Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
9 / 11
k'afa ta har tsakiyar kaina, shi kuwa D'an matsawa yayi nisa dani ganin yadda duk na tsorata ni kuwa sauke ajiyar zuciya nayi ganin ya matsa,
Addu'a yayima yarinyar yana bata dabino a baki ai kuwa ta camke tana amsa hud'uba yayi mata da sunan Ummah na wato Khadeeja sosai nayi farin ciki har na kasa b'oye wa yace "wane suna zaki rink'a kiranta dashi" sosai nake jifarsa da murmushin da ya kusa zauta shi numshe ido yayi yana kiran Ya salam yarinyar nan zata min illafa da wannan murmushin nata can ya tsinkaye muryata nace "Allah ya raya Anam" murmushi yayi yace "sunan yayi dad'i sosai" rungume yake da Anam sosai yake jin sun yarinyar har jinin jikinsa banyi tunin yazo kusa dani ba kawai naji ya had'a mu da Anam ya rungume sauke ajiyar zuciya nayi ina mutsu-mutsun tashi ganin duk ya kanainaye ni yasa ba yadda na iya na kwanta lamo a k'irjinsa mai yalwar fad'i da gargasa ga wani irin masifaffan kamshi da nake shik'a ta jikinsa d'agowa yayi yana kaimin kiss tundaga goshi har hanci dai-dai wajan bakina ya tsaya yana kallon d'an k'ara min bakin nawa idanuwana dake rumtse yake bin fuskata da kallo baisan sadda ya had'e bakinsa da nawa ba da sauri na bud'e ido na sai kuma na rumtse jin tattausan bakinsa mai fitar da wani irin masifaffan kamshi mai dad'in shak'a a cikin nawa wani irin yanayi na tsinci kaina daban tab'a jin makamancinsa ba sosai yake tsotsar bakina ni kuwa nayi luf a jikinsa ji nake inama mu dauwama a haka harni kaina bansan sadda na fara basa had'in kaiba can kuma mina tuna saina janye jikina dukanmu sauke ajiyar zuciya muke cike da tsananin kunyar sa nayi k'asa da kaina shi kuwa gogan naku har idonsa ya canza launi tashi yayi jiki a sukwane yace "matata ni zan wuce kar dare yayi ko za'a ban wajan kwana" sosai naji sunan matar tasa d'aya Kira Ni murmushi nayi kawai ina tashi mik'e ji nake kamar karya tafi kuma tashin danayi ya k'ara rungume ni sosai kamar za'a kwace masa ni wasu irin sakwanni yake aika min dasu cikin gangar jikina masu tsayawa a ruhi saida ya gaji dan kansa sana ya sake ni yana aji min kud'i masu uban yawan da suka ban mamaki zanyi magana yasa d'an yatsan sa a bakina yana girgiza min kai yace "kinfi haka a waje na" shuru nayi kawai ina danne wasu hawayen farin ciki ashe nima zan samu mai sona kamar haka banyi aune ba naji tattausan harshan yana shanye hawayen dake zub'o min ashe hawayen nake ban sani ba da sauri yace "bana so kina min asarar hawayenki kinji" ya k'are maganar da wata shu'umar muryarsa mai kashe min jiki da ruhi.
Sana ya juya ya fita a tsakar gida ya tadda su Gwaggo suma yayi masu alheri sosai Gwaggo cewa take "gaskiya Khaleesat kinyi sa'ar miji wallahi karkiyi wasa da damarki dole kishiyarki ta haukace" suma su Haneefa dai haka suke ta ce min Inna gaje mai dai sharawa take min sosai y'an barka ke shigowa su mutane sun zata auran danayi ne harna samu ciki sai akabarshi a hakan gudun tsagumin mutane k'anwar Mahaifiyarta ma washe garin ranar ta sauka gidanmu sosai nake ganin gata kota ina kamar su d'aya da Ummah na shi yasa kullum ina mak'ale wajanta sosai sukai murnar sunan da akasa ma yarinyar.............✍️
*Gaskiya ya kamata y'an group kuje ma Khaleesat suna fa a'ato da masu zuwa jajanta ma Hjy Sa'adha kuje mata dannar k'irji fah*🙃🤣
*FATEEMAH RABI'U (ZAHRA ROYAL STAR CE)*🥰✍️
Comment and share Fisabilillahi🥰🙏
[9/13, 5:18 PM] ZAHRAH ROYAL STAR 🥰: *🤦‍♀️💔ITA CE K'ADDARATA 🤦‍♀️💔*
*©ZAHRA ROYAL STAR CE*
*ROYAL STAR WRITIN'S ASSOCIATION*
PAGE4️⃣1️⃣➡️4️⃣2️⃣
DA SUNAN ALLAH MAI RAHMA MAI JIN K'AI
____________________✍️ Sosai nake ganin gata kota ina ranar suna yarinyar tace sunan Khadeeja (Anam) sosai mutane suka taro Uban gayyar kuwa wato Alhaji Mustapha sosai ya kashe kud'i wajan sunan Anam nima kaina abun ba'a cewa komai,
Washe garin sunan aka kawo akwati sha biyu wai a matsayin lefina sosai y'an gidanmu suka girgiza da mamakin irin kayan da aka narka a lefan sosai nayi yawo cikin dangin Abba na sana na dawo gida aka fara min gyaran jiki tunda na haihu dama ake min gyara wajan su Inna gaje Anam kuwa kwata-kwata yariyar bata da rigima kullum tana wajan su Sakina sosai suka shik'u da ita k'annuwar Mahaifiyata itama sosai take bada gudunmuwa kamin ta tafi inda tace "Khaleesat ki rik'e mijinki da hannu bibbiyu kinga dai irin gidan da zaki shiga sai kinyi taka tsantsan sai kin iya takunki dan naga kishiyar nan taki kwata-kwata ba Allah a ranta dan haka saifa kinyi hakuri kuma dama shi aure dan hakuri ne" sosai abinda ta gaya min ya shiga cikina kuka nake kamar yau ne za'a kaine sosai nayi kukan rabuwa da ita ta k'ara cewa "haba Khaleesat ke daina kukan nan haka mana insha Allah zanzo har inda kike keda muke gari d'aya ma baccin nabar yara su kad'ai ai da dani za'a kaiki amma insha Allah ranar zanzo karki damu" rungume nake a jikinta sai aikin rarrashi take haka muka rabo cike da k'ewar juna.
Bayan sati biyu
Sakina ce ta shigo ta tadda inaba Anam nono gashi na tasa yarinya gaba sai kuka nake dan kuwa yau ne za'a kaini gidan Alhaji Mustapha a matsayin mata har an aiko da mota dan kuwa daga ni sai Inna gaje sai su Haneefa da dawowa zasuyi da an kaini sosai ake fama dani nak'i ko fitowa d'aki Sakina tace min "kinga fa Khaleesat kefa ake jira wallahi Abba yana d'aki yana son magana dake" kallon nayi ina turo baki tashi nayi kawai na aje mata Anam a jikinta yadda na ajeta yariya tasa kuka ni kuwa banbi ta tataba nayi gaba dan yau haushin kowa nake ji Sakina kuwa murmushi tayi tace "kinga yau uwar taki sai a hankali" ta ida maganar tana kallon Anam tana mata wasa Anam kuwa sai kallonta take da idonta sak irin na Babanta.
Ni kuwa ina fitowa Inna gaje na fitowa daga d'akin Abban domin kirana da sauri tace "tunda d'azo fa ke ake jira kinsan halin Abbanku" wani kukan na k'ara saki nifa ji nake kamar za'a kaine wata uwa duniya ne ina cewa "Inna gaje banfa shirya ba" da sauri ta jawo ni tana nufar d'akinta dan nan ta aje min kaya amma ko tab'a su banyi ba nata cewa "yanzu Khaleesat duk wannan abun baki shirya ba zo maza nasa miki da kaina tunda naga alama aka biye miki to za'a kwana a nan" jawo ni tayi tsaf ta samin kaya cikin lefena da aka d'ibi wasu aka d'inka dan jiyama nasa wasu domin Gwaggo tayi walima domin ni sosai mutane akazo ina cikin tunani naji tana fesheni da wani irin turare mai matsifar k'amshi ga dama wani irin masifaffan k'amshin turaren wuta da ake min kusan kullum ko gittawa nayi sai anji shi ga fatata da tayi wani irin taushi da shalk'i ni kaina nasan nasha gyara ciki da waje kota ina, "tashi muje kinga tun d'azo aka kai duk wasu kayanki a mota" cewar Inna gaje jiki duk a sanyaye nabi bayanta itama kanta a shirye take.
Koda muka shiga Abba sai sababi yake danme za'a biye min Gwaggo dake zaune tace "haba Malam ayi mata a hankali mana kasan bata saba ba dole taji wani irin" gyara zama yayi naya sauke fushinsa yace "Allah yayi miki albarka Khaleesat ki rik'e mijinki tsakini da Allah kinga irin son da yake miki duk wata hidima data dace nayi miki shi yayi amma duk da haka gudun gori nace mishi dole yabarni zanyi wani abu dan haka nima nayi iya bakin k'ok'arina domin na sauke nauyin dake kaina dan haka dan Allah kiyi biyayya kibi mijinki ki guje b'acin ransa shi zaman tare dole sai anyi hakuri kiyi hakuri kiyi hakuri kiyi kuma biyayya kinji inata mai-maita miki kiyi hakuri to duk mai hakuri wata rana zaiga ribar hakurin dayayi" ya idasa maganar yana kallon yadda nake kuka ina kaina k'asa sosai shima jikinsa yayi sanyi hatta su Inna gaje ya waiga wajansu yace "kuna da abin cewa?" Gwaggo tace "ai Malam ka gama magana muma kanmu munyi mata irin wannan nasihar" Inna gaje tace "hakane Malam" waigowa yayi inda nake duk'e yace "zaku iya tafiya Allah ya tsare hanya Allah yayi miki albarka keda y'an uwanku" ni kuwa dake duk'e na bud'e baki da kyar nace "Abba dan Allah kabar min Sakina mana ta zauna dani a can" kallo na yake yana nazarin abun ganin na k'ara balun d'in kuka yasa Inna gaje tace "kware kuwa nima nayi wannan tunanin Malam ya kamata a had'ata da wani domin dai zatafi sakewa tunda kaga babban gida ne koda mukaje jeran kayanta nidai a shawarce" Gwaggo kuwa uffan bata ce ba itama tasu tace a tafi da wani saboda dai kishiyar Khaleesat komai zata iyayi Malam kuwa sauke ajiyar zuciya yayi yace "hakane da wannan dan wannan bazan hanata tafiya da Sakina ba yanzu zaku iya tafiya da ita inya so zan kira shi mijin naki sai nayi mai bayani kar yaga anje an zauna mai gida ba sanarwa" sosai nayi murna murmushi hawaye masu d'umi na zub'o min muna zaune ya kirasa ina jin muryarsa jike da kamala ya amsa da shima yaso yace hakan sai kuma aka riga shi dan haka ba matsala su taho kawai, sosai Abba ya k'ara jin kimarsa da darajar sa.
Murna ce fal a raina kiran Sakinar yasa akayi ya bata umarnin ta had'a kayanta zata koma waje sosai tayi murna itama kamar mi sai tsalan murna take Haneefa kuwa ko a jikinta saima cewa tayi "nad'an huta nima na zama y'ar gata ni d'aya a gidan".
Haka muka d'au hanyar Kano ina sak'e-sak'e a raina har muka shiga cikin garin Kano banma sani ba.
A wajan Hjy Sa'adha kuwa sosai ta k'ara d'aga hankalin ta kwata-kwata ta rame sosai ta d'ora ma kanta bak'in kishi saifa ranar data ga y'an gidan su Khaleesat d'in sunzo wai jere sosai hankalin ta ya k'ara tashi Innee sosai take tausarta saidai abinda bata sani ba tana tare da masu zugata ko ranar saida tayi wulak'ancin a cikin gidan sosai take tafkama Alhaji Mustapha rashin kunya amma kota kanta baiyi tak'i ta kwantar da hankalinta shifa kallonta yake kamar marar ilimi ina ta kai karatun nata ina takai wayewarta.
Zaune suke itada Dr Aysha su Ummeeta suna school dan basu san yaune za'a kawo Khaleesat d'in ba Dr Aysha tace "haba y'ar ki daina wannan kukan mana dan Allah insun shigo karki nuna masu wani abu" kallonta Hjy Sa'adha tayi bata ce komai ba dan bata jin zata iya bin shawar ta jin k'arar shigowar part d'inta yasa ta tashi tsaye cike da b'acin rai take kallonmu, tun d'azo muka iso saida muka huta a part d'ina dan kuwa anba Inna gaje key d'in part d'in nawa duk abinda ke cikin Part d'in Hjy Sa'adha to nawama akwai dan kuwa ginin iri d'aya ne sosai nima part d'in nawa ya birgeni bare su Haneefa sai k'ara santinsa suke Inna gaje ce tace "ya kamata muje wajan uwar gidan dan tasan da zuwanmu a bata a bata amanar Khaleesat d'in duk da bana hangan zuwa wajan zai haifar da d'a mai ido amma haka ake a adalce" tab'e baki su Haneefa sukai dan kuwa kwata-kwata Hjy Sa'adha batai masu ba dan kuwa sadda zasuzo jere ba k'ara mar rashin kunya suka gani ba wajan k'ananta sai dai suma sun iyata ai tana kallon yadda suke masu rashin ta ido sai tace ai ita ta basu Okay d'in yin hakan suma kuma ba hakuri ne dasu ba kamar uwarsu (Gwaggo) shi yasa haka nan suka biyo Inna gaje domim shigowa part d'in Hjy Sa'adar, ina cikin tunano abinda ya faru nima kaina banso shigowata shashinta ba dan kuwa izuwa yanzu bana tsoronta ko musuk'ala zarratin,
Ji nayi akwai magana a tsakiyar kaina wadda ita tasa ni katse tunanin dana fad'a Hjy Sa'adha take cewa "ku dakata daga nan ubanmai ya kawo ku part d'ina tsofaffin munafukai" ta idasa maganar tana mana kallon uku saura Haneefa zata maida mata martani da sauri Inna gaje ta girgiza mata kai alamar tayi shuru Inna gaje ta dawo da dubanta tace "haba baiwar Allah amarya ce muka kawo gata nan Amana" da sauri Hjy Sa'adha tace "aman har kunsan wata amana to bazan amsa ba nace bazan amsa ba tunkan raina ya k'ara b'aci ku fice min daga part" ta ida maganar tana nuna masu hanyar waje Dr Aysha kuwa dake zaune sai wani kallon banza take aika mata ta taso tana cewa "bakuji mita ce bane duk kun cika mana parlo da wari" cike da bak'in ciki Sakina dake huce da sauri Inna gaje da bata son fitina tace "karku yi magana ku wuce mu tafi kawai" juyowa mukai muna k'ok'arin fita mukaci garo dasu Maryam wani irin jan birki sukai suna mana wani kallon k'ask'anci ni kuwa da raina ke dagule ban tsaya ta kansu ba nayi shashina Maryam ce ta buga wani uban tsakin dana jishi har sakiyar kaina lallai waccan yarinyar saina saita manata zama ban dai juyoba nida Inna gaje danta lura fa ba kunyace dasu ba su Haneefa na niyar rab'a su su wuce kawai taji an bangaje ta ba kowa bace sai Ummeeta dake maka masu wata uwar harara da sauri Haneefa tace "ke baki kallon mutune ne ko salon rainin naku ne zaku nunawa mutane" ta ida maganar tana kallon su ido cikin ido Sakina kuwa murmushi mugunta tayi tana magana a zuci itace dai-daiku sauk'in ku baku tab'o ni ba da sai nabar yarinya kwance wallahi amma bari na ga wannan wasan ta idasa maganar zucin tana kallon yadda suke wani shan mur da sauri Ummeeta tace "dallah can dakata anje an bige kin ko kina da abinda zakiyi ne?" Kamin ma ta rufe bakinta taji saukar mari da sauri Ummeeta ta d'ago tana kallon Haneefa data zafga mata tafi tana cewa "kinga abinda zanyi Nan" Maryam dake huce zata kawo hannu dan Marin Haneefa da sauri Sakina ta rik'e hannun tace "karki sake karki fara dan kuwa wallahi duk wadda yayi gigin tab'a ta to k'ila sai uwarsa tayi jinyarsa" ta ida maganar tana kallonsu ganin yadda sukai tsuro-tsuro tsaki Haneefa taja tana kama hannun Sakina suka wuce.
Wani ashar Maryam ta dank'ara tace "wai ashe ku shashashu ne ban sani ba har ku tsaya haka ai sarkin yawa yafi sarkin k'arfi ai wallahi kamin nabar gidan nan sai nace uwar Khaleesat d'in nan" wani murmushin takai ci Hanan tayi tace "yanzu dai tunda ga abinda ya faru karma mu sake Aunty taji k'ila saita kusa dukanmu tace mun bayar da ita mi yasa bazamu yi masu dukan kawo wuk'a ba" tsaki Ummeeta taja zuciyar ta sai tafasa take lallai saita rama abinda tsamayan can sukayi mata lallai saita nuna masu ruwa ba sa'an gwando bane in bata rama ba kuwa k'ila bazata tab'a yafema kanta ba, ta ida maganar zuci tana wuce fuuuuu a zuciye shiga sukai su duka basu tadda kowa a parlon ba yasa kai tsaye suka wuce nasu d'akin.
Ganin su Haneefa suna shigowa part d'ina da murmushi yasa nasan sunyi maganinsu shi yasa na tafi hankalina kwance dan kuwa ni nasan y'an gidan namu, bayan sun d'an k'ara hutawa suka shirya jar wajan mota muka rako su sosai naji ba dad'in tafiyar su harda d'an matse hawaye Sakina ma duk jikinta yayi sanyi haka dai muka koma,
A parlon muka zauna da Sakina Anam na hannunta sai baccinta take labari ta d'akko min dan taga kamar inada damuwa ai danda nan na wartsake.
Can wajan dare ina d'akin Sakina data zab'a a k'asa Anam na kwance a jikinta na gama bata mama Sakina tace "please Khaleesat kisa fa rigar nan dana ce" tab'e baki nayi nace "ke Sakina wallahi bazan iya ba kinga yadda rigar take duk rabin jikin ka ana gani" tashi tayi zaune tace "amma Khaleesat kamar kin waye ashe baki waye ba haba kishiya face dake saifa kin dage inba hakaba sai dai kiga mijinki wajanta a haka da wannan kunyar taki zaki kwace mijin tab ai kuwa saikin cire ta wallahi" ta idasa maganar tana d'akko min rigar dole badan nasu ba nasa na d'ora hijab a kai da sauri tace "wani irin hijab zaki zakisa kuma?" Turo baki nayi da shagwabar data zame min jiki nace "innaje zanfa cire kuma kinga zai iya neman muje wajan matar sa zai tara mu ko?" "Ifa da wannan ke ni harma na mantawa dake da ita wallahi" cewar Sakina ni kuwa kallon Sakina nayi nace "Allah ya shirki yanzu fa kiga gama maganar ta" dariya mukai kawai, jin bud'ewar parlo yasa da sauri Sakina tace "kije kawai nikam gobe mun gaisa" tashi nayi jiki na a sanyaye na fito parlon ganin baya parlon nasan ya haura sama saman nahau zuciyata na tsananin ta bugawa shiga nayi d'akin da sallama a bakina jin k'arar ruwa a ban d'aki yasa nasan ya shiga wanka kenan bakin gadon na zauna, shu kuwa Bahbah ransa ne a b'ace ya shigo dan kuwa ya biya ta wajan Hjy Sa'adha ba irin cin fuskar da batai mai ba wulak'anci iri iri har cewa yayi zai tara so yanzu a part d'inta yayi masu nasiha wani kallo data yi mai tace "har kana da abinda zaka ce minne dan haka wallahi naga k'afar yarinyar can a part d'ina duk abinda nayi mata to kai ka saya da kud'in ka dan haka bana buk'atar wata nasiharka dan ba wani anfanin da zata min" sosai ransa ya b'aci baiyi magana ba ya juya yabar part d'in nata dan kuwa inya ce zaiyi magana to zai iya furta kalmar da zatayi dana sani, shi yasa yana shigo ya haura sama da sauri yana zuwa kawai ya shiga wanka, runtse idanuwansa yayi jin ya gama tunano irin abinda Hjy Sa'adha tayi masa ya fara gajiya da sabon halayan data d'akko tasama kanta mace har mace da amma yanzu ta koma sai a hankali jijjiga kansa yayi jin wani ciwon kai na neman kamasa da sauri yayi wankan yana fitowa d'aure da tawul da sauri na kauda kaina daga kallonsa wani miskilancin murmushi ya saki iya lab'b'ansa.
Wani irin masifaffan k'amshin sabulon wanka ke fita ta jikinsa a tsanake yake shiryawa ya shafa wannan ya mursa wannan a cikin zuciyata nace yo ba dole kullum fatarsa ke k'ara kyau ba, ga wasu irin turarika da yake murzawa ya shafa dandanan d'akin ya bud'e da wani irin k'amshi mai dad'in shak'a jallabiya yasa mai taushi gaske kai daka kalleta kasan kud'i sunyi kuka bansan ya zo kusa dani ba kawai naji ya kwanta a kan cinyata kansa a kan cinyata sosai nayi gabana ya fad'i domin ban saba jin irin wannan yanayin ba samun kaina nayi da shafa lallausan sumar kansa ina kallonsa yadda ya lumshe idonsa gashin idonsa zarara sun kwanta yadda kasan ya k'ara su sosai nake mamakin kyau da Allah yaba Bahbah duk shekarunsa amma kwata-kwata jikinsa bai nuna ba sai kace d'an shekara 30, shi kuwa sosai yake jin yadda nake shafa sumar kan nasa har wani bacci mai dad'i ya fara d'aukar sa can kuma ya bud'e idonsa yana watsasu kaina da sauri rantse idona dan kuwa kwata-kwata bana iya jurar kallon cikin idonsa murmushi ya saki da muryar sa mai dad'an sauraro ga wani irin taushi data k'ara na baccin daya fara d'aukar sa yace "please ki bud'e idonki ki kalli mijinki Mana" wani irin yanayi na cince kaina da muryar tasa ta sani turo baki nayi ina d'age kafad'a nufin bafa zan bud'e ba dariya yayi mai sauti yana shafa d'an k'aramin bakina da hannunsa wani irin masifaffan yanayi da nake shiga yasa dole na d'an bud'e idon nawa shi kuwa tashi yayi yana cewa "kina da alwalla" d'aga mai kai kawai nayi ga wank irin masifaffan tsoro daya d'irar min tashi nayi bayan yayo alwallar janmu yayi sallah raka'a biyu sosai ya dafe kaina yana kwararo addu'a sai da ya jima yana mana addu'a sana yayi min tabbayo game da addini sosai nanfa na saki jiki ina bashi amsa sosai yayi farin ciki bayan mun gama na gaji kawai yasa na hau gado shi kuwa kusa dani ya zauna yace "labari fa zamuyi" turo baki nayi a shagwabe nace "ni dai Allah bacci" wani irin masifaffan abu yaji har tsakiyar kansa, ya Allah wannan yarinyar data san yadda wannan shagwabar tata ke sani cikin wani yanayi tada rink'a d'agan k'afa ya fad'a a zuciyar sa ni kuwa dabansa wani yanayi yake ciki ba yasa na k'ara shagwabe ina tab'ara ni kuwa bandan komai nakeyi ba ya barni nayi bacci dama gani duk a tsorace kuma shagwabar ce a jinin jikina take.
Kashe fitila yayi yana kwanciya a kusa dani sai da yayi addu'a banyi saton ba naji ya rungume ni tsam a k'irjinsa sauke ajiyar zuciya mukai a tare da sauri ya yaye hijabin dake jikina yana rad'a min cewa "ba'a kwanar mai da kaya masu nauyi" ni kuwa ganin haka yasa na k'ara mak'alewa jikinsa ashe bansan wuta nake kunno mai ba k'ok'arin zare y'ar ficiciyar rigar dana sa yasa na rik'e hannunsa gam cike da wata shu'umar muryarsa wadda yasan zata kashe min jiki da ruhi "ki bari mana kinsan nace ba'a kwanar min da kaya ko" turo baki nayi ina sakin hannun nace "to ba kacire hijab d'in ba" cike da wani irin salon nasa yasan takan duk wani salo da zaisa mace zauce wa, dai-dai kunne na ya hura min wata irin iska yana cewa "to ki bari na cire Mana" bansan sadda ma ya cire rigar ba yana wurgi da ita da yasa na k'ara shige masa, shi kuwa jin wasu abubu masu taushin gaske a k'irjinsa yasashi fara sakin layi ni kuwa da bansan dawan garinba sai mutsu-mutsun nake a jikinsa bansan wannan motsin da nake yi ba wata wutar fitina nake taso mai.
Jin hannunsa nayi yana yawo a jikina yasa bansan sadda na gantsare ba wani irin numfashi ya sauke wani irin masifaffan yanayi nake jina a ciki wata duniyar da ban tab'a zuwa Bahbah kuwa ganin na fara amsar sak'o yasa yasa ya k'ara d'ora hannunsa a inda yasa numfashi na kamar zai d'auke k'irjina da suka ciko kamar bana shayarwa naji hannunsa a kai da yasa numshina gudu da sauri wani irin masifaffan k'aik'ayi naji a kansu banyi aune ba naji ya saka baki yana sha kamar k'ara min yaro sai dai shi nashi salon na dabanne bansan sadda na sakar mai kuka mai tafe da shagwaba ba dan kuwa jin abun nake bazan iya jurewa shi kuwa wannan kukan dana saki ashe wani abun na k'ara kunnowa ban sani ba muryata dake rawa nace "please Babahhhh kaminhhhh" a rarrabe nayi maganar dan kuwa muryata ta shak'e na kasa k'ara sa maganar jin yadda yake min cike da wata shu'umar murya yace "kina so nehhhhh" muryar tasa ce ta k'ara sanyani wani irin masifaffan yanayin da yasa na kasa magana kawai kawai na girgiza mai yace "please kibar mijinki ya rab'e ki" da sauri cikin shak'akkiyar murya nace "a'a bazan iya d'aukar wannan abun ba yafi girman kwakwalwata" wani shu'umin murmushi yayi yace "ai ko wacce mace da haka ta saba please kina so mala'uku suyi fushi dake" girgiza kaina nayi, jin k'arar wayarsa yasa ya saki tsaki d'an d'aga idona nayi ganin sunan dake yawo a cikin wayar yasani raina ya b'ace lallai ma wannan matar ta haka zata b'illo kuma zaikai hannu ya tab'a bansan sadda na had'e bakinmu waje d'aya ba ina aika mai da wani shu'umin kiss d'in daya sa shi zauce wa ni kaina bansan yadda na iya ba kawai shawar zuciyata nabi

Chapter 9 of 11