bar maganar nan matuk'ar yana son zaman lafiya a cikin gidan nan." Aliyu yace, "ko kuma Mama ta hak'ura ba ta bar shi da ita domin kuwa da zarar maganr taje gaban Takawa zancen ta ya k'are kuma yanzu haka suna kan hanyar zuwa gare shi."
A haukace Mama tace, "Kira min shi Aliyu, maza ka kira shi" ta fad'a jikin ta har rawa yake tana zaga falon tana ji kamar zuciyar ta zatayi bindiga ta fashe. "Mama baiyi picking ba nasan daman ko Mama ce ta kira shi yanzu bazai d'auka ba balle kuma ni" yana fad'ar hakan ya fita daga falon hankalin Mama da Mum ya sake tashi Mama kamar ta zubar da hawaye haka take ji.
A b'angaren su Asad ana idar da sallar la'asar Asad ya shiga b'angaren su Hydar ya fita bai wuce ko ina ba sai wajan mai martaba ransa a b'ace. Basu san mai ya faru ba dukkan su sun samu kiran gaggawa daga gare shi har Asad suka isa b'angaren nasa ba tare da sanin abinda ya faru ba. A zaune Asad ya tarar da Mama ga Hydar a gefe nan take gaban sa ya fad'i abinda ya faru yazo ransa ganin su kad'ai ne a ciki ya samu waje ya zauna Mai martaba yace, "Asad abinda Hydar ya sanar dani haka ne?." Shiru Asad yayi dan bai san mai Hydar yace ba ya d'ago ya kalli Hydar d'in kafin ya girgiza kai yace, "Haka ne takawa."
"To ma sha Allah. Bazan ce komai ba a yanzu zan tura aje a tawo min da mahaifin yarinyar da kuma ita yarinyar, Hydar kaje kazo dasu ka kai su b'angaren baya dan bana son cikin gida su san abinda yake faruwa in yaso in kazo dasu ka sanar dani zan zo da kaina."
Hydar ya amsa da to ya tashi ya fita babu wanda ya kuma magana a cikin su mai martaba baice komai ba ran Mama a b'ace tana ta hararar Asad shi kuma kansa na k'asa baya ganin me take yi. Ba jima Hydar yazo da girmawawa ya sanar dashi gasu can yazo dasu ya yace, "Ku je can gani nan zuwa." Tashi sukayi Mama kamar ta shak'e wuyan Asad haka take ji sai binsa take da kallo tana kwafa suka fita shi kuma ya kasa ma had'a ido da ita.
Ta wata k'aramar k'ofa mai martaba ya fita babu wanda ya lura da fitar sa sai gashi ya bayyana a harabar b'angaren da yace a ajjiye su ya shiga falon kowa ya mik'e tsaye banda Rauda da take k'okarin tashi ya kalle ta yace, "yi zaman ki" ya fad'a yana k'arasowa ya zauna a akan kujera duk suka zauna a k'asa.
Mai martaba ya kalli Baba yace, "Malam Adam mun same ku lafiya?." Baba jikin sa har rawa yace, "Allah ya ja da ran mai martaba, lafiya lau."
"To ma sha Allah. Ya akaji da abinda ya faru kuma?."
"Mun gode Allah ranka ya dad'e."
"Muna sake baku hak'uri akan abinda aka yi muku tabbas ba'a yi muku adalci ba. Meye sunan naki?" Mai martaba ya fad'a yana kallon Rauda.
"Rauda" ta furta a hankali mai martaba yace, "Kiyi hak'uri kinji Rauda duk abinda aka aikata muku ga wacce ta saka nan, babu babu wanda yasan abinda ya faru sai bayan ta saka an aikata d'in da baza mu bari hakan ya faru ba" ya fad'a yana nuna Mama da take zaune a gefe kana yace, "Mahaifiyar su ce komai ya faru itace ta saka ayi muku. gaku gata nan in kun yafe mata a k'yaleta in baku yafe ba kuma a yi mata hukunci daidai da ita kowa yasan mulkina baya lamuntar zalunci koda jinina ne ya aikata."
Rauda zatayi magana Baba yayi saurin katse ta yace, "Allah ya k'arawa sarki lafiya, babu komai mu hakan ma da akayi mana an nuna mana mahimmacin mu, an nuna mana muna muna da darajar da Mai martaba da kansa sai bamu hak'uri,ya wuce mun gode sosai." Mai martaba yace, "ka barta tayi magana ita aka yiwa ba kai ba, Fad'i abinda yake ranki."
Rauda ta kalli Baba yana kallon ta tace, "Babu komai ya wuce." Mai martaba yace, "kin tabbatar ya wuce ba'a takura ki ba?."
Rauda tace, "Ya wuce ranka ya dad'e."
Mai martaba yace, ma sha Allah. Rabi'atu basu hak'uri" ya fad'a yana kallon Mama.
A firgice ta kalli Mai martaba suka had'a ido kallon da yayi mata ya saka ta d'auke kai tana girgiza kai tare da taune leb'en ta na k'asa cikin wani abu wai shi bak'in ciki da taikaici ta kalli Rauda da take kallon ta itama ido cikin ido ta cize bakin ta kafin tace, "Ayi hak'uri." Murmushin jin dad'i Rauda tayi har cikin zuciyar ta taji abinda aka yi musu ya wanke tass ko babu komai mace mai izza ta basu ko iya nan sun ci riba.
Baba ya washe baki yace, "babu komai ranki ya dad'e, ya wuce." Mai martaba yace, "mun samu labarin an buge wata yarinya kwanaki amma bamu san ba'a kula da lafiyar ta ba tunda Hydar ya kwanta ciwo, Shima muna neman afuwa a kan hakan kuma nasan Asad zaiyi duk abinda ya dace in sha Allah." Baba yace, "Allah ya taimaki Mai martaba, komai ya wuce mu a wajan mu. Kamar yadda mai martaba yace Asad yana iya bakin k'okarin sa akan rashin lafiyar Rauda."
Mai martaba ya girgiza kai yace, "mun gode da karamcin ku a gare mu baki d'aya, muna tabbatar muku da babu abinda zai sake samun iyalan ku ta k'ark'ashin wannan gida in sha Allah."
Shiru babu wanda yayi magana kafin mai martaba yace, "Tunda hakan ta kasance ina neman wata alfarma a wajan ka." Baba yace, "A wajena kuma Ranka ya dad'e?."
"Eh wajan ka."
"Umarni shine naka a gare ni ba alfarma ba."
"Alfarmar dai nake nema ka amince na fad'i abinda nake so."
"A shirye nake da sauraron ka, Allah ya ja zamanin ka."
Mai martaba ya kalli Asad yaga kansa yana k'asa ya kalli Mama yaga tana kallon sa kafin ya kalli Baba yace, "D'ana Aliyu wanda nakewa lak'abi da Asad gashi a gefe yaga y'ar ka Rauda ya yaba da hankalin ta da kuma tarbiyyar yace yana so. Bama shi ba ni kaina na yaba da ilimin ta da kuma tarbiyyar ta da nuna b'acin ranta a kan abinda zai tab'a iyayen ta. Muna neman alfarmar a bashi ita inda damar hakan!." A take k'irjin mutane hud'u suka buga a wajan, Mama, Asad, Rauda, da Baba. A tare suka kalle shi shi kansa Asad d'in ya gigice bai san abinda zai fad'a ba kenan dan bai shiryawa hakan ba a lokacin kwata-kwata.
Baba baki na rawa yace, "Allah yaja zamanin mai martaba, maganar da naji ce nake kokwanto anya ba mafarki nake ba?." Mai martaba yace, "ba mafarki kake ba Malam Adam abinda kaji gaskiya ne. Amincewar ka da tata amincewar nake so a d'aura auren ranar juma'ar nan mai zuwa dan bana son a d'auki lokaci. amincewar ku kawai nake nema amma babu dole in taga bai mata ba karta takura kanta, in kaga kaima baza ka iya bashi auren ta ba duka ba abin damuwa bane. Ina tambayar ka a matsayin siriki ne ba matsayin shugaba a gare ka ba, ka kalle ni matsayin sirikin ka ka fad'a min amsar da take zuciyar ka. Zaka iya bawa Asad auren Rauda ko A'a?!."
Tirk'ashi!ππΌββοΈπ
#Vote
#Share
#Comments
*KWANTAN ΖAUNA*
Fitattubiyar 2023
Β©οΈ *Nana Haleema.*
*Book 1*
*023.*
Kallon kallo ake tsakanin Baba da Rauda da kuma Mama kowa fuskar sa d'auke da rud'ani, Asad dai kansa yana k'asa ko motsin kirki ya kasa balle ya iya d'ago idanun sa yace wani abun yayi shiru yana jiran yaji abinda za'a ce dan zuciyar sa duka take kamar ana doka ganga. Baba ya kasa magana shud'ewar wasu dak'ik'u kana Baba yace, "Allah yaja da ra. mai martaba, abin ne naji shi wani iri shiyasa na kasa magana."
Mai martaba yayi murmushi irin nasu na manyan mutane yace, "Kar ka damu na baku lokaci kuje kuyi shawara in tana sonsa Alhamdulillah haka muke fata, in kuma bata so kar ayi mata dole a barta da ra'ayin ta. Ina sauraren ku nan da wasu kwanaki da kun yanke hukunci a sanar dani ayi komai a gama cikin watan nan bana so a d'auki lokaci mai tsaho."
Baba yace, "angama ranka ya dad'e, in sha Allah zaka ji komai daga bakina kamar yadda ka umarta. Allah ya k'ara lafiya da nisan kwana, ya jiqan iyaye ya sanya suna Aljanna." Da amin suka amsa dukkan su kafin mai martaba ya kalli Hydar yace, "A mayar dasu gida, a kuma tabbatar an basu kulawar da ya kamata bana so su nemi wani abun su rasa." Ba musu Hydar ya tashi suma suka tashi akayi godiya suka fita.
Falon ya rage daga Asad sai Mama sai mai martaba babu mai magana a cikin su kowa ta ciki na ciki, hawayen bak'in cikin da Mama take b'oye ne suka zubo mata daga idanunta ta share tana kallon wani wajan daban zuciyar ta nayi mata zafi da k'una sabida k'askantar da akayi a gaban talakawa.
"Dole ki kawar da kai gefe ai domin abinda kika aikata kin san ba abu bane mai kyau, da ace yarinyar nan bata furta ta hak'ura ba wallahil azim ko wanne hukuncin da take so ayi miki sai an miki sai dai hakan ya zama silar bugawar zuciyar ki sabida bak'in ciki. Yarinyar da Hydar ya buge har ta samu matsala a k'afar ta ki saka a kore ta daga asibiti kawai sabida banza ra'ayin ki..? Ke kullum a idanun ki talaka da mai kud'i suna da banbanci, dan ta kasance talaka wannan Allah ne ya k'addara amma d'anki ne yayi silar nakasar ta amma ke ko yaushe tunanin ki daban yake dana kowa. kin kyauta ai abinda kika aikata yayi miki kyau" ya fad'a yana mik'ewa dole ta mik'e Asad ma ya mik'e tsaye.
Ya sake kallon ta yace, "Ko nan gaba kika sake aikata wannan kuskuren Rabi'a sai na saka anyi miki hukuncin da baki tab'a tunani ba, sai na nuna miki talaka daidai yake dake a duniya tunda ke mutum ce shima mutum ne. Ki kuma ji tsoron ranar da zaki je neman alfarma a wajan talaka" ya fad'a da zallar b'acin raina tare dashi.
Tare suka fita da Asad yana kallon irin kallon da take masa take gaban sa ya cigaba da fad'uwa har suka koma b'angaren mai martaba Asad baya tare da nutsuwar sa nutsuwar sa. Ganin hakan ya saka yace, "Kada ka damu Asad zan tsaya maka a wannan karon sai naga ka samu abinda kake so koda ita d'in bata so, bazata cigaba da tauye maka hakki ina kallo ba a wannan karon alqawari nayi maka."
Kamar zaiyi kuka ya kalle shi yace, "Abba amma zatayi fushi dani kuma ni ban saka Hydar ya fad'a maka abinda yake faruwa ba, at least ban tabbatar da abinda nake ji akan yarinyar ba, a janye maganar Abba." Mai martaba ya dafa kafad'ar sa yace, "kana sonta, Asad na tabbatar da kana sonta. itace mace ta farko da saka kanka a cikin lamuran ta, kuma fuskar ta kake gani a mafarkin ka Asad. Akwai tarin alkhairi a zaman ka da ita nayi istikhara akan hakan Allah ya nuna min kaima yana da kyau kayi. Ka bawa zuciyar ka abinda take so kar ka cutar da kanka a wannan lokacin kamar yadda ka saba yi a baya, ka daure ka zama namiji ka Jajirce kar barazanar babar ka ta baka tsoro ka tsaya a akan ra'ayin ka. Shigowar ta rayuwar ka itace zata canja komai Asad, ka rubuta ka ajjiye koda bana raye hakan zata kasance amma dole ka jure, ka ajjiye wannan raguwar zuciyar taka ka zama namiji kamar kowa dan Allah" mai martaba yana gama fad'a yana kallon sa.
Asad kansa yana sunkuye mai martaba ya kuma cewa, "Yau ba gobe ba ina so kaje gidan su yarinyar ka fara yak'in neman amincewatar, tana da ilimin addini babu abinda ban sani ba a kanta. Tana da tarbiyya mai kyau duk da ta kasance kuna da banbanci ta b'angaren matsayi amma itace daidai da kai tunda kana sonta. Ilimin ta da tarbiyyar ta shine ya saka na sake baka goyan baya d'ari bisa dari ta ko wacce fuska bata da aibu haka dangin ta. Ka nemi amincewar ta umarni nake baka Asad." Yana gama fad'ar hakan ya shige ciki ya bar Asad da sanyi jiki dole ya jawo k'afar sa ya nufo b'angaren Mama k'irjin sa na bugawa.
Zagaye take hankalin ta a tashe ita kad'ai fuskar ta har ta fad'a sabida tashin hankalin da k'unar zuciyar da take ciki, jin motsin da taji ya saka ta juyo ta kalle shi ya sunkuyar da kansa k'asa baice komai ba ta gyara tsayuwa ta fuskance shi tace, "Asad kayi gaggawar samun mahaifin ka ka fad'a masa kai ba son yarinyar nan kake ba, ka janye maganar nan tun kafin nayi maka baki Asad" ta fad'a tana nuna shi.
Asad ya sauke numfashi amma baice komai ba ta kuma cewa, "in ma asiri tayi maka zan warware shi amma baza ta tab'a zama mallakin ka ba ko bayan raina, babu kai babu ita tsakanin ka da ita taimako ne bayan shi babu maganar aure Asad!."
Yadda ta d'aga murya ya saka shi runtse idanu zai iya cewa lokaci na farko kenan da Mama ta d'aga murya dan kowa yasan bata d'aga murya in tana magana a ganin ta fad'uwa ne a gare ta ya bud'e a hankali kana yace, "Ina sonta Mama!."
Tassss shine sautin abinda ya sauka a kuncin sa daidai lokacin da kalmar mama ta gama fitowa daga bakin sa. Rai a b'ace take kallon sa tana nuna shi da yatsa da yake tsaye har lokacin tace, "K'arya kake Asad! Baka isa ba ba kuma zaka isa ba. Meye a wajan ta da zaka so ta?, me take dashi?, bak'a, gurguwa, y'ar talakawa, y'ar tallan abinci a kan titi me zaka nema a wajan ta wanda Jidda bata shi?. Meyasa baka son Jidda sai ita?."
Yayi shiru zuciyar sa na zafi rana ta farko kenan da Mama ta d'aga hannu ta mare shi duk sai yaji duniyar tana yi masa zafi komai yana fice masa daga ransa.
"Asad Jidda itace daidai kai mahaifin ta ambassador ne, na zab'e ta sabida ita kanta a k'asan ka take talakar kace dalilin da ya saka ban nemo jinin sarauta irin ka ba dan bana son matar da zaka aura ya zama tana had'a kanta da matsayin ka. Ita ta dace da rayuwar ka ba waccan banzar ba, ka tuna kai d'an sarki ne, wanda ya haifi mahaifin ka sarki ne, wanda ya haifi mahaifiyar ka sarki ne, wanda ya haifi mahaifin mahaifiyar ka sarki ne, kaine kuma sarki mai jiran gado me zakayi da y'ar talaka mara ilimi da wayewa!?."
Ta bugi kujera ta cigaba da fadin, "Kask'anci ne a gare ni da dangi na gabad'aya matuk'ar ka auri yarinyar nan, baza ka aure ta ba indai ina da rai ka ajjiye wannan batun indai kana son farin cikina, in kuma ka dage akan kud'irin ka ka tabbatar min da y'ar talakawa ta fini a wajan ka." ta fad'a tana nuna shi da yatsa idanun ta a waje sabida bala'i da bak'in ciki.
Muryar sa a tausashe kamar ko yaushe yace, "K'addara ce ta had'a ni da ita Mama ba soyayya ba, kece mahaifiyata wacce ta haife ni ta raine ni na tsahon shekaru da dama har gobe take kan bani tarbiyya. Ta yaya zan had'a matsayin ta da nata wacce na tsince ta a sama?, ta yaya zan fifita wata a kanta?. Ki amince min Mama ki yarje min kaddarar da ta had'a ni da ita na d'auke ta tamkar jarabawa ce wacce Allah ya k'addaro min, ki bani dama na amshe ta hannu biyu-biyu na rubuta nayi nasara. Agajin ki nake nema akan komai a wannan gab'ar ma yarjewar ki nake nema. ki duba yanayin da abin yazo ban shirya zuwan sa ba balle nayi rigakafi tun kafin lokacin, K'aunar ta nake ba sonta nake ba, ki amince min a wannan lokacin na gayyato ta zuwa rayuwata" ya k'arasa fad'a yana runtse idanun sa dan shi kansa ji yake kawai maganar na fitowa daga zuciyar sa zuwa kan harshen sa.
K'are masa kallo take cike da dunbin mamaki jin doguwar maganar da ya tsaya yana yi mata akan wata mahaukaciyar yarinya da bata wuce mai bawa doki abinci a gidan su ba, ba k'aramin hasala ta sake yi ba tace, "baka isa ba Asad! wallahil azim baka isa ba, dole a wannan karon ma kaso abinda nake so in ba haka ba zaka jawowa yarinyar bala'i da masifar da baza ta iya fidda kanta ba; zan iya sakawa a kashe ta kuma na kashe banza da wofi kai ka sani, ina tabbatar maka matuk'ar ka bari abinda mai martaba ya fad'a ya tabbata wallahi sai kayi dana sani!."
Idanun sa sunyi jahh sosai sabida tashin hankalin da zuciyar sa take ciki, zai iya rantse da Allah bai tab'a tsintar kansa a yanayi mara dad'i kamar wannan lokacin hatta yanayin fuskar sa ya koma ja. K'asa tayi da murya ta juya masa baya tace, "Yau ni kake fad'awa doguwar magana akan wata banzar mahaukaciyar yarinya ko Asad?, baka tab'a min irin wannan maganar mai tsaho ba sai yau sabida ta fini a wajan ka, ina cewa ga abinda nake so kana cewa kai ba shi kake so ba sabida ita ko Asad....?" ta k'arasa maganar a sanyaye sai kuma ta ta zauna akan kujera tana hawaye.
Ganin hakan hankalin Asad ya tashi ya bita ya zauna a k'asan carpet yace, "Allah ya wuci zuciyar mahaifiyata, ina rok'on mahaifiyata akan tayi hak'uri ta daina zubar da hawaye akan Asad" ya fad'a a sanyaye yana dafa guiwar k'afar ta kamar shima zaiyi kuka.
"Asad kar ka aure ta, bana sonta wallahi na tsane ta kar ka aure ta Asad" ta fad'a tana rik'e hannun sa gam hawaye na zuba a idanun ta.
Kamar zaiyi kukan yake ji zuciyar sa tayi rauni matuk'a tana cigaba da bugawa rana ta farko da Maman sa take kuka a kansa hakan ya saka yace, "Zan iya hak'ura da komai akan Mamana duk k'aunar da nake masa, Allah ya wuci zuciyar ki."
Hydar dake tsaye a bayan su ya shigo yana fad'in, "A karo na farko meyasa Mahaifiyata baza ta amince da ta amince da abinda Asad yake so ba....? ya bar aikin sa da yake buri tun yana yaro sabida Maman sa, ya bar damammaki da yawa a rayuwar sa sabida Mahaifiyar sa abinda Mama take so shi yake yi. Baya son Jidda amma ya amince da ita duk sabida Mama tana so yau kad'ai Mama ya nuna yana son Rauda meyasa mahaifiyar mu bazata amince masa ta bashi goyan baya ba?. Meye aibun ta kawai dan ta kasance ta fito daga jinin talakawa shikenan ba abar so bace ba?. Dan Allah dan annabi ranki ya dad'e a yiwa Asad adalci a karon farko a barshi ya aure ta tunda yana sonta" ya fad'a a sanyaye yana durk'usawa a gaban Mama cikin girmamawa.
A fusace tace, "Hydar ba da kai nake magana ba dashi nake magana, ka fice ka bani waje." Hydar yace, "Allah ya wuci zuciyar ki, ina neman afuwa in abinda na fad'a ya b'ata miki rai" ya mik'e ya kalli Asad yace, "kazo muje takawa yana son ganin ka."
Jin abinda Hydar yace ya saka Asad mik'ewa Mama tana rik'e da hannun sa har lokacin tace, "kar ka amince Asad, na yadda zan bar ku kuyi mata ko wanne irin taimako amma banda aure tsakanin ku bazan iya jure ganin wannan ranar ba, zuciyata zata iya bugawa a lokacin da hakan ta faru. Na rok'e ka matsayina na mahaifiyar ka Asad ka sanar dashi baka sonta." Kai Asad ya girgiza kawai ya fita Hydar yabi bayan sa.
Hanyar wajan mai martaba Asad ya nufa Hydar yace, "Zo muje ba wani kiran mu da yake yi, na fad'a ne dan ka taso kalaman ta zasu karya maka zuciya ka hak'ura da abinda kake so" ya fad'a yana jan hannun sa suka nufi hanyar apartment d'in su. Bayan sun shiga Asad ya kalli Hydar a sanyaye sosai yace, "Hydar zan hak'ura kamar yadda Mama take so, bazan iya ganin Mama a halin da take ciki ba ina da damar cire ta kuma na barta; zan hak'ura kawai kome nake ji a zuciya ta zan jure Hydar; ba yau ne na fara rasa abinda nake so ba" ya fad'a a sanyaye yana zama akan kujera ya dafe kansa.
Tausayin sa ya kama Hydar domin yasan soyayya tayi masa mugun kamu lokaci d'aya ba tare da ya shirya ba ya zauna kusa dashi yace, "Baza ka hak'ura ba deaf, sai ka mallake ta domin itace wacce kake so ba Jidda ba. Kana fa da hakki akan Mama ba itace kawai take da hakki a kanka ba tauyen ka da take yi yayi yawa a ko yaushe kanta ta sani bata duba kai halin da zaka shiga in ka rasa abinda kake kawai cikar burin tane a gabanta." Ya juyo ya fuskanci Asad ya rik'e hannun sa yace, "Deaf u lovers her right?."
Ya lumshe ido yace, "Hydar!." Hydar ya katse shi yace, "Na tambaye kane kawai ka amsa min." Shiru yayi yana tunani kafin yace, "eh ina sonta Hydar, but yanzu na bar batun ta sabida Mama."
"Baza ka bari ba abu nawa ka bari sabida Mama a duniya? Meyasa ita baza ta yi maka adalci a wannan lokacin ba?. Tana so ka auri wacce take so kaji zaka aura amma kaima zaka auri wacce kake so ba shikenan ba anyi equal why zata ce kai sai ka hak'ura?."
"Hydar mu bar maganar nan dan Allah" ya furta yana dafe kansa da hannu d'aya kansa yana harbawa yana ajiyar zuciya.
Hydar yace, "Na bari; amma inaso ka sani bazan zuba ido ka rasa abinda kake so a karo na babu adadi ba deaf, zanyi iya yina wajan ganin ka mallake ta" yana fad'a ya tashi ya fita daga falon ya bar Asad a zaune yana sauke numfashi.
_Suna zancen wani Asad ni meye had'ina da wani Asad?._ kalaman Rauda suka fad'o masa a zuciyar sa ya runtse idanu zuciyar sa na bugawa da sauri-sauri ya lumshe idanu yana tuno yadda fuskar duk taji ciwo, wani abu yaji yana masa suka a zuciya ya runtse idanun sa da k'arfi yana cize baki, bud'e ido yayi ya kalli falon kamar mai neman wani abun kafin ya tashi ya shiga d'aki jikin sa duk a sanyaye.
*βββ*
Umma da take sauraron abinda Baba yake fad'a mata da mamaki take binsa da kallo jin abu kamar a shirin film ko a hausa novel tace, "Malam wai auren Rauda ake nemawa Asad d'in? Nifa ban gane ba ka saka ni a duhu wallahi." Baba yace, "Abinda kika ji na fad'a shine, Asad d'in ne da kansa yace yana son tane shiyasa mahaifiyar sa ta turo ayi mana wannan aikin dan daman nasan labarin ta ana cewa bata son had'a jini da talaka; shiyasa ta d'auki wannan matakin kafin abin yayi nisa."
Umma ta rik'e baki tace, "Tabd'ijam,
All Chapters
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 21 Chapter of 24