mana yawa."
Hajiya tace, "Sai nake ganin kamar yaudara ce amma baya tare damu." Master tace, "yana cikin mu yana kuma saka idanu akan ku gabad'aya duk motsin ku ya sani, tafiya dashi zata yi mana amfani sosai amma sai nan gaba zaku fahimci inda na dosa. Tsarin da ya saka muka jawo shi cikin mu yanzu babu batun sa tunda shi Asad d'in zai bar k'asar nan da wasu kwanaki ba buk'atar mu canja shi da Aliyu."
Waziri yace, "kuma kina ganin tsarin zai tafi yadda muke so kuwa?."
"Sosai ma kuwa fiye da hakan ma ku dai ku shirya ta kusa fashewa mu samu abinda muke so, boom!" Ta fad'a tana yanke wayar compress call d'in ya rage daga shi sai Hajiya a kai. "kana ganin abinda tace haka ne kuwa? Nifa ban ji maganar aure a cikin gidan nan ba ta ya akayi ita ta san da ita?."
"Tunda tace haka tofa haka d'in ne, zan bincika yanzun nan naji gaskiyar lamarin koma meye ai bazai b'uya ba, in da gaske akwai maganar auren ai sai munfi kowa farin ciki da hakan. Ki saurare ni zan sanar dake abinda na binciko" ya fad'a yana yanke wayar shima.
*☆☆*
Rauda haka ta wuni sukuku bata son Anas amma bata jin dad'in raba su d'in da akayi lokaci d'aya ba gabad'aya sai taji tana jin zafi a zuciyar ta hakan ya haifar da sanyin jiki a gangar jikin ta. Tana zaune a d'akin da suke kwana ita da Ummulkhairi tana juya wayar da ya bata gabad'aya wani iri take jin ta kamar ba ita ba zuciyar ta a jagule kamar ta zubar da hawaye. Shigowar sak'o taji wayar ta tayi kamar bata ta duba ba sai kuma ta duba ta bud'e tana karantawa.
_Assalamu Alaikum Rauda ina fatan kin wuni lafiya ya jikin ki da jikin Umma?. Nasan kin ji labarin abinda yake faruwa wata k'ila zaki ji babu dad'i duk da ba sona kike yi ba amma nasan zaki tausaya min tunda kin san ke kad'ai ce a zuciyata ke kad'ai kuma nake k'auna. Wallahil azim ke nake so Rauda har gobe har jibi har na mutu amma iyayena sun nuna min wacce suke so na aura babu yadda zanyi na amince musu sabida matsayin su gare ni. Bazan ce ki jira ni nayi aure na dawo na aure ki ba nasan abu ne mai wahala shiyasa na saka a raina na rasa ki har abada, wallahi ina rubuta miki message d'in nan ina hawaye Rauda domin na tabbatar na rasa abinda nake so wanda bazan mayar da kamar sa ba har abada. Ina sonki Rauda, ina k'aunar ki har gobe, naso ace zan rayu dake har abada amma hakan bai yu ba duk da har yanzu ban cire rai dake ba amma ni kaina ina ganin wahalar hakan. Ki yafe min wallahi ba'a son raina ba banyi kuma dan na yaudare ki ba, kunyar ki nake ji shiyasa na kasa ko kiran ki a waya dan ban san me zance miki ba in na kira ki, ina fatan zaki yafe min za kuma ki dinga min addu'ar Allah ya bani ikon yiwa wacce za'a aura min adalci domin matuk'ar ba ke ba bana tunanin akwai wacce zan zauna da ita da zuciya d'aya. Ina miki fatan alkhairi Allah ya baki miji na gari ya baki lafiya Amin. ANAS._
Babu tsammani taji hawaye yana bin fuskar ta wanda batayi tunanin zasu zuba ba a wannan lokacin ba, ta ajjiye wayar tana kuka mara sauti tana fad'in, "Allah ya baka juriyar rashi na Anas, ni kaina zanyi rashin wanda yake sona da zuciya d'aya, ko bana son ka zan iya zama dakai Anas sabida kai me k'auna tane na tabbata bazan yi dana sanin zab'ar ka ba, Allah bai amince zan zama matar ka ba, Allah ya baka hak'urin rashi na" ta fad'a tana goge idanun ta jikin ta duk ya mutu murus.
Asad ne ya fad'o mata a rai nan take gaban ta ya fad'i ta dafe k'irjin ta tana jin yadda yake bugawa tayi shiru ta nutsu tana sauraron bugun zuciyar tata a hankali, ta rasa meyasa in ta tuna shi take jin bugun zuciya ta rasa dalilin hakan. kawar da tunanin tayi ta d'auki wayar ta ta shiga mayarwa da Anas amsa da kalamai masu sanyaya zuciya da taushi had'i da tausasawa har ta kammala ta ajjiye wayar a gefe tana tunani.
'Matuk'ar bai bayyana min yana k'auna ta ba bazan amince da auren sa ba, a soyayya ba'a nuna mulki da izza shi na lura abinda yafi mayar da hankali kenan a kai, zan nuna masa ba'a samun ko wacce mace da k'asaita ko izza.' Abinda take fad'a a zuciyar ta kenan a bayyane tace, "to ma in ya furta zan amince kenan? Anya na dace da rayuwar sa na kuma yiwa kaina adalci..? ga abinda mahaifiyar sa take fad'a ban kai kaina inda za'a kashe ni ba kuwa?. To wai duk da nake wannan tunanin sonsa nake kome..?" Ta fad'a tana jan dogom tsaki tana kallon sama abubuwa sun mata yawa a kanta duk sun cushe mata zuciya.
K'arar wayar ta taji duk a tunanin ta a Anas ne ta jawo ta ta d'auka bata duba waye ba ta d'aga wayar ta kara a kunnen ta tana jiran taji maganar Anas sai taji sab'anin hakan, nan take zuciyar ta ta sake bugawa ta cigaba da bugu kamar ana doka ganga tunanin ta ya tsaya cak lokacin da taji ance, "Ina sonki, na fara sonki lokacin da ban shirya ba........!."
*End of Book1*🤗⛹♀️
_Waye ya kira Rauda wannan lokacin..? Asad ne ko kuma Hydar ne ya kira a madadin sa...?. Rauda zata amince da Asad tunda babu maganar Anas a halin da ake ciki ko a'a..? In ta amince dashi tayi ya da Mama wacce take shirin kashe ta? Anya auren su zai kasance Mama tana raye...?. In ya kasance kuma ta yaya ta wacce hanya hakan zata faru...?. Ina matsayin Jidda da kuma Mum da suke son ganin bayan Mama? Asad zai amince da Jidda kuwa har ya aure ta? In ya aure ta kuma ya kenan in suka raba shi da Maman sa?. Aliyu fa? Anya shima zai bar Asad zaman lafiya duba ds yadda ya koma acting like Asad..? Anya babu abinda yake shiryawa a kan hakan tunda dukkan mu mun shaida yana son ganin bayan Asad?. Wacece master planer? A ina take da zama da take sanin sirran cikin gida tun kafin na gidan su sani?. Ina makomar su Waziri zasuyi nasara ko a'a? Shin Asad zai mulki katagum ne ko a'a? Shin Rauda zata zata aure shi ko a'a? Shin Jidda zata aure shi ko a'a?. Akwai rikici, akwai makirci, akwai tashin hankali, akwai dana sani, akwai soyayya, akwai akasin ta duk a cikin book2._
_Duka amsar wannan tambayoyi suna cikin littafin kwantan b'auna book2 da zai fara zuwa nan bada jimawa ba in sha Allah akan naira 500 kacal. domin biya tuntub'e ni akan number via whatsapp 09030398006. Kar ku sake a baku labari tabbaci nake dashi akan KWANTAN B'AUNA salon sa ba irin wanda kuka saba karantawa bane, daban yake a cikin littafan sai kayi sa'a zaka samu irin sa._
Sai na jiku mutanen amana🥰
#Vote
#Share
#like
#Comments
#gidan sarauta
#makarci
#fuska biyu
#Soyayya
An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya
Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online,
Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan
Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490
A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu,
Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu
Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC
Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku
This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng
You can download more hausa novels there
Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online
It is free we do not charge for uploading novel
Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services
Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us
Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it
Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC
those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT
This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng
to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng
For feedback and support
Facebook : https://facebook.com/taskarnovels
Twitter : https://twitter.com/taskarnovels
Telegram : https://t.me/taskarnovels
All Chapters
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 24 Chapter of 24