kanta ba kenan? Da asuba Rahma take tafiya amma ke y'ar ki y'ar gwal ce baza taje ba sai ku zauna haka ni kinga tafiya ta" ya fad'a yana ficewa ya bar Umma a tsaye.
Ummulkhairi ta taso tace, "Umma barshi ba sai munci komai ba ni zan iya dawowa haka in kina da wani abun ki bawa Khalil kawai." Girgiza kai tayi tace, "A'a Ummulkhairi muje ina da naira d'ari biyu ku siyo awara kuci ku tafi." D'aki ta shiga ta d'auko musu Khalil ya siyo musu awara suka ci suka tafi makaranta.
Rauda bayan ta gama aikin gidan tayi wanka shiga wajan mahaifiyar tata ta same ta a zaune tayi tagumi tace, "Umma ki daina saka damuwa a ranki, indai batun abinci ne zan dinga zuwa ina karb'owa sai muje tare da Rahman mu dawo."
"A'a Rauda ban amince da fitar asuba d'in nan ba, ban kuma amince da ki nemo abinda zaki ci da kanki ba Allah bazai hanani abinda zan baku ba in ya hana mu. Kin san bana son rok'o ne ko yawan cewa a bani da y'an uwana duk wanda na tambaya sai ya bani, yanzu ma ina da shinkafa kwano guda da aka aiko min dashi har gida wanke ki dafa canjin awarar da suka kawo ki siyo mai na hamsin yaji na hamsin muci har dare." Da to ta amsa ta mik'e ta tayi abinda mahaifiyarta ta ta saka ta.
Gab da azahar Baba ya dawo ya kwab'e babbar riga ya shiga aikin dafa d'an wake ya gama nan da nan ya kwashe ya lissafa na nawa ne ya zuba masu ya fara kwala musu kira, ita da Rahma suka fito ya kalle su yace, "to gashi nan na naira dubu biyu ne ko waccen ku, wallahi Allah biyar d'ina baza tayi ciwon kai ba." Komawa Rauda tayi ta d'auko hijjabin da tayi sallah ta d'auki abincin ta fita itama Rahma ta fita ba wacce tace kanzil.
Daga can inuwa ta hango motar Anas ta ja tsaki a zuciyar ta ta sake d'aure fuskar ta dan ma kar yaga fuskar da zai kulata, hango ta yayi ta tawo ya fito daga motar yana murmushi tazo zata gifta shi kenan ta jiyo amon sautin muryar Baba yana fad'in, "ki tabbatar sai kin biya ni hamsin d'ina ta jiya dan ba bar miki na yi ba!."
Runtse idanun ta tayi cikin takaicin dizgi irin na Baba ganin wanda yake tsaye ya saka Baba k'arasowa yana fad'in, "Anas yau kaine da rana haka?." Murmushi Anas yayi ya duk'a har k'asa ya gaida Baba ya amsa da fara'a yana fad'in, "Gashi mutuniyar zata tafi wajan sana'ar ta, kana jina da ita ko? Jiya ta yar min da hamsin shine nace sai ta biya ni shine duka ranta a b'ace."
Rauda kamar ta matse bakin Baba haka take ji amma babu dama ta d'aga k'afa zata bar wajan taji Anas yana cewa, "Baba har yanzu Rauda bata daina yawon siyar da abincin nan ba?."
"To ya za'ayi Anas dashi muka dogara ai."
"Bana son yawon Allah ya sani Baba, inda dama a siyar a gida in ya zama dole, in kuma akwai sana'ar da za'a canja a canja basai sun dinga fitowa ba."
Baba ya gyara tsayuwa yace, "Daman sana'ar keke napep d'in nake so to ance kud'i ne dashi tsububu shiyasa muka ganewa abincin."
"Babu damuwa Indai za'a daina bata abincin nan ta fita zan siya maka napep Baba."
"Kai amma nagode d'an albarka, wannan abu mai shegen kud'i za'a siya min? Wallahi na rasa ma me zance maka dan murna." Anas yace, "Babu komai ai Baba."
Baba yace, "talla ai daga yau ta daina zuwa yau d'in ma dan kar ayi asara ne" ya fad'a yana murmushi yana kallon sa.
Kallon Rauda yayi yace, "Rauda na nawa ne abincin?." Kafin ta bada amsa Baba yace, "Na dubu uku ne." Da sauri ta kalle shi shima ya kalle ta ya d'auke kai Anas ya zaro dubu biyar ya bawa Baba yace, "na siye na yau, dan Allah Baba a daina bata tallan nan bana so wallahi."
Hannun Baba har rawa yake ya karb'a yana zuba godiya Anas yace, "Babu komai Baba, zanyi tafiya yau bazan jima ba zan dawo dana dawo za'a kawo maka napep d'in in sha Allah, amma dan Allah a hak'ura da tallan nan dan Allah badan ni ba."
"Ai an gama Anas baza a kuma ba in Allah ya yadda."
"Na gode Baba."
Baba ya kalle ta yace, "bani kular na shiga ciki ku gaisa" ya fad'a yana karb'a ya wuce ya tafi gida ita kuwa ji take takaici kamar ya shek'e ta. Kallon ta Anas yayi yace, "kiyi hak'uri nasan na takura miki Rauda, Ina son ki ne da zuciya d'aya kuma auren ki zanyi." Bata ce komai ba ya kuma cewa, "Dan Allah kice wani abu mana Rauda."
"Me zance to? Na fad'a maka ni ba aure zanyi ba ka fita daga rayuwata ka nemi dai-dai kai amma kak'i."
"Kece dai-dai Rauda ko shekara nawa zakiyi nan gaba zan jira ki har ki shirya yin auren, Ina son ki Allah ya sani."
Bata ce komai ba yace, "ki bani number wayar ki zanyi tafiya ina so muryar ki ta dinga debe min kewa."
"Bani da waya, na gode da abinda ka bawa mahaifina Allah ya saka alkhairi, sai anjima" ta fad'a zata wuce yayi saurin cewa, "Dan girman Allah ki tsaya." Ba musu ta tsaya ya ya bud'e mota ya d'auko farar envelop ya mik'o mata yace, "ki karb'i wannan kya sha ruwa."
Kallon sa tayi ta kalli takardar tace, "na gode."
"Dan Allah ki karb'a."
"Kayi hak'uri bazan iya ba."
"Da hannu a jikin ki kice baza ki iya karb'a ba?, Rauda meyasa kike.mayar da hannun kyauta baya bayan kin san babu kyau hakan?!" Baba ya fad'a yana k'arasowa wajan yana kallon ta.
*KWANTAN ƁAUNA*
FitattuBiyar 2023.
©️ *Nana Haleema.*
*004.*
Runtse idanu Rauda tayi ji take ina ma k'asar wajan ta tsage ta shiga sabida kunya da takaicin abinda Baba yayi mata a wajan, ba'a b'ata yi mata abinda ta jishi a zuciyar ta kamar wannan lokacin ba, kafin ta gama wani tunani har ya k'araso kusa da ita daidai kunnen ta yace, "y'ar bak'in ciki baza ki karb'a ba?." Idanun ta ta bud'e ta kalli Anas da yake kallon su ta kalli Baba da yake ta yi masa murmushi.
K'arasowa yayi ya sake mik'a mata kud'in ta nok'e hannun ta idanun ta na kawo ruwa Baba yace, "Ki karb'a mana ai ba'a mayar da hannun kyauta baya." Hawaye ya sakko daga idanun ta ta mik'a hannu ta karb'a hannun ta har rawa yake Baba ya washe baki ganin kud'in sun shiga hannun ta yace, "Madallah Anas ana ta shan hidima Allah ya saka da alkhairi."
Murmushi yayi yace, "Babu komai Baba, zan koma a gaida mutanen gidan" ya fad'a da girmamawa har yana rage tsayin sa Baba yace, "to ba madallah, a gaida mutanen gidan dakyau."
Anas ya amsa yana wucewa ya shiga mota ya ja ya bar unguwar zuciyar sa kamar sake kwarara masa son Rauda ake yi domin ya tabbatar in ya same ta ya samu wacce ta aure shi ba dan kud'in shi ba.
A guje ya rufa mata baya ya tare ta a soro yace, "Ke Rauda! Bani kud'in mu ga." Ba musu ta mik'a masa ya b'are takarda ya ciro kud'in yana lissfawa. Dubu ashirin ne cif a ciki Baba baki yak'i rufuwa ya raba biyu ya d'auki dubu goma ya mik'a mata goma yace, "sai ku raba ke da babar ki badan na haife ki ba ai da baki samu ba" ya fad'a yana sokawa aljihu yana gyara zaman hular kansa.
Babu yadda ta iya ta karb'a ta wuce ciki ta shiga d'akin Umman ta fuskar ta a chucule, a zaune ta same ta zauna itama Umma tace, "kiyi hak'uri Rauda babu yadda zakiyi da halin mahaifin ki bazai canju ba shekaru sun riga sun tafi, yace min wai saurayin ki ya siye d'an waken gashi nan mu ci har gobe da safe." Rauda ta goge idanun ta tace, "haka yaje ya saka shi a gaba fa Umma har yace zai siya masa napep bayan nan ya bani kud'i naki karb'a Umma yazo ya saka dole sai na karb'a ya raba kud'in biyu ya d'auki rabi wai in da bai haife ni ba ai bazan samu ba. Yanzu Umma dan Allah ko Anas d'in na aura bai riga ya zubar min da mutunci a idanun sa ba?."
"To ya zakiyi ba'a canja mahaifi sai hak'uri, halin sane wannan mazajen yayyen ki ma da basu da kud'i ya suka cika dashi balle Anas mai kud'i?."
"Ga kud'in Umma, ni gidan Yaya Ummi ma nake so naje" ta fad'a tana mik'a mata kud'in ta karb'a tana kallon kud'in tace, "Allah ya sani bana son karb'ar kud'i hannun saurayi musamman ma irin Anas, a haka dai bashi da hali mara kyau amma.....to Allah dai ya kyauta" ta fad'a tana ajjiye kud'in jikin ta duk babu dad'i.
"Amin. Zanje gidan Yaya Ummi Umma, anjima zan dawo."
"To d'auki d'ari biyar ki hau motar zuwa da dawowa kar kije can ki d'ora mata nauyin kud'in mota itama ba k'arfi ne da mijin nata ba." Ba musu ta karb'a ta tashi ta saka talamin ta ta fita.
Bata jima ba ta samu abin hawa ta tafi gidan yayar tata, har k'ofar gidan ta abin hawan ya tsaya ta sauka ta basa kud'in sa ta shiga cikin gida. Tana tsakar gida tana aiki gidan shiru yara an tafi makaranta ta shiga da sallama, amasawa tayi ta d'ago tana kallon ta tana fad'in, "Maraba da amaryar Anas" ta fad'a cikin zolaya tana dariya.
Sai kuwa ta d'aure fuska ta k'arasa kan tabarmar da ta gani a shinfid'e ta zauna tana fad'in, "Allah Yaya shiyasa bana son zuwa gida nan wani lokacin."
Dariya tayi ta bar abinda take yi ta dawo kusa da ita ta zauna tace, "to k'arya nayi? Ke a tunanin ki Baba zai bar Anas ya kufce masa bai bashi ke ba?, ai wallahi ko auren dole ne sai Baba yayi miki sai dai ki mutu."
"Hmmmm bari kawai Yaya, lamarin Baba sai shi."
"Yanzu dai ya Ummana tana lafiya?."
"Lafiya lau, tana gaishe ki."
"Yau ina tallan?."
"Na fito zan tafi Anas yana k'ofar gida shine fa ya siye har da ninkawa Baba kud'in yace a daina bani talla, wai Baba yace masa wai napep yake so ya siya kuma babu kud'i, a tak'aice dai yace zai siya masa."
Yaya ta girgiza kai tace, "Allah ya kyauta, lamarin Baba sai addu'a."
"Amin, kin san me Yaya."
"Sai kin fad'a."
"Mafarki nayi ina makaranta ina karantar aikin jarida." Yaya Ummi ta dara kad'an tace, "Wannan mafarki naki na aikin jarida Allah yasa ya tabbata Rauda."
"Badai a gidan Baba ba."
"Ha! Ha! Daman sai dai in kin auri Anas" Yaya Ummi ta fad'a tana dariya.
Rauda tace, "Kin san kuma kwana biyun nan sai na dinga mafarkin mutane masu fuska iri d'aya ko wanne da rawani a kansa, d'aya yana b'angaren dama d'aya hana haggu, a tsakiya kuma nice in na tafi wajan d'aya sai na kasa k'arasawa in na koma wajan d'aya ma sai na kasa zuwa. Ina yawan wannan mafarkin amma har yanzu na kasa rik'e fuskokin mazan guda biyu."
Yaya tace, "tofa, Allah mai hikima shi kad'ai yasan meya b'oye a cikin mafarkin naki, koma dai meye Allah yasa alkhairi ne shine fatan mu."
"Amin Yaya." Daga nan suka cigaba da hirar su.
*☆☆☆*
Tunda garin Allah ya waye ya samu labarin mai martaba da Asad sun fita hankalin sa yayi mugun tashi, safa da marwa yake a d'akin ransa a b'ace zuciyar sa yske so ta bashi mafita akan Asad amma har lokacin ya kasa samun matsaya.
Tashin hankalin sa da damuwar sa bai san me zasu tattauna da mai martaba ba abinda yake sake d'aga masa hankali kenan ya kasa zaune ya kasa tsaye, Suhail ne ya shigo ganin halin da mahaifin sa yake ciki ya saka yace, "Ranka ya dad'e lafiya?."
"Asad ya fad'a maka dalilin fitar su da mai martaba?."
"A'a bai fad'a min ban ma san zasuyi tafiyar ba."
"Oh god! Laifin kane Suhail da ka bashi madarar nan jiya duk da ba haka ba, yanzu gashi sun tafi taro Kaduna ko ni ba'a nema ba matsayina na waziri a masarauta daga shi sai ni amma ya tafi daga shi sai Asad, me suke so su mayar dani ne a masarautar nan?."
Yadda yake fad'a tashin hankali ya bayyana k'arara a tare dashi Suhail ya kwantar da murya yace, "Kayi hak'uri Abba ka bani lokaci matuk'ar ina raye babu wanda zai mulki garin nan sai kai."
"Kana shirme a haka zan mulki garin?! Ka manta kane ka b'arar da damar da ya k'i shan madarar nan jiya?, kasan mahimmacin maganin da na baka kuwa Suhail?. Na baka sabida na yadda dakai amma sai ka bani kunya" Ya fad'a da fad'a sosai yana kallon sa.
"Abba indai kaine ka haife ni nayi maka alqawarin zan yi duk abinda zanyi wajan ganin bayan Asad bama shi kad'ai ba dukka su ukun a hankali kowa zai k'are, ka bar komai a hannuna barewa baza tayi gudu d'an ta yayi rarrafe ba, zan baka mamaki Abba zan tabbatar maka da Jarumi ka haifa" yana fad'a ya fita daga falon ya ya bar mahaifin nasa a tsaye yana kallon sa.
Murmushin jin dad'i yayi jin abinda Suhail yace ko babu kowa hankalin sa ya kwanta kad'an. Sai a lokacin ya samu dama da kwanciyar hankalin fita daga gidan.
A cikin gidan sarki kuwa Mama tana zaune a falon ta ita da k'awar ta kuma aminiyar ta mai suna Sadiya suna tattaunawa Mama tace, "Sadiya bana son wani tsaiko ko katanga da zata shiga tsakanin Asad da mulkin garin nan, in wani daga cikin yaran nan baiyi mulki a garin nan ba na shiga uku Sadiya."
"Baza ki shiga uku ba ranki ya dad'e, ai mulki ma kamar Asad yayi ya gama ne, in kika cire rashin son magana irin na Asad bashi da wani aibun da za'a hana shi mulki, to a tak'aice ma waye yake da qualities d'in da yake dasu kaf gidan nan da dangin mai martaban?."
Mama tace, "Babu, amma kin san akwai y'an taka haye, tsaf waziri da Sa'adatu zasu shiga su fita wajan ganin buri na bai cika ba, zasu iya ni na sani hatsabibai ne sune suka mayar min da Aliyu na haka, sune suka mayar da Hydar haka, Asad ma ya gagare su ne shiyasa suka kasa yi masa komai. In kika duba su galadima da sauran y'an uwan mai martaba basu damu da sarautar nan ba harkar gaban su kawai suke banda shi. Sadiya idan Asad baiyi mulkin nan ba zan iya mutuwa."
"Baza ki mutu ba ranki ya dad'e sai kin d'auki jikan ki d'an sarki kuma jikan sarki shima kuma sarki, Muma ai ba zuba idanu zamuyi muna kallon su muna da namu hanyoyin da zamu bi wajan ganin mun b'arar da duk wani hatsabiban cin su." Numfashi ta sauke tace, "ni bana jin wannan Sadiya, duk wani jifa da zasu yo mana su sun san nima ba kanwar lasa bace, abinda yake gabana a yanzu bai wuce Asad, baya son mulkin nan ko kad'an balle ya mayar da hankali a kai, ki duba inda yana da hankali yana kuma son abin yadda ake maganar nan da yanzu bai nemi matar aure an yi biki an gama ba?."
Jin hakan sai Sadiya ta sake gyara zama tana murmushi tace, "Abinda ya kamata kenan Ranki ya dad'e, ki tilasta masa yazo yaga Jidda ayi komai a gama tunda sai yana da aure za'a bashi mulkin nan. Kuma Jidda y'ar gida ce ba buk'atar a tsaya bincike ko wani dogon jawabi ba."
"Bari kawai Sadiya, Asad baud'ad'en hali ne dashi baya ganewa ko kad'an abinda yake gaban sa kawai shi yake yi, dole ma a dawo da maganar Jidda ko bai sani ba za'a d'aura auren sa da ita sai dai yaji labari kawai."
Sadiya tace, "A'a ranki ya dad'e sai aita magana kuma a masarautar nan ace dan a bashi mulki kika yi masa auren dole, ki bar shi ayi komai da sanin sa na tabbata ai bazai k'i zab'in ki ba." Kai take girgizawa kafin tace, "Sadiya duk wanda zai shiga tsakani na da mulkin nan sai na kawar dashi, bana son wani tsaiko ko katanga a tsakanin Asad da karagar mulkin garin nan, burina na zama uwar sarki kuma zai ta tabbata, bazan lamunci wani abu da zai b'ullo daga sama ba, ko meye shi bazan lamunta!."
Sadiya tace, "babu shi ranki ya dad'e, ko meye shi munfi k'arfin sa, ko aljan ne a gaba muke dasu balle mutum, haba shi d'in yasan karo da aljani ba dad'i." Kai take girgizawa ta lumshe idanu kafin tace, "Ina da buk'atar zuwa Kano."
"Kina da iko ranki ya dad'e." Cize baki take zuciyar ta nayi mata tiriri bata son duk abinda zai hana Asad yin sarauta ko meye shi.
A b'angaren waziri a zaune suke a katafaran falo na alfarma shida Hajiya uwar gidan sarki kenan sai Suhail a gefen su a zaune waziri yace, "kina da masaniya akan fitar da mai martaba yayi da Asad?."
"Ina nake da ita a gaba dai ya fad'a masa amma bai ce ga abinda zai kai su ba. Nifa na gaji a wannan tafiyar da sukayi Allah kad'ai yasan abinda suka k'ulla shiyasa ko kai ba'a nema ba, a kawar da Asad kawai shine jin dad'i na."
Numfashi waziri ya fesar yana kallon sama kafin yace, "farkawa rana d'aya tsaka a rasa Asad ba k'aramin abu bane sai dai muyi masa abinda zai bi jikin sa ta yadda koda mutuwar yayi ba wanda zai zargi komai." Tace, "to ya za'ayi kenan?." Wani abu ya jawo a gefen sa ya d'auko ya kwance ya fito da wata laya k'arama an nannad'e ta da bak'in zare ya nuna mata yace, "Wannan nake so a saka a k'asan kafitar da yake kwanciya, matuk'ar yayi kwana uku yana kwanciya a kai zance ya k'are. A hankali abin zai dinga shiga jikin sa rana d'aya kawai sai a neme shi a rasa."
Kallon sa take yi hakan ya saka yace, "babban aikin shine wanda zai saka shi a k'asan katitar tasa, kin san ko a cikin nasu d'akin sa yana da wahalar shiga." Hajiya ta kalli Suhail tace, "Suhail shine zaiyi wannan aikin domin Asad ya amince dashi koda ya shiga d'akin sa bazai kawo komai ba."
"Anya Suhail zai iya?, bana so a samu matsala ne kamar wancan lokacin" ya fad'a yana kallon Suhail d'in.
Suhail ya gyara zama yace, "a wannan karon baza'a samu wata matsala ba Abba, zanyi iya bakin k'ok'arina wajan ganin na saka masa ina da tabbacin bazai kawo komai a ransa ba." Hajiya ta girgiza kai tace, "ni nasan zaka iya kai kad'ai ne daman ya cancanci ka yi wannan aikin in ka duba ko bayi basa shiga d'akin Asad, har kawo gobe ban san wacece ko waye yake gyara masa d'aki ba."
Waziri ya girgiza kai yace, "gashi Suhail ka kula kar a samu matsala kamar wancan, ka tabbatar ka saka masa wannan layar a k'asan Katifar sa." Karb'a Suhail yayi ya juya layar a hannun sa sannan ya saka a aljihu yace, "babu damuwa an gama."
"Shikenan tashi kaje" mahaifin sa ya basa umarni ba musu ya tashi ya fita.
"Wai kana da tabbacin wannan abinda ka bayar zai yi mana abinda muke so kuwa?." Kallon ta yayi yace, "kar ki damu ni nasan abinda na bayar ai in kin amince da abinda zan iya to ki yadda."
"Allah ya bamu sa'a."
"Amin. Zan fita yanzu daga gidan daga baya sai ki fita kema." Kai ta d'aga ya fita ta bishi da kallo tana tunanin mafitar waziri ba mafita bace dole ta samo mafita da kanta.
Suhail yana barin gidan cikin gidan sarki ya tafi yana zuwa kasancewar bashi da shamaki da ko ina b'angaren mazan ya tafi, nan ya samu Aliyu baya nan sai Hydar shida abokin Asad Hafiz suna zaune duk da ba hira suke ba, da sallama ya shigo ya samu waje ya zauna yace, "Hydar barkan ku." Amsawa sukayi dukkan su daga nan kowa yayi shiru.
Can ba jimawa Suhail ya mik'e tsaye direct ya nufi k'ofar da zata kai shi d'akin Asad yana gab da shiga Hafiz yace, "Suhail Asad baya nan." Cize baki yayi tare da runtse idanun sa kafin ya juyo bayan ya daidaita fuskar sa yace, "yeah I know, zanyi amfani da toilet d'in sa ne."
"Nooo ga public a falon nan in ma ba shi ba why not kayi using dana Hydar."
Suhail ya kalle shi shima shi yake kallo kafin yace, "okay" abinda yace kenan ya juya zuwa band'akin da yake falon ya shiga badan zaiyi wani abun ba sai dan ya kawar da shakku. Babu wanda ya yi magana a cikin su har ya fito ya zauna nan ma babu wanda ya tanka kowa da abinda yake yi.
Sun jima a haka babu wanda ya motsa kafin Hydar ya tashi ya shiga d'akin sa ya barsu a falo, shi Hafiz yana so Suhail ya fita dan baya son barin sa wajan shi kad'ai shima kuma yana so ya tafi domin ya cimma k'udurin sa.
Dukkan su haushin juna suke ji babu wanda yake magana babu wanda kuma yayi yunk'urin motsawa.
Ganin Hafiz yana yi masa wani kallo na rashin gaskiya kawai sai ya tashi ya fita ya bar masa falon da sabuwar niya da kuduri a zuciyar sa.
*☆☆☆*
Rauda kuwa bayan sallar azahar ta dawo unguwar su tana gab da shiga layin su ta had'u da k'awayen ta guda biyu Walida da Habiba suna fitowa ta tsaya tana kallon su tace, "ku kuma ina zuwa da rana haka?." Habiba tace, "Rauda manyan gari ke daga ina kike?."
"Gidan Yaya Ummi naje."
"Gidan sarki zamu je zan raka Habiba karb'o sak'o" Walida ta bata amsa tana kallon ta.
"Sai kun dawo Allah ya kiyaye." Habiba tayi y'ar dariya tace, "banza matsoraciya, kizo muje."
"Ni y'ar gidan baban mu, rufa min asiri babu inda zani."
Walida tace, "ke kuwa kizo muje mana yanzu fa zamu dawo." Ta rausayar da kai tace, "kin san ni tsoron doki nake kuma wannan dogaran bulalar hannu su na bani tsoro wallahi."
Habiba tace, "to ina ruwan ki da doki muda ba turken su zamu je ba?, dogarai kuma ai ba ciki zamu shiga bafa k'ark'arin mu wajan Gwaggo ta sai mu dawo." Rauda tace, "kedai Habiba dan kin saba dasu ne kina zuwa ni kam tsoro nake ji."
Jan hannun ta Walida tayi tace, "Dallah can muje an fad'a miki baza mu shiga ciki ba ko banza kya kashe kwarkwatar idanun ki dan nasan baki tab'a shiga ba."
Haka suka rankaya tafi suna hira Habiba tace, "Wallahi Rauda ke kam matsoraciya ce meye abin tsoro a doki da dogarai?." Dariya tayi kad'an tace, "to abinda baka saba gani ba mana Habiba ai dole naji tsoro, nifa ban tab'a shiga cikin gidan ba tunda nake, zaki ga ko hawan sallah ake bana lek'owa sabida tsoron doki kar yayo kaina."
"Shiyasa muka ce kizo muje ai" Walida ta bata amsa suna cigaba da tafiya. Sun yi tafiya mai d'an nisa kafin suka iso babban gate d'in farko na gidan sarki.
Ganin Rauda zata bayar dasu jiki har ya fara rawa ya saka ta suka rik'o ta suka shiga ciki, gate d'in farko suka fara wucewa na cikin masarautar suna ta tafiya domin da nisa kafin kaje gate na biyu, sun wuce gate na biyu suka zo wajan dokuna zasu wuce Rauda ta tsaya cak a wajan idanun ta na kawo ruwa tana girgiza musu kai, "Habiba tace, "kizo mu wuce Rauda babu abinda zasu yi miki."
Kai take girgizawa tana kallo dokunan tace, "bazan
All Chapters
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 4 Chapter of 24