a hankali bane bagi dajiyar inace ke"...... Zata sake wata maganar sai dai mukaji k'arar mari har sau biyu mu duba rintse idanuwanmu mukai har Hjy Sa'adha dake so tayi magana da amma ji k'arar mari ya ankarar damu sai yanzu naji porlon ya ture da wani irin masifaffan kamshi d'agowa nayi na zubama mutunan da yayi wannan aiki ba kowa bane sai Alhaji Mustapha da dawowar shi kenan wannan bala'in da suke har motoci suka gama tsayawa bamu ji ba yana shigo yaga an d'auke wata da mari sosai yaji b'acin rai da marin baisan sadda ya k'araso ba yana d'auke Ummeeta da wani masifaffan mari wadda har saida ta fad'i da sauri su duka suka natsu dan kuwa baida wasa ko kad'an ba kad'an suke tsoronsa ba juyowa yayi saiti na mu dukanmu daga ni harshi zuciyoyinmu sukayi wata mahaukaciyar bugawa kallonsa nake kyakkyawa ne na k'arshe ana cewa wai inada kyau to yau naga wadda yaci ubana a kyau babban mutum karku ce wai yaro ne dan kuwa ya kai shekara 43-45 amma duk da shekarunsa hakan bai hana kyawunsa fitowa ba kwata-kwata saika rantse d'an shekara 30 ne jikinsa a murd'e yake da alama yana kula da jikinsa ga wani irin saje mai masifar kyau daya jagaye fuskar tashi mai masifar shek'i ga wani siririn hanci dogo daga k'asa yad'an bud'e kad'an ga d'an k'ara min bakinsa mai zanan love mai d'auke da jan leb'e shiba jaba shiba pick ba yana da tsawo sosai ingarman najimi ne na nunawa a sa'a dan kuwa banga laifin Hjy Sa'adha ba akan kishin da take a kansa wata irin murya naji mai masifar taushi da dad'in saurara yace "Sa'adha fa?" Yana nuna ni danya yayi mamaki shima da kyawuna dan baiyi zaton wai y'ar aiki bace da sauri Hjy Sa'adha dan ita ma ba k'ara min shakkarsa take ba tace "wallahi y'ar aiki ce" da sauri ya juyo yana kallo na y'ar aiki ya fad'a a zuciyar sa zama yayi kan kujera cike da izza da kyar ya iya bud'e bakinsa dan kuwa ya gaji sosai yace "to kuma dan y'ar aiki ce sai akace ko rink'a wulak'antata" ya ida maganar a tsawace yana nuna su Ummeeta da sauri su duka suka had'a baki wajan bashi hakuri har ita kanta Maryam d'in ba k'ara min tsoro yake bata ba amma k'arfin hali zuciyarta ta fad'a sonsa ya k'ara cewa "ai bani zaku ba hakuri ba ita zaku bawa" ya ida maganar ko a jikinsa kallon kallo suke wa junansu taya za'ai suba wannan hakuri kai haba ai..... Tunkan su ida maganar zucin da suke ya d'aga masu wata irin tsawa yace "ku bata hakuri nace sana ku fice min a nan" ya ida maganar yana tsare su da wa'innan idanun nasa masu matuk'ar haske da shek'i ai har suna rige-rigen cewa inyi hakuri ni kuwa cewa nake shikenan daga zuwanka zaka jamin bala'i ai nasan wallahi sai sun rama na ida maganar a zuci ina b'alla mai harara ta k'asan ido nima duk kwarjinin da yake min amma bana jin tsoronsa ko kad'an.
Su kuwa ganin baya kallonsu suka wuce da sauri suna sauke ajiyar zuciya Hjy Sa'adha kuwa itama a zuciyar ta cewa take ai gashi mai maganinku nan ya dawo sai kuma ta matsa kusa da shi tana k'ak'alo murshi dan kuwa taji haushin marin daya yima Ummeeta sai dai abinda yasa bazata d'auki mataki a kaina ba wannan k'udirin nata da take so ta cika a kaina kamin tayi magana yace ki had'a min ruwa zanyi wanka tashi tayi kawai tana nufar shashinsa.
Ni kuwa ganin dagani sai shi a porlon dan kuwa tun d'azo Asabe ta wuce yasa har ina hard'e k'afa sai da nazo dai-dai saitin sa na k'ara sakar mai harara na wuce da sauri zuciyar na wata irin masifaffiyar bugawa k'arfin hali ne kawai shi kuwa bina yayi da kallo baima sani ba ta k'asan ido gani yayi ina tafiya kamar da gayya duk wasu halinton jikina motsawa suke ina gaf da shigewa d'an kwalina ya sub'oce gashi na mai sulb'i ya zube bak'ik'k'irin dashi da sauri ya kauda idonsa daga kallo na yana mamakin irin halitar da Allah ya zuba min gashina nane yafi basa mamaki Anya kuwa nata ne yana k'ara mamakin cewa wai y'ar aiki ce ni kwata-kwata bata dace da y'ar aiki ba tsaki ya d'an ja yana jin haushin zuciyar sa miye ma na tunani na to...........✍️
*FATEEMAH RABI'U (ZAHRA ROYAL STAR CE)*🥰✍️
Comment and share Fisabilillahi🥰🙏
[9/6, 10:00 AM] ZAHRAH ROYAL STAR 🥰: *🤦♀️💔ITA CE K'ADDARATA 🤦♀️💔*
*©ZAHRA ROYAL STAR CE*🌟✍️
*ROYAL STAR WRITIN'S ASSOCIATION*
PAGE2️⃣7️⃣➡️2️⃣8️⃣
"Yanzu Zuby kinji fa abinda yake faruwa shi yasa ma nace ina son ganinki" ta ida maganar tana kallon Zuby da zuwanta kenan gyara zama Zuby tayi tana d'an tunani can tace "hmm lallai da kuwa kinsa k'afa kin fita zaifa iya yimiki komai wallahi har yanzu wai baki fahimci halin maza bane yanzu dai abinda nake so dake shine ki fara shiri da waccar matar Gwaggo suke ce mata komi ki lallab'a ta kinga akwai bikin da zamuyi kibar fitar yanzu zuwa k'arshen watan nan kinga ya kusa tunda yanzu tsakiyar wata muke kiyi hakuri zuwa lokacin sai ki tafi da Sakina ko Haneefa bikin inya so ai dai bazai zarge ki ba sai mu wuce daga can kinsan bokan nan baya wasa dan ko rako kaji saiya had'a dakai shi yasa dole mutum yaje da kansa bawai aike ba" Narna kuwa sauke ajiyar zuciya tayi mai nauyi tace "amma gaskiya Zuby bazan iya shigewa waccan matar ba haba bafa mutumci ne da ita ba y'ar masifa ce da kike ganinta gara ma dai da ace Gaje tana da yara ne sai tafi da d'aya sai dai inzan tafi shi Malam d'in nayi mai dabara yaban d'aya daga cikin su" tashi Zuby tayi tana d'an gyara d'an kwalinta tace "tace ai yadda kika gani dai kidai kauda duk wani zargi dazai miki" nan suka ci gaba da tattauna abunda suke son cimmawa.
KANO
Jin haushin zuciyar sa miye ma na tunanin na to.
Sakkowar Hjy Sa'adha tana k'ara sowa kusa dashi cike da wani irin sonsa tace " na had'a Y'allabai da yake haka take kiransa dashi shi kuwa yana ce mata Fulani, murmushi ya sakar mata yace "Fulani naga yau kina cikin farin ciki miye sirrin ne?" Ya idasa maganar cike da wata shu'umar muryarsa mai kashe mata jiki kai bama ita ba duk wacce akai ma magana da irin wannan muryar saita shiga wani hali numshi idanuwanta tayi cikin sanyin murya tace "kai Y'allabai kana so ka rud'a ni daga dawowar kafa" wani murmushi ya saki maisa da yawa y'an mata zauce wa yace "ke dai dama a k'agare kike na dawo" yana d'aga mata gira da sauri ta tashi cike da tsantsar son mijin nata tace "farin cikin dawowar kane sai kuma bari dai saika huta ina so muyi magana dakai kaji mijina" tashi yayi yace "to da alama wannan tattaunawar mai mahimmanci ce zamuyi" yana tafiya yana haurawa sama, harya wuce tana binsa da kallo yadda yake tafiya cike da k'asaita sauke ajiyar zuciya tayi duk numfashin da zatai yana fitowa ne cike da k'aunar mijin nata.
Saida ta kira Asabe ta kwashe kayan dake kan darning d'in ta goge ko ina sana aka jere wasu,
K'amshinsa kawai tasan ya sakko wani irin masifaffan kamshi yake tashi a jikinsa d'agowa tayi tana kallonsa yanzu sanye yake da wani farin yadi mai taushi yayi mai wani irin sihirintaccan kyau mai tafiyar da zuciya harya iso bata sani ba saida yasa y'an yatsu sa yana rufe mata ido yana d'aga mata gira yace "yaya dai ko kin kyasa ne?" Dariya tayi tace "sosai ma kuwa mijina a gaskiya kullum in zaka fita wallahi gaba na har fad'uwa yake fa" ta ida maganar cike da tsantsar kishinsa shi kuwa idasawa yayi yana zama kan darning d'in yana mamakin tsananin kishinta sun manyanta amma bazata daina kishi ba.
Ni kuwa dake gaf da fitowa dan zuwa kiran su Maryam nasan dai nufin Kiran nasu yau Allah ne kad'ai yasan mi zasu min nazo fitowa naga irin yadda yake zuba Soyayya koni kaina sun matuk'ar birgeni ji nayi inama nice Hjy Sa'adha tsakani harga Allah tayi dacen samun miji na nuna a ko ina ne ma kauda zancan nayi inama zuciyata fad'an bazata tab'a samun irin wannan ba har lokaci yad'an ja ban sani cike da fargaba na nufi shashin su koda na isa ko wanne da d'akinsa to wanne zan fara shiga ne jin hayaniya a d'ayan d'akin yasa na tura na shiga idanuwa suka zuba min cike da tsana ni kuwa duk sai naji wani iri na tsani wulak'anci da sauri Maryam wadda tafi kowa tsanata tace "zaki shigo koko munafirci zaki tsaya ne" da sauri na idasa ina duk'awa k'asa nace "gani" da sauri Ummeeta itama cikin fushin marin da akai mata da bata gama hucewa ba tace "harke zakiyi sana diyyar Barbah ya bige ni(haka suke kiransa dashi) ke a wa" tayi maganar a tsawace ta k'ara cewa maza-maza tashi duk sai kin gyara d'ako nan dan uwar..... Tunkan ta idasa na tashi tsaye zunbur duk kallo na suke tashi sukai Maryam data fi kowa d'aukar zafi tace "ance uwar taki mi zakiyi naga kin tashi tsaye mi zaki iyayi?" Ta ida maganar tana matsoni kamar zata dake ni da sauri na nunata da yatsa nace "karki sake ki k'ara zagar min uwa" ina kallonta ido cikin ido su duka mamaki ne ya kashe su rashin kunyar tawa harta kai haka "au lallai yarinya idonki yakai tsaiko ni zaki kalla kina gayama wannan maganar" d'aga hannu tayi nufin ta mare ni taji an rik'e hannun ba kowa bace sai Hjy Sa'adha tana kallonta tace "anya kuna da hankali kuwa yanzu baccin nace ma Y'allabai sadda yaga Khaleesat na shigowa part d'inku da biyota zaiyi yaga miye dalilinku na kiranta da ya zo ya tadda abunda kuke shirin aikatawa mi kuke tunanin zai faru ke da yau inaga Maryam da kinbar gidan nan kun dai san baya son wulak'ancin nan da kuke ko?" Ta ida maganar tana kallonsu da sauri Ummeeta tace "amma Aunty kina ganin yarinya zata rainamu kibarta mu koya mata hankali" "ko kuma ko ta koya muku ko" cewar Hjy Sa'adha da sauri ta waigo waje na da d'an haushi na da mijinta taga halama ya fiye shiga harkar yarinyar tace "ke kuma banda abunki kiba kowa ba in kinyi rashin kunyar miye ribarki ki tabbatar kiyi masu aikin kamin ki fito" ni kuwa wasu irin hawaye ne suka cika min ido ni ba kowa bace kware kuwa amma bazan tab'a bari a rink'a zagar min uwa da bata raye in kyale ina maganar a zuci ji nayi ta k'ara cewa "ku kuma ku kiyaye" tana ida maganar ta fice tsaki sukaja suna zama Ummeeta tace "to marar kunya kin wani tsaya mana a kai zaki wuce kiyi aikin da aka saki ko kowa".
Tana fitowa ta saki murmushi yace "yadai Fulani" da sauri tace "a'a ba wani abu bane ai kasan suna jin maganarka" murmushi ya saki kawai yana girgiza kai dan kuwa yasan halinsu su duka har ita Maryam d'in yasan miyasa take zaune gidansa sai dai ya zuba masu ido kawai har ita Fulanin da bata gane mai sunta da wadda bai k'aunar ta da sauri ta matsa kusa dashi tace "yauwa Y'allabai kaji maganar da mukeyi fatan zaka bari naje Abujar bikin wata k'awata ake tare zamuje da Dr Aysha" ta ida maganar tana kallonsa ganin irin kallon da yake mata kamar na tuhuma sai kuma duk ta rud'e tayi k'asa da kanta..............✍️
*FATEEMAH RABI'U (ZAHRA ROYAL STAR CE)*🥰✍️
Comment and share Fisabilillahi🥰🙏
[9/7, 12:11 PM] ZAHRAH ROYAL STAR 🥰: *🤦♀️💔 ITA CE K'ADDARATA 🤦♀️💔*
*©ZAHRA ROYAL STAR CE*🌟✍️
*ROYAL STAR WRITIN'S ASSOCIATION*
PAGE2️⃣9️⃣➡️3️⃣0️⃣
DA SUNAN ALLAH MAI RAHMA MAI JIN K'AI
__________________✍️Tun daga wannan lokacin Narnah ta fara shige masu su duka har Inna gaje sai dai sun san abinda suke yi bare Gwaggo data san duniyanci kallonta kawai take ta zuba mata ido ne kawai taga iya gudun ruwanta.
Kamar yauma tafe take ta nufi d'akin Malam dan kuwa bikin nasu ya tahu yau baifi saura kwana hud'u kuma ana uku take son su tafi,
Shiga tayi d'akin Malam d'in ta tadda shi shida Inna gaje gaisawa sukayi sama-sama dan kuwa taji haushin tadda Inna gaje taso ace shi kad'ai ta tarar zaunawa tayi tace "Malam dama ina son magana dakai ne" aje abinda yakeyi yayi yana kallonta yace "ina jinki" da sauri Inna gaje ta tashi domin basu waje da sauri Malam ya tsayar da ita da cewa "dawo ki zauna" kallonsa ta d'an yi tace "magana zaku fa na sani kota sirri ce" "a'a ki dawo ki zauna nace" cewar Malam Inna gaje kuwa dawowa tayi ta zauna badan taso ba dan kuwa taba son shiga harkar kowa inba dole ba.
Narna kuwa wani irin bak'in ciki ne rufeta a zuci take cawa lallai anya kuwa duk shirin dataiwa Malam bai riga da ya kare ba dole wannan yafiya ta dawo da shiri sosai katse mata tunani yayi da cewa "ke nake saura fa inada abinyi" gyara zama tayi tace "dama Malam biki ne gare mu shine nazo gayama gobe ne nake son tafiya shine nace ko zaka had'a ni da Haneefa ko Sakina sai mu tafi tare" ta ida maganar tana kallonsa ganin irin kallon da yake mata gyara zama yayi yana murmushi a zuci yace yadai fi miki dan kuwa dake kad'ai ce wallahi baki zuwa sai kuma a fili yace "Eh to zaku iya tafiya amma ki tabbatar duk inda inba inda ya shafi bikin ba to bada yawuna ba" da sauri ta d'ago tana kallonsa ganin shi ko a jikinsa tashi tayi tana maganar zuci ai wallahi baka isa hanani fita ba mudai je bikin tukun amma gani ma can naje wajan boka ta ida maganar zucin tana ficewa a d'akin.
Inna gaje kuwa girgiza kai tayi tana cewa a zuci anya kuwa Malam bai d'akko rigima ba taya za'ai Gwaggo tabar d'iyarta tabi wannan matar amma abinda ba ruwanka dad'in kallo ne dashi katse mata tunani yayi da cewa "inkin fita ki kira min y'ar uwar taki" amsawa tayi da "to".
Kai tsaye d'akin Gwaggo ta nufa shiga tayi ta taddasu suna zaune ba laifi yanzu kam suna d'an shiri Inna gaje tace "Gwaggonsu kije inji Malam yana son magana dake" da sauri Gwaggo tace "to ko lafiya kuwa" "to inkinje dai kyaji" cewar Inna gaje tana ficewa daga d'akin ta nufi d'akin ta su Haneefa kuwa suka ce "kije kiji kawai" tashi tayi ta nufi d'akin Malam d'in da sallama ta shiga bayan ta zauna fuskar sa ba wasa ko kad'an itama ganin haka yasa ta bada hankalin ta yace "dama dalilin kirakin shine ina so ko Haneefa ko Sakina d'aya ta shirya zasu raka Narnah can garinsu Dutse biki" ya ida maganar cike da bada umarni da sauri Gwaggo ta d'ago tana kallonsa cike da mamaki da masifar dake taso mata duk da taga fuskar shi ba wasa cike da k'arfin hali ta bud'e baki tace "haba Malam kamar ya kafa san wannan matar bafa wani shiri nake da ita ba kuma sai ace na d'au d'iya ta na bata su tafi wata uwa duniya" kallon ta yayi ba wasa ya k'ara shan mur yace "umarni ne na bada na gama magana zaki iya tashi kiban waje" tashi tayi cike da bak'in ciki a zuciyarta ita Narnah zata kullawa wannan munafurcin.
Su Haneefa dake zaune ganinta ta dawo a hargitse da sauri har suna had'a baki wajan cewa "Mama lafiya dai" "wai ni waccar y'ar banzar bak'ar matar zata ma haka" cewar Gwaggo da sauri Sakina tace "wai Mama wacce mata?" Gwaggo a tsawace tace "Matar Ubanku mana wai na bata d'aya daga cikin ku wai biki zata" sakin baki sukai suna kallonta sai kuma can Haneefa tace "to Mama miye abun tada hankali ai dai da wayanmu kawai kisa a ranki da abinda take shirin yi ne shi yasa amma ko tatai damu ta isa tayi mana wani abunne" Sakina kuwa tab'e baki tayi dan ita yanzu bata fiye shiga harkar gidan nasu ba Gwaggo kuwa zama tayi tace "hakane amma sai dai inke kije dan duk abinda ya faru zaki sanar dani amma wannan y'ar uwar taki Sakina da zuwanta ma gara babu" ta ida maganar tana wuraga Sakina harara Sakina kuwa bata damuwa ba tace "ni dama Mama wallahi banda lafiya gara dai Haneefar taje" Gwaggo tace "ke dai kika sani saiki tashi ki shirya wai gobe ne tafiyar".
KANO
Ta ida maganar tana kallonsa ganin irin kallon da yake mata kamar na tuhuma sai kuma duk ta rud'e tayi k'asa da kanta da kyar ya bud'e baki cike da Miskilanci yace "kuma dole akace sai da wannan y'ar aikin zaku (Khaleesat)?" "Ai ta tayi ni wasu abubuwan a can ko bafa dad'ewa zamuyi ba fa Y'allabai" ta ida maganar tana kallonsa da d'an murmushi a fuskar ta shi kuwa yace "to shikenan Allah ya kaimu sati mai zuwa amma zuwa gobe ko jibi zanyi wata tafiya amma ranar zan dawo zanje katsina ne" wata irin masifaffiyar bugawa da fad'uwar gaba ce ta riski Hjy Sa'adha data rasa dalili jin ya ambaci Katsina da sauri tace "amma Y'allabai mi zakaje yi ne?" Kallon yake ya sakar mata murmushin nan nasa yace "wani abu ne mai mahimmanci a gare ni kema kuma zaki sani nan bada dad'ewa ba zan miki Albishir dashi" kallonsa take ita dai wannan Tafiyar Allah wallahi bata kwanta mata ba shi kuwa magana yake a zuci anya wannan abun da yake shirinyi bazai d'akkowa kansa rigima ba amma dai zai san yadda zai b'ullowa al'amarin.
Ni kuwa da nake zaune dawowa kenan da gama aikin su Ummeeta duk jikina ciwo yake dan mugunta saida na gyara duka d'akunan su harda mai-maitawa gashi d'azo nake jin fad'uwar gaba na rasa dalili har kiran gida nayi da wayar da Inna gaje taban kafin na taho muka gaisa da Inna gaje har taba Sakina muka sha fira haka shima Abba muna waya dashi yana tabbayata akwai matsala ban tab'a gaya mai wane irin hali nake cika ba duk inna kira Abba sai rink'a min nasiha na rasa wacce iri ce.
Shirye-shirye muke sosai ta zuwa Abuja da aka gaya min wai dani za'a Abuja nayi murna domin kuwa ban tab'a zuwa ba su Ummeeta sai dariya suke min wai y'ar k'auye zata Abuja nidai ban damu ba dan takai nama nake haka nan ina zaune kamar yauma saura kwana biyu mu tafi inda yaune Alhaji Mustapha ya nufi katsina tunda safe wajan k'arfe d'aya dai-dai ina zaune kawai naji wata irin masifaffiyar bugawar zuciya da wani irin nauyi naji ya hau kaina shin na miye hakan kawai bansan miya sa ba na saki kuka da sauri Asabe dake kusa dani ta matsoni tace "anya lafiyar ki kuwa Khaleesat tun jiya naga yanayink duk ya sauya?" Ta ida maganar tana kallon yadda nake kuka marar dalili da shashshakar kuka nace "wallahi Asabe tun jiya nake jin wani iri a zuciyata rabona da jin haka tun sadda za'a kawo ni nan kukanne kawai zai sani naji sanyi" cike da tausayi tace "tashi kiyi alwalla ki karanta Al'k'urani Insha Allah ba abinda zai faru sai alkhairi" kamar yadda tace haka nayi tabbas na samu sanyi a zuciya amma dai kwata-kwata banjin dad'in duniyar gaba d'aya.
Can wajan dare Alhaji Mustapha ya dawo bayan yayi wanka ya sakko k'asa ganin Hjy Sa'adha zaune kan kujera tana tunani ita kanta tunda ya tafi Katsinar nan gabanta keta fad'uwa kwata-kwata duk yau bata jin dad'in jikinta ganin ya dawo lafiya kuma saita jiki ranta tace "bari nasa a jera abinci ko?" Amsawa yayi kawai da kai yana danna computer kiranmu tayi muna zaune da Asabe da sauri muka tashi muka fara jera abincin kan darning d'in duk sadda zan wuce ta gabansu muke wucewa sai na rink'a jin ana kallo na d'agowa nayi karaf idona ya sark'afe da nasa wani irin mukaji mu duka dagani harshi b'allamai harara nayi da sauri ya ware ido yana min nuni da ido cewar ni kike harara lallai yarinyar can bata tsoronsa fa sai kuma ya saki murmushi ya rasa dalili yarinyar na sashi nishad'i ni kuwa da sauri na dukar da kaina ina wucewa d'akin mu da sauri kuma Hjy Sa'adha tace "yau Khaleesat kifa shirya gobe da wuri jirginmu zai tashi" cike da d'oki nace "to Insha Allah" dan kuwa ban tab'a hawa jirgi ba amma zan hau sadda na ida d'aki wani tsallan murna na buga inka kalleni saika yi zaton cewa yanzu ba wata damuwa dake damuna sai dai can k'asan zuciyata wani irin nauyi nake ji dama ni tuni na had'a kayana tuni.
Can wajan Alhaji Mustapha kuwa shi wallahi yama manta da wata tafiya jin an anbaci tafiya sai gabansa yad'an fad'i kwata-kwata tafiyar bai yarda da ita ba amma ba yadda zaiyi tunda ya riga da yace su tafi ganin yanayinsa ya canza yasa Hjy Sa'adha tace "ya dai Y'allabai naganka wani iri" gyara zama yayi yace "ba komai kawai dai harna fara kewarki ne tafiyar nan da zakiyi" ya idasa maganar dan kar ta gane ma akwai wani abu cike da son mijinta tace "ayya ai ba wani dad'ewa zanyi ba mijina". Nan dai suka ci abinci bayan sun gama ta haura sama ta basa waje yana wani aiki a computer.
Koda ta shiga d'akin nata bakin gado ta zauna tana kiran Dr Aysha bayan ta d'auka tace "Dr kifa shirya kinsan jirgin k'arfe tara ne kuma fatan an shirya komai?" Dr Aysha daga cikin wayar tace "Eh munyi waya da shi likitan da zaiyi aikin yace min an riga da an shirya komai mu kad'ai ake jira goben da mun isa za'a yi komai tunda ba wahala ne dashi ba maganar shiryawa da wuri kuma kinsanni bana wasa da lokaci" "Okay shikenan na kuwa sani amma kinsan Dr wallahi tun jiya nake jin zuciyata ba dad'i fa" cewar Hjy Sa'adha daga cikin wayar Dr Aysha tace "haba ki kwantar da hankalinki ba wani abu" ita Dr Aysha ta zata akan abinda zasuje yi ne, Sauke ajiyar zuciya Hjy Sa'adha tayi sukai sallama akan cewa su had'u a filin jirgi zuwa goben................✍️
*Shin miye Khaleesat take ji game da Alhaji Mustapha ne? Miye dalilin zuwan Alhaji Mustapha Katsina ne? Mi yake shiryawa ne? Wane Albishir ne zaiwa Hjy Sa'adha? Mi yasa Hjy Sa'adha take jin ba dad'i game da zuwan Alhaji Mustapha Katsina ne?*
To nima dai masoya na ina buk'atar jin miye dalili🤔🤓
*FATEEMAH RABI'U (ZAHRA ROYAL STAR CE)*🥰✍️
Comment and share Fisabilillahi🥰🙏
[9/8, 11:12 AM] ZAHRAH ROYAL STAR 🥰: *🤦♀️💔ITA CE K'ADDARATA 🤦♀️💔*
*©ZAHRA ROYAL STAR CE*🌟✍️
*ROYAL STAR WRITIN'S ASSOCIATION*
PAGE3️⃣1️⃣➡️3️⃣2️⃣
DA SUNAN ALLAH MAI RAHMA MAI JIN K'AI
___________________✍️Washe gari kuwa tunda safe Narnah ta aika kiran Haneefa domin su tafi ba yabo ba fallasa suka gaisa sunzo tafiya Gwaggo ta fito tana cewa "Haneefa ki tabbatar kin rik'e addu'a shirrin mutum ko aljan ya koma ma kowa" ta ida maganar tana kallon Haneefa cike da jin wani iri Narnah tace "Haba dai sai kace kinba wata bare d'iyarki?" "Yo wani lokacin ma ba gara baran ba da wani na kusa da kai d'in" cewar Gwaggo ita dai Narnah bata k'ara tankawa ba dan kuwa tasan abinda ta taka dan kuwa ita basu Haneefar ne a gabanta ba ta mallaki Malam shine burinta kawai.
Bayan sunje sunyi ma Malam sallama suka kama hanya ba laifi tana sakarma Haneefa fuska itama da take Haneefar ba wani damuwa tayi da itaba illama haushi da take bata haka dai suka isa garin Dutse bata yadda ta sauka a gidansu saita sauka a gidan Zuby ba laifi gidan Zuby sai dai ace akwai
Su kuwa ganin baya kallonsu suka wuce da sauri suna sauke ajiyar zuciya Hjy Sa'adha kuwa itama a zuciyar ta cewa take ai gashi mai maganinku nan ya dawo sai kuma ta matsa kusa da shi tana k'ak'alo murshi dan kuwa taji haushin marin daya yima Ummeeta sai dai abinda yasa bazata d'auki mataki a kaina ba wannan k'udirin nata da take so ta cika a kaina kamin tayi magana yace ki had'a min ruwa zanyi wanka tashi tayi kawai tana nufar shashinsa.
Ni kuwa ganin dagani sai shi a porlon dan kuwa tun d'azo Asabe ta wuce yasa har ina hard'e k'afa sai da nazo dai-dai saitin sa na k'ara sakar mai harara na wuce da sauri zuciyar na wata irin masifaffiyar bugawa k'arfin hali ne kawai shi kuwa bina yayi da kallo baima sani ba ta k'asan ido gani yayi ina tafiya kamar da gayya duk wasu halinton jikina motsawa suke ina gaf da shigewa d'an kwalina ya sub'oce gashi na mai sulb'i ya zube bak'ik'k'irin dashi da sauri ya kauda idonsa daga kallo na yana mamakin irin halitar da Allah ya zuba min gashina nane yafi basa mamaki Anya kuwa nata ne yana k'ara mamakin cewa wai y'ar aiki ce ni kwata-kwata bata dace da y'ar aiki ba tsaki ya d'an ja yana jin haushin zuciyar sa miye ma na tunani na to...........✍️
*FATEEMAH RABI'U (ZAHRA ROYAL STAR CE)*🥰✍️
Comment and share Fisabilillahi🥰🙏
[9/6, 10:00 AM] ZAHRAH ROYAL STAR 🥰: *🤦♀️💔ITA CE K'ADDARATA 🤦♀️💔*
*©ZAHRA ROYAL STAR CE*🌟✍️
*ROYAL STAR WRITIN'S ASSOCIATION*
PAGE2️⃣7️⃣➡️2️⃣8️⃣
"Yanzu Zuby kinji fa abinda yake faruwa shi yasa ma nace ina son ganinki" ta ida maganar tana kallon Zuby da zuwanta kenan gyara zama Zuby tayi tana d'an tunani can tace "hmm lallai da kuwa kinsa k'afa kin fita zaifa iya yimiki komai wallahi har yanzu wai baki fahimci halin maza bane yanzu dai abinda nake so dake shine ki fara shiri da waccar matar Gwaggo suke ce mata komi ki lallab'a ta kinga akwai bikin da zamuyi kibar fitar yanzu zuwa k'arshen watan nan kinga ya kusa tunda yanzu tsakiyar wata muke kiyi hakuri zuwa lokacin sai ki tafi da Sakina ko Haneefa bikin inya so ai dai bazai zarge ki ba sai mu wuce daga can kinsan bokan nan baya wasa dan ko rako kaji saiya had'a dakai shi yasa dole mutum yaje da kansa bawai aike ba" Narna kuwa sauke ajiyar zuciya tayi mai nauyi tace "amma gaskiya Zuby bazan iya shigewa waccan matar ba haba bafa mutumci ne da ita ba y'ar masifa ce da kike ganinta gara ma dai da ace Gaje tana da yara ne sai tafi da d'aya sai dai inzan tafi shi Malam d'in nayi mai dabara yaban d'aya daga cikin su" tashi Zuby tayi tana d'an gyara d'an kwalinta tace "tace ai yadda kika gani dai kidai kauda duk wani zargi dazai miki" nan suka ci gaba da tattauna abunda suke son cimmawa.
KANO
Jin haushin zuciyar sa miye ma na tunanin na to.
Sakkowar Hjy Sa'adha tana k'ara sowa kusa dashi cike da wani irin sonsa tace " na had'a Y'allabai da yake haka take kiransa dashi shi kuwa yana ce mata Fulani, murmushi ya sakar mata yace "Fulani naga yau kina cikin farin ciki miye sirrin ne?" Ya idasa maganar cike da wata shu'umar muryarsa mai kashe mata jiki kai bama ita ba duk wacce akai ma magana da irin wannan muryar saita shiga wani hali numshi idanuwanta tayi cikin sanyin murya tace "kai Y'allabai kana so ka rud'a ni daga dawowar kafa" wani murmushi ya saki maisa da yawa y'an mata zauce wa yace "ke dai dama a k'agare kike na dawo" yana d'aga mata gira da sauri ta tashi cike da tsantsar son mijin nata tace "farin cikin dawowar kane sai kuma bari dai saika huta ina so muyi magana dakai kaji mijina" tashi yayi yace "to da alama wannan tattaunawar mai mahimmanci ce zamuyi" yana tafiya yana haurawa sama, harya wuce tana binsa da kallo yadda yake tafiya cike da k'asaita sauke ajiyar zuciya tayi duk numfashin da zatai yana fitowa ne cike da k'aunar mijin nata.
Saida ta kira Asabe ta kwashe kayan dake kan darning d'in ta goge ko ina sana aka jere wasu,
K'amshinsa kawai tasan ya sakko wani irin masifaffan kamshi yake tashi a jikinsa d'agowa tayi tana kallonsa yanzu sanye yake da wani farin yadi mai taushi yayi mai wani irin sihirintaccan kyau mai tafiyar da zuciya harya iso bata sani ba saida yasa y'an yatsu sa yana rufe mata ido yana d'aga mata gira yace "yaya dai ko kin kyasa ne?" Dariya tayi tace "sosai ma kuwa mijina a gaskiya kullum in zaka fita wallahi gaba na har fad'uwa yake fa" ta ida maganar cike da tsantsar kishinsa shi kuwa idasawa yayi yana zama kan darning d'in yana mamakin tsananin kishinta sun manyanta amma bazata daina kishi ba.
Ni kuwa dake gaf da fitowa dan zuwa kiran su Maryam nasan dai nufin Kiran nasu yau Allah ne kad'ai yasan mi zasu min nazo fitowa naga irin yadda yake zuba Soyayya koni kaina sun matuk'ar birgeni ji nayi inama nice Hjy Sa'adha tsakani harga Allah tayi dacen samun miji na nuna a ko ina ne ma kauda zancan nayi inama zuciyata fad'an bazata tab'a samun irin wannan ba har lokaci yad'an ja ban sani cike da fargaba na nufi shashin su koda na isa ko wanne da d'akinsa to wanne zan fara shiga ne jin hayaniya a d'ayan d'akin yasa na tura na shiga idanuwa suka zuba min cike da tsana ni kuwa duk sai naji wani iri na tsani wulak'anci da sauri Maryam wadda tafi kowa tsanata tace "zaki shigo koko munafirci zaki tsaya ne" da sauri na idasa ina duk'awa k'asa nace "gani" da sauri Ummeeta itama cikin fushin marin da akai mata da bata gama hucewa ba tace "harke zakiyi sana diyyar Barbah ya bige ni(haka suke kiransa dashi) ke a wa" tayi maganar a tsawace ta k'ara cewa maza-maza tashi duk sai kin gyara d'ako nan dan uwar..... Tunkan ta idasa na tashi tsaye zunbur duk kallo na suke tashi sukai Maryam data fi kowa d'aukar zafi tace "ance uwar taki mi zakiyi naga kin tashi tsaye mi zaki iyayi?" Ta ida maganar tana matsoni kamar zata dake ni da sauri na nunata da yatsa nace "karki sake ki k'ara zagar min uwa" ina kallonta ido cikin ido su duka mamaki ne ya kashe su rashin kunyar tawa harta kai haka "au lallai yarinya idonki yakai tsaiko ni zaki kalla kina gayama wannan maganar" d'aga hannu tayi nufin ta mare ni taji an rik'e hannun ba kowa bace sai Hjy Sa'adha tana kallonta tace "anya kuna da hankali kuwa yanzu baccin nace ma Y'allabai sadda yaga Khaleesat na shigowa part d'inku da biyota zaiyi yaga miye dalilinku na kiranta da ya zo ya tadda abunda kuke shirin aikatawa mi kuke tunanin zai faru ke da yau inaga Maryam da kinbar gidan nan kun dai san baya son wulak'ancin nan da kuke ko?" Ta ida maganar tana kallonsu da sauri Ummeeta tace "amma Aunty kina ganin yarinya zata rainamu kibarta mu koya mata hankali" "ko kuma ko ta koya muku ko" cewar Hjy Sa'adha da sauri ta waigo waje na da d'an haushi na da mijinta taga halama ya fiye shiga harkar yarinyar tace "ke kuma banda abunki kiba kowa ba in kinyi rashin kunyar miye ribarki ki tabbatar kiyi masu aikin kamin ki fito" ni kuwa wasu irin hawaye ne suka cika min ido ni ba kowa bace kware kuwa amma bazan tab'a bari a rink'a zagar min uwa da bata raye in kyale ina maganar a zuci ji nayi ta k'ara cewa "ku kuma ku kiyaye" tana ida maganar ta fice tsaki sukaja suna zama Ummeeta tace "to marar kunya kin wani tsaya mana a kai zaki wuce kiyi aikin da aka saki ko kowa".
Tana fitowa ta saki murmushi yace "yadai Fulani" da sauri tace "a'a ba wani abu bane ai kasan suna jin maganarka" murmushi ya saki kawai yana girgiza kai dan kuwa yasan halinsu su duka har ita Maryam d'in yasan miyasa take zaune gidansa sai dai ya zuba masu ido kawai har ita Fulanin da bata gane mai sunta da wadda bai k'aunar ta da sauri ta matsa kusa dashi tace "yauwa Y'allabai kaji maganar da mukeyi fatan zaka bari naje Abujar bikin wata k'awata ake tare zamuje da Dr Aysha" ta ida maganar tana kallonsa ganin irin kallon da yake mata kamar na tuhuma sai kuma duk ta rud'e tayi k'asa da kanta..............✍️
*FATEEMAH RABI'U (ZAHRA ROYAL STAR CE)*🥰✍️
Comment and share Fisabilillahi🥰🙏
[9/7, 12:11 PM] ZAHRAH ROYAL STAR 🥰: *🤦♀️💔 ITA CE K'ADDARATA 🤦♀️💔*
*©ZAHRA ROYAL STAR CE*🌟✍️
*ROYAL STAR WRITIN'S ASSOCIATION*
PAGE2️⃣9️⃣➡️3️⃣0️⃣
DA SUNAN ALLAH MAI RAHMA MAI JIN K'AI
__________________✍️Tun daga wannan lokacin Narnah ta fara shige masu su duka har Inna gaje sai dai sun san abinda suke yi bare Gwaggo data san duniyanci kallonta kawai take ta zuba mata ido ne kawai taga iya gudun ruwanta.
Kamar yauma tafe take ta nufi d'akin Malam dan kuwa bikin nasu ya tahu yau baifi saura kwana hud'u kuma ana uku take son su tafi,
Shiga tayi d'akin Malam d'in ta tadda shi shida Inna gaje gaisawa sukayi sama-sama dan kuwa taji haushin tadda Inna gaje taso ace shi kad'ai ta tarar zaunawa tayi tace "Malam dama ina son magana dakai ne" aje abinda yakeyi yayi yana kallonta yace "ina jinki" da sauri Inna gaje ta tashi domin basu waje da sauri Malam ya tsayar da ita da cewa "dawo ki zauna" kallonsa ta d'an yi tace "magana zaku fa na sani kota sirri ce" "a'a ki dawo ki zauna nace" cewar Malam Inna gaje kuwa dawowa tayi ta zauna badan taso ba dan kuwa taba son shiga harkar kowa inba dole ba.
Narna kuwa wani irin bak'in ciki ne rufeta a zuci take cawa lallai anya kuwa duk shirin dataiwa Malam bai riga da ya kare ba dole wannan yafiya ta dawo da shiri sosai katse mata tunani yayi da cewa "ke nake saura fa inada abinyi" gyara zama tayi tace "dama Malam biki ne gare mu shine nazo gayama gobe ne nake son tafiya shine nace ko zaka had'a ni da Haneefa ko Sakina sai mu tafi tare" ta ida maganar tana kallonsa ganin irin kallon da yake mata gyara zama yayi yana murmushi a zuci yace yadai fi miki dan kuwa dake kad'ai ce wallahi baki zuwa sai kuma a fili yace "Eh to zaku iya tafiya amma ki tabbatar duk inda inba inda ya shafi bikin ba to bada yawuna ba" da sauri ta d'ago tana kallonsa ganin shi ko a jikinsa tashi tayi tana maganar zuci ai wallahi baka isa hanani fita ba mudai je bikin tukun amma gani ma can naje wajan boka ta ida maganar zucin tana ficewa a d'akin.
Inna gaje kuwa girgiza kai tayi tana cewa a zuci anya kuwa Malam bai d'akko rigima ba taya za'ai Gwaggo tabar d'iyarta tabi wannan matar amma abinda ba ruwanka dad'in kallo ne dashi katse mata tunani yayi da cewa "inkin fita ki kira min y'ar uwar taki" amsawa tayi da "to".
Kai tsaye d'akin Gwaggo ta nufa shiga tayi ta taddasu suna zaune ba laifi yanzu kam suna d'an shiri Inna gaje tace "Gwaggonsu kije inji Malam yana son magana dake" da sauri Gwaggo tace "to ko lafiya kuwa" "to inkinje dai kyaji" cewar Inna gaje tana ficewa daga d'akin ta nufi d'akin ta su Haneefa kuwa suka ce "kije kiji kawai" tashi tayi ta nufi d'akin Malam d'in da sallama ta shiga bayan ta zauna fuskar sa ba wasa ko kad'an itama ganin haka yasa ta bada hankalin ta yace "dama dalilin kirakin shine ina so ko Haneefa ko Sakina d'aya ta shirya zasu raka Narnah can garinsu Dutse biki" ya ida maganar cike da bada umarni da sauri Gwaggo ta d'ago tana kallonsa cike da mamaki da masifar dake taso mata duk da taga fuskar shi ba wasa cike da k'arfin hali ta bud'e baki tace "haba Malam kamar ya kafa san wannan matar bafa wani shiri nake da ita ba kuma sai ace na d'au d'iya ta na bata su tafi wata uwa duniya" kallon ta yayi ba wasa ya k'ara shan mur yace "umarni ne na bada na gama magana zaki iya tashi kiban waje" tashi tayi cike da bak'in ciki a zuciyarta ita Narnah zata kullawa wannan munafurcin.
Su Haneefa dake zaune ganinta ta dawo a hargitse da sauri har suna had'a baki wajan cewa "Mama lafiya dai" "wai ni waccar y'ar banzar bak'ar matar zata ma haka" cewar Gwaggo da sauri Sakina tace "wai Mama wacce mata?" Gwaggo a tsawace tace "Matar Ubanku mana wai na bata d'aya daga cikin ku wai biki zata" sakin baki sukai suna kallonta sai kuma can Haneefa tace "to Mama miye abun tada hankali ai dai da wayanmu kawai kisa a ranki da abinda take shirin yi ne shi yasa amma ko tatai damu ta isa tayi mana wani abunne" Sakina kuwa tab'e baki tayi dan ita yanzu bata fiye shiga harkar gidan nasu ba Gwaggo kuwa zama tayi tace "hakane amma sai dai inke kije dan duk abinda ya faru zaki sanar dani amma wannan y'ar uwar taki Sakina da zuwanta ma gara babu" ta ida maganar tana wuraga Sakina harara Sakina kuwa bata damuwa ba tace "ni dama Mama wallahi banda lafiya gara dai Haneefar taje" Gwaggo tace "ke dai kika sani saiki tashi ki shirya wai gobe ne tafiyar".
KANO
Ta ida maganar tana kallonsa ganin irin kallon da yake mata kamar na tuhuma sai kuma duk ta rud'e tayi k'asa da kanta da kyar ya bud'e baki cike da Miskilanci yace "kuma dole akace sai da wannan y'ar aikin zaku (Khaleesat)?" "Ai ta tayi ni wasu abubuwan a can ko bafa dad'ewa zamuyi ba fa Y'allabai" ta ida maganar tana kallonsa da d'an murmushi a fuskar ta shi kuwa yace "to shikenan Allah ya kaimu sati mai zuwa amma zuwa gobe ko jibi zanyi wata tafiya amma ranar zan dawo zanje katsina ne" wata irin masifaffiyar bugawa da fad'uwar gaba ce ta riski Hjy Sa'adha data rasa dalili jin ya ambaci Katsina da sauri tace "amma Y'allabai mi zakaje yi ne?" Kallon yake ya sakar mata murmushin nan nasa yace "wani abu ne mai mahimmanci a gare ni kema kuma zaki sani nan bada dad'ewa ba zan miki Albishir dashi" kallonsa take ita dai wannan Tafiyar Allah wallahi bata kwanta mata ba shi kuwa magana yake a zuci anya wannan abun da yake shirinyi bazai d'akkowa kansa rigima ba amma dai zai san yadda zai b'ullowa al'amarin.
Ni kuwa da nake zaune dawowa kenan da gama aikin su Ummeeta duk jikina ciwo yake dan mugunta saida na gyara duka d'akunan su harda mai-maitawa gashi d'azo nake jin fad'uwar gaba na rasa dalili har kiran gida nayi da wayar da Inna gaje taban kafin na taho muka gaisa da Inna gaje har taba Sakina muka sha fira haka shima Abba muna waya dashi yana tabbayata akwai matsala ban tab'a gaya mai wane irin hali nake cika ba duk inna kira Abba sai rink'a min nasiha na rasa wacce iri ce.
Shirye-shirye muke sosai ta zuwa Abuja da aka gaya min wai dani za'a Abuja nayi murna domin kuwa ban tab'a zuwa ba su Ummeeta sai dariya suke min wai y'ar k'auye zata Abuja nidai ban damu ba dan takai nama nake haka nan ina zaune kamar yauma saura kwana biyu mu tafi inda yaune Alhaji Mustapha ya nufi katsina tunda safe wajan k'arfe d'aya dai-dai ina zaune kawai naji wata irin masifaffiyar bugawar zuciya da wani irin nauyi naji ya hau kaina shin na miye hakan kawai bansan miya sa ba na saki kuka da sauri Asabe dake kusa dani ta matsoni tace "anya lafiyar ki kuwa Khaleesat tun jiya naga yanayink duk ya sauya?" Ta ida maganar tana kallon yadda nake kuka marar dalili da shashshakar kuka nace "wallahi Asabe tun jiya nake jin wani iri a zuciyata rabona da jin haka tun sadda za'a kawo ni nan kukanne kawai zai sani naji sanyi" cike da tausayi tace "tashi kiyi alwalla ki karanta Al'k'urani Insha Allah ba abinda zai faru sai alkhairi" kamar yadda tace haka nayi tabbas na samu sanyi a zuciya amma dai kwata-kwata banjin dad'in duniyar gaba d'aya.
Can wajan dare Alhaji Mustapha ya dawo bayan yayi wanka ya sakko k'asa ganin Hjy Sa'adha zaune kan kujera tana tunani ita kanta tunda ya tafi Katsinar nan gabanta keta fad'uwa kwata-kwata duk yau bata jin dad'in jikinta ganin ya dawo lafiya kuma saita jiki ranta tace "bari nasa a jera abinci ko?" Amsawa yayi kawai da kai yana danna computer kiranmu tayi muna zaune da Asabe da sauri muka tashi muka fara jera abincin kan darning d'in duk sadda zan wuce ta gabansu muke wucewa sai na rink'a jin ana kallo na d'agowa nayi karaf idona ya sark'afe da nasa wani irin mukaji mu duka dagani harshi b'allamai harara nayi da sauri ya ware ido yana min nuni da ido cewar ni kike harara lallai yarinyar can bata tsoronsa fa sai kuma ya saki murmushi ya rasa dalili yarinyar na sashi nishad'i ni kuwa da sauri na dukar da kaina ina wucewa d'akin mu da sauri kuma Hjy Sa'adha tace "yau Khaleesat kifa shirya gobe da wuri jirginmu zai tashi" cike da d'oki nace "to Insha Allah" dan kuwa ban tab'a hawa jirgi ba amma zan hau sadda na ida d'aki wani tsallan murna na buga inka kalleni saika yi zaton cewa yanzu ba wata damuwa dake damuna sai dai can k'asan zuciyata wani irin nauyi nake ji dama ni tuni na had'a kayana tuni.
Can wajan Alhaji Mustapha kuwa shi wallahi yama manta da wata tafiya jin an anbaci tafiya sai gabansa yad'an fad'i kwata-kwata tafiyar bai yarda da ita ba amma ba yadda zaiyi tunda ya riga da yace su tafi ganin yanayinsa ya canza yasa Hjy Sa'adha tace "ya dai Y'allabai naganka wani iri" gyara zama yayi yace "ba komai kawai dai harna fara kewarki ne tafiyar nan da zakiyi" ya idasa maganar dan kar ta gane ma akwai wani abu cike da son mijinta tace "ayya ai ba wani dad'ewa zanyi ba mijina". Nan dai suka ci abinci bayan sun gama ta haura sama ta basa waje yana wani aiki a computer.
Koda ta shiga d'akin nata bakin gado ta zauna tana kiran Dr Aysha bayan ta d'auka tace "Dr kifa shirya kinsan jirgin k'arfe tara ne kuma fatan an shirya komai?" Dr Aysha daga cikin wayar tace "Eh munyi waya da shi likitan da zaiyi aikin yace min an riga da an shirya komai mu kad'ai ake jira goben da mun isa za'a yi komai tunda ba wahala ne dashi ba maganar shiryawa da wuri kuma kinsanni bana wasa da lokaci" "Okay shikenan na kuwa sani amma kinsan Dr wallahi tun jiya nake jin zuciyata ba dad'i fa" cewar Hjy Sa'adha daga cikin wayar Dr Aysha tace "haba ki kwantar da hankalinki ba wani abu" ita Dr Aysha ta zata akan abinda zasuje yi ne, Sauke ajiyar zuciya Hjy Sa'adha tayi sukai sallama akan cewa su had'u a filin jirgi zuwa goben................✍️
*Shin miye Khaleesat take ji game da Alhaji Mustapha ne? Miye dalilin zuwan Alhaji Mustapha Katsina ne? Mi yake shiryawa ne? Wane Albishir ne zaiwa Hjy Sa'adha? Mi yasa Hjy Sa'adha take jin ba dad'i game da zuwan Alhaji Mustapha Katsina ne?*
To nima dai masoya na ina buk'atar jin miye dalili🤔🤓
*FATEEMAH RABI'U (ZAHRA ROYAL STAR CE)*🥰✍️
Comment and share Fisabilillahi🥰🙏
[9/8, 11:12 AM] ZAHRAH ROYAL STAR 🥰: *🤦♀️💔ITA CE K'ADDARATA 🤦♀️💔*
*©ZAHRA ROYAL STAR CE*🌟✍️
*ROYAL STAR WRITIN'S ASSOCIATION*
PAGE3️⃣1️⃣➡️3️⃣2️⃣
DA SUNAN ALLAH MAI RAHMA MAI JIN K'AI
___________________✍️Washe gari kuwa tunda safe Narnah ta aika kiran Haneefa domin su tafi ba yabo ba fallasa suka gaisa sunzo tafiya Gwaggo ta fito tana cewa "Haneefa ki tabbatar kin rik'e addu'a shirrin mutum ko aljan ya koma ma kowa" ta ida maganar tana kallon Haneefa cike da jin wani iri Narnah tace "Haba dai sai kace kinba wata bare d'iyarki?" "Yo wani lokacin ma ba gara baran ba da wani na kusa da kai d'in" cewar Gwaggo ita dai Narnah bata k'ara tankawa ba dan kuwa tasan abinda ta taka dan kuwa ita basu Haneefar ne a gabanta ba ta mallaki Malam shine burinta kawai.
Bayan sunje sunyi ma Malam sallama suka kama hanya ba laifi tana sakarma Haneefa fuska itama da take Haneefar ba wani damuwa tayi da itaba illama haushi da take bata haka dai suka isa garin Dutse bata yadda ta sauka a gidansu saita sauka a gidan Zuby ba laifi gidan Zuby sai dai ace akwai