Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
9 / 10
sau duhu daga sallar Asuba zuwa faxuwar rana. ** Bayan su zuhairu sun yada zango a kusa da inda suka yaqi sansanin na biyu, suka kwana da gari ya waye suka yi sallah Asubahi suka yi shiri suka ci gaba da tafiya. Suka sake yin tafiya har ta kwanaki uku, sannan suka iso inda sansani na qarshe yake wato Darul mautu wanda daga shi sai fadar matsafi Bahalu. Da suka isa inda wannan tsauni yake suka yada zango a bayansa don su huce gajiya su kuma shirya sosai yadda za su kai farmaki akan wannan sansani, da yake sun gama fahimtar yadda za sy riqa samun nasara akan wannan barada sai suka bari sai da tsakar dare, sannan suka tafi cikin duhun itatuwan da ke kusa da tsaunin suka voye. Yadda baradan ba za su gansu ba, suka soma kai farmaki akan su cikin duhun darebayan sun kashe hasken manyan fitilun da suka haske wajen. Su zuhairu sun samu nasara matuqa kamar yadda suka so, sai dai an xan samu tsaiko da turjiya daga sansanin baradan inda suka jajirce da nuna juriyarsu ta qoqarin da tabbatar da tsaro da kiyayewa akan fadar matsafi Bahalu, suka kuma 120 BAKAR GUGUWA fahimci daga inda ake kai hari akan su duk da tsananin duhun dare, don haka suka tasarma wajen da su zuhairu suke voye cikin duhun itatuwa da nufin hallaka su abinda ya haifar da artabu da arangama mai matuqar muni, har mutum biyar daga cikin jaruman da suke tare da su zuhairu suka hallaka ita kuma Buniyatu da wasu jaruman su shida suka samu munanan raunuka. An yi xauki-ba-daxi, artabu da baqin gumurzu mai tsanani a tsakaninsu kafin zuhairu ya samu nasarar kaiwa inda wannan gunki da suke bauta a gare shi yake ya sare kansa da takobinsa. Wanda sare kan gunkin ne ya kawo qarshen turnuqu da baqin gumurzun da ake kwafsawa a tsakaninsu. Gangar jikin gunki ta kama da wuta, tsaunin da ke wajen ya yi qara da rugugi mai tsananin qarfi ya fashe. Tartsatsin wuta ya yi tsiri ya tashi sama ya riqa watsuwa a jikin baradan da ke wajen suna kamawa da wuta, suna qonewa, suna hallaka. Baradan suka yi matuqar firgita da razana mara misaltuwa saboda ganin abinda yake faruwa, suka yi nufin su arce don tsira daga hallaka sai dai babu wanda ya samu damar kuvuta daga cikinsu har sai da feshin wutar nan ya riske su,ya qarar da su baki xaya suka qone qurmus. Ba a kawo qarshen wannan arangama ba har sai da kusan asubahi bayan ketowar alfirjir. Su zuhairu suka yi godiya ga Allah bisa ga nasarar da suka samu na karya wannan rundunar baradan. Suke nemi ruwa suka gabatar da sallah Asubahi, sannan suka xauki gawarwakin ‘yan uwansu da suka hallaka suka yi musu sallah suka binne su. Wanda suka samu raunuka aka yi musu magani, suka matsa kusa da wani rafi suka yada zango a wajen, daga inda suke suna hangen Darul sabar inda matsafi Bahalu yake 121 BAKAR GUGUWA an zagaye ta da manya katangu masu matuqar tsawo da kauri. Akwai qofa ta baqin qarfe da ke farko a kulle daga vangaren da suke. Da gari ya gama wayewa sosai rana ta fito sai zuhairu ya dubi Buniyatu da sauran jaruman da suke tare da su yace da su. “Tunda Allah ya nufe mu da samun nasarar isowa inda wannan fada take, sai ku tsaya anan gaba xayanku ku jirani a wannan waje,ni kuma zan je na shiga fadar don yaqar matsafi Bahalu na kuvutar da Gimbiya Hasima daga hannunsa, ku ci gaba da yi mini addu’a don fatan samun nasara, tare da jinyar wanda suka samu rauni har zuwa sanda zan dawo, idan na samu nasara akan wannan shu’umin matsafi cikin yarda Allah”. Buniyatu da sauran jaruman da suke tare da zuhairu suka amince da wannan shawarar tasa. Da su zauna a bakin wannan rafi su jira shi har ya dawo, suka yi masa addu’a ta fatan samun nasara, sannan zuhairu ya tashi ya kama hanyar tafiya ya tunkari inda wannan fada take. Da isarsa inda qofar fadar take ta farko ya dubeta da kyau. Ya ga an yi ta ne da xanyan baqin qarfe, yadda babu wani abin hallita daga jinsi mutum ko aljani da zai iya karya qofar ya shiga cikin fadar komai qarfinsa na jarumta da sadaukantaka. Ya sa hannu ya fiddo da mukullin da Boka Afrahu ya basa daga xamararsa ya saka a jikin qofar ya murxa a hankali. Qofar ta xan yi qara a hankali, sannan ta soma ja da baya tana buxewa da kanta. Zuhairu ya zare makulllin daga jikin qofar ya maida xamararsa sanda qofar ta gama buxewa da kanta, sannan ya zare takobinsa ya ja daga bai yi gaggawar shiga qofar ba, kamar yadda aka aka umarce shi. Ya yi saurare 122 BAKAR GUGUWA don ganin abinda zai fito daga cikinta ya gama da shi kafin ya kai ga shiga ciki. Huci ya fara ji irin na tahowar iska da ke cuxanye da mutsanancin zafi kamar tiriri ya bugo daga cikin qofar sannan sai ga wani qaton baqin maciji mai matuqar girma da kauri ya fito daga cikin qofar a fusace, ya fasa kai girmansa ya zarce na macijiyar da suka hallaka a cikin ruwan kogin da suka wuce kafin su shiga lardin Ashtar. Zuhairu ya yi sauri ya sanya takobinsa cikin azama da zafin nama ya sare kan baqin macijin tun kafin ya kai masa sara. Macijin ya yi wata tsiwa ta azabar fitar rai ya zube qasa matacce. Wani irin baqin jini mai kauri da yauqi ya zubo daga inda zuhairu ya sare kan macijin. Sannan sai macijin ya riqa narkewa yana zagwanyewa har ya zama jini gaba xaya. Zuhairu ya sake tsayawa a wajen yana saurare.ko zai sake ganin wani abin cutarwa ya fito daga cikinta, amma har aka xau lokaci mai tsawo babu abinda ya sake fitowa daga cikinta. Daga nan sai ya tafi gareta ya shiga ciki, babu abinda ya gani a tsakanin wajen illa wata doguwar hanya ta miqe ya zuwa qofa ta gaba. Ya bi wannan doguwar hanya da ta miqe ya ci gaba da tafiya har ya isa inda qofa ta biyu take. Yana isa wajen ya iske qofar a buxe kamar yadda aka sanar da shi, tun kafin zuwansa. Yana iya hangen abinda yake cikin qofar daga inda yake akwai wasu bishiyu na ‘ya ‘yan itatuwa masu zaqi na marmari tare da furani masu matuqar qayatarwa ga wasu fararan tsuntsaye suna shawagi a sararin subahana tare da sauka daga wannan bishiya ya zuwa waccan bishiya. Ya hangi wani xawisu yana tafe a qasa daga cikin qofar ya taho zai fito waje ya zuwa inda zuhairu yake. 123 BAKAR GUGUWA Zuhairu ya yi sauri ya lave daga gefe inda xawisun ba zai ganshi ba. Ya xara hannunsa akan takobinsa har zuwa lokacin da xawusun ya iso gare shi. Yana fitowa daga cikin qofar sai zuhairu ya xaga takobinsa ya sari xawisun ya raba kan shi gida biyu. Gashin jikin xawisun ya fatattake ya tashi sama, tamkar auduga a cikin iska, wani abinda ya bawa zuhairu mamaki da al’ajabi shi ne; duk inda gashin xawisun ya zuba a qasa sai ka ga qasar wajen ta kama da wuta ta qone qurmus ta yi baqi, saboda musiba. “Wa’iyazubillahi” Ya ce a zuciyarsa don neman tsari da wannan masiba sannan ya wuce ya zuwa inda qofar take. Bayan ya iso gare ta ya maida takobinsa ya kama qofar ya rufe kamar yadda aka umarce shi. Sannan ya sanya mukulin da aka ba shi ya murxa a hankali qofar ta buxe da kanta. Zuhairu ya zare makullin ya maida a xamararsa, sannan ya shiga cikin qofar ta biyu. Da shigarsa sai ya ga babu wannan bishiyu, tsuntsaye da furanin da yake hange tun da farkon kafin ya shigo. Sai dai wata doguwar hanya da ta nufi inda qofar qarshe take makamanciyar wadda ya wuce a baya. Ya bi hanyar ya ci gaba da tafiya har ya isa ga qofar ta uku. Yana zuwa wajen da qofar take ya tadda ita a kulle. Jikinta jajawur tamkar qarfen da aka ciro daga wutar maqera. Tiriri da huci mai tsananin zafi yana ketowa daga jikin yana bugun jikin duk wanda ya tunkari inda take. Zuhairu ya matsa a hankali ya isa ga qofar ya fiddo mukulli da aka bashi ya saka a hankali ya murxa qofar ta buxe da kanta ya zare mukullinsa ya ja daga yana mai saurare da ganin abinda zai fito daga cikinsa. 124 BAKAR GUGUWA Wuta ce ta fara tasowa daga cikin qofar ta yo wajen tiririnta da zafinta tamkar zai narkar da jikin zuhairu ya kama da wuta ya hallaka. Zuhairu ya yi sauri ya duba gefensa akwai mulmulallun farin dutse kamar yadda aka sanar da shi, ya xaga takobinsa ya sari farin dutsen ya raba shi biyu, nan take wutar ta mutu tun kafin ta qaraso inda yake, hayaqi ya turnuqe bakin qofar har sai da ya daina ganin komai. Bayan lafawar hayaqin sai ya ga qofar ta zama tamkar qofofin da ya wuce a baya. Ya bi ta cikin qofar ya shiga harabar fadar anan ne ya ga wajen na da matuqar faxi da girma. An qawata fadar da ado mai kyau na ginin qananan duwatsu abin yiwa ado da jauhari, ga furani da qoramu masu gudanawa a tsakiyar wajen tamkar wani lambun shawatawa. DARUL SABAR Zuhairu ya qarewa wajen kallo da ganin yadda aka qawata ginin fadar irin na fadar manya sarakunan duniya da suka shahara a fagen tarin dukiya wadata tamkar wanda ya gina fadar baya tunanin zai mutu ya barta. “Babu shakka wanda ya gina wannan fada ya shiryawa zaman duniya da tunanin dauwama a cikinta abadan ba zai hallaka ba” Zuhairu ya ce a ransa sannan ya wuce ya ci gaba da tafiya ya zuwa cikinta. Kafin ya isa inda fadar take sai ya ji qaqqarfar iska da ke cuxanye da baqar guguwa ta taso ta tunkaro inda yake. Aka 125 BAKAR GUGUWA yi tsawa da rugugin aradu mai matuqar qarfi gaba xaya fadar ta gauraye da duhu mai tsanani, mafi munin gani daga yankin duhun dare. Zuhairu ya ja daga cikin shirin artabu da arangama yana duban wannan baqar guguwa don ya san wanda yake tafe gare shi a cikinta. Baqar guguwar ta qaraso gaban shi ta tsaya sannan sai ta soma lafawa a hankali, daga cikinta sai ga matsafi Bahalu ya bayyana gaban zuhairu. Haqiqa yana tare da tsananin damuwa da vacin rai mara misaltuwa hannunsa na hagu yana riqe da gorarsa na sihiri na dama kuma riqe da sandarsa ta tsafi. Ya dubi zuhairu cikin tsananin fushi da fusata yace da shi. “Makoma ta munana gareka cikin wa’adin shigowarka fadata. Duk da ban yi zato ga faruwar hakan ba, amma tunda har ka shigo cikinta to kuwa ya inganta na tabbatar da hallaka a kanka, ba za ka samu nasarar abinda ya kawo ka ba, bare ka fita daga cikinta duk da ka samu nasara a kan sansanoni ma’abota tsaro ga wannan fada da ka hallaka a baya kafin ka kawo gare ta, hakan bai tabbatar da sahihancin samun nasara akai na ba, kuma na rantse da girman darajar mahaifina da abinda ya mallaka na daga alqaluman sihiri da tsafi sai na hallaka ka da kisa mafi muni da qasqanci sababin shigowarka wannan fada” Zuhairu ya dube shi da duba irin na qasqanci ya maida masa raddi da cewa. “Kai da bari ga ambato abinda ba shi da amfani ambato a gareka. Don kuwa kai ne makoma ta munana gareka da za ka hallaka cikin shirka da kafirci tunda har ma’abota tsaro da bada kariya da kake alfahari da su suka gaza bada kariya da kiyayewa akan wannan fada na shigo cikinta. Wadda ka yi imani da cewa babu wani mahaluki da ya isa ya shigo cikinta 126 BAKAR GUGUWA har abada. To kuwa lokaci ya qure a gareka rayuwa ta munana akan ka, ajali ya kusanto ka cikin wa’adinka na barin duniya, yau ne ranar da za ka yi nadamar halittarka a doron qasa da wanzuwarka cikin abinda kake aikatawa na shirka da sihiri. Yau ne ranar da za ka tabbatar da cewa akwai ubangijin gaskiya mai rinjaye akan kowanne aikin sihiri da kake ainkarin tabbatarsa”. Ya zare takobinsa cikin kabbara da maxaukakiyar murya mai qarfi ya taso kan matsafi Bahalu da nufin cim masa ya keta shi gida biyu ya hallaka. Matsafi Bahalu ya nuna shi da sandar tsafinsa ya soma karanto xalasimai na aikin sihiri da nufin aikata wani abu da zai hallaka zuhairu da shi. Amma ga mamakinsa sai ya ga dukkanin xalasiman da ya mallaka na aikin sihiri sun lalace duk abinda ya yi nufin aikatawa akan zuhairu ya kasa tasiri akansa. Shi kuwa zuhairu da ya ga haka sai ya tuna da maganar da tsohuwa Diyanuwa ta sanar da shi na cewa; idan har ya samu nasarar shiga fadar matsafi Bahalu shi kenan babu wani aikin sihiri da zai qara tasiri akansa. Don haka ya qara himmatuwa da qarfin zuciyarsa ya tasar ma matsafi Bahalu don ya hallaka shi. Matsafi Bahalu ya jefar da sabdarsa ta tsafi da kurtun sihirinsa da suke hannunsa saboda rashin muhimmanci da amfaninsu a wannan lokaci. Ya zaro wata baqar takobinsa da ke xaure a xamararsa ya yi qaraji da kururuwa irin ta fusatuwa ya taso kan zuhairu suka haxu a tsakanin filin wajen suka kaiwa juna sara,kaifin takubbansu ya haxu a sararin samaniya hakan ya haifar da wata tsiwa mai tada tsigar jiki, tare da tartsatsin wuta da ya watsu a sararin samaniya suka ci gaba da 127 BAKAR GUGUWA kaiwa juna sara cikin mugun nufi na hallaka abokin gaba, amma har suka rabu babu wanda ya samu nasara akan wani. Suka sake zaburowa suka kaiwa juna sara. Zuhairu ya shammace shi ya kai masa wata irin suka da tsinin takobinsa ya same shi a kafaxa. Bahalu ya yi qaraji da kururuwa saboda azaba ya zabura ya maida martani akan zuhairu da kai masa wani gawurtaccen sara. Ya samu sulken yaqin da yake jikinsa har sai da sulken ya kece gida biyu. Suka sake yunqurawa suka kai xauki kan juna, kaifin takubbansu ya sake haxuwa kan iska. Suka ci gaba da sokekeniya da bugaiya irin ta zaratan sadaukai. Kowannensu na neman makasa da hanyar samun nasara akan abokin karawarsa. Haka suka yi ta gabza artabu xauki-ba-daxi da kafsawa a tsakaninsu, amma babu wanda ya samu nasara akan wani har sai da kaifin takubbansu ya dakushe, hasken su ya dusashe. Saboda yawan haxuwa da suke yi yayin kaiwa juna sara. Suka watsar da takubban suka farma juna da bugu da hannu. Aka soma ‘yar damtse,kowannensu na kai duka da dukkanin qarfinsa. Nan fa aka soma sabon timiri da timimiya irin ta manya jarumai da suke ji da kan su, tun daga farkon harabar fadar har sai da suka dangata da qarshenta suka sake dawowa inda suke kafsawa tun da farko. Suka yi tirjiya irin ta matuqar buguwa da jin jiki gaba xayansu. Matsafi Bahalu a sake fusata da ganin ya kasa samun nasara akan zuhairu tunda suka soma kafsawa. Ya yunqura ya kai masa sura ya xaga shi sama ya juya shi zai cake kansa a qasa, kamar yadda ake cake tsinin mashi ya karya masa wuya, ya hallaka shi zuhairu ya juye cikin azama da zafin nama ya dire da qafafunsa. 128 BAKAR GUGUWA Suka sake zuburowa suka riqe hannun juna aka yi ‘yar gwajin qwanji babu wanda ya murxe wani daga cikinsu. Zuhairu ya shammace shi ya yi masa karo da kai a tsakiyar fuska kuvus! Matsafi Bahalu ya yi baya taga-taga kamar zai faxi ya turje bai faxi ba. Zuhairu ya sake narka masa bugu a tsakiyar qirji, Bahalu ya tafi da baya ya faxi a zaune. Hannunsa ya kai kan takobinsa ya yi sauri ya xaukota ya taso kan zuhairu a fusace ya kai masa sara da ita. Zuhairu goce ya sake kai masa sara da ita zuhairu ya sake gocewa sannan ya riqe hannun matsafi Bahalu da yake riqe da takobin ya juya tsinin takobin a saitin qirjin matsafi Bahalu ya danna tsinin takobin da qarfi ya shiga ciki har sai da tsinin takobin ya nutse. Matsafi Bahalu ya yi qaraji da kururuwa mai tsanani qarfi saboda azaba. Ya sa hannunsa ya ture zuhairu daga jikinsa ya tafi ya faxi qasa. Shi kuma ya zare tsinin takobin daga qirjinsa jini ya yi tsartuwa sama. Ya xaga takobin cikin qaraji da kururuwa ya tasarma zuhairu zai kai masa sara da ita. Zuhairu ya hangi tasa takobin yashe a qasa kusa da shi ya sa hannu ya xauka ya kare saran da ya kawo masa. Sannan ya sanya qafarsa ya tokare havar matsafi Bahalu da ita, matsafi Bahalu ya yi baya taga-taga kamar zai faxi. Zuhairu ya miqe cikin azama da zafin nama ya xaga takobinsa ya kaiwa matsafi Bahalu sara da dukkanin qarfinsa ya same shi a tirken dokin wuyansa, kan matsafi Bahalu ya yi tsalle sama ya rabu da gangar jikinsa saboda qarfin saran da zuhairu ya yi masa,kuma kafin gangar jikin ta faxi qasa itama zuhairu ya sanya takobinsa ya tsinka shi kashi biyu. Cikin zafin nama da gwanintar sara irin na hamshaqin sadauki. Kowanne vangare ya faxi qasa gefe daga sassan jikin matsafi Bahalu, daga nan 129 BAKAR GUGUWA tasa ta qare, ya hallaka bai ko shura ba. Zuhairu ya yi sujjada don nuna godiya ga Allah da ya bashi nasarar hallaka wannan shu’umin matsafin. Duk abinda yake faruwa tsakanin matsafi Bahalu da zuhairu Gimbiya Hasima da sauran dukkanin ‘yan matan da ke cikin fadar sun fito waje suna ganin wannan artabu da baqin gumurzu da suke yi a tsakaninsu. Da suka ga zuhairu ya samu nasara akan matsafi Bahalu ya hallaka shi sai suka yi matuqar murna da farin ciki, don sun san cewa ranar kuvutarsu ce da komawarsu hannun iyayensu ce ta zo. Suka taho da farin ciki Gimbiya Hasima ta tsaya a gaban zuhairu tana duban sa cikin matuqar farin ciki na ganin ya kawo qarshen mawuyacin halin da rayuwarta ta kasance a ciki ya hallaka matsafi Bahalu. Ta yi godiya ga Allah tare da jin begen zuhairu da qaunarsa ya qaru a zuciyarta. Shi ma zuhairu ya dubeta cikin farin cikin sake ganinta, sannan ya yi murmushi na tabbatar mata da alqawarin da ya xauka na kawo qarshen matsafi Bahalu da irin mayuwancin halin da ya sanya rayuwarta a ciki. Bayan sun nutsu zuhairu ya tambaye ta waxannan ‘yan mata da yake gani tare da ita su wanene su? Gimbiya Hasima ta amsa masa da cewa, “suma waxannan mallaka fada ne ya xauko su daga hannun iyayensu ya kawo su ya ajiye su a matsayin kuyangi da masu yi masa hidima kamar yadda itama matsafi Bahalu ya xaukota”. Daga nan ya sake tambayarsu a ina rijiya take don ya je gareta ya xebo ruwan cikinta ya yi amfani da shi don karya aikin sihirin da yake jikinsa. Gaba xaya ‘yan matan da suke fadar babu wadda ta san inda rijiyar take sai sanawiyatu Assad wadda aka fara kawowa cikin fadar, don haka ta yi masa rakiya 130 BAKAR GUGUWA har inda rijiyar take a cikin tsakiyar fadar zuhairu yana zuwa ya ga rijiyar ba ta da tsananin zurfi cikinta yana kusa-kusa. Ya kama gavar rijiyar ya taka ya shiga cikinta. Ya sanya sulkarsa na xibar ruwa ya xebo ruwan da yake cikin rijiyar ya fito. Bayan ya fito ya kafa kai yana shan ruwan da ya xebo a cikin rijiyar. Nan take sai aikin sihirin da yake jikinsa ya karye. Kamaninsa suka sauya daga siffar dattijo mai tarin shekaru ya zuwa siffar matashin jarumi, kuma sadauki gaba xaya ‘yan mata dake tare da Gimbiya Hasima suka cika da matuqar mamaki wannan lamari. Zuhairu ya sake yin godiya ga Allah sannan ya maida sauran ruwan a xamararsa ya xaure don kaiwa tsohuwa Diyanuwa kamar yadda suka yi alqawari. Daga nan ya shaidawa Gimbiya Hasima da sauran ‘yan mata da suke tare da ita cewa ba shi kaxai ba ne yana tare da abokan tafiya da suka taho tare, don su taimaka masa ya baro su a wajen fadar. Don haka suka kama hanyar ficewa daga fadar don su koma inda ya baro su Buniyatu da sauran jaruman da suka taho tare da su. Da fitar su zuhairu daga cikin fadar suka xan yi nisa kafin su kai ga inda abokan tafiyarsa suke sai suka ji wata irin tsawa da rugugi mai tsananin qarfi a bayansu. Suka juya don su ga abinda yake faruwa sai suka ga wannan fada tana girgiza da raurawa tana rushewa da kanta har ta gama ragargajewa. Sannan dukkanin wajen ya kama da wuta fadar ta qone qurmus da suka gama ganin abinda ya faru sai suka ci gaba da tafiya har suka isa inda su Buniyatu da sauran abokan tafiyarsa suke. Buniyatu da sauran jaruman da zuhairu ya bari a wajen suka yi matuqar murna da farin cikin ganin zuhairu ya dawo lafiya,tare da samun nasarar kuvutar da Gimbiya Hasima da 131 BAKAR GUGUWA sauran dukkanin matan da ya tarar a cikin fadar da kuma samun nasara karya sihirin da yake tare da shi. Ya dawo siffarsa ta asali daga siffar tsoho da matsafi Bahalu ya mayar da shi. Bayan sun nutsu zuhairu ya kwashe labarin dukanin abinda ya faru tsakaninsa da matsafi Bahalu ya sanar da su da kuma labarin ‘yan matan da ya tarar a fadar tare da Gimbiya Hasima, kamar yadda ta sanar da shi suka sake yin godiya ga Allah bisa wanna nasara da suka samu sannan suka zauna a wannan wajen don su qara huce gajiya kafin gari ya waye su ci gaba da tafiya su kama hanyar komawa gida. ** Da gari ya waye bayan su zuhairu sun yi sallar Asunahi suka yi shiri, suka kama hanyar komawa gida suka shafe tafiya har ta tsawon kwanaki a cikin lardin Ashtar suna keta tsaunuka da kwazazzabai sallah da cin abinci ne kawai yake tsayar da su, har suka iso bakin kogin nan da suka qetaro kafin su iso wannan lardi. Da yake babu jirgin ruwa a wajen sai da suka sa ke yin tafiyar kwanaki biyar a gefen kogin kafin su qure tsayinsa su zagayo inda suka bar dawakansu. Da suka iso wannan waje sai suka yada zango suka kwana don su huce gajiya, da gari ya waye suka sake yin shiri suka kama dawakansu suka hau don ci gaba da tafiya Gimbiya Hasima da sauran ‘yan matan da aka xauko daga fadar matsafi Bahalu suka hau dawakan jaruman da suka hallaka a cikin lardin Ashtar da yake suna da yawa wasu ‘yan matan sai suka hau doki xaya su biyu. Aka ci gaba da tafiya. Bayan tafiyar wasu kwanaki suka iso dajin sa tsohuwa Diyanuwa take zaune. Suka isa bukkar ta take suka sauka daga kan dawakansu.Tsohuwa Diyanuwa ta fito daga cikin bukkar 132 BAKAR GUGUWA tana dogarawa da sandarta. Ta tare su cikin murna da farin ciki na dawowarsu cikin fatan samun nasara. Buniyatu ta tafi tare da rungumeta cikin murna, sannan ta shaida mata sun samu nasarar abinda suka tafi aikatawa a fadar matsafi Bahalu. Tsohuwa Diyanuwa ta sake yin murna da farin ciki. Sannan zuhairu ya kwanto salkar ruwan rijiyar wubaisa da ya xebo a fadar matsafi Bahalu ya miqawa Buniyatu don ta bata ta wanke idanunta da shi ta samu waraka daga aikin sihirin da yake tare da ita, kamar yadda suka yi mata alqawari kafin su tafi. Buniyatu ta karvi salkar ruwan ta bawa tsohuwa Diyanuwa ta wanke idanunta da shi. Nan take aikin sihirin da yake tare da ita ya karye, idanunta suka buxe. Ta samu waraka daga halin makantar da take ciki tsawon lokaci. Ta dubi jikarta Buniyatu da sauran jama’ar da ke wajen ta sake yin murna da farin ciki daga nan su zuhairu suka yada zango a wanan wajen suka kwana kafin gari ya waye su ci gaba da tafiya. Da gari ya waye suka tashi gaba xaya har tsohuwa Diyanuwa suka ci gaba da tafiya ya zuwa birnin Bahazum. Kuma cikin hukunci Ubangiji ba su sake haxuwa da wani abin cutarwa ba, ko kuma wanda zai vata musu lokaci, sallah da cin abinci ne kawai yake tsayar da su, ko kuma idan sun yi matuqar gajiya su yada zango don su kwana. Haka suka shafe kwanakin da za su kai su birnin Bahazum. A ranar da suka isa birnin tun suna bayan gari sarki shaiban ya samu labarin dawowarsu kuma ga yadda aka shaida masa da alamun samun nasara a tare da su. Don haka shi da kansa da tawagar manya gari da ke fadarsa suka hau dawakai suka fito bayan gari don taryarsu. Da isowarsu zuhairu tun daga nesa sarki shaiban ya hangi ‘yarsa Gimbiya Hasima a 133 BAKAR GUGUWA cikin ayarin ‘yan mata da suke tafe da su. Ya sauko daga kan dokinsa ita ma Gimbiya Hasima tana qarasowa wajen ta sauka daga kan nata dokin ta tafi ga mahaifinta sarki shaiban suka rungume juna cikin tsananin murna da farin ciki mara musaltuwa suna masu godiya ga Allah da ya sake haxa fuskokinsu. Bayan sun nutsu suka rankaya gaba xayansu suka tafi fadar sarki shaiban. Labari ya ishe jama’ar gari na dawowar Gimbiya Hasima suka fito suka tare su cikin murna da farin ciki har zuwa fada. Da suka isa fada ne zuhairu ya kwashe labarin abinda ya faru daga tafiyarsu har ya zuwa dawowarsu ya sanar da sarki shaiban da sauran jama’ar birnin. Sarki ya sake yin godiya ga Allah abisa wannan nasara da suka samu na kuvutar da ‘yarsa daga hannun shu’umin matsafi Bahalu sannan suka yi jimamin rashin jaruman da suka hallaka a hanya ya yin wannan tafiya. Sarki ya sa aka bawa iyalinsu da sauran dangin wanda suka rasu dukiya mai tarin yawa, don kula da rayuwarsu kada su shiga mayuwancin hali na rashin ‘yan uwansu. Suma sauran jarumai da aka dawo tare da su ba su hallaka ba aka ba su kyautar dukiya mai tarin yawa. Bayan an gama da wannan sarki shaiban ya tambayi Buniyatu abinda take so na ladan aikinta na taimakon Zuhairu da ta yi. Aka samu wannan nasara ta kuvutar da Gimbiya Hasima, Buniyatu ta dubi sarki shaiban cikin girmamawa tace da shi. “Allah ya baka nasara ni babu abinda nake so na daga dukiya a matsayin lada aikin da na yi duk abinda na aikata na yi ne saboda Allah burina kawai zuhairu ya amince ya aureni saboda shi ne abinda nake muradi” Da faxar wannan maganar 134 BAKAR GUGUWA ta ta tun kafin zuhairu ya ce wani abu Gimbiya Hasima ta yi sauri ta amsa da cewa. “Idan dan wannan ne qudurinki babu shakka zuhairu zai aureki ki zama matarsa” Shi

Chapter 9 of 10