Asad in baso kike wani abun ya same ki ba."
Rauda tace, "babu abinda zai same ni sai abinda Allah ya nufa. Sannan babu wanda ya isa ya saka ni yin abinda banyi niya ba, in naga dama kuma zan iya cewa ina sonsa na aure shi kodan naga yadda zaki koma a lokacin."
A fusace Mama ta mik'e tace, "Kee! Kar ki sake hasashen wannan ranar a rayuwar ki domin baza tazo ba har abada. Ke wacece da zaki zama matar d'an sarki jikan sarki kuma sarkin gobe? Wacece ke? Banza kike, bak'a, mummuna, matsiyaciya, gurguwa mai tallan abinci a titi. Ke ko a mafarki akace zaki zama matar sa sai ki amince?."
Murmushin rainin hankali Rauda tayi tace, "Da alama sirikata kina wasa da ikon Allah kinga ta inda muka samu banbanci kenan ni nasan duk wahalar abu a wajan Allah mai sauk'i ne." ta fad'a tana kallon ta itama tana kallon ta.
Mum tace, "kul kar ki sake kiran ta da wnanan sunan bai dace a bakin mace irin ki ba, ki sani akwai matan da suka amsa sunan su mata sama da d'ari da suke son su furta wannan suna amma yafi k'arfin su." Rauda tace, "ba tsoron ta kar na amsawa Asad zan sa aure ba? To ina so ku sani da zarar lokacin da aka d'iba yayi zan tabbatarwa da mai martaba ina son Asad kuma zan aure shi kodan naga ya zakuyi a lokacin da Bak'a, mummuna, gurguwa, y'ar talaka, mai tallan abinci ta zama matar sarki Asad; kuma sirikar y'ar sarkin Kano babar sarkin jibi. Kunga sai ku d'auki bindiga ku harbe kan ku" ta fad'a tana kallon su one by one.
A fusace Mama tayi kanta zata mare ta Mum ta rik'e tana girgiza mata kai Mama a fusace tace, "matuk'ar kika aikata haka zakiyi dana sanin da baki tab'a yi ba tunda Allah ya kawo ki duniya. Zan iya sakawa a b'atar dake daga duniyar gabad'aya wannan ba komai bane a wajena matuk'ar zan samu abinda nake so. Sai na tabbatar baki tako k'ofar gidan sarauta ba balle ki kasance a matsayin da kika lissafa domin yafi k'arfin kaf dangin ki gabad'aya. Zan miki biyu babu, babu Asad babu sauran wanda suka zo taimakon ki su aure ki tunda abin naki rashin kunya ce" ta fad'a tana nuna ta da yatsa cikin murya mai amo da alama kamar wani abun ma bata san tana fad'a ba sabida b'acin rai.
Rauda ta tab'e baki tace, "Ina jira na gani sirika ta, in kuma nice naci wasan na shigo gidan matsayin sirikar ki nice nayi nasara bake ba." K'wafa tayi fuskar ta har ja tayi sabida b'acin ran da take ji a zuciyar ta wanda bata tab'a jin irin sa ba sukayi hanyar waje kafin Mama ta tsaya ta juyo ta kalli Umma da Anty Ummi tace, "Duk abinda ya samu y'ar ku kuyi kuka da kanku.." Rauda ta d'aga murya tace, "babu abinda zai same ni sai alkhairi. Kii gaida min mijina kinji sirika ta!." Juyowa tayi ta kalle ta Rauda tayi dariya kafin ta girgiza kai ta fita daga falon a fusace.
Kallon Rauda Umma tayi bayan sun fita cikin fad'a tace, "Wannan wanne irin rashin hankali kike aikatawa haka Rauda?. Ke kuma babbar banza mai biye mata ina yi mata magana kina tab'a ni wai na k'yale ta tana yiwa wacce ta haife ta rashin kunya, Ni in aka yi min haka zaku ji dad'i ne?. Matar sarki ce fa bamu yi mata komai ba ta saka anzo gida an ci mana mutunci ina ga kun fad'a mata wad'annan maganganun marasa dad'i...? Ba kaina nake ji ba ke nake ji Rauda zata iya yi miki komai dan ganin bayan ki." Yaya Ummi tace, "Umma ai ke baza ki aikata abinda ita tazo tayi mana har cikin gida ba bayan wanda ta saka akazo har gida aka ji miki ciwo, ai wallahi munyi mata da sauk'i ma irin ta'asar da tayi kamata yayi mu kamata mu rama irin abinda ta saka akayi miki. gani take kud'i shine komai zata iya juya mu tayi mana rashin mutuncin da taga dama bata san bata isa ba wallahi. Dan tana matar sarki baza muji tsoron ta ba tunda ita ta d'auko k'afa tazo har inda muke ko zane ta mukayi itace ta jawo."
Umma ta kalle su tace, "ya dai isa haka bana son tashin hankali da yiwa na gaba rashin kunya. Ku tuna a gidan d'anta muke ko a yanzu mun ci albarkacin ta dan ba bata haife shi ba damu zauna ba, da badan yazo inda muke ba da wataƙila yanzu bamu san a inda muke zaune ba. Kar na sake ganin kin yiwa wani haka koda nan gaba ne, wannan ba tarbiyya ce." Umma ta fad'a tana kallon Rauda kafin ta tashi ta shiga d'aki.
Yaya Ummi ta kalli Rauda tace, "Ke me kika yanke game da auren shi Asad d'in?." Rauda ta kalle ta tace, "Ban yanke komai bani domin bana ra'ayin auren sa gabad'aya. Ya cika rainin hankali da yawa bazan jure ba."
"Kuna tare da Anas har yanzu?."
"Tun dai ranar yazo har yace min bashi ya aiko mana da kayan abinci ba ban sake jinsa ko a waya ba gaskiya."
"Kuma baki neme shi ba?."
"Na kira shi jiya amma layin a kashe." Yaya Ummi tace, "inda nice ke Rauda da Asad d'in nan zan aura badan yafi Anas kud'i da mulki ba sai dan na nunawa uwar sa ba'a ja da ikon Allah, duk k'ask'ancin mu da take gani in Allah yace yes bata isa tace no ba duk abinda take ji dashi sai dai tayi ta gama ta d'auki jikan da zaki haifar mata. Gurguwa, bak'a mai tallan abinci da take rainawa ta zama mata ga d'an nata da take ji dashi sai naga uwar abinda zatayi." Rauda tayi murmushi tace, "Nima zan so hakan Yaya kodan naga yanayin da zata shiga a wannan lokacin, amma sam ni bana ra'ayin auren sa."
"Kiyi ra'ayin yanzu Rauda, kar ki manta tun ba yau ba kina yawan ce min kinyi mafarki da namiji mai rawani a kansa wataƙila Allah ne ya nuna miki auren sa tun a mafarki. sannan istikhara da kika yi Allah ya nuna miki a mafarki ko?."
Rauda tace, "Haka ne Yaya Ummi amma hakan ba yana nufin shi zan aura ba. Nifa bazan iya zama matar sa ba gaskiya in na aure shi nayi ya da k'iyayayar mahaifiyar sa?." Yaya Ummi ta dawo kusa da ita ta dafa ta tace, "Shi zaki aura Rauda, ki saka a ranki shine mijin ki da zarar an tambaye ki kice kin amince." Rauda ta kalli Yaya Ummi tace, "Nifa bana son sa ta yaya zan amince?."
"Sabida mu nunawa babar sa iyakar ta, mu nuna mata duk abinda kake ji dashi baka isa kaja da ikon Allah ba."
"Ni tsoron gidan sarauta nake fa Allah ya sani."
"Ki ajjiye tsoron ki saka a ranki a nan aka haife ki."
Rauda ta kalle ta da mamaki tace, "Yaya Ummi in na amince da Asad Anas fa? Nayi masa adalci kenan duk tarin d'awainiyar da yayi dani dan na samu wanda ya fishi na watsar dashi...?."
#Vote
#Comments
#Share.
*KWANTAN ƁAUNA*
Fitattubiyar 2023
©️ *Nana Haleema.*
*Book 1*
*025.*
Yaya Ummi tayi shiru alamun tunani kafin ta sauke numfashi ta kalli Rauda tace, "Tabbas Anas ba abin yarwa bane ba, in muka watsar da Anas bamuyi adalci ba." Rauda rausayar da kai tace, "Abinda na gani nima kenan, zan iya auren Anas na zauna dashi duk da bana jin sonsa a zuciya ta har gobe, amma halayyar sa da yadda yake nuna tsantsar so a gare ni zata saka naso shi nan gaba."
Yaya Ummi tace, "Haka ne Rauda, ki cigaba da addu'a kedai kawai duk abinda ya zama alkhairi Allah ya zab'a maki."
"Ina yi sosai." Yaya Ummi zatayi magana kenan aka bud'e k'ofar aka shigo Baba ne da kuma maza guda biyu a bayan sa ganin su waye ya saka Yaya Ummi tashi tsaye tana fad'in, "Sannun ku da zuwa."
D'aya daga cikin su yace, "Yauwa Ummi, ya mai gidan naki?." Yaya Ummi tace, "Alhamdulillah." Gaisawa sukayi har Rauda kana d'aya daga cikin su yace, "Jiya nazo wucewa ta k'ofar gidan ku na tarar an baje gidan gabad'aya ya koma fili ana sabon gini na bulo, daman kuma ina ta ji a gari ban tabbatar ba sai dana gani da ido na; sai yanzu mahaifin ku yake shaida min abinda yake faruwa."
Kawu Badamasi yace, "Ke daman kin san shi ne tun a baya har ya furta yana sonki?." Rauda ta girgiza kai tace, "A'a Kawu bansan shi ba." Ya girgiza kai yace, "ikon Allah kenan, abinda baka tsammaci faruwar sa ba sai kaga ya faru." Kawu Lawan yace, "To ke meye a ranki kenan?." Rauda tayi shiru bata amsa ba Baba yace, "ita bata yanke hukunci ba har yanzu; akwai wani yaro Anas da yake sonta yana hidima da ita sosai ina tunanin shine a ranta."
Kawu lawan yace, "ba d'an gidan Alhaji Tasi'u mai farin gida ba?." Baba yace, "Shi." Kawu lawan yace, "to ai ni Alhaji Tasi'un ya aika min da mutane guda biyu na d'auka ma ko neman auren ta suka zo wajena sai suke shaida min shine ya turo su yace a sanar damu ya yiwa d'ansa mata kar a jishi shiru kwana biyu zai masa aure ne. Sun shaida min bazasu iya had'a ido da kai ba sabida kunya shiyasa suka je wajena kai tsaye." Baba yace, "ikon Allah! Amma baka sanar dani ba."
"Na d'auka shi yaron ai ya sanar dakai ko ya sanar da ita."
Baba ya girgiza kai ransa fari karr har hakan ya bayyana a kan fuskar sa yace, "basu zo inda nake bama shiyasa kwana biyu shiru babu motsin yaron, Allah sarki ni shaida ne yana son Rauda amma da alama iyayen sa basa son alaqar su tare shiyasa suka yanke wannan hukuncin, Allah ya zab'a mafi alkhairi." Kawu Badamasi yace, "Amin. Baza muyi saurin cewa iyayen ne basa son alaqar ba wataƙila alqawarin aure ne sukayi zasu had'a shi yaron bai san dashi ba shiyasa yake neman Rauds. Rauda karki yiwa kanki dole dan ganin kud'i ko dukiya ko kuma sarauta, yanzu maganar Anas ta k'are kinji duk abinda yake faruwa da kunnen ki, kar kice tunda babu batun Anas yanzu bara na amince da d'an sarkin kar kiyi haka kiyi addu'a ki kuma bi zab'in zuciyar ki."
Kai ta girgiza alamun gamsuwa Baba yace, "Ai ana ta addu'a duk inda na bayar ayi mana istikhara sai kaji ance auren sa da ita alkhairi ne ba kad'an ba. Daman Anas d'in nan nake ji tunda abin yazo da haka wallahi nafi kowa farin ciki ya auri zab'in iyayen sa itama ta auri Asad d'in shikenan an huta." Kawu Badamasi yace, "A'a, ka barta ta zab'i abinda take so dan Allah kar abin duniya ya rufe mana idanu mu kaita inda zamu zo muna dama mun sani bamu kaita ba, dan ni Allah ya sani wani lokacin bana yi mata sha'awar shi yaron mai martaba sabida abinda zata tarar ba abu kad'a bane. Na farko da ga babar sa, na biyu ga sauran jama'ar gidan, na uku har abada gidan sarauta bazasu tab'a girmama ta ba k'ask'ance zata rayu dan su gidan sarauta indai ba y'ar gidan sarauta ka d'auko ba talaka sunan ka balle kuma Rauda."
Umma da take zaune tace, "tun a yanzu ya fara bayyana kansa dan mahaifiyar yaron bata jima da fita daga gidan nan ba tayi b'adda kama ta shigo tana yi mata gargad'! akan auren d'anta, har da ikirarin in ta aure shi sai ta b'atar da ita daga duniya, ina dalili d'an sarki ai ba d'an wani annabin bane da za'a so a aure shi. Kuma shi yaron ita dashi bai ma ce yana son ta balle yace zai aure ta, haka zasuyi zaman auren?." Kawu Lawan yace, "sai a bar maganar in mai martaban ya nemi jin ra'ayin ta ace bata amince ba ai ba dukan mu za'ayi ba."
Baba yace, "A'a bafa za'ayi haka ba zata amince ma in sha Allah, meyasa kuke haka ne ku? Alkhairi ya biyo mu kuna k'okarin saka mu guje masa?. Ni ina goyan bayan auren d'ari bisa d'ari kuma in sha Allah sai ta aure shi." Umma tayi murmushi tace, "Daman Malam ai baza ka k'i ba kai." Kawu Badamasi yace, "Muma bamu k'i ba muna fatan abinda yafi alkhairi Allah ya zab'a, in shine alkhairin Allah ya tabbatar da arzuk'i a gidan wasu ai gwara a gidan ku, kuma kowa yana so yaga nasa cikin jin dad'i da kwanciyar hankali, abin alfaharin mu ne gabad'aya ace Rauda ta auri d'an sarki dan kaf dangin mu ba'a tab'a ba sai a kanta. In kuma babu alkhairi Allah ya watsa lamarin waje duk kud'i ko mulki bazai saka mu kaita inda zamu zo muna dana sani ba."
Baba yace, "Da alkhairi ma in Allah ya amince." Shiru sukayi dukkan su kafin suyi sallama su wuce. Baya fitar su Yaya Ummi ta kalli Rauda tace, "to kinji yanzu babu batun maganar Anas sai ki dawo da hankalin ki kan Asad." Rauda ta murmusa tace, "Wallahi Yaya sai nake jin zuciyata tayi min nauyi da akace ya fasa aurena, ashe shiyasa ya kasa nema na a waya."
Umma tace, "Ni kaina zuciyata babu dad'i Rauda balle ke, Anas ya cancanci aso shi kodan soyayyar da ya nuna miki ashe Allah bai rubuta zai mallake ki matsayin matar sa ba, Allah sarki! Allah ya zab'a masa abinda yafi alkhairi ya basu zaman lafiya shida wacce aka zab'a masa." Rauda tayi shiru tana jin babu dad'i a zuciyar ta.
*☆☆*
Gudu yake sosai a motar yadda Mama ta kira shi a wayar tana kuka ta d'aga masa hankali sosai hakan ya saka yake gudu kamar zai tashi sama burin sa yaje yaji kiran da take masa. Ko gama faka motar baiyi ba ya fita da sauri zuwa wajan ta yana shiga falon farko bata nan ya shiga ciki ya tarar da ita ita da Mum a zaune sunyi jugum-jugum kamar an musu rasuwa. Hankalin sa tashe yace, "Mama lafiya?." Kallon sa tayi da jajayen idanun sa ta yafito shi da hannu ya k'arasa kusa da ita ya zauna ta rik'e hannun sa tace, "Asad dan Allah ka janye batun maganar auren yarinyar nan, bata da tarbiyya ko kad'an bata da kirki."
Juya idanun sa yayi ya rik'e hannun ta da yake cikin nasa yace, "meya faru?." Mum da take gefe tace, "zuwa gidan su yarinyar mukayi da niyar ta rok'e ta kar ta amince maka; yarinyar ta dinga zazzaga masa rashin kunya har da k'okarin dukan mahaifiyar ka tana fad'in bata ga wanda ya isa ya raba ku ba. Bata da tarbiyya gabad'aya yarinyar in kaji cin mutuncin da tayi mata baza ka d'auka tana da hankali bama."
Asad da yake jinsu yayi shiru kawai baice komai ba jin yayi shiru ya saka Mama tace, "Asad dan Allah ka fasa auren ta, ka aure ta zan iya mutuwa dan zuciya ta zata iya fashewa ko wanne lokaci." Asad sanyaye yace, "Mamana bazata mutu ba, Allah ya wuci zuciyar ki, I'm sorry" ya furta a hankali yana kallon ta.
"Ka fasa d'in?" Ta tambaya tana kallon idanun sa. Kasa magana yayi dan bai san me zaice mata ba hakan ya saka shi yin shiru kana yace, "zan fad'a sanar da mamana in anjima, ina zuwa yanzu" ya fad'a yana tashi ya fita daga falon zuciyar sa duk babu dad'i.
Mum ta kalli Mama tace, "bafa zai amince ba an riga an juyar masa da tunani daga kanki, in badan haka ba Asad ne kike rok'on abu a wajan sa amma yake cewa ki jira ya dawo anjima, yaron da kince zo kayi yake cewa to in ba asiri ba meye?." Mama sabida abinda take ji bata ce komai ba amma ta amince da asiri aka yi masa dan ga zahiri ta gani.
Mum tace, "Ai hanya ta biyu dole zamu bi, ko a kashe yarinyar, ko a haukata ta. Cikin biyu zamuyi guda d'aya." Mama tace, "Kisan yafi haukan, ta b'ace bat daga duniyar yafi ace tana cikin duniyar hankali ne babu. Kije ayi duk abinda za'ayi aga bayan ta tsakanin yau zuwa gobe kin san bana son b'ata lokaci, sai dai bana so a samu matsala, bana so sunana na ya fito, bana so ayi mata kisan da za'a fahimci kashe ta akayi." Mum ta tashi tsaye tace, "Baki da matsala Fulani wannan ki d'auka an gama." Ta d'auki jakar ta da makullin mota kana tace, "Sai kin jini" tana fad'a ta fice daga cikin falon.
Asad da ya fita daga wajan Mama daga gidan ya fice gabad'aya dan bazai iya jure abinda yake ji ba ya hau mota ya tafi gidan da ya saba keb'e kansa, yana zaune a falon gidan ya zubawa waje d'aya ido yana kallo zuciyar sa na bugawa da gudu ko ya ya kulle idanun sa Rauda yake gani. 'Ina sonta sosai, amma nafi son Mama da ita bazan iya ganin Mama cikin wani hali sabida ita ba, zan cire komai a raina.' Abinda yake fad'a a zuciyar sa kenan gabad'aya ransa a jagule yake.
Motsi yaji a bayan sa ya juya suka had'a ido da Hydar ya k'araso kusa dashi ya zauna yana kallon sa kana yace, "Deaf indai zaka biyewa Mama baza ka tab'a samun farin ciki ba." Da sauri Asad ya kalle shi Hydar yace, "yeah sabida duk hanyar da ka biyo ta neman farin cikin ka sai Mama ta toshe ta, ka bar abubuwa da yawa sabida ita ya kamata zuwa yanzu kaima ka samu abinda kake so a karona farko, farin cikin ta kawai ta sani banda naka."
"She's my mother tana da ikon zab'a min duk abinda take so, bana son rasa ta a cikin rayuwata" Asad ya fad'a a raunace yana kallon k'asa.
"Even me i love her because itace ta haife mu bamu da wata kamar ta a kaf dunitar nan, but tana son kanta da yawa ne Asad musamman akan abinda ya shafe ka, tana tauye maka hakki ka always abinda take so kake yi meyasa wannan baza ta baka dama ba?."
"I can leave anythings because of her" ya sake furtawa yana lumshe idanun sa.
"I know Asad but ka aikata hakan zaka cutar da kanka ne fiye da lokacin baya, Sabida you loves Rauda so much itace ta farko da ka fara yiwa wannan son, lokaci d'aya Allah ya d'ora maka k'aunar ta a zuciyar ka cire ta ba abu bane mai sauk'i. Try to understand soyayya ba irin aiki da mukaman da ta saka ka bari a baya bane, wannan rayuwar kace domin soyayyar ta ta riga ta kama ka barin ta illa ce a gare ka." Asad ya furzar da iska ya kalli Hydar da idanun sa yace, "Meye mafita?."
"Addu'a. Nasan kana yi but ka k'ara a kan wacce kake yi, in Rauda alkhairi ce a rayuwar ka Allah ya baka ita in ba alkhairi bace ya fitar da ita daga ranka."
Asad ya girgiza kai alamun gamsuwa da maganar Hydar kafin Hydar ya kuma cewa, "then yana da kyau ko number yarinyar ne ka nema sabida ku dinga gaisawa, hakan zai rage maka wani abun a zuciyar ka." Asad ya girgiza kai alamun a'a kafin yace, "I can't."
"U can" ya bashi amsa shima yana kallon sa. Murmushi Asad yayi har hak'oran sa suka bayyana fuskar sa ta washe sosai annurin ta ya fito kyau da zatin da Allah yayi mata ya fito k'arara ba tare da ya shirya ba. Ganin hakan ya saka Hydar yayi murmushin shima yace, "Kayi murmushi mana nasan zaka iya sabida kana sonta."
Baice komai ba Hydar daman yasan bazai ce ba sai yace, "Deaf nifa ina ganin rashin gaskiya a tare da Aliyu cikin kwanakin nan, bana amincewa da yanayin sa gabad'aya." Tab'e baki Asad yayi kawai baice komai ba dan shima ya fahimta musamman ma halayya da shiga da ya canja ya koma sak irin nasa kafin ya d'auki wayar sa ya fara dannawa. Haka suka zauna shiru babu mai magana a cikin su sai daga baya suka tafi suka bar gidan.
*☆☆*
Mum ce a zaune a gaban wani malamin daban ba wanda suka je wajan sa da Mama ba yana ta dube-duben sa kafin ya d'ago ya kalle ta yace, "Auren nasu yana da wahalar rabuwa amma za'a raba shi." Mum ta girgiza kai tace, "haka nake so naji Malam, so nake a raba auren a saka masa tsanar yarinyar itama a saka mata tsanar sa ta har abada." Malam yace, "wannan baki da matsala Hajiya Sadiya, sai dai za'a kashe kud'i."
"Kud'i ba matsala ta bane ba Malam ayi kawai."
Malam yace, "Zaki ga aiki kuwa nan bada jimawa ba." Gyara zama tayi tace, "Aiki na biyu so nake a saka masa k'aunar Jidda a ransa fiye da yadda yake k'aunar ita gurguwar, ya manta da kowa da komai Jidda kawai yake gani. Hatta uwar sa Rabi'atu ya manta da ita gabad'aya ya zama Jidda ce zata juya shi yadda take so duk abinda tace shi zaiyi." Girgiza kai tare da yin dariya kad'an yace, "Za'ayi hakan tabbas. Amma yana da wahala kasancewar sa mai ibada da zama cikin alwala muna buk'atar lokacin da ya kasance babu tsarki a jikin sa a sannan aikin mu zai tafi yadda muke so. Dan aikin da zamuyi masa akan Jidda ba k'arami bane ba gaskiya."
Mum tace, "ta yaya zamu san bashi da tsarki?." Malam yace, "Wannan ba abin damuwa bane ba zamu gano hakan da kanmu." Mum tace, "to ma sha Allah haka nake so naji. Batun auren sa da Jiddan yana nan dai ko?." Malam yace, "yana nan kawai dai akwai sauran lokaci amma akwai maganar auren su kamar yadda nake shaida miki, kuma dole sai ita gurguwar bata tare dashi sannan zai kalli Jidda."
Mum tace, "Za'ayi maganin ta ai. Ina maganin da mukayi zaka bani?." Malam ya juya gefen sa ya d'auko wani turare a k'aramar kwalba ya mik'a mata yace, "Wannan turaren zaki shafa in zaki je wajan ta ko in zaki had'u da ita a ko wanne lokaci, ina tabbatar miki tana shak'ar sa a lokacin babu wani sirrin ta da zata b'oye miki komai sai kinji sai kuma abinda kika ce mata shi zatayi."
Mum ta karb'a ta saka a jaka ta fito da kud'i masu yawa ta ajjiye masa kafin tace, "Na gode Malam, a cigaba da aiki in komai yazo mana yadda muke so duka tare zamu ji dad'i, sauri nake mayi waya" ta fad'a tana mik'ewa ta fita da sauri.
*☆☆*
"Me kike so kice mana kenan master planer? Asad zaiyi aure?" Waziri ya fad'a a bayyane cike da mamaki da kuma al'ajabi. Daga cikin wayar Hajiya tace, "Nima dai jin abun nayi wani iri, kika ce kuma gurguwa zai aura?."
Dariyar tayi tace, "tabbas Asad zaiyi aure nan bada jimawa ba zai bar k'asar Nigeria zai tafi can wata k'asar yaje kula da matar sa, a wannan lokacin muke da damar sake nisanta shi da k'asar gabad'aya."
Waziri yace, "To ya maganar Aliyu kuma? Ya amince min amma har yanzu bai sake tuntub'a ta ba nima kuma haka."
"Ya fika wayo wannan yaron raba k'afa yayi yana nasa aikin yana kuma naku aikin, duk maganar auren nan shine assasata badan komai ba sai don cikar burin sa. Zai mana amfani a tafiyar mu sosai domin kansa yana ja fiye da tunanin ku zai kawo mana mafita lokacin da abubuwa suka yi
All Chapters
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 23 Chapter of 24