Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
2 / 10
koma inda ya saba zama ya zauna yana jiran zuwanta. Bai daxe da zama ba sai ga Gimbiya Hasima tare da kuyanginta sun nufo bakin wannan lambu da take zuwa, zuhairu ya yi farin ciki da sake ganinta yana dubansu har suka iso bakin wannan lambun suka sauka daga kan dawakansu 16 BAKAR GUGUWA sannan sai ya tashi ya tunkari inda suke dan ya sanr da ita abinda yake ransa na daga begenta ko dan yaga wannan matsafi da aka bashi labari kamar yadda ya yi alqawari a ransa. Tunda ya tunkari inda suke sai yaga sunja sun tsaya suna dubansa a tsorace kamar wanda suka ga wani abin cutarwa ya tunkaro inda suke, zuhairu bai karaya ba saboda sanin lamarin da aka bashi labari, ya isa garesu ya yi musu sallama kuyangin Gimbiy Hasima suka amsa masa ita bata yi masa magana ba, ta ma kauda kai ga barin dubansa kamar yadda ta yi a waccan lokacin da ya taimake su. Ya ci gaba da magaa yana mai faxin cewa “Idan har na yi dace da zuwana gareki bai zama laifi ga Gimbiya ba, ina miqa gaisuwata gareki cikin girmamawa da martaba ‘yar sarki jikan sarki abin bibiya da koyi a fagen adalci ga sauran sarakunan duniya, na zo gareki ne dan neman yarda bisa ga begenki da yake zuciyata idan kin amince dani cikin lamarinki” Yana faxar wannan magana sai yaga Gimbiya Hasima ta xago kanta da sauri ta dubeshi cikin yanayin tsoro da razana, kamar wadda ya faxa mata mummunan kalami mafi munin ambato amm bata yi masa magana ba. Kafin zuhairu ya sake yi mata magana sai suka ji wata irin tsawa mai tsananin qarfi tare da wani rugugi mai hauhuwa tamkar faxowar aradu ya guraye wajen, qasa ta soma girgiza tana raurawa tamkar zata tsage su nutse a cikinta su halaka, iska mai tsananin qarfi tare da baqar guguwar nan mai fesar da wuta daga cikinta, irin wadda zuhairu ya gani a waccan karan ta keto daga vangaren yamma ta nufo inda suke. Zuhairu ya ji zoben dake hannunsa ya yi motsi alamar wani matsafine ya tunkaro inda yake. 17 BAKAR GUGUWA Baqar guguwar nan ta taso kan zuhairu kamar zata rufeshi ya halaka da ganin haka sai Gimbiya Hasima da sauran kuyangun da suke tare da ita hankalinsu ya tashi, suka shiga halin kixima, shi kuma zuhairu sai yaci gaba da kallon baqar guguwar dake tafe tana feshin wuta cikin jarumta da qarfin zuciya, kuma yasan duk wannan abun ba komai bane face aikin sihiri da tsafi irin na ma’abota shirka, wa’iyazubillah yace a ransa yana duban guguwar har ta qaraso inda yake. Da guguwar ta qaraso bata rufe shi ba kamar yadda ya yi zato sai yaga ta tsaya a gabansa tayi tsiri sama tana juyawa, sannan ta sake yo qasa har sai da talafa wajen ya washe sai wani farin hayaqi da ya tsaya a gabn zuhairu, suka sake jin wani qaraji mai ban firgici daga cikin hayaqin sannan suka ji anyi zagi da kalma mafi munin ambato akan zuhairu, aka ci gaba da yi masa magana cikin kakkausar murya mai hauhuawa da faxin cewa. “Kaicon rayuwa da kusantar ajali sababin abinda ka ambata na begen Gimbiya Hasima, zai zama mafi munin abinda ka ambata ka sani cewar Gimbiya Hasima mallakina ce kuma na yi alqawarin hallaka duk wani namiji da ya kusanci inda take matuqar ba mahaifinta ba bare ya ambata mata qauna kamar yadda ka ambta na rantse da qarfin tsafi da sihiri na sai na halakashi kamar yadda na halaka wasu mazaje da dama saboda begenta”. zuhairu ya maida raddi ga inda yake jin maganar cikin qarfin zuciya da cewar. “Da zan ga wanda yake ambato wannan kalamin har ya voye kana cikin aikin sihiri da kuwa na yi jihadin kawar da mushiriki ma’abocin aikin tsafi daga doron qasa, wane ne kai 18 BAKAR GUGUWA kuma ka bayyana gare ni ko kazama daga wanda suka isa sufaxa aji ba masu voyuwa cikin aikin shiri ba”. Yana faxar maganar sai ya sake jin wata tsawar mai matuqar razanarwa ta sake cika wajen sannan iskar da take kaxawa mai matuar qarfi ta tsaya cak daga cikin farin hayaqin nan dake tsaye a gabansa sai yaga wani mutum ya bayyana ta cikinsa qotone qarqarfa babu alamar tausayi ko imani a tare da shi. Yana sanye da suturu irin na mashahuran matsafa hannunsa na dama yana riqe da ‘yar qaramar sanda wadda aka yiwa ado da zinare na hagu kuma yana riqe da wani gora irin wanda ya gani a hannun matsafiya Buniyatu an zagaye bakin gorar da wasu guraye da kambuna irina aikin sihiri ya dubi zuhairu yace da shi. “Ahir xinka da ambaton waxannan kalaman akan wadda ya buwaya cikin aikin sihiri, nine matsafi BAHALUL HAJARI BIN KAUWAS, mahaifina shi ne sarkin bokaye da matsafa ma’abota bautar gumaka da ke yammacin birnin sinar, bayan rasuwarsa na gaji kashi casa’in da tara na sirrin tsafinsa ‘yar uwata ta gaji kashi xaya dan haka yau duniya babu wani masani cikin alqaluman sihiri da yasan kashi goma cikin xari n abinda na gada wajen mahaifina. Sannan ina qaunar Gimbiya Hasima ne da nufin ta zama matata saboda na yi bincike a cikin alqaluman sihirina sun tabbatar babu wata mace da ta kai ta kyau da cikar halitta a wannan zamanin don haka na yi alqawarin aurenta ta ko wanne hali, duk da ita tace ba zata auri mushiriki ba, ni kuma na xauki alqawarin halaka duk wanda ya kusanci inda ta ke bare ya ambata mata kalmar qauna, na halaka mutane da yawa akanta wasu ma bata san da su ba, wucewa ta zo yi suka yaba 19 BAKAR GUGUWA kyawunta surarta na halakasu kuma na yi rantsuwa da abin bautata tare da qarfin tsafi da sihirina sai na hallaka duk wanda yace yana qaunarta ko waye shi har zuwa ranar bayyanar wasu bayanai cikin alqaluman sihirina da za su tabbatar da mallakar Gimbiya Hasima gareni ta zama matata”. Da jin wannan bayanin na matsafa Bahalu sai zuhairu ya gane cewa shi ne yayan Buhaiyatu Hajari da ta tava zuwa gareshi cikin halin aikin sihiri tace dashi tana qaunarsa da muradin ya aureta. Zuhairu ya sake maida masa raddi da cewar “Kaiconka masu munin ambato zan yi ishara gareka da zuwan qarshen wannan ta’asa da zalunci da kake aikatawa idan har ba ka rabu da Gimbiya Hasima ba babu shakka ajali zai gabata gareka sababin haxuwar ka da ni” Bahalu ya fusata da jin maganar zuhairu yace da shi. “Da ka yi sanin makoma da qarshen wanda ya ambaci irin wannan kalamin gareta da ba ka yi sha’awar ambata shi da bakinka ba na yi rantsuwa da ni kaina sai na halaka ka da kisa mafi muni ta hanyar qarfin tsafi da sihirina”. Ya yi qaraji da kururuwa mai qarfi da ke tattare da aikin sihiri, dajin ya yi amsa kuwwa da amo mai hauhawa qasa ta yi girgiza ya juya sandar sihirin dake hannunsa nan take ta rikixa ta zama shafceciyar takobi tana sheqi kaifinta kamar zai zuba a qasa, ya taso kan zuhairu a fusace baqar guguwar nan ta biyo bayansa. Zuhairu ya zare tasa takobin ya tare shi suka yi karon battar qarfe.takubbansu suna haxuwa wata qarqarfa iska tayi jifa da zuhairu har sai daya tafi ya faxi a qasa, Bahalu ya kai masa sara zuhairu ya goce, sannan ya miqe cikin sauri da azama shima ya kai masa nasa saran, babu abinda ya tare kaifin 20 BAKAR GUGUWA takobin zuhairu amma tana zuwa jikin Bahalu sai ya kece gida biyu saran takobin ya wuce. Suka ci gaba da fafatawa cikin mugun nufi na san halaka abokin karawa. Da matsafi Bahalu yaga ba zai iya halaka zuhairu ta hanyar jarumta ba sai ya koma aikin sihiri. Ya yi qaraji ya nuna zuhairu da tafin hannunsa yana surutai irin na aikin sihiri, nan take wuta ta kama ta taso kan zuhairu za ta qonashi zuhairu ya yi tsalle da majaujawa ya goce wutar ta wuce ba ta samu jikinsa ba, ya watso masa wasu kibiyoyi irin na aikin sihiri zuhairu ya sanya takobi ya kaxe kibiyoyin suka tafi suka zube a qasa wajen yama da wuta. Matsafi Bahalu ya sake yin wani siddabaru cikin alqaluman sihirinsa, nan take sai ga wani qaton dutse daga sama yana ci da wuta ya mirgino ya nufo kan zuhairu zai danneshi ya halaka, Gimbiya Hasima ta qwala qara mai tsanani qarfi saboda razana, saboda tasha ganin da irin wannan sihirin ya hallaka wasu daga cikin masoyanta, zuhairu ya ji hucin tahowar dutsen daga samansa ya yi tsalle ya kauce dutsen ya faxi a wajen ya kama da wuta qasar wajen ta qone qurmus ta yi baqi. Bahalu ya fusata da ganin zuhairu bai halaka ba, ya sake yin wani siddabaru cikin alqaluman tsafinsa, ya sari qasa da takobin dake hannunsa nan take qasar ta riqa darewa tana ruftawa da duk abinda yake kanta ta nufo zuhairu yake za ta rufta da shi ya halaka zuhairu ya sake gocewa qasar bata rufta da shi ba. Matsafi Bahalu ya sake yin wani qaraji dake tare da aikin sihiri, iska mai tsananin qarfi tare da baqar guguwar nan suka sake turnuqe wajen, Bahalu ya biyo ta cikin baqar guguwar ya taso kan zuhairu zai halakashi, idan ya yi qaraji sai 21 BAKAR GUGUWA ka ga feshin wuta yana zuba daga cikin guguwar saboda aikin sihiri. Gimbiya Hasima ta sake qara wata razananniyar qara saboda firgici don ta sha ganin a gabanta ya halaka wasu daga cikin wanda suka ce suna qaunarta da irin wannan aikin sihirin. Kafin baqar guguwar ta isa kan zuhairu sai ya yi kabbara da maxaukakiyar murya mai qarfi, tare da ambaton sunayen ubangiji yana mai tasbihi gareshi dan yin tawassali da neman kariya daga gareshi akan wannan aikin sihiri. Guguwar tana qarasowa gareshi ya kai sara cikinta da dukkanin qarfinsa cikin sa’a ya samu matsafi Bahalu a hannun kurtun sihirin dake hannunsa ya faxi qasa ya fashe. Bahalu ya yi wata razananniyar qara mai qarfi saboda azaba, guguwar da ta tunkaro zuhairu ta koma baya ta vace, sannan wajen ya washe zuhairu ya duba bai ga matsafi Bahalu ba ya shiga nemansa cikin taka tsantsan amma bai sake ganin ya bayyana gareshi ba. Bayan wani lokaci sai ya ji maganar matsafi Bahalu yana cewa da shi cikin kakkausar murya “Azaba ta tabbata gare ka ya kai wannan jarumin dake nufin tozarci ga girman matsayina. Na yi rantsuwa da taurari tare da qarfin sihiri da tsafi sai na halakaka da kisa mafi qasqanci da azaba mai tsanani sabida abinda ka aikata gareni” zuhairu yace da shi. “Banu razanarwa ko ban tsoro ga wanda ya zama gajiyayye ma’abocin rauni da rashin tasiri, kaicon wanda yake gudun ceton rai cikin tsoro da firgici akan abin da ya sha alwashin ganin bayansa, alhalin abinda ka dogara da shi ya kasa baka nasara, idan kana inkarin abinda na ambata ka sake bayyana a gareni na rantse da wanda raina ke hannunsa sai na 22 BAKAR GUGUWA halakaka da shafe ruhinka daga doron qasa, kamar yadda ka halaka waxanda ka samu nasara akansu kake alfahari da hakan. Matsafi Bahalu ya bayyana cikin fushi amma nesa da inda zuhairu yake jini yana zuba a inda kaifin takobin sa ya sareshi sannan kurtun sihirin da yake hannunsa ya fashe ya dubi zuhairu yace da shi. “Zai zama abin kaico gareni idan na bar wannan waje ba tare dana hallaka ba, sai dai ya zama dole gareni na koma ga bagirena don sake yin shiri a kanka, sababin fashewar kurtun sihiri da yake hannuna amma ina mai sake yin rantsuwa da duk abinda nake yin rantsuwa da shi, halaka za ta tabbata gare ka a duk sanda na sake bayyana gareka, sababin abinda ka aikata a kaina” Yana gama faxar wannan maganar sai suka ga ya vace, sannan baqar guguwar nan da ya bayyana ta cikinta ta sake turnuqewa ta yi tsiri sama, ta nausa ta nufi inda ta fito har ta vace, duhun daya rufe wajen ya washe komai ya koma yadda yake. Da zuhairu yaga matsafi Bahalu ya tafi sai ya yi ajiyar zuciya irin na jarumta sannan ya maida takobinsa ya juya wajen Gimbiya Hasima da sauran kuyanginta suke tsaye suna kallon abinda ya faru tsakaninsu da matsafi Bahalu, suna haxa ido da ita sai ta fashe da kuka sannan ta soma yi masa magana cikin wata tattausar murya mai ban tausayi tace masa “Wannan shi ne abin da yake damuna a rayuwata ta duniya, tun daga ranar da wannan matsafin yace yana qaunata na rasa sukuni da farin ciki har ya zuwa yau, babu shakka duk abinda ya faxa haka yake wannan matsafin ya halaka jama’a da dama saboda ni tun daga ‘ya ‘yan sarakuna da manyan attajirai da suka gabata suna neman aurena har ta kai a yanzu babu wani namiji 23 BAKAR GUGUWA da ya isa kusantar inda nake bare ya yi min magana matuqar ba mahaifina ba, har sai wannan shu’umin matsafin ya halakashi, wannan ne yasa ban yi maka magana ba bare godiya a sanda ka tava taimakona a farkon haxuwata da kai don jaka ina roqonka ka nisanta kanka da kusantar inda nake matuqar ba kana so wannan matsafin ya halakaka ba kamar yadda ya halaka wasu mutane a baya”. Zuhairu yace da ita “Ka da ki zama mai raunin zuciya da zai saka imaninki ya raunana, ki sani cewa tsafi da sihiri shirka ne wadda ba ta tasiri akan gaskiya, wato addinin musulunci kuma Allah yana tare da duk wanda ya dogara da shi zai kuma kareshi daga sharri ma’abota tsafi da sihiri komai tasirin tsafi sa gareshi na dogara garesa kasancewar shi mai rinjaye ne akan duk wani aikin sihiri na samu labarin abinda yake faruwa gareki game da wannan shu’umin matsafin wannan shi ne dalilin da ya kawoni gareki har na ambata ina qaunarki cikin yarda Allah sai na rabaki da wannan matsafin na kuvutar da ke daga halin da kike ciki”. Gimbiya Hasima ta sake cewa da shi “Ka yi haquri ya kai wannan bawan Allah, ba na so ka halaka a kaina kamar yadda wasu da dama suka hallaka saboda ni” Zuhairu yace da ita “Idan ya samu nasara hallaka wasu mazajen saboda ke a baya Allah ne ya qaddara faruwar hakan a kansu kuma wannan ba yana nufin cewa ya fi qarfin hukuncin ubangiji ba, cikin yarda Allah ni zan zama sanadiyyar halakarsa matuqar bai rabu da ke ba. Daga kaina ba zai sake halaka wani ba”. Gimbiya Hasima ta yi shiru ba ta sake yin musu akan maganarsa ba, bayan wani lokaci ta xago kanta tace da shi 24 BAKAR GUGUWA “Yaya sunanka kuma ina labarin garinku da abinda yake kawoka wannan wajen?” Zuhairu yace “Sunana Zuhairu bin Safwan kuma na kan zo wannan wajen ne daga birnin samaras dake qarqashin masarautar mahaifinki” Nan ya sanar da ita dukkanin labarinsa sannan suka yi sallama, ta kama dokinta ta hau sauran kuyanginta suma suka kama nasu dawakan suka hau suka yi masa sallama suka kama hanyar komawa birnin Bahazum sai da suka yi nisa sannan shima ya kama dokinsa ya hau ya nufi hanyar komawa gida. ** Da isar Gimbiya Hasima gida ta sauka daga kan dokinta ba ta tsaya a ko ina ba sai cikin xakin mahaifinta ta shiga cikin matuqar murna da farin ciki ta sameshi a zaune cikin halin damuwa, saboda baqin cikin da ‘yarsa take ciki. Da shigowarta sarki shaiban ya ganta cikin murna da farin ciki abinda ya daxe rabon da ya ga ‘yarsa Gimbiya Hasima a cikin irin wannan yanayi tun daga sanda matsafi Bahalu ya ambata yana qaunarta ya miqe cikin sauri yana mai matuqar mamakin tare da tambayarta abinda ya sanyata wannan farin ciki. Gimbiya Hasima tace da shi “Ya kyautu gareni na yi godiya ga ubangiji Allah buwayi a bisa taimakon da rahamarsa da ya saukar gareni” Ta kwashe labarin abinda ya faru gareta tsakanin matsafi Bahalu da jarumi zuhairu a bakin lambun da take zuwa ta sanar da mahaifinta. Ta ci gaba da cewa “Ya samu nasara akansa har sai da matsafi Bahalu ya gudu da kansa dan neman tsira,ya kuma xauki alqawarin taimakona da raba tsakanina da wannan shu’umin matsafin cikin yarda Allah” Sarki shaiban ya yi 25 BAKAR GUGUWA matuqar mamaki da al’ajabi na jin wannan labari tare da yabon jarumta da bajinta jarumi zuhairu tare da farin cikin jin cewar ya xauki alqawarin zai taimakawa ‘yarsa Gimbiya Hasima ya rabata da wannan shu’umin matsafi ya xaga hannunsa ya yiwa Allah godiya sannan ya dubi Gimbiya Hasima yace da ita. “Idan kin koma bakin wannan lambun da kike zuwa ki ka haxu da wannan jarumin ki ce masa ya zo birnin Bahazum ni sarki shaiban ina son ganinsa” Gimbiya Hasima ta amsa masa da cewa za ta sanar da zuhairu abinda ua umarceta sannan ta tashi ta koma cikin gida wajen mahaifiyarta. ** Shi kuwa zuhairu da ya koma gida bai sanar da kowa abinda ya faru tsakaninsa da Gimbiya Hasima ba ya ci gaba da harkokinsa kamar yadda ya saba. Washe gari da yamma ya sake yin shiri ya tafi bakin wannan lambu kamar yadda ya saba, yana zuwa ya sauka daga kan dokinsa ya xaureshi sannan ya koma inda ya saba zama ya zauna. Bai daxe da zama ba sai ya hangi Gimbiya Hasima tafe ta nufo inda yake ya cika da mamaki ganinta ita kaxai ba tare da kuyanginta ba kamar yadda ta saba wani abu da ya qara bashi mamaki shi ne bai ganta akan doki ba, kuma ya san ba zai yiwu ta taho daga birninsu zuwa bakin wannan lambun da qafarta ba. Zuhairu ya ci gaba da dubanta har ta qaraso inda yake tana mai yi masa murmushi sai dai ya sake yin mamaki da ya ga bata yi masa sallama ba, kamar yadda yake a shari’ar musulunci ga duk wanda ya zo ga xan uwansa musulmi sai ya ji ta ci gaba da yi masa magana da cewa “Zuciyata na cike da farin ciki sake ganinka masoyina, marhabin da zuwanka abin 26 BAKAR GUGUWA begena cewa dai ni na kasance mai ni’imtuwa da qaunarka a raina tamkar buguwar numfashi ga dukkan mai rai” Duk da zuhairu ya ji murya tare da ganin surar mai yi masa magana tamkar ta Gimbiya Hasima amma sai ya ji yana kokonton tabbatar da cewar ita ce ya ci gaba da dubanta bai yi magana ba, zuciyarsa tana shakka ace Gimbiya Hasima ce ya ji a jikinsa cewa akwai yaudara a cikin lamarin don haka ya yi takatsantsan. Ta sake matsowa gareshi tana mai yi masa magana cikin tattausar murya da cewa “Ya ya na ga ka yi shiru ba ka yi magana ba, kuma ka qi sakin jikinka da ni kamar kana cikin wani hali na damuwa”.Ta kai hannu zata tava jikinsa a sannnan ne ya ji zoben da yake hannunsa ya yi motsi. Alamar wani ma’abocin sihiri ne ya kusanceshi cikin sauri ya miqe daga inda yake zaune ya zare takobinsa da take xaure a xamararsa ya dubeta yace da ita. Duk da jin murya da ganin sura irin ta Gimbiya Hasima ban yi imani da cewar ke ce Gimbiya Hasima ta gaskiya ba, don haka ki sanar da ni wace ce ke kuma daga wane jinsi ki ka kasance, idan ba haka ba kuma na halakaki dan na ga akwai aikin sihiri irin na ma’abota shirka da vata a cikin lamarinki”. Matar nan dake tsaye a gabansa cikin surar Gimbiya Hasima ta dubeshi ta bushe da dariya sannan lokaci guda sai ta rikixa daga wannan surar ta koma surarta ta asali wato Buniyatu Hajir qanwar matsafi Bahalu dake hallaka duk wanda yace yana qaunar Gimbiya Hasima ta sake dubansa tace da shi “Lallai ka yi zurfi cikin begen Gimbiya Hasima yadda har ka ke iya gane cewa ba ita bace koda an suffantu da irin surarta da ni kake bege kamar yadda kake begenta a zuciyarka babu 27 BAKAR GUGUWA shakka da na yi farin cikin da babu wata halitta da ta tava yin kamarsa a duniya. Zai kyautu gareka ka cire qaunarta daga zuciyarka dan ita ‘yar sarki ce mafi girman daraja daga ‘ya ‘yan sarakunan duniya ba za ta auri wanda ba xan sarki kamarta ba. Zuhairu yace da ita “Ba zan so ki ba ba zan aminta da maganarki ba, kuma babu shiriya tsakanina da duk wani mutum ma’abocin tsafi da sihiri a duk inda yake ina mai sake jaddada nasiha gareki ki gaggauta tuba daga halin da ki ke ciki dan samun rahama idan ba haka ba kuma ki nisanta da inda nake ko kuma na salwantar da kaifin takobina”. Buniyatu ta sake yin dariya sannan ta ce da shi “Mai ya haddasa irin wannan gaba da qiyayya tsakanina da kai masoyina? Me Gimbiya Hasima tafi ni da kake matuqar qaunarta har ka kasa amincewa ka so ni kamar yadda ka ke sonta” Zuhairu ya ce da ita “Shirka tsafi da sihiri sune suka haddasa gaba da qiyayya tsakanina da ke. Kuma ba zan tava aminta da ke ba cikin wannan hali da ki ke ciki har abada, ita kuma Gimbiya Hasima ta fi ki daraja ta addini da hasken musulunci. Ta fi ki nasaba ta xaukaka da daraja, sannan ke najasace a bar qi kasancewar kina halin vata da tavewa kuma za ki zama mafi munin halin vata da tavewa kuma za ki zama mafi munin makoma idan ki ka mutu cikin halin da ki ke ciki a yanzu” Buniya ta fusata da jin maganar da ya faxa ta ce da shi “Haqiqa ka zama mai muzanci da tozarci matsayina akan wadda ka ke bege na rantse da girman daraja abin da na gada na sihirin tsafi da sihirin mahaifina ba don na yi alqawarin aurenka ba, kuma ba na so ka shiga halin damuwa har ka 28 BAKAR GUGUWA halaka da sai na xauke Gimbiya Hasima na hallakar da ita yadda ba za ka sake ganinta ba har abada. To amma ka sani na yi alqawarin aurenka ta kowane irin hali, kuma ko ba ka amince ba sai ka zamo miji a gareni har qarshen rayuwarka, ba za ka auri Gimbiya Hasima ba, ka yi saurare da zuwan abin da zai faru gareka nan gaba a duk sanda na sake dawowa muka haxu”. Tana gama faxar maganar ta vace a fusace cikin alqaluman sihirinta ba tare da ta saurari abinda zuhairu zai sake cewa ba da zuhairu ya ga Buniyatu ta tafi sai ya maida takobinsa sannan ya koma wajen da yake zaune ya zauna yana tunanin abinda ta ce cikin kalamanta. Bayan tafiyar Buniyatu ba da daxewa ba, sai ga Gimbiya Hasima tare da kuyanginta sun iso bakin wannan lambu da zuwansu ba su shiga ciki lambun ba kamar yadda suka saba sai zuhairu ya ga sun tunkaro inda yake zaune, suna zuwa Gimbiya Hasima da kanta ta yi masa sallama zuhairu ya amsa mata sannan tace da shi. “Na zo gareka ne domin na sanar da kai saqon mahaifina sarki shaiban ya ce na shaida maka ka zo yana son ganinka a bisa ga taimakon da ka yi min” Zuhairu ya xan yi shiru kamar yana tunani sannan ya ce da Gimbiya Hasima “To” Ya tashi ya je ya kama dokinsa ya hau suka juya baki xaya suka kama hanyar komawa birnin Bahazu suna tafe suna hira har suka isa qofar shiga birnin. Tun daga bakin qofa masu tsaron qofar suka fara duban zuhairu cikin mamaki da al’ajabin ganinsa tare da Gimbiya Hasima ba tare da ya hallaka ba kamar yadda suke da masaniyar cewa duk wani namiji da ya kusanci inda take sai wannan matsafin ya halaka shi matuqar ba mahaifinta ba. Da 29 BAKAR GUGUWA suka shiga cikin birni duk inda suka wuce sai jama’ar gari su bi zuhairu da kallo saboda ganin sa tare da Gimbiya Hasima suna masu mamaki da ganin wannan al’amarin shi kuma zuhairu bai damu da abinda yake faruwa ba, suka ci gaba da tafiya har suka isa fadar sarki shaiban. Bayan sun isa fada Gimbiya da sauran kuyanginta suka shiga ciki ta je ta sanar da mahaifinta sarki shaiban zuwan zuhairu ta yi masa iso. Sarki ya bada umarnin zuhairu ya shiga aka je aka shigo da shi har cikin fadarsa. Tun da aka shigo da zuhairu cikin fadar sarki shaiban ya dubeshi sai ya sake cika da matuqar mamaki saboda ganin shi ne jarumin da ya yi mafarki da shi mahayin doki da ya yaqi matsafi Bahalu ya halakashi a cikin mafarkinsa, gashi yanzu ya ganshi a zahiri kuma shi ne wanda ya xauki alqawarin taimaka wa ‘yarsa. Zuhairu ya kai gaisuwa gaban sarki shaiban, sarki ya amsa masa aka yi masa ishara da wajen zama, ya zauna suka kaxaita daga shi sai sarki a fadar sannan sarki shaiban yace da shi. “Labari ya isheni game da taimakon da ka yiwa ‘yarta Gimbiya Hasima, tare da alqawarin da ka yi na kuvutar da ita daga halin da ta ke ciki shi ya sa na umarceta cewa idan ta koma inda ku ka haxu da ita ta sanar da kai cewar ina son ganinka. Ya kamata na sake yin godiya ga ubangijina bisa baiwa da ni’imar da yake saukarwa akan bayin sa, don kafin faruwar wannan lamari na yi mafarki da zuwan wani jarumi mahayi doki da ya zo ya halaka wannan shu’umin matsafi ya kuvutar da ‘yata daga halin da take ciki, sannan a yanzu da aka shigo da kai fadata sai na ga cewa babu shakka kaine jarumin da na yi mafarki da shi ya halaka wannan matsafi, don haka 30 BAKAR GUGUWA nake mai kyakkyawan zato na samun nasara mafarkina ya zama gaskiya. Ba za mu zama masu yawaitar mamaki akan abinda ya faru ba don buwaya ubangiji da ikonsa ta wuce haka, sai dai mu yawaita godiya gareshi da addu’ar neman nasara, kuma na yi maka alqawarin cewa matuqar ka rava Gimbiya Hasima da wannan shu’umin matsafin da ya sanya rayuwarta cikin qunci, to kuwa zan baka aurenta tunda itama tana qaunarka, wannan shi ne dalilin da ya sa na ce ta sanar da kai ina son ganinka Allah ya yi maka albarka”. Zuhairu ya yi matuqar farin ciki da jin wannan bayani na sarki shaiban saboda qaunar da yake yiwa Gimbiya Hasima ya yi masa godiya cikin girmamawa tare da tabbatar masa da alqawarin da ya xauka na taimakawa Gimbiya Hasima akan sha’anin matsafi Bahalu. Daga nan suka yi sallama da sarki shaiban zuhairu ya tashi ya fita daga fada ya koma wajen su Gimbiya Hasima ya sanar da ita abinda ya faru tsakaninsa da mahaifinta Gimbiya Hasima ta yi matuqar murna da farin ciki, sannan ta sa aka kai zuhairu wani xaki na hutawa, abin

Chapter 2 of 10