Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
kowa ko kun lura da abinda yake min?" Dariya ya sub'ucewa zee tace"muje kawai" Jan hanun yusura sadiya tayi suka tafi Murmushi Abdul yayi yace"duk ku gama dawowa zakuyi" Jibrin ne ya karaso Abdul yace"ka d'auka da kyau ko?" Yace"eh" Amsar cameran yayi sai yace"good job" Su Rahma saloon sukayi direct Nan fa aka tsansara musu lalli da kitso lalli yusura sai kyalli yakeyi sai kace itace amarya ga kitso mashaallah" Sadiya tace"ke ai kwaliyar tayi yawa ko?sai ka ce kema satinan ne bikin ki" Murmushi tayi tace"ai kinsan Umar na gari Nima bari in me kwalliya" Sai yamma ligis suka bar saloon din a gajiye Rahma tace"mu fara zuwa gidan mu sai mu duba me cake din daga gidan sai in raka ku" Zee tace"nidai Rahma kiyi hakuri gobe zanyi tafiya sai bayan biki zan dawo ummina ba lafiya" Rahma tace"Allah sarki dan Allah in kin je ki gaisheta" Babu inda basuyi da ita ta bisu gidan su Rahma kafin ta wuce taki haka Suka hakura Da sallama su Rahma suka shiga gida abinda ya Bata mamaki tana expecting ta gan jama'a sai ta gan ba kowa umma ce zaune ta zauna sai karkada kafa takeyi Yan biyu na zaune sun natsu da alamu Zane su tayi Ko gaisuwar su yusura da sadiya Bata amsa ba tace"ke Ramatu zo nan" Ganin yanayin umma yasa jikinta fara rawa domin tasan halinta no no sense ce Karasawa tayi tace"umma dan Allah kiyi hakuri layine yayi yawa a saloon din " Ji tayi umma ta wanka Mata mari kuka ta fashe dashi tace"umma kiyi hakuri bazan Kara kaiwa magrib a waje ba" Umma ta d'auki dorina dake ajiye a gefe ta fara zaneta Yusura ne ta karasa ta sunguna tana rokon umma umma ta had'a da ita tana zane Rahma tana kuka sai cewa"take dama ashe ke Yar iskace?iskanci kike zuwa ban sani ba toh ai kin huta tunda an fasa auren ki" Sadiya kuka take sosai tana rokon umma Umma ta kama hanun Rahma taja ta sai d'aki tace"duk kokarin da nikeyi dan ganin kun Zama wani abu a rayuwa Ashe in kin je waje iskancin ki kikeyi?toh daga yau bazaki Kara fita ba kuma ko wayar amir Kika d'auka ban yafe Miki ba" Sanda zuciyar Rahma ta buga cikin kuka tace"umma meke faruwa ne?ki fadamin amma Dan girman Allah karki rabani da amir dina" A fusace umma tace"manufuka dama kina son shi kike zuwa iskanci har kin sa yau ana zargin Ina kawo maza gidan nan" Itadai abin ya d'aure mata Kai Kuma duk inda taso umma tayi Mata bayani kin sauraronta tayi karshe ma sai Kara rufe ta da duka Umma na dukanta tana cewa"shegiya makira ai hankalin ki ya kwanta tunda kin sa an biyoni gida an cimin mutunci Kuma kin sakani a kunya" Tasowa tayi daga zaune da take a kasa ta kama kafar umma tace"dan girman Allah ki fad'a min meke faruwa?" A fusace umma tace"me zan fad'a Miki toh Ina so ki sani har gida mahaifiyar amir ta biyoni akan sun fasa auren ki ai bannga laifin su ba tunda ke Yar iskace yanzu sai ki zauna Amma Ina tabbatar Miki zaiyi wuya ki samu miki tunda a gaban kowa akayi abin duk Wanda ya zo ma Yan anguwa zasu fad'a me ke kariya ce Rahma kin cuce ni" Rahma da har yanzu a rude take cikin tashin hankali Tace" Maman nur [2/20, 8:25 PM] Maman Noorul Hudah: πŸ‘„πŸ‘„πŸ‘„πŸ‘„πŸ‘„πŸ‘„ *BANA SONSHI* πŸ’‹πŸ’‹πŸ’‹πŸ’‹πŸ’‹πŸ’‹ _By maman noorul_ _Hudah__ Dedicated to my fans πŸ…Ώ2⃣3⃣&2⃣4⃣ Bismillahir Rahmanir Rahim Tace"umma kamar cewa kikayi Aamir ya fasa aurena ko?" Umma tace"eh an fasa" Ai ji umma tayi ta fadi kasa summamiya" Yusura ta shige d'akin jikinta sai rawa yake ta bude fridge ta ciro ruwa Mai sanyi ta yayyafa Mata Umma dai ko motsi batayi ba yusura da sadiya su suke ta komai har suka samu ta farfado tana farfadowa ta fashe da wani mugun kuka tace"me nayiwa my amir da zai fasa aurena bayan yasan bazan iya rayuwa babu shi ba" Kallon yusura tayi tace"yusura rakani inje gidansu in rokeshi wallahi ko house girl ne ya d'auke ni please ya dai barni a inda zanyi ta ganin shi" Kuka sosai Rahma keyi cikin haushi umma ta kalli yusura tace"Allah ya waddaran halayen ku yanzu rayuwar da kuka zabarwa kanku yayi kenan?" Yusura zatayi magana umma tace"Yi min shiru munafukai ai nasan duk abinda Rahma takeyi kema kinayi shiyasa naje gidan ku tun d'azu na sanar su d'au mataki tun kan kema asirin ki ya tonu ki rasa mijin aure " Yusura ta fashe da kuka tace"wayyo na shiga uku da Abba yau zai kasheni na tuba umma wallahi sharri akayi Mana" Umma tace"in gan abu da idona namiji akan Rahma shine Zaki ce sharri ai allah ne ya toni asirin ku maza tafi gida hukunci ki na nan Yana jiran ki" Kuka sosai yusura take sadiya ta ja hanunta suka tafi Zama umma tayi tace"ke zo Nan" Tashi Rahma tayi tana rike setin zuciyarta jiri na d'ibarta Umma tace"sunguna ki d'aga hannuwarki sama" Haka tayi domin ta ma kasa magana zuciyarta yayi nauyi Umma tace"fad'a min gaskiya ubanwa yake iskancin dake?" Shiru ba amsa hakan yasa umma jin haushi ta rufeta da duka Kuma ko kuka Rahma takiyi balle ta motsa tsayawa tayi Kamar gunki hakan ba karamin tsorata umma yayi ba sai ta fara jijjigata tana Kiran sunanta Amma Ina Rahma tayi nisa d'aukanta tayi ta kwantar taje waje ta dino ruwa ta watsa Mata Ajiyar zuciya ta sauke sai a sanan ta fashe da mugun kuka tana Kiran sunan amir B'angaren Amir ko bayan ya koma gida daga aiki Ya tarar da mummy zaune da Abba sai anty hafsat da maganin malam ya gama tasiri akan su saboda rashin azakar Zama yayi bayan ya gaida su Anty hafsat da sai cin abu take kamar cingum tace"Kai fa muke jira fa" Yace"akwai matsala ne a shirye -shiryen bikin?" Anty hafsat tace"eh amaryar aka canza ma domin yanzu neesa zaka aura ba Rahma ba" Murmushi yayi yace"what" Tace"yes" Abba yace"Mahmud na haramta auren ka da wanan yariyar bamu ba ita ashe Yar iska ce bamu sani ba toh na yanke shawaran Yar uwarka Aneesa zaka aura karka damu naje gidan kawon nata name bayani mun bar musu kayan" Amir ji yayi kamar yana mafalki da mamaki ya kalle su Zaiyi magana mummy tace"ban yarda ka kara Bari ko wace alaka ya shiga tsakanin ka da wanan Yar isakan ba in hakan ta faru ban yafe maka ba duniya da lahira" Kawai sai hawaye yakeyi anty hafsat tace"oh kuka zaka mana?" Ai bamu muka ce ka auri Yar iska ba kuma yanzu ma rufa maka asiri Aneesa zatayi " .tashi yayi jiri na dibar shi ya rike Kai Anty hafsat ta bishi da kallo a ranta tana murna domin da ya taka maganin da ta ajiye me a kofar d'aki zai mance Rahma Allah dai yasa Kar yayi sallama in zai shiga d'akin shi (Yan uwa sallama Yana da matukar muhimanci Koda kuwa babu kowa a d'akin" Aiko haka akayi beyi sallama ba Yana shiga kanshi ya fara jujjuyawa har ya fadi saman kujera Su yusura na fita sadiya tace"wai meke faruwa ne?ni ban gane maganar umma ba" Cikin kuka yusura tace"Nima haka wallahi nidai nasan na Shiga uku yau sai abbana ya yankani" Babu wani nisa tsakanin gidansu yusura da Rahma a bakin hanya suka rabu da sadiya Abin mamaki yusura na sallama a falon Abba sai ta gan Abdul zaune Wani kallon Abba yayi Mata sama da kasa kafin yace"kefa Nike jira" Zama tayi tana kuka cikin kuka tace"Dan girman Allah Abba kayi hakuri ni ban aikata laifin komai ba" Kallonta yayi yace"yanzu yusura irin tarbiya Dana baki kenan?ni Ina gida na tura ki kiyi karatu ashe ke kina can kina iskancin ki,toh tunda abinda kike so kenan toh kafin ki jawo matsifa jibi bayan sallah jumma'a zan d'aura Miki aure da shi Abdullah ki godema Allah shi ya tsaya akan yana sonki" Da mamaki ta kalli Abdul da ya dukar da Kai kamar mutumin kirki Zatayi magana Abba yace"karki damu ya min bayanin komai dama shi kike so ba Umar ba madadin ki zo ki fadamin in basu hakuri shine kike son zubarmin da mutunci harda cewa ku gudu yanzu ke kinsan ayi sumbata bama a kebe ba a tsakiyar titi?ki godewa Allah har yanzu Yana sonki" Kama kafar Abba tayi tace"Abba kamin rai wallahi ban sanshi ba kuma *BANA SONSHI*" Cikin jin haushi Abba yace"makira munafuka asirin ki ya tono ki barnan " Tashi tayi tana kuka tana shiga falon Mami ta ganta zaune wani kallo Mami ta Mata kafin tace"Ashe Zaki dawo?yanzu ke yusura ashe kinyi girman da zaki cewa namiji ku gudu ku bar gari ko?" Yusura ta fashe da kuka ta rungume maminta tace"Mami wallahi ban San meke faruwa ba ki fadamin" Mami tace"ai saurayin ki ne ya zo ya fad'a Mana komai ashe bayan Umar kina da wani saurayi yusura?" Yusura tace"wallahi Mami ban sanshi ba sai yau na fara ganin shi" Mami tace"kinga dakata bana son karya mutuniyar banza mutuniyar ofi Dan kin gan min kyale ki,karki raina min hankali domin har hoton ku da kike me kiss ya nuna Mana Kuma auwalu ya fad'a Mana komai domin mutane har uku sun shaida mana kina ta rokanshi ku gudu a bakin hanya yanzu in badan ya fiki hankali ba da sai dai ya tafi dake muji shiru ko?yanzu duk inda Nike sake Miki yusura bazaki iya zuwa ki fad'a min matsalan ki ba in baki son Umar ai babu dole sai ki fito fili ki fad'a bawai ki fake da kunya ba tunda kin San ba dole za a Miki ba" Yusura tace"Mami in na fahimce ki zuwa yayi yace"soyyaya muke amma Ina jin kunya in fad'a tunda na riga da na kawu Umar gida ko?" A fusace Mami tace"karya yake?karki kawo min iskanci in Miki dukar tsiya sha-shasha ai auren za a Yi Miki jibi tunda kin San kiyiwa saurayi kiss a titi kafin ki jawowa mutane matsifa zamu rabu dake Allah ma yasa d'an kirki ne" Kuka yusura ta fashe dashi cikin fushi ta tashi ta bar falon Washe gari Maman Nur Pls share [2/20, 8:25 PM] Maman Noorul Hudah: πŸ‘„πŸ‘„πŸ‘„πŸ‘„πŸ‘„πŸ‘„ *BANA SONSHI* πŸ’‹πŸ’‹πŸ’‹πŸ’‹πŸ’‹πŸ’‹ _By maman noorul_ _Hudah__ Dedicated to my fans πŸ…Ώ2⃣5⃣-2⃣6⃣ Bismillahir Rahmanir Rahim Washe gari da safe misallin karfe 8:am Aayan ne cikin shigar shadda sky blue yayi bala'in kyau sai Abdul cikin milk colour shadda mota d'aya suka Shiga jibri na jansu direct gidan kawo sukayi inda ko sukayi sa'a be fita ba Aikawa sukayi a musu sallama dashi sai ko gashi ya fito Kallonsu yayi daga sama zuwa kasa Nan fa ya gane manyan mutane ganin jibrin cikin uniform yasa tsoro ya kamashi cikin tsoro ya sunguna har kasa ya gaishesu Hakan ya Basu kunya suma Suka sunguna Bayan sun gaisa yace"sai dai ban waye ku ba" Gyran murya abdull yayi yace"kawo mun zo niman auren Rahma ne Kuma Dan Allah muna so ayi shi cikin gaggawa" Kawo ya tabe baki yace"me zakuyi da Yar iskan yariyar nan ne jiya fa mijin da za a d'aurawa musu aure da ita ya fasa akan an kamata tana iskanci da wani amma karku damu ya'ta zeenat na ciki ko yau sai a d'aura"wani kallo Aayan yayi mishi da yasashi shiga tateyin shi Cike da raini Aayan yace ba wanan ya kawo mu ba sai dai kuma yana mamaki abinda ya fad'a kallon captain jibrin yayi jibrin ya d'auke Kai Abdul yace"je mota ka ciro me abinda yafi kauna" Da gudu jibrin yaje ya ciro kudi masu yawa a leda ya kawo Wurga me Abdul yayi yace"auren zai yiwu gobe? Kawo da jikin shi ya fara rawa yace"ko yanzu kuke so za a d'aura" Aayan yace"gobe muke so Kuma in kayi Mana Wasa da hankali wallahi sai na bindiga ka kuma sai ka dawo da filin da ka fi karfin su ka kwace" Kawo yace"ni kaina da zan gan Wanda zai hana wanan auren da ni zan fara halaka shi"rungume ledar yayi yace"ai kudi abin so ne" Aayan yace"gobe in angama komai zamu baka kyautar fili a hanyar eagle square" Kawo yace"yallabai me zai hana ayi auren yau wallahi ko Mata nawa kake so zan nimo maka yanzu dai ku tafi zanje in yiwa mahaifiyarta bayani" Aayan yace"banda hantara da cin zarafin ban yarda ka hantaresu ba' Yace"ai me zai sa in hantaresu aini har kasa zan runsuna in gaida Rahmatu ai dama tun tana jaririya nasan ita arziki ce domin farar kafa ce da ita Allah ya albarkace rayuwarki Rahmatu" Wani kallo Aayan ke mishi shiko ko a jikin shi sai ma rungume ledar kudin da yayi ya shige gida sab'a rudewa ya dawo sai Kuma ya Kara komawa ciki B'oye kudin yayi a karkashin gado laure nayi me magana ko kulata beyi ba ya tafi Gidan umma ya tafi direct inda tun daga nisa yake rangada sallama Fitowa umma tayi da mamaki domin be saba sallama ba Karasawa yayi yace"maman Yan biyu kin tashi lafiya?"abin mamaki har kasa ya duka Bayan sun gaisa ya fashe da kuka yace"Ashe abinda ya faru kenan sai jiya mahaifin yaron ya zo ya fadamin" Umma tace"rabu da Yar iskan yari...." Katseta yayi yace" An kusa fara wasan Maman Nur Share [2/20, 8:25 PM] Maman Noorul Hudah: πŸ‘„πŸ‘„πŸ‘„πŸ‘„πŸ‘„πŸ‘„ *BANA SONSHI* πŸ’‹πŸ’‹πŸ’‹πŸ’‹πŸ’‹πŸ’‹ _By maman noorul_ _Hudah__ *πŸ‘„πŸ’‘NUR WRITERS ASSOCIATIONπŸ’‘πŸ’‹* πŸ’‘ *N W AπŸ’‘* *Lightning and bringing smile to your world is our perority* *NUR WRITERS* ~it a beautiful~ ~world*~ *Dedicated to my Husband* πŸ…Ώ2⃣7⃣-2⃣8⃣ Bismillahir Rahmanir Rahim Katseta yayi da cewa"ah'ah babu kyau kina aibata Yar ki albarka Zaki sa mata Kuma ni ban yarda Rahma ta aikata abubuwan da ake zarginta ba sharri ne irin na yan adam" Umma ta fashe da kuka tace"yanzu bansan Ina zan saka kaina ba in na fita kallona akeyi a gari nasan yanzu zaiyi wuya Rahma ta samu mijin aure" Kawu ya gyra hulan shi yace"maman Yan biyu Ina raye kike fadin haka ai komai lalacewa na banzan bari Yar Yaya na ta wulakanta ba karki damu na samo Mana mafita domin inshaallah Rahma bazata kunyata a idon duniya ba" Umma tace"yanzu ma dan gulma jama'a sai zuwa suke da sunan sun zo aikin biki wata ma har cemin take zata rufawa Rahma asiri a had'ata da d'an ta mashayi" Kawo yace"duk ki bar wanan maganar aini nace Miki bazan Bari ta kunyata ba ko?kuma in Suka zo ki fito musu da aikin da za ayi domin inshaallah gobe za a d'aurawa Rahma aure da mijin da yafi wanan d'an iska kamar inda za ayi me aure gobe itama za ayi Mata " Umma dai mamaki ya bata domin be tab'a nuna damuwa a al'umaransu ba hakan yasa ta fara zarginshi Kallon tuhuma tayi me kafin tace"shi waye wanan da za a musu aure da gaggawa haka?" Kawo yace,"dan abokina ne yana tsaye a lokacin da alhaji ya zo fadamin sun fasa auren Rahma shine ranshi ya matukar b'acewa yace"toh sai ya nuna musu ba kwantai tayi ba kuma babu abinda ya Kara b'atame rai Kamar inda Amir ke ta fadin mugayen kalamai akan Rahma harda tara Mana jama'a toh shine yace shi zai aureta a goben yanzu ma mahaifin ya bar gidan mu" Umma ta d'anyi shiru tana tunani kafin tace"nifa bana son in kai ya'ta inda za a wulakanta ta ko a Mata gori bana son abin ya Zama kamar taimakon mu yayi dan haka a hakura kawai ko mutuwa zatayi babu aure na gommace ta tsaya gabana" Kawu a ranshi yace"ka ji Yar bakin ciki dole in Yi da gaske" Fashewa yayi da kuka yace"yanzu kina nufin dani da ya'yan Yan uwana ban Isa ba kenan dasu?yanzu a ce kamar ni nayi Rahma Miji Amma ki ki amincewa ai inda Kara ai kyamin Kara ko?" Umma tace"toh a gaskiya zan amince amma sai an turomin yaron nayi me tambayoyi" Kawo yace"yanzu kuwa" Waya ya ciro da card din Aayan da ya gani cikin ledar kudi da Suka bashi Kiran wayar yayi sanda yayi missed call biyar ya d'aga Yace"kawo ne so Nike ka zo gidansu Rahma yanzu nan mahaifiyarta na son ganin ka" Aayan dake gaban oganshi ganeral da zaiyi me walihi yace"ok ku bani minti 30 dan Allah " Kawo yace"toh kayi a hakali duk lokacin da ka Gama ka zo zan jira ka" Bayan ya yanke wayar yace"bani kujera zaman jira ta kamani " Umma tace"oh Dan samun wuri mu zamu jirashi?" Yace"kedai Yi me uzuri a rayuwa ana son mutum me yin uzuri" Shigewa tayi ta barshi waje yace"ki Kira min Rahma" Umma tace" Rahma bata jin dadi ta kwanta Umma na shiga ta zauna kusa da Rahma tana shafa kitson kanta ba bacci takeyi ba jikinta ne ba dadi domin ko tashi Bata jin zata iya tunanin da kewar amir ya lullubeta gashi ta Kira wayar shi ya ki d'auka da ta Kira da wayar umma sai yace shi besan wata Rahma ba har yanzu she can't believe amir ya Mata haka,ita tasan ba haka kawai bane ji take dama mutuwa zata d'auketa ta huta Umma cikin tausayin ta domin Rahma ta bata tausayi hakan yasa ta manta fushinta cikin tausayawa tace"Rahma ki manta duk wani abinda da ya faru a baya ki manta da amir Allah zai musaya Miki da Wanda ya fishi " Cikin kuka tace"umma ki min rai wallahi Ina matukar son amir umma bazan iya rayuwa babu shi ba,umma mutuwa zanyi,umma nasan yana sona an Shiga tsakanin mu ne" A fusace umma tace"Yi min shiru inda yana sonki da be bari mahaifiyarshi ta biyo mu har gida ta ci Mana mutunci ba, inda yana sonki da ya aureki ko a wani irin hali kike,Rahma inda yana sonki da ya rufa Miki asiri koda bazai aureki ba da be tona Miki asiri ba,Rahma inda yana sonki da bai Bazai yarda a d'aura me aure gobe ba da wata dama dai Yana niman dalili ne" Rahma ta kalli umma tace'kina nufin gobe zai aura wata" Kafin umma ta bata amsa kawo ya shigo yace"kwarai kuwa ai yaron nan beda mutunci shi ya addasa wanan fitina baya sonki maimakon ya fito fili ya fad'a sai ya fake dake Yar iskace Ina fad'a Miki Rahmatu duka na ya rage beyi ba akan na bashi hakuri ya Bari ayi aure"karya ya sharara musu domin ko kashe kawo za ayi bezai Fadi kamanin Amir ba so d'aya ya taba ganin shi so d'aya ma da daddare Itadai Rahma shiru tayi amma tasan ba haka kawai amir zai ki taba sai dai in shiga tsakaninsu akayi koma waye bazata yafe me ba Lumshe ido tayi tana jin radadi a zuciyarta Umma tace"kin ji ai sai kiyiwa kanki karantun ta natsu kema ki cireshi a zuciyar ki" Kawo ya zauna kusa da ita Yana ja Mata kafa domin ji yake Kamar ya maidata ciki Umma ta mike tace"sai muje waje ka jira shi ni Ina da aikin yi" Yace"toh toh ai ko Nan zuwa Isha ne zan jira kinsa zan iyawa Rahma komai" Tace"na ga alama B'angaren Aamir ko Maman nur [2/20, 8:25 PM] Maman Noorul Hudah: πŸ‘„πŸ‘„πŸ‘„πŸ‘„πŸ‘„πŸ‘„ *BANA SONSHI* πŸ’‹πŸ’‹πŸ’‹πŸ’‹πŸ’‹πŸ’‹ _By maman noorul_ _Hudah__ *πŸ‘„πŸ’‘NUR WRITERS ASSOCIATIONπŸ’‘πŸ’‹* πŸ’‘ *N W A* πŸ’‘ *Lightning and bringing smile to your world is our perority* *NUR WRITERS* ~it a beautiful~ ~world~ Dedicated to my fans πŸ…Ώ2⃣9⃣-3⃣0⃣ Bismillahir Rahmanir Rahim B'angaren Aamir ko tunda ya shiga d'akin be fito ba domin wani mugun ciwon Kai ke damunshi ya rasa me ke me dadi ji yake kamar ya rasa wani abu kwata-kwata ya mance Rahma Jin shiru yasa mummy binshi ta tarar dashi zaune Tace"Aamir ya Kuma Zama a d'aki?" Yace"wallahi mummy kaina ke mugun ciwo yanzu ma a d'aki nayi sallah Mummy tace"Sannu " Yace"mummy ji nikeyi a jikina Kamar na rasa wani babban abu mummy akwai Wanda ya rasu ne?" Tace"ah'ah kayi wanka ka Sha magani ka fito yau dinner" Be amsa ba ya kwanta abinshi Aneesa ne ta shigo d'akin bayan fitar mummy Ganin shi tayi zaune a falonshi cikin jallabiya ya zauna ya lumshe ido Murmushi tayi ta karasa inda yake ta rufe me ido Cire Mata hanun yayi yace"waye" Murmushi tayi ta dawo gaban shi tace"nice amaryar ka" Kallonta yayi sai Kuma ya basar ya d'auki waya ya fara latsawa Fisge wayar tayi tana dariya kallonta yayi yace"bani wayana" Sai tace"haba amir a ce Ina amaryar ka kayi ta basar dani haba Kallonta yayi yace"bani wayata ni ban masan lokacin dana amince zan aure ki ba" Murmushi tayi ta kamo fuskarshi tana kokarin hade bakin su ya wani mugun tureta ta fadi tsaki yayi ya tashi ya shige bedroom ya barta a kasa Su Aayan ko daga barrack direct gidan su yusura suka je da ogan nasu A falon Abba suka zauna inda suka samu tarba Mai kyau Nan fa ogansu da abokansa biyu suka fara me bayani da bashi hakuri inda abin ya zo cikin gaggawa General ya fad'a me dalilin da yasa auren ya zo a haka saboda bayan bikin zasu je peace keeping ne shiyasa" Malam haruna yace"karka damu yarka a hanun na gari zata fad'a domin munyiwa abdullahi kyakyawar shaida Kuma Nima kasan ni bazan maka karya ba" Abba dai yaji nauyin malam haruna domin mutumin kirki ne Kuma babba malami kowa yasanshi a garin Niger bazai iya Musa me ba' Cikin jin nauyi yace"babu komai Allah ya Sanya alkhairi" Malam yace"Amin Dan Allah Ina niman alfarma ka bari a d'aura massalaci na" Abba yace"babu komai ai kaima Yar ka ce" A nan take akayi abinda ya kamata ayi kafin aure har sadaki sun biya maganar lafe Kuma general yace"ayi musu afuwan sai bayan auren a kano zasu zauna" Abba yace"ba komai ai dama lafe maganar matane " General yace"matar shi tayi ordering" A haka suka sallami juna Abdul Yana so yace"a Kira me yusura amma Yana jin kunya ashe Abba ya lura akwai magana a bakin shi sai yace"Bari in turota ta gaida ku" General yace"toh" Yana shiga gida b'angaren Mami ya ganta zaune tana kallo" Zama yayi yace"hajara akwai magana" Tattara hankalinta tayi tace"Ina ji baban Walid" Yace"hajara aure fa ya tabbata domin gobe za a d'aura auren yusura " Tace"dama da gaske kakeyi jiya na d'au andai fad'a ne Dan a bata tsoro ta natsu" Yace"toh yanzu maganar da Nike Miki suna falona kudin nan ma sadakinta ne sun taho da Wanda nikeji kunyar shi babu inda zanyi kwata-kwata yaron nan be bani breathing space ba daga magana jiya ashe ya d'au da gaske nike nifa harga Allah jiya na dai fad'a ne sai gashi ya d'aureni yanzu maganar da nike Miki general sojoji na falona ga malam haruna da alhaji mansur wai duk waliyar shi ne,dama ai kowa yasan malam haruna da general aminan juna ne" Mami ta zaro ido tace"Amma dai ba mal haruna Mai wa'azi a tv ba" Abba yace"shifa" Mami tace"toh gaskiya an d'aure mu ko Allah ma yasa ba a amshi ko sisin Umar ba Amma me zai hana mu roki alfarma su bamu lokaci?muma mu shirya" Abba yace"hmmn hajara kenan ai duk nayi iya kokarina amma Suka ce Kar in damu basa bukatar ko sinke Kuma yaron zai tafi peace keeping ne a wata kasar ba a asa ran zai dawo da wuri kin San sojane" Mami tace"toh Allah ya Sanya alkhari amma naso a bamu lokaci" Yace"yanzu ba wanan ba kirata taje ta gaishesu" Tashi mami tayi taje d'akin yusura ta ganta kwance ido a kumbure Tace"ki saka hijabi kije ki gaida iyayen mijin da Zaki aura minti uku na baki"tana gama magana ta bar d'akin Tashi yusura tayi jiki ba kwari ta d'auki hijabi babba tasa sai kuka takeyi Fitowa tayi ta tarar da Abba zaune har kasa ta duka ta gaishe shi Be damu da ya amsa gaisuwarta ba sai cewama yayi saura in kinje ki nuna musu baki da tarbiya sha-shasha " Kuka ta fashe dashi tace"Abba ka bani dama in Yi maka bayani wallahi ban sanshi ba kuma *BANA SONSHI* bigeta Mata baki yayi yace"shasha-shayi mun shiru munafuka so kike ki mayar dani karamin mutum maza jeki ki gaishesu kan ranki ya b'ace Mara mutunci" Tashi tayi ta fara tafiya tana kuka Ko da taje falo Abdul ne kadai Dan tuni su general Suka tafi Suka barshi" Da sallamar ta shiga falon tana kuka Lumshe ido Abdul yayi ya budesu Duba falon tayi sai ta gan shi kadai ne Wani haushin shi take ji a fusace tace"malam me na tare maka a rayuwa?me nayi maka ka had'ani da iyayena?meyasa kamin sharri kana kokarin rabani da iyayena" Ba tare da ya bata amsa ba yace"gobe bayan an d'aura aure za a kaiki barrack jibi zamu tafi kano dan haka ki had'a muhimman abinda kike so domin kina barin garin Minna baki da ranan dawowa sai in kin haihu muzo nunawa Abba yaro,and next thing ki bani size din takalmin ki da na

Chapter 3 of 11