why" ta fad'a a gigice tana kallon sa kamar zata zubar da hawaye. Marairaicewa yayi baice komai ba yana kallon ta, "Asad meyasa baka ganewa ne kai? Meyasa kake d'auka yadda zuciyar ka take mai kyau haka ta kowa take da kyau?, meyasa yadda kake ganin baza ka cutar da kowa ba haka kowa yake?. Baka san a yanzu ba abincin kowa zaka ci ba?, meyasa kaci abin hannunta?, akan me baka sanar dani kafin kaci ba?!" Ta k'arasa fad'a cikin fad'a tana kallon sa.
Runtse idanun sa yayi ya sunkuyar da kansa baice komai ba, sake tunzura ta yayi ganin yayi mata shiru tace, "baza kayi magana ba sai na mare ka?." D'agowa yayi ya kalle ta a sanyaye yace, "Allah ya wuci zuciyar ki."
"Asad meyasa kaci yanzu in ta zuba maka guba a ciki ka mutu fa? Ya kake so nayi kenan?." Nan ma shiru yayi baice komai ba ta rik'e hannun sa tace, "muje duk yadda zakayi ka amayar da abinda kaci zai maka illa Asad" ganin duk ta rud'e sai ya rik'e nata hannun shima yace, "Calm down Mama, babu abinda zai same ni sai Allah ya nufa."
"Asad tana so ta cutar da kai ba tun yau ba zata iya aikata komai wajan ganin ka cutu, kar ka kuma cin abin hannun ta dan Allah" ta fad'a kamar zata zubar hawaye tana kallon sa.
Kai ya girgiza alamun to yana kallon Maman tasa da girmamawa kamar ko yaushe kallon sa take itama kafin tace, "Baka jin komai a jikin ka?." Kai ya d'aga alamun eh kafin tace, "jikin Hydar ya tashi Asad kazo muje ka gan shi" ta fad'a tana fita shima ba musu ya biyo bayan ta. D'akin da yake suka shiga yana kwance kamar ko wanne lokaci Aliyu na tsaye a gefen sa yana kallon sa Asad ya k'arasa d'aya barin yana masa addu'a yana tofa masa a fuskar sa.
"Mama garin ya hakan ta faru?" Aliyu ya tambaya yana kallon Mama. Mama tace, "akan wata banza y'ar talakawa ya fita da safe, yarinyar nan da ya buge wai yaje dubawa da safe nayi masa warning akan zuwa inda take amma baiji ba gashi ya kwashi sanyi ciwon sa ya tashi." Aliyu ya tab'e baki yana kallon gefe baice komai ba.
"Assalamu alaikum, surprise" aka fad'a daga baya ana shigowa d'akin.
Dukkan su kallon k'ofar suka yi banda Asad da har lokacin yake wa Hydar addu'a, Suhaima ta wara idanu tace, "Sis oyoyo" ta fad'a tana hugging nata itama ta rike ta tana murmushi. Har k'asa ta duk'a ta gaisa Mama ta amsa da fara'a tace, "lallai kam surprise, ina Mum d'in?."
Murmushi tayi wanda ya bayyanar da asalin kyaun ta tace, "Mom tana gida. Mama Yaya Hydar ne babu lafiya?." Kai ta d'aga mata kawai ta k'arasa inda Asad yake tsaye tana kallon Hydar. Sai kuma ta kalli Asad da bai kalle ta ba ta d'an bugi kafad'ar sa tace, "Kana gani na ko magana babu ko bro? I'm sorry in kaji babu dad'i jiya bance maka zan zo ba, ina so na baka mamaki ne."
D'ago idanun sa yayi yana kallon ta nan take gaban ta ya fad'i ta d'an yi baya ta kalli Suhaima da take kunshe dariya tace, "deaf kenan, ga Bro Aly nan kina gani." Wara idanu tayi tana kulle bakin ta tana kallon Asad ya d'auke kansa daga kallon ta takaici kamar ya kashe shitace, "Sorry Boss."
In ta samu kallon arzuk'i ma da ta godewa Allah ta bar wajan ta koma inda Aliyu yake shima bai kalle ta ba tace, "Yau sai naga kai ka koma min shi shi ya koma min kai."
Irin kallon da ta samu daga wajan Asad shi yayi mata shima sai ta kalli Mama sai taga Mama tayi murmushi tace, "Yau suna so su rikita ki ne." Sai kuma Aliyu ya murmushi ya mik'a mata hannu alamun su gaisa.
Sai tayi murmushi ta bashi nata hannun suka gaisa kafin yace, "Welcome" yana furta hakan ya mik'e tsaye har lokacin hannun sa na cikin nata yana binta da kallo itama haka kafin ya zame hannun sa ya fita. Mama ta kalle ta tace, "Jidda kije ki huta, Asad kaje ina zuwa." A hankali yake takawa ya fita ta bishi da kallo tana murmushi Mama na kula da ita itama ta murmusa bata ce komai ba suka fita aka bar Hydar dake kwance.
Asad tunda ya bar wajan zuciyar sa take masa zafi har ya koma apartment d'in su ji yake kamar ya fashe da kuka sabida takaici. A bakin window ya tsaya yana furzar da iska mai zafin gaske jikin sa har zafi ya d'auka sabida takaici da zallar bak'in ciki. Ta yaya Mama zata ce wannan yarinyar ce zata kasance matsayin matar sa nan gaba?, yarinyar da a gaban sa take gaisawa da namiji wanda ya kasance yayan sa kuma jinin sa, kenan sun saba tunda gashi yana bata hannu ta bashi suka gaisa. dogon tsaki yaja lokacin da ya tuna dukan kafad'ar sa da tayi alamun sun saba ma irin wannan banzayen halayen da Aliyu.
Kowa yasan shi yana da kishi ko takalmi akace wannan mallakin sane tofa bai aminta yaga wani da takalmin ba sai shi kad'ai balle matar aure, kai yake girgizawa a hankali yace, "Mama bazan iya auren ta ba, I'm sorry" ya fad'a yana barin wajan.
So yake ya bar gidan yaje company amma ya kasa baya son fita gabad'aya wani irin abu yake ji a jikin sa kamar ana zare masa kuzarin jikin sa.
Zama yayi a kan kujera yana furzar da iska kafin ya buɗe idanun sa ya mik'e zaune yana wara idanun sa a bangon d'akin, dafe kai yayi ya jingina da kujera ya rasa gane fuskar yarinyar da yake mafarki da ita amma yana jin tashin amon muryar ta a kunnen sa amma fuskar ta tak'i tsayawa a idanun sa.
Ko yanzu yaji maganar ta zai iya ganewa amma banda fuskarta gashi ta maqale a zuciyar sa kowa ya motsa sai ya tuna da ita.
B'angaren Mama suna shiga d'aki ta kalli Jidda tace, "Amma kwanaki zaki mana ko?." Ta yi farrr da idanun ta kana tace, "A'a Ranki ya dad'e anjima da daddare zan wuce."
"To kije yanzu wajan Asad ku gaisa amma nasan Aliyu abokin kine ki daina nuna hakan a gaban Asad, lemme tell u something about your husband to be. yana da kishi, in ya nuna abu aka ce wannan naka ne yace kuma inaso to duk duniya babu wanda zaiyi amfani da abun nan sai shi kad'ai, in kuwa yaga wani ya rab'i wannan abin da yake so tabbas zai bar masa ne shi ya hak'ura. So u have to be very careful Jidda in kuna tare bakya ganin kowa sai shi koda Aliyun ne in ba haka ba zaku yi fad'a" ta fad'a tana kallon ta.
Juya idanu Jidda tayi jin abinda akace mata sai farin ciki ya mamaye mata zuciya cikin muryar ta mai dad'in ji tace, "In sha Allah zan kiyaye ranki ya dad'e, bara naje wajan sa" ta fad'a tana ficewa Suhaima ta bita da kallo ta kalli Mama tace, "Mama Asad da Jidda sunyi bala'in dacewa, wannan suka tashi haihuwar yara za'a ga larabawa." Murmushi kawai Mama tayi dan ita badan kyau ta had'a su aure ba akwai manufar ta kafin ta fita ya koma d'akin da Hydar yake kwance.
Asad yana zaune a inda yake aka shigo da sallama ya amsa ba tare da ya kalli wacce ta shigo ba yaji an zauna kusa dashi bai kalle ta ba tace, "barka da hutawa my Asad." Bai kalli inda take bama balle ta saka ran zai amsa. Daman tasan za'ayi haka tayi murmushi cikin shagwaba tace, "Kayi min magana mana." Nan ma bai kalle ta ba idanun sa a kulle suke.
"Dan kai fa na baro gida nazo nan amma shine baza ka kula ni ba?" Ta fad'a a shagwab'e. Nan ma banza babu amsa ta kuma cewa, "My Asad please." Numfashi ya sauke ya juyo ya kalle ta baice komai ba ya sake d'auke kansa yana cize baki lokaci d'aya yaji cikin sa na k'ullewa.
Ganin hakan sai tayi shiru bata sake magana ba dan tasan kallo na kin ishe ni ne hakan ya saka ta yin shiru tana kallon sa yana yamutsa fuska. Sun jima a haka a zaune kafin ya cize bakin sa ya furta, "Ya salam!." Mugun ciwo cikin sa yake yi bai san sanda ya furta hakan ba idanun sa lokaci d'aya sun canja kala zuwa jajaye haka fuskar sa ma tayi ja jikin sa har rawa yake yi.
"Asad!, Asad me ya faru!?" Ta fad'a tana kallon sa ganin lokaci guda ya canja. Idanun sa da taga ya kulle yana sauke numfashi hannun ta na rawa ta kira number Mama tana d'auka tace, "Mama Asad zai mutu! Kizo Mama" ta fad'a da k'arfi tana kallon Asad da yake jingine a kan kujera kamar baya numfashi..
*KWANTAN ƁAUNA*
FitattuBiyar 2023
©️ *Nana Haleema.*
*Book 1*
*009.*
Tunda Mama tazo inda yake hankalin ta yake a tashe tana zaune kusa dashi tana fad'in, "Asad me kake ji a cikin naka? Kayi min magana dan Allah. Yaushe ya fara yi maka ciwo? Me kake ji?, zafi yake kome?." Bud'e idanu yayi ya zauna sosai yace, "Mama, I'm okay fa."
"Ban amince ba Asad, kalli face d'in ka fa yadda ya koma, tashi muje asibiti da sauri daman nasan babu ta yadda za'ayi kaci abincin Hajiya ba tare da ka samu wani abun ba."
Hannun ta ya rik'e duk da ciwon da cikin sa yake masa yace, "Mama kar ki tayar da hankalin ki."
"Ta yaya bazan tayar da hankali ba Asad? Abincin fa ta baka kaci gashi har kana ciwon ciki wanda baka tab'a yi ba, hankalina kake so na kwantar ko me?." Shiru yayi bai amsa na kafin ya lumshe idanun sa yace, "bacci zanyi."
"Baza kayi bacci ba Asad sai munje asibiti, kar ka kulle idanun ka ka bud'e mu tafi." Suhaima ce suka shigo tare da Dr Yasir Mama na ganin sa tace, "Zo da sauri ka duba shi." Da saurin kuwa ya k'arasa yana yanayin jikin nasa yana tambayar sa abinda yake ji duk da yasan babu lallai ya basa amsa.
Allurar ciwon ciki yayi masa kafin ya d'ago ya kalli Mama yace, "Ranki ya dad'e ba wani abin tayar da hankali bane nayi masa allura zai daina ciwom." Jidda tace, "are you sure zai daina?."
"I'm very sure." Mama tace, "in akwai damuwa muje asibiti ko scanning ne ayi masa."
"A'a ranki ya dad'e zai ji sauk'i." Kai ta d'aga shi kuma ya fita da sauri baya so tayi masa maganar Rauda da take asibiti.
Aliyu da ya shigo a lokacin ta kalls tace, "Ka rik'e shi ku shiga d'aki ya kwanta, please Aliyu take care of him bana so wani abun ya same shi."
Mik'ewa Asad yayi ya tafi d'akin da kansa Aliyu ya kalli Mama yace, "basai na taimaka masa ba kin gani" yana fad'a ya shiga d'akin da yake kusa da na Asad d'in ya kullo k'ofa. Fita Mama tayi suma su Suhaima suka fito suka ga ta mik'e alamun b'angaren mai martaba zata je su suka kuma koma ciki.
Mai martaba yana zaune shi kad'ai kamar ko yaushe aka mata izinin shiga ta shiga da sallama ta nemi k'asa ta zauna tana kallon wani wajan daban.
Ganin hakan sai ya murmusa yace, "Rabi'atul adawiya ya akayi ne?."
"Allah yaja da ran mijina burin mutanen gidan nan suga bayan y'ay'ana me suka tare musu? Hydar gashi can ciwo ya tashi, ga Asad ma Hajiya ta bashi zogale yaci gashi can a kwance yana ciwon ciki. Ya suke so nayi ne me na tare musu?." Mai martaba ya mik'e daga kashingidar da yayi yace, "Ciwon Hydar ya tashi baki sanar dani ba?." Ta kalle shi tace, "Na rud'e ne gabad'aya ana kira na naje asibitin da je duba wata yarinyar da ya buge a can ciwon ya same shi na dawo dashi nan, ga Asad ma a kwance ya suke so nayi ne?" Ta fad'a kamar zatayi hawaye.
Mai martaba yace, "kar ki zubar da hawaye ban sanki da raguwar zuciya ba ki daure kamar yadda kike daurewa a koda yaushe. Yanzu ya jikin Asad d'in?." Idanunta ta goge tace, "yayi bacci. zogale yaci wanda Hajiya ta bashi daman na tabbatar ba da zuciya d'aya ta bashi ba, yanzu gashi can a kwance babu lafiya, burin su suga Asad ya mutu sai sun kashe sa hankalin su zai kwanta."
Mai martaba ya kalle ta sosai yace, "bana son zargin da kike saurin yi ki fara tabbatar da abinda kika ga gani kafin ki yanke hukunci."
Bata ce komai ba hakan ya saka ce sake cewa, "kar ki damu duka zasu samu lafiya babu wanda ya isa yayi musu abinda Allah bai nufa ba, Asad yana da ibada sosai k'aramin abu ko babba bazai kama shi ba sai wanda Allah ya nufa. Hydar zai samu sauk'i nan kusa ki daina tayat da hankalin ki."
Bata ce komai ba a nan ma amma ta d'an ji sanyi a zuciyar ta yace, "muje na duba jikin su da kaina" ya fad'a yana mik'ewa tsaye ita kuma bata mik'e ba. Ganin hakan ya saka hannayen sa da kansa ya mik'ar da ita tsaye yana kallon fuskar ta da murmushi yace, "kar ki bada ni mana, ko yaushe ina fad'in ke jaruma ce samu mace mai irin tsayayyiyar zuciyar ki abu ne mai wahala ya zaki bani kunya kum?. Come on ban san ki da haka ba, muje."
Tare suka fito ganin fitowar mai martaba babu tsammani aka tawo a guje aka saka masa takalmi aka bud'e lema tana takawa a hankali tana gefen sa ana zuba masa kirari har cikin d'akin da Hydar yake. Daga shi sai ita sai shamaki a gefen sa wanda aikin sa duk inda sarki yake yana kusa dashi sune kawai a d'akin kowa yana waje ya kalle ta yace, "meyasa ba'a bar shi a asibitin ba?."
"Nan yafi safe."" ta bashi amsa a tak'aice tana kallon sa itama.
A tare suka kuma fitowa ana ta kallon su bayi masu gulma suna yi tuni har an kaiwa sauran labari tun kafin su gama ma abinda ya fito dasu. Inda Asad yake suka shiga har cikin d'akin sa, mai martaba ne ya shiga d'akin kawai bai jima ba ya fito daga d'akin ana kirari aka raka shi har b'angaren sa.
Bata zauna ba ta koma nata b'angaren mai martaba shi kansa abin ya d'aure masa kai sosai duk da yasan ciwon ciki lalura ce amma ya tabbata na Asad yana da sila baya so ya nuna mata ne ya sake tunzura zuciyar ta shiyasa yayi shiru.
B'angaren Hajiya da labari yazo mata Asad yana kwance sai ta damu tana ta zaga d'akin ta cikin tunani dan dai ita ta tabbatar bata sakawa Asad komai a cikin zogale ba wanda ta bashi ko ita zata iya ci, amma meyasa akace bayan yaci yana ciwon ciki?, meye dalilin ciwon cikin nasa?, Anya babu wanda ya jefi tsuntsu biyu da dutse d'aya?. Ta jima tana wannan tunanin kafin wayar ta d'auki k'ara, d'auka tayi taga sunan mai gidan ta Yana kiran ta ta d'auka a kunne ta saurari abinda yace kafin ta yanke wayar.
Numfashi ta fesar ta fito cikin takun isa da k'asaita ta tafi amsa kiran mai martaba.
Daga shi sai Wambai sai Mama a zaune ta shiga da sallama ta zauna gaban ta na fad'uwa sosai zuciyar ta duk ta cika da tsoro, mai martaba yace, "Rabi'atu gata." Mama ta kalle bowl d'in gaban ta da yake d'auke da ragowar zogalen a ciki ta fito da farar takarda tace, "wannan shine sakamakon gwajin ragowar zogalen nan da akayi ya tabbatar kuma an bawa Asad guba kuma itace wacce ta bashi yaci." Hajiya ta dafe k'irjin ta da yayi mugun bugawa fuskar ta tayi kalar tausayi ta kalli mai martaba shima ita yake kallo kafin yace, "Sa'adatu ya akayi haka?."
"Allah ya taimake ka wallahi Allah ban bawa Asad wani abu a cikin zogalen nan ba, inda nayi niyar cutar dashi bazan bari yasan nice na bayar ba sai dai yaci. Ko ni zan iya ci ban san ya akayi hakan ta faru ba, mai martaba yasan bazan rantse a kan k'arya ba" ta fad'a muryar ta na rawa sosai.
Mai martaba ya kalli Mama yaga ta kawar da kanta gefe alamun bata ma yarda ba kafin ya kalli wambai ya dawo da kallon sa a gare su yace, "zaku iya tafiya. Amma bana so na sake yin maganar nan a barta a wajan nan kar na kuma ji. Zaku iya tafiya." Ba musu suka tashi suka fita mai martaba ya kalli Wambai yace, "Mubarak mai ka fahimta game da lamarin nan?."
"Allah ya ja zamanin ka abu ne a bayyane kai tsaye baza'a ce Hajiya ce ta bashi gubar ba, kai tsaye kuma baza'a ce Fulani itace ta mata sharri ba. Komai zai uya faruwa kowa yana da gaskiya a cikin su." Mai martaba ya sauke numfashi yace, "Sa'adatu bazata bashi guba ba ni nasan da hakan, koda ma ace zata bayar d'in kamar yarda tace baza tayi yadda za'a gane ba ta taka sahun b'arawo ne tabbas akwai wanda yake son ganin bayan Asad a cikin gidan nan, amma waye?."
Wambai yace, "koma waye Allah zai tona asirin sa. Asad mutum ne mai addu'a kuma power of du'a tana canja destiny komai girman ta, kafin mummanar k'addarar ta samu Asad addu'a ta canja ta." Mai martaba ya girgiza kai zuciyar sa taf da tunani yace, "Rabi'atu dole ta shiga damuwa yau ta shirya zuwa Kano ga Asad ba lafiya ga kuma Hydar a kwance ba'a san ranar da zai farfad'o ba."
"Gaskiya ta b'angaren yaranta tana karb'ar jarabawa daga Allah, amma in ta kwantar da hankalin ta Asad sai ya zamarwa makiya ciwon ido."
"Allah yasa mu dace" mai martaba ya furta ya amsa da amin.
B'angaren Hajiya tunda ta koma take zagaye hankalin ta ya tashi sosai ganin maganar har taje gaban mai martaba, babban tashin hankalin ta bai wuce yardar da mai martaba yayi da ita kar ta zube ba hakan ya saka ta shiga d'aki can k'arshe ta d'auki waya ta kira Waziri. kira 1,2 ya d'auka yana d'auka kafin tayi magana yace, "kin bawa Asad zogale yaci yanzu kuma yana ciwon ciki an yi binciken ragowar da ya rage an gano akwai guba a ciki, hankalin ki ya tashi domin kedai kin san baki saka komai ba kar hakan ya jawo rushewar yardar da kike so Asad yayi dake, shine kawai tashin hankalin ki amma bawai dan yaci guba ba haka ne?."
Da zallar mamaki tace, "duk ya akayi kasan wannan bayan kai kana wani wajan daban ina nan daban?." Murmushi yayi mai sauti yace, "kar ki raina basira da y'an leken asirin da master planer take dashi a gidan nan, itace ta sanar dani duk abinda ya faru gashi kuma na tabbatar hakan ne."
"Wai wacece master planer d'in nan? A ina take?, ya akayi ta san duk abinda yake faruwa a gidan nan bayan bata cikin sa?, su waye suke sanar da ita har abinda ya faru a falon mai martaba?. Lamarin ta ya fara bani tsoro fa na fara zargin tana kewaye damu a cikin gidan nan koma wacece" ta fad'a tana girgiza kanta.
"Hhhhhh kar lamarin ta ya baki tsoro tsabar mayar da hankali ne akan abinda aka saka a gaba. Tace ki kwantar da hankalin ki ki cigaba da abinda kika fara kar abinda ya faru ya baki tsoro, baki saka guba a cikin zogale ba itama ta sani kawai dai akwai wanda yake so yayi amfani dake ne a cikin gidan shiyasa ya d'ana miki tarko kuma kika fad'a. Tabbas bayan mu akwai wanda yake son ganin bayan Asad tambayar itace waye? Ko wacece? Ko kuma su waye?, ita kanta master planer bata gano waye ba."
"Gano ko waye shine abinda ya kamata mu saka a gaba in ba haka ba akwai babbar matsala tunda aka fara haka."
"Kada ki damu ki kwantar da hankalin ki komai zai zo mana da sauk'i tunda master planer tana tare damu, kedai ki cigaba da abinda yake gaban ki, ke kan ki kinga nasara a tafiya da master planer a jiya tace sai Hydar ya kwanta ciwo ya kwanta, a jiya tace za'a hana Rabi'atu zuwa Kano gashi kuwa duka ta faru. Ki mayar da hankali muyi abinda yake gaban mu nasara a tare damu take" yana fad'ar hakan ya yanke wayar tabi wayar da kallo.
"Kenan akwai wanda yake son ganin bayan Asad bayan mu? Waye yake k'okarin shafa min kashin kaji?, wanne bak'in fenti yake k'okarin shafa min....?" Bata da wannan amsar hakan ya saka ta sauke numfashi tana sake tafiya duniyar tunani zuciyar ta cike da tsoro.
A b'angaren Mama lokacin da ta koma kanta ta kulle a d'aki tana neman mafita dan zuwa lokacin kanta ya kulle, sai da ta jima sosai sannan ta fito ta tarar da Jidda da Suhaima a zaune bata ce komai ba ta shiga d'akin da Hydar yake. Yana nan yadda yake ta k'arasa kusa dashi tana shafa kansa tayi masa addu'a sannan ta fito ta sake komawa d'akin ta.
Babban tashin hankalin da ya addabe su dukkan su shine su waye suke son ganin bayan Asad.....?.
*☆☆☆* _Ina nan zan iso a gare ka zan baka kariya ga dukkan makiyan ka, makiya sun saka ka a tsakiya ka tashi tsaye kayi yak'i dasu kafin isowata gare ka, zan zo nan bada jimawa ba kafin na k'araso ka tabbatar ka tsaya da k'afafun ka, ina nan zuwa.....!_ a firgice Asad ya mik'e zaune yana zare idanun sa jikin sa yayi bala'in mutuwa ga ciwon cikin da yake damun sa har lokaci. Tuno mafarkin da yayi yake yi tiryan-tiryan suna dawo masa kansa ya dafe kai da duka hannu biyu yana yanutsa fuska.
Kusan kwanaki goma kenan a jere kullum sai yayi mafarki da yarinyar da baya ganin fuskar ta sai dai yaji maganar ta itama kuma baya jin maganar tarrr dan baya tunanin zai iya gane mai maganar a zahiri, "who is she?" Ya tambaya a bayyane yana dafe cikin sa yana cize bakin sa.
Tsaye ya tashi ya kalli agogo yaga har lokacii ya tafi yana dafa bango ya shiga band'aki yayi wanka da alwala ya fito ya tayar da sallah ya idar lokacin akayi la'asar yayi. Shiryawa yayi cikin manyan kaya maroon d'in yadi
All Chapters
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 8 Chapter of 24