yace a kawo miki ki zaɓi wanda kike so”
Cewar Asra, tana yi wa bayin alama da su nunawa gimbiya kayan da suka zo da su. Iqrah ta nufi wurin bayin, ta ci gaba da duba sarƙoƙin, sai fara'a take abinta.
“Wannan sun fi kyau”
Ta nuna wadda ta fi burgeta. Hakan ya sa Asra ta duba wadda ta zaɓa, ba tare da ta furta komai ba ta sallami bayin, sai da suka fita sannan ta dubi 'yar uwarta da kyau.
“Ina mai fatan Allah yasa ba wani abin kike shiryawa ba”
Cewar Asra, Iqrah ta kuma yin murmushi.
“Kada ki damu 'yar uwa, ba zan aikata abin da yake ba dai-dai ba!”
“Ni ma haka nake fata”
Cewar Asra tana jinjina kai, da haka ta fita ta bar Iqrah a wurin.
Salma

Ahmad

Isah

✍️
_Pages ɗaya ya rage book 1 ya ƙare, idan regular group kike so za ki tura ₦400 through account details ɗin da zan rubuta a ƙasa. Idan kuma VIP ne sai a tura ₦800._
5487270431
Salma

Isah
Monie

point
Shaidar

biya

kuma

ta

08130172704.
°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°

🪄

...JUYIN

KWAƊO...🪄
©️Salma

Ahmad

Isah

SalmaAhmadIsah

@ArewaBooks
SalmaAhmadIsah

@Wattpad
Page-14
MAMLAKATUL AFSAH.
Zaune a gaban Malik Safraz Natila ce, sanye cikin baƙaƙen kaya, amma yau fuskarta ba a rufe take ba. Ta nutsu tana sauraron buƙatar Malik da yake so ta biya masa.
“Idan dan ta wannan ne kada ka damu Shugabana. Zan tattaro sauran yarana, za mu bisu har zuwa cikin dajin da suke, kuma zan tabbatar da na ƙwato maka takobinka!...”
Malik Safraz ya yi murmushi, dan ya san aikin Natila, idan tace za ta yi to za ta aikata. Ya sha sakata ayyuka makamantan wannan, kuma cikin sa'a tana nasara. Miƙewa tsaye ya yi, yana goya hannayensa a baya, sannan ya ƙarewa katafaren falon da suke ciki kallo, kana ya juya bayansa yana faɗin.
“Idan kuwa har kika kawo min wannan takobin, zan miki gagarumar kyautar da ban taɓa miki irinta ba!”
Natila ta miƙe tsaye, sannan ta amsa da.
“Zan kasance me cika alƙawari kan abin da na alƙauranta maka shugaba, ba zan taɓa baka kunya ba!”
Malik Safraz ya sake murmusawa, sannan ya juyo ya dubeta.
“Ki je domin ƙwato min takobina!”
Ta risina alamun ta amsa. Kana ta ɗaga kai, kafin kace me har ta ɓace. A lokacin kuma Anser mahaifin Safraz ya iso falon shaƙatawar sarkin tare da masu take masa baya. Sai da ya isa falon sannan ya yi musu izini da su jira shi a waje, sai da suka fita sannan ya dubi ɗansa.
“Wata magana nake ji haka Safraz?...”
“Wata magana kuma?”
Safraz ya mayar masa da tambayar.
“Magana nake a kan ƙwatar takobi daga hannun Uwais!”
“Shin laifi ne dan na karɓi abin da yake nawa?”
Safraz ya tambaya cikin halin ko in kula.
“Abin da nake so ka fahimta a nan shi ne, yanzu kai ne sarkin Afsah, wannan takobin ba zai kareka da komai ba, tun da ko a da rashinsa bai sa ka kasa zama sarki ba”
Safraz ya girgiza kai.
“Ba wai mallakar takobin ne kaɗai abin da ya

Chapter 12 of 13