yana Nazariin abinda yake yi.
Rufe na farko yayi ya bud'e na biyun yana sake bi a hankali har ya kammala karanta inda yake da buk'ata ya kulle ya kifa kansa a kan littafin kamar mai bacci.
Juma'a ce gobe kuma shine zai gabatar da hud'uba shiyasa yake ta dube-duben littafai amma zuciyar sa ta kasa bashi topic guda d'aya da zaiyi hud'ubar a kansa, d'ago kai yayi ya saka hannu biyu ya d'an daki kansa a hankali ya furzar da iska waje yana kallon d'akin gabad'ayan sa. Zuciyar sa yaji yana bugawa da sauri har yana jin sautin ta a kunnen sa ya runtse idanun fuskar Rauda ta bayyana a gare shi.
"Hasbunallahu wani'imal wakil" ya furta a hankali yana dafe da kansa har lokacin bai kuma daina jin bugun zuciyar ba.
Cize bakin sa yayi ya runtse idanu kafin ya koma ya jingina da kujerar, sautin muryar ta yake tunowa a hankali tana shiga ilarin jikin sa, tasirin muryar da dad'in ta ya saka shi kulle idon sa yana sauke numfashi gashin jikin sa na tashi. sautin muryar yarinyar mafarkin sa yaji sai ya bud'e idanun sa; ya kasa banbance shin itace yake gani a mafarki ko kuma ba ita bace?, bai tab'a ganin waccan fuskar ta completely ba amma idanun ta da goshin ta irin na Rauda ne, akwai banbanci a maganar su waccan muryar ta tafi zak'i a kan ta Rauda, ita kuma ta Rauda tafi sanyi da taushi kamar mai mura in tana magana.
Tashi yayi ya kashe hasken d'akin ya fita daga cikin da ya dawo d'akin sa ya zauna a gefen gado ya rasa tunanin ma mai zaiyi.
Kiran wayar Suhail ya gani ya jawo wayar ya d'auka ya saka a kunnen sa yayi shiru alamun ana yi masa magana kafin yace, "Alright" daga haka ya yanke wayar ya tashi ya shiga band'aki. Sai bayan ya gama komai sannan ya kwanta da burin Allah ya sa yau yayi mafarki da yarinyar da yake gani ko zai gane ta.
Washe gari da ya farka yaso yaje ofishin fasko amma sabida juma'a ce dole ya tsaya yayi hud'uba ya saka babu inda yaje har aka shiga masallacin cikin gari, kamar ko yaushe yayi hud'uba ya kuma yi sallah bayan an idar ya hau mota ya wuce office d'in. Da kansa ya karb'o faskunan nasu guda uku da hotuna yana shiga mota ya zauna yana kiran agent d'in su a waya, ana d'auka yace, "Egyptian visa nake so guda uku" Shiru ya kuma yi kafin yace, "Okay better" yana fad'a ya yanke wayar ya ja motar sa ya bar wajan.
Gida ya wuce ya ajjiye faskunan ya fito zuwa wajan Mama kamar yadda ya saba. A hakimce ya same ta tana danna waya kamar koda yaushe ya zauna a gefen ta kana yace, "Barka da juma'a."
"Barka Asad" ta furta kawai ba tare da ta kalle shi ba. Shiru ya biyo baya babu wanda ya kuma yin magana kafin yace, "Mama anyi inviting d'ina wani event a Cairo"
"Kwana nawa zakayi?."
"I think one week."
"I'm not allow u to go."
Kallon ya yayi itama ta kalle shi yace, "but Mah...." D'aga masa hannu tafi tace, "Na gama magana Asad, tafiya indai ba ta kwana biyu bace ban amince ka jeta a yanzu ba maybe kaje wani lokacin."
Numfashi ya sauke ya tashi ya fita daga falon nata zuwa falon Hajiya kamar yadda ya saba duk juma'a, tana zaune ita da hidiman ta ya shiga da sallama, "Barka da zuwa Yarima, barka da zuwa fari mai farar wutsiya, fari mai farar aniya, indaroro sai kan soro, kaga tufa mad'aukar d'aki, sikari bakayi farin banza ba, walikiya kake duk inda kabi sai ka haska......" zasu kuma magana ya d'aga hannu sama sukayi shiru cikin girmawawa.
Murmushin yake take tana kallon sa ya zauna a k'asa yana kallon yace, "Barka da Juma'a Hajiya"
"Barka dai Asad, ya jama'a ya kuma k'ok'ari?."
"Alhamdulillah, ina suke?" Ya fad'a yana kallon falon alamun yana neman kannen sa.
"Sunje gidan Yayar ku sai zuwa anjima zasu dawo." Tunda tace Yayar ku ya gano wacce take nufi dan babar yar ta wacce ta kasance babba a gida gabad'aya bata fad'ar sunan ta daman. "Na barki lafiya" ya fad'a yana mik'ewa tsaye tace, "Na gode Asad." Bai amsa ba ya fita ya tafi b'angaren Umma, kamar ita tana zaune itama a zagaye da hadimai suka gaisa kamar waccan ya tafi.
Kasancewar rana ce bai samu mai martaba ya bada kud'in da ake rabawa dan bazai samu damar yi da kansa ba ya koma apartment d'in sa.
Sai yamma sannan wanda zai karb'i faskunan yazo ya bashi ya wuce Abuja dasu domin a buga musu visa. Bayan wanda karb'a ya tashi yana zaune Suhail ya kira shi, bai d'auka ba har ta katse bayan ta katse ya d'auki wayar ya kira hidiman k'ofar ya bada umarnin a bar shi ya shigo ya ajjiye wayar.
Da sallama ya shigo ya zauna kusa dashi Asad yace, "Suna bin umarnin Mama ne."
Suhail ya murmusa yace, "Hakan yana da kyau sosai tsoron lafiyar kace, sai naga kamar ka rame." Tab'e baki yayi baice komai ba kafin Suhail ya kuma cewa, "me yake faruwa?."
Iska ya furzar a hankali yana sauke numfashi amma bai ce masa komai ba, jin hakan sai shima yayi shiru ya saka hannu a aljihun gaban rigar sa kamar mai neman wani abu, "me kake saka min?" Yaji muryar Asad a kansa yayi saurin janye hannun sa daga kusa dashi.
Had'a idanu sukayi Asad ya d'aga gira alamun ya bashi amsa, nutsuwa ya aro ya saka a fuskar sakana yace, "me kuwa zan shafa maka Asad? Kalli hannu na mana" ya fad'a yana nuna masa tafikan hannun sa. Murmushin gefen baki Asad yayi kafin ya d'auke kansa daga kallon sa yace, "lafiya ka ke nema na?."
"Normal ina so mu had'u ne kawai."
"Really?" Asad ya fad'a yana wara idanun sa waje.
"Sure, naga duk ka canja Asad kamar baka yadda dani ba, ko da Aliyu nake tare ne ban sani ba?."
Baice masa komai ba ya shafa kai kawai kafin yace, "u can go." Suhail ya kalle shi yace, "Okay bye" ya fad'a yana mik'ewa ya fita yana mamakin canjawar Asad. Waya aka kuma yi masa ya kalla yaga masu tsaron k'ofar sane ya share kiran ya katse aka kuma kira ya ja k'aramin tsaki ya d'auka baice komai ba, daga can b'angaren suka ce, "Ranka ya dad'e Allah ya wuci zuciyar ka na dame ka, wata yarinya ce take so tayi magana da kai, tana ta magiya mu barta ta ganka."
Jimm Asad yayi yana tunani kafin ya bada umarnin tazo, ba jimawa ta shigo da sallama jikin ta har rawa yake ta zube a kan carpet tace, "Barka da yamma ranka ya dad'e."
"Wacece ke?" Ya furta a hankali yana kallon ta.
"Sunana Habiba ni jikar Gwaggo Gambo ce da take gidan nan. K'awa tace ta samu matsala da Yallab'ai Aliyu to tsoro take ji kar ya mata wani hukunci shiyasa muka kawo k'ara gaban ka a taimaka a bashi hak'uri. "
Shiru yayi bai amsa ba hakan ya saka tace, "Sunan ta Rauda tana da matsalar k'afa shiyasa bamu zo tare ba, mun tab'a zuwa gidan nan da ita ta buge shi bata sani ba ya mare ta, had'uwar su ta biyu kusan hakan ce ta faru, had'uwar su ta uku shine ta mayar masa da abinda ya fad'a mata. Yayi alwashin sai ya d'auki mataki a kanta duk taji tsoro sai kuka take hankalin ta ya tashi matuk'a. A bashi hak'uri ranka ya dad'e wallahi y'ar talakawa ce kar ya cutar da ita."
Yana sauraron ta dan a hankali take maganar hakan ya saka shi nutsuwa yana jin ta, tunda ta ambaci Rauda gaban sa ya fad'i ya sake bata hankalin sa har taje k'arshe kafin, "kar ki damu."
"Na gode ranka ya dad'e, Allah ya k'ara lafiya da nisan kwana, ya ja da ran Mama da mai martaba." A lab'b'an sa ya amsa da amin ya sanya hannu a aljihun sa ya d'auko kud'i ya mik'a mata ta karb'a hannu na rawa zatayi godiya ya d'aga mata hannu ta tashi ta fita.
Numfashi ya fesar kalmar ya mare ta tana yi masa amsa kuwa a kunnen sa nan take ransa yaji ya b'aci ba kad'an ba yaja tsaki baiyi niyar fita ba amma ya tashi ya fita daga gidan gabad'aya.
Habiba na barin gidan wajan Rauda taje ta bata labarin duk abinda ya faru har kud'in da ya bata ta nuna mata, Rauda tace, "Bari kawai Habiba baki san me ya faru washe garin da kika zo nan ba."
"Meya faru to?."
Kwashe duk abinda ya faru tayi ta fad'a mata sannan ta d'ora da cewa, "Jiya ya saka aka kai mu ofishin fasko za'ayi mana zai kaini waje ayi gyaran k'afa madadin k'anin sa."
Habiba tace, "ban sani ba ai da banje na same shi yanzu ba tunda komai ma ya wuce. Amma nayi murna da za'a yi miki aikin k'afar nan Allah ya sa ayi a sa'a."
"Amin."
"Kika dinga zagin wanda ya kad'e ki kina ganin kamar wasa ne babu wani rashin lafiya ashe gashi wanda muka sani ne ma."
"Wallahi kuwa, na d'auki hakki."
"Ina Anas ne wai?." Rauda tace, "Yaje Abia."
"Masoyin ki kenan, wai har yanzu baki bashi dama ba?."
"Na bashi Habiba tunda ina sauraron sa yanzu. Tunda ya siya min maganin da aka wulak'anta ni a kai ya kawo mana kayan abincin da ko rabin rabin sa bamu ci ba wallahi nake ganin k'imar sa sosai. Ta silar abincin nan Baba ya daina d'orawa Rahma tallah."
Habiba tace, "Ai yana son ki wallahi zaiyi komai sabida ke; Allah ya saka masa da alkhairi."
"Amin."
"Kin fara son sa kenan?."
"Ina fa, kedai Allah ya kyauta." Habiba tayi dariya ta amsa da amin kafin su cigaba da hira suyi sallama ta tafi.
Maganar Habiba ta dinga tunawa musamman halayen Asad sai taji ya burge ta sosai ko babu komai baya wulak'anta talakawa kamar Aliyu.
B'angaren Asad bai dawo ba sai dare direct ya wuce b'angaren mahaifin sa sai da aka bashi izinin shiga sannan ya shiga, baya babbar fada ta farko ya shiga ta biyu nan ma baya nan hakan ya bashi tabbacin yana d'aki kenan. Shi kad'ai mai martabawa yake lamuncewa ya shiga amma gudun kar ya shiga ya tarar da wata matar tasa a ciki ya saka yaja tunga tunda ba girkin Mama bane ba. Kamar kuwa ya sani yana nan tsaye Ammi ta fito ganin sa ya saka tace, "Asad daman kai yake nema kuwa, kaje ciki" ta fad'a tana wucewa shima ya shiga d'akin da ya san mallakin mahaifin sane.
A zaune ya same shi a kamalance ya k'arasa ya zauna a akan carpet yace, "Barka da dare Takawa." Murmushi yayi yace, "Barka dai Asad."
"Ya k'arfin jikin?."
"Jiki Alhamdulillah ana ta samun lafiya."
"Allah ya k'ara lafiya yasa kaffaara ce."
"Amin Asad. Allah ya yi maka albarka ka rayu cikin aminci da walwala."
A labban sa ya amsa da amin kafin mai martaba yace, "Ya batun zuwa taron malamai masu shekarun naka a Dubai?."
"Mama ta hana Abba" ya furta a sanyaye.
Kai ya girgiza yace, "Rabi'atu manya, ko kad'an bata so kayi nisa dani gudun kar ka tafi a bawa wani sarauta ba kai ba, tana mantawa da Allah ya riga ya rubuta wanda zai gaje ni."
Shiru Asad yayi bai ce komai mai martaba yace, "Ta hana ka aikin da kake mafarki tun kana yaro, ta hana ka komawa Dubai kamar yadda sarkin su ya nema, ta hana ka aiki da Saudia yanzu kuma ta hana ka zuwa taron kwana bakwai kacal; in kana so ka shirya ka tafi na baka damar hakan."
"Allah yaja zamanin mahaifina, tunda tace na bari na bari d'in."
Mai martaba yayi murmushi mai kyau yace, "Shiyasa albarka take baibaiye dakai a koda yaushe, indai nace kar ayi ko tace kar ayi baza kayi koda a bayan idanun mu. Amma tauye ka da take yi yayi yawa nan gaba indai aka kuma zuwa irin wannan gab'ar bazan bari ta tauye ka sai kayi abinda kake so." Shima murmushi Asad d'in yayi yana kallon mahaifin nasa.
"Ya batun yarinyar da take nema maka?." Take fuskar sa ta koma yadda take a d'azu yace, "bata dace dani ba Abba, na sanar da Mama tace ba haka ba ita ta zab'a min, amma na karb'a."
"Da zarar ka samo wacce kake so ko wacece a fad'in duniya ka sanar dani Asad, zan shige maka gaba wajan ganin ka mallake ta ko waye mahaifinta a garin nan ko a k'asar nan."
D'ago idanu yayi suna had'a ido da Abban nasa kwarjini ya saka ya sauke kai k'asa ba tare da ya shirya ba yaji bakin sa yace, "Ko y'ar talakawa ce?."
Mai martaba ya tashi sosai yace, "Ko y'ar wace Asad; shi talaka ba mutum bane? Ko y'ar shugaban k'asa ce indai ba y'ar gidan sarauta bace y'ar talaka ce a gidan sarauta. Indai da tarbiya da ilimin addini zance ya k'are. Inda za'a samu matsala in aka bincika aka gano wata dabi'a a tare da ita ko tare da dangin ta, kasan gida irin wannan baya d'auko irin wannan yaran."
Jin abinda mai margaba yace sai kuma ya rud'e amma bai nuna hakan ba shima mai martaba ya lura bai san yayi maganar ba sai ya murmusa kawai baice komai ba.
"Ina neman izinin tafiya" ya fad'a kai a k'asa. Mai martaba yace, "Dan kada a fad'a min wacece sirikar tawa ya saka zaka gudu?, to Allah ya tashe mu lafiya." Murmushi sosai Asad yayi har hakoran sa suka bayyana yana son zama da mahaifin sa shine yake damuwa da damuwar sa sab'anin Mama da kanta kawai ta sani. Mik'ewa yayi ya fita yana jin sanyi a zuciyar sa.
_Na bayyana a zahiri na a gare ka yau Asad, kayi gaggawar kawo ni rayuwar ka kafin su hallaka, Asad kana da tarin mak'iya na jikin ka sune mak'iyan ka, zanzo gare ka Asad amma akwai tarin qalubale a gaban mu, sai ka jure sai kuma ka daure._ a firgice ya tashi zaune ya dafe kansa abinda ta fad'a masa yana dawo masa cikin kansa, tabbas Rauda ce domin fuskar ta yau ta bayyana sosai a gare shi, itace domin ya ganta ido da ido sosai ta fito tarr itace.
"Meyasa take taimako na tun a mafarki?." Ya tambayi kansa gabad'aya a rud'e yake hankalin sa kuma a matuk'ar tashe.
Agogo ya kalla yaga karfe biyu na dare ya tashi ya shiga band'aki ya d'auro alwala ya fito ya tayar da sallah. Ya jima yana sallah har k'arfe hud'u kafin ya koma lazimi yana zaune har lokacin k'irjin sa bugawa yake yi bai dawo daidai ba. Ana kiran sallah ya tashi ya fita zuwa masallacin cikin gida.
Safiyar asabar yaji gabad'aya babu abinda yake so ya gani ya kuma saka a idanun sa face fuskar Rauda, ya kasa kai komai bakin sa Rauda kawai yake son gani, k'okarin daurewa yake amma abin yaci tura zuciyar sa sake azalzala masa take yi a kan haka dak'yar ya iya zama a gidan bai fita yaje gidan su ba.
Koda ya fita daga gidan Company ya wuce ya tarar da Hafiz suna ta had'a kayan wanda sukayi order za'a kai ya wuce office gabad'aya jikin sa babu k'wari. Bai bar company ba sai yamma wajan cin abinci yaje yaci ya gito ya shiga mota ya nufi unguwar su Rauda kan sa tsaye.
A k'ofar gidan ya tsaya yana kallon gidan nasu amma ya rasa me ya kawo shi sai kallon gidan yake kawai amma ya rasa dalilin da ya kawo shi, hango ta yayi a tsaye da sandinan ta tana dariya ita da wata babbar mace mai shigen maka da ita da alama Yayar tace.
K'arewa mata kallo yake cikin hijjabi mara tsaho fuskar ta a washe da kyakykyawan murmushi a kan fuskar ta, lumshe idanun sa yayi gaban sa na fad'uwa sosai yana kallon ta domin ta k'ara yi masa kyau ga annuri da take fitarwa. Numfashi ya sauke mai nauyi bai daina kallon ta ba bai kuma sauke glass ba har matar da suke tsaye ta bar k'ofar gidan ita kuma koma cikin gidan.
Sai da ta bar wajan ya lumshe ido ya dafe saitin zuciyar sa da take bugawa da sauri ya bud'e ido daidai lokacin da wayar sa ta sake cika masa kunne da ihu, sai da ya dawo hankalin sa ya dawo nutsuwar sa duk da zuciyar sa na bugawa, kallon wayar yayi yaga sunan Mama bai yi k'asa a guiwa ba ya d'auka ya saka a kunne, "Asad ka dawo gida Hydar ya farka!" ta furta daga can b'angaren baice komai ba ya yanke wayar ya tashi motar sa zuwa gida.
_tirkashi fan's mai Asad yake nufi da Rauda ne?._
*KWANTAN ƁAUNA*
©️ *Nana Haleema.*
*Book 1*
*020.*
Lokacin da Asad ya shiga falon Mama ya tarar da Hydar a zaune ya rame sosai yayi haske jikin sa babu k'arfi sai idanu da yake bin mutane dashi, a nutse ya tako ya zauna kusa dashi ya kalli Mama da take zaune itama a gefen sa sai Suhaima da take tsaye yace, "Sannu Hydar, ya kake ji?."
Maganar sa bata fita sosai yace, "da sauk'i."
"Asad ka taimaka masa yayi wanka ya sai yaci abinci." Asad ya kalli Hydar yace, "Zaka iya tashi?." Kai ya d'aga alamun eh ya rik'e shi suka tashi zuwa d'akin da yake kwance. A nan yayi wanka aka kawo masa kaya ya saka yayi sallah ya fara cin abinci. Suna zaune zagaye dashi ya gama cin abincin ya sha magani kana ya kalli Asad yace, "Akwai yarinyar dana buge deaf a tambaya min Dr Yasir tana ina."
Ran Mama ya b'aci jin da abinda ya fad'a tace, "na saka an sallame ta." Hydar ya kalli Mama ya dafe kansa yace, "meyasa Mama? Yarinyar tana buk'atar taimako sai an mata aiki fa."
Mama tace, "kuma indai nice na haife ka dole ka bar maganar ta ba, bana son sake jin zancen wata wacce ka buge a bakin ka ya wuce ka manta da babin ta." Zaiyi magana Asad ya d'an ja rigar sa sai yayi shiru ya saukar da kansa k'asa baice komai ba. Tsaki Mama tayi tace, "kana farkawa ka rasa da abinda zaka tashi sai maganar wata banza y'ar talakawa, kenan daman da ita ka kwanta a ranka da yake baka da hankali, na tsani yarinyar tsana mai muni." Babu wanda ya ce komai ba sukayi shiru zuwa lokacin magariba ta kawo kai.
Tare suka fita da Hydar sai a sannan jama'ar masarautar suka san da farkawar sa aka dinga gaishe shi zai amsa duk da ba wani k'arfi ne dashi ba.
Bayan an idar da sallah suka je wajan mai martaba daga nan suka dawo apartment d'insu. Aliyu baya nan Hydar ya zauna a falo jin jiri yana d'aukar sa yana sauke numfashi yace, "Deaf ban san inda zan ga yarinyar ba, basu da kud'in da za'a yi mata aiki in wani abun ya same ta Allah sai ya saka mata."
"Relax" abinda Asad yace kenan daga nan bai kuma cewa komai ba.
"Deaf ina cikin damuwa tunda na tashi itace tazo raina, ta yaya zan ganta ina so na ganta wallahi."
Wani irin kallo Asad yayi masa jin abinda yace nan take sai gaban sa yayi mugun fad'uwa amma bai nuna masa ba bai kuma yi masa magana ba.
Hydar ya yi shiru amma zuciyar sa gabad'aya tana ga tunanin inda zai ganta gabad'aya hankalin sa yana kanta gashi bai san inda zai nemo ta ba abin duk ya dame shi.
Washe gari Asad tare da Hydar suka fita zuwa company dan ya samu k'arfin jikin sa suna tare har yamma, a yamman aka kawo masa passports d'insu Rauda an buga musu visa ticket ya rage a siya, bayan tafiyar wanda ya kawo passports Hydar ya kalle shi yace, "Passports d'in su waye?." Bai bashi amsa ba sai da ya gama abinda yake yi ya tashi suka shiga mota suka bar company.
Gidan su Rauda ya wuce Hydar bai san gidan ba yaga dai sun tsaya a k'ofar gidan ya kalli Asad yace, "Ina ne nan?."
Bai magana ba ya sauke glass d'in motar nan ya hango Khalil yana ta wasa ya yafito shi da hannu ba musu ya k'araso Asad ya kalle shi yace, "Abban ka yana nan?." Khalil yace, "Eh yana nan."
"Jeka kace ana sallama dashi" yana fad'a ya ja bakin sa yayi shiru Khalil ya shiga cikin gidan.
Hydar yace, "Asad ban gane ina muka zo ba fa." Kallon sa yayi baice masa komai ba a lokacin Baba ya fito ganin haka ya saka Asad ya fito daga motar shima Hydar ganin ya fita shima ya fito lokacin Baba ya k'araso, hango Asad sai ya washe baki ya k'araso da sauri yana zuwa yace, "Barka da zuwa ranka ya dad'e." Murmushin k'arfin hali Asad yayi suka gaisa da Baban Hydar ma ya gaishe shi kafin Asad yace, "Shine Hydar wanda ya buge ta jiya ya farka daga rashin lafiya" ya fad'a yana nuna masa Hydar.
Baba ya washe bakiyace, "Allahu Akbar! Naso na gane fuskar sa yadda ya rame ya saka ban gane shi ba, sannu Hydar ya jikin ka?." Fad'ar hakan nan take sai Hydar ya gane shi shima yace, "Alhamdulillah, ya jikin ta?."
"To jiki da sauk'i dai za'a ce."
"Zan iya ganin ta?" Hydar ya fad'a yana kallon Baba.
"Mai zai hana, bara na sanar dasu shigowar ku" ya fad'a yana komawa ciki da sauri Asad baice komai ba har Baba ya dawo yace su shigo. Yana gaba suna binsa a baya Hydar na k'arewa gidan kallo har suka shiga ciki. suna zaune dukkan su a kan tabarma a tsakar gidan suka shigo da sallama cikin takun nutsuwa da k'asaita, dukkan su manyan kaya suka saka sun karb'i jikin su sosai tunda suka shigo khamshi ya mamaye gidan. S tare suka amsa Rauda da take zaune a akan kujera ta d'ago ido suka had'a ido da Asad nan take gaban ta ya fad'i tayi saurin janye idanun ta.
"Bismillah ku k'araso mana" Baba ya fad'a yana nuna musu wajan zama. Basu musa ba suka zauna suka gaisa da Umma kafin Hydar yace, "Mama ayi hak'uri nayi fama da rashin lafiya ne shiyasa ban kuma waiwayon ta ba, amma in sha Allah komai zai wuce yanzu." Umma tace, "Babu komai lafiya ai tafi gaban wasa, Allah ya k'ara lafiya." Hydar ya amsa da amin kafin ya kalle ta yace, "Ya jikin ki?."
Sai da ta saukar da kanta k'asa kafin tace, "Da sauk'i." Bai kuma cewa komai ba Asad daman tunda aka gaisa bai sake magana ba. Khalil ne ya shigo yana fad'in, "Baba ga Yaya Anas yazo." Baba yace, "To ina zuwa." Hydar yana so ya basu kud'i amma bai fito da komai ba duk sai yaji kunya tana baibaye shi ganin hakan Asad ya d'auko kud'i a aljihun sa ya ajjiye kusa da Umma sannan yace, "ku fara shiri tafiyar ku baza ta wuce nan da sati ba" yana fad'ar hakan ya mik'e sai Hydar ne yayi musu sallama dan yasan Asad ya gama magana suka fita tare da Baba.
A tsaye jikin mota suka ga Anas Baba ya k'arasa gare shi suna tare dasu Asad, har k'asa Anas ya gaida Baba kafin Baba yace, "Ranka ya dad'e wannan shine Anas mai neman auren Rauda, yana ta d'awainiya damu hatta maganin ta shine yake siya duk da lalurar da ta same ta bai saka ya guje ta ba" ya fad'a yana kallon Asad yana fad'a masa fuskar sa a washe da a nutsuwar magana da kamar Asad.
Abinda Asad yake ji a zuciyar sa sabida abinda Baba yace bai tab'a jin irin sa ba tunda Allah ya kawo shi duniya, k'irjin sa har d'agawa yake sabida bala'in tashi hankalin da bai san zai same shi ba a lokacin, bai tab'a jin k'una da rad'ad'in da yake ji ba tunda yazo duniya. Suka yake ji a zuciyar sa in ya tuna kalaman Baba da yake cewa 'mai neman auren Rauda' nan
All Chapters
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 18 Chapter of 24