koma inda ya saba zama ya zauna yana jiran zuwanta.
Bai daxe da zama ba sai ga Gimbiya Hasima tare da
kuyanginta sun nufo bakin wannan lambu da take zuwa,
zuhairu ya yi farin ciki da sake ganinta yana dubansu har suka
iso bakin wannan lambun suka sauka daga kan dawakansu
16
BAKAR GUGUWA
sannan sai ya tashi ya tunkari inda suke dan ya sanr da ita
abinda yake ransa na daga begenta ko dan yaga wannan
matsafi da aka bashi labari kamar yadda ya yi alqawari a ransa.
Tunda ya tunkari inda suke sai yaga sunja sun tsaya
suna dubansa a tsorace kamar wanda suka ga wani abin
cutarwa ya tunkaro inda suke, zuhairu bai karaya ba saboda
sanin lamarin da aka bashi labari, ya isa garesu ya yi musu
sallama kuyangin Gimbiy Hasima suka amsa masa ita bata yi
masa magana ba, ta ma kauda kai ga barin dubansa kamar
yadda ta yi a waccan lokacin da ya taimake su. Ya ci gaba da
magaa yana mai faxin cewa “Idan har na yi dace da zuwana
gareki bai zama laifi ga Gimbiya ba, ina miqa gaisuwata gareki
cikin girmamawa da martaba ‘yar sarki jikan sarki abin bibiya
da koyi a fagen adalci ga sauran sarakunan duniya, na zo
gareki ne dan neman yarda bisa ga begenki da yake zuciyata
idan kin amince dani cikin lamarinki”
Yana faxar wannan magana sai yaga Gimbiya Hasima
ta xago kanta da sauri ta dubeshi cikin yanayin tsoro da razana,
kamar wadda ya faxa mata mummunan kalami mafi munin
ambato amm bata yi masa magana ba.
Kafin zuhairu ya sake yi mata magana sai suka ji wata
irin tsawa mai tsananin qarfi tare da wani rugugi mai hauhuwa
tamkar faxowar aradu ya guraye wajen, qasa ta soma girgiza
tana raurawa tamkar zata tsage su nutse a cikinta su halaka,
iska mai tsananin qarfi tare da baqar guguwar nan mai fesar da
wuta daga cikinta, irin wadda zuhairu ya gani a waccan karan
ta keto daga vangaren yamma ta nufo inda suke.
Zuhairu ya ji zoben dake hannunsa ya yi motsi alamar
wani matsafine ya tunkaro inda yake.
17
BAKAR GUGUWA
Baqar guguwar nan ta taso kan zuhairu kamar zata
rufeshi ya halaka da ganin haka sai Gimbiya Hasima da sauran
kuyangun da suke tare da ita hankalinsu ya tashi, suka shiga
halin kixima, shi kuma zuhairu sai yaci gaba da kallon baqar
guguwar dake tafe tana feshin wuta cikin jarumta da qarfin
zuciya, kuma yasan duk wannan abun ba komai bane face aikin
sihiri da tsafi irin na ma’abota shirka, wa’iyazubillah yace a
ransa yana duban guguwar har ta qaraso inda yake.
Da guguwar ta qaraso bata rufe shi ba kamar yadda ya
yi zato sai yaga ta tsaya a gabansa tayi tsiri sama tana juyawa,
sannan ta sake yo qasa har sai da talafa wajen ya washe sai
wani farin hayaqi da ya tsaya a gabn zuhairu, suka sake jin
wani qaraji mai ban firgici daga cikin hayaqin sannan suka ji
anyi zagi da kalma mafi munin ambato akan zuhairu, aka ci
gaba da yi masa magana cikin kakkausar murya mai hauhuawa
da faxin cewa.
“Kaicon rayuwa da kusantar ajali sababin abinda ka
ambata na begen Gimbiya Hasima, zai zama mafi munin
abinda ka ambata ka sani cewar Gimbiya Hasima mallakina ce
kuma na yi alqawarin hallaka duk wani namiji da ya kusanci
inda take matuqar ba mahaifinta ba bare ya ambata mata qauna
kamar yadda ka ambta na rantse da qarfin tsafi da sihiri na sai
na halakashi kamar yadda na halaka wasu mazaje da dama
saboda begenta”. zuhairu ya maida raddi ga inda yake jin
maganar cikin qarfin zuciya da cewar.
“Da zan ga wanda yake ambato wannan kalamin har ya
voye kana cikin aikin sihiri da kuwa na yi jihadin kawar da
mushiriki ma’abocin aikin tsafi daga doron qasa, wane ne kai
18
BAKAR GUGUWA
kuma ka bayyana gare ni ko kazama daga wanda suka isa
sufaxa aji ba masu voyuwa cikin aikin shiri ba”.
Yana faxar maganar sai ya sake jin wata tsawar mai
matuqar razanarwa ta sake cika wajen sannan iskar da take
kaxawa mai matuar qarfi ta tsaya cak daga cikin farin hayaqin
nan dake tsaye a gabansa sai yaga wani mutum ya bayyana ta
cikinsa qotone qarqarfa babu alamar tausayi ko imani a tare da
shi. Yana sanye da suturu irin na mashahuran matsafa
hannunsa na dama yana riqe da ‘yar qaramar sanda wadda aka
yiwa ado da zinare na hagu kuma yana riqe da wani gora irin
wanda ya gani a hannun matsafiya Buniyatu an zagaye bakin
gorar da wasu guraye da kambuna irina aikin sihiri ya dubi
zuhairu yace da shi.
“Ahir xinka da ambaton waxannan kalaman akan
wadda ya buwaya cikin aikin sihiri, nine matsafi BAHALUL
HAJARI BIN KAUWAS, mahaifina shi ne sarkin bokaye da
matsafa ma’abota bautar gumaka da ke yammacin birnin sinar,
bayan rasuwarsa na gaji kashi casa’in da tara na sirrin tsafinsa
‘yar uwata ta gaji kashi xaya dan haka yau duniya babu wani
masani cikin alqaluman sihiri da yasan kashi goma cikin xari n
abinda na gada wajen mahaifina.
Sannan ina qaunar Gimbiya Hasima ne da nufin ta zama
matata saboda na yi bincike a cikin alqaluman sihirina sun
tabbatar babu wata mace da ta kai ta kyau da cikar halitta a
wannan zamanin don haka na yi alqawarin aurenta ta ko wanne
hali, duk da ita tace ba zata auri mushiriki ba, ni kuma na xauki
alqawarin halaka duk wanda ya kusanci inda ta ke bare ya
ambata mata kalmar qauna, na halaka mutane da yawa akanta
wasu ma bata san da su ba, wucewa ta zo yi suka yaba
19
BAKAR GUGUWA
kyawunta surarta na halakasu kuma na yi rantsuwa da abin
bautata tare da qarfin tsafi da sihirina sai na hallaka duk wanda
yace yana qaunarta ko waye shi har zuwa ranar bayyanar wasu
bayanai cikin alqaluman sihirina da za su tabbatar da mallakar
Gimbiya Hasima gareni ta zama matata”.
Da jin wannan bayanin na matsafa Bahalu sai zuhairu
ya gane cewa shi ne yayan Buhaiyatu Hajari da ta tava zuwa
gareshi cikin halin aikin sihiri tace dashi tana qaunarsa da
muradin ya aureta.
Zuhairu ya sake maida masa raddi da cewar “Kaiconka
masu munin ambato zan yi ishara gareka da zuwan qarshen
wannan ta’asa da zalunci da kake aikatawa idan har ba ka rabu
da Gimbiya Hasima ba babu shakka ajali zai gabata gareka
sababin haxuwar ka da ni” Bahalu ya fusata da jin maganar
zuhairu yace da shi.
“Da ka yi sanin makoma da qarshen wanda ya ambaci
irin wannan kalamin gareta da ba ka yi sha’awar ambata shi da
bakinka ba na yi rantsuwa da ni kaina sai na halaka ka da kisa
mafi muni ta hanyar qarfin tsafi da sihirina”. Ya yi qaraji da
kururuwa mai qarfi da ke tattare da aikin sihiri, dajin ya yi
amsa kuwwa da amo mai hauhawa qasa ta yi girgiza ya juya
sandar sihirin dake hannunsa nan take ta rikixa ta zama
shafceciyar takobi tana sheqi kaifinta kamar zai zuba a qasa, ya
taso kan zuhairu a fusace baqar guguwar nan ta biyo bayansa.
Zuhairu ya zare tasa takobin ya tare shi suka yi karon
battar qarfe.takubbansu suna haxuwa wata qarqarfa iska tayi
jifa da zuhairu har sai daya tafi ya faxi a qasa, Bahalu ya kai
masa sara zuhairu ya goce, sannan ya miqe cikin sauri da
azama shima ya kai masa nasa saran, babu abinda ya tare kaifin
20
BAKAR GUGUWA
takobin zuhairu amma tana zuwa jikin Bahalu sai ya kece gida
biyu saran takobin ya wuce. Suka ci gaba da fafatawa cikin
mugun nufi na san halaka abokin karawa. Da matsafi Bahalu
yaga ba zai iya halaka zuhairu ta hanyar jarumta ba sai ya
koma aikin sihiri.
Ya yi qaraji ya nuna zuhairu da tafin hannunsa yana
surutai irin na aikin sihiri, nan take wuta ta kama ta taso kan
zuhairu za ta qonashi zuhairu ya yi tsalle da majaujawa ya goce
wutar ta wuce ba ta samu jikinsa ba, ya watso masa wasu
kibiyoyi irin na aikin sihiri zuhairu ya sanya takobi ya kaxe
kibiyoyin suka tafi suka zube a qasa wajen yama da wuta.
Matsafi Bahalu ya sake yin wani siddabaru cikin
alqaluman sihirinsa, nan take sai ga wani qaton dutse daga
sama yana ci da wuta ya mirgino ya nufo kan zuhairu zai
danneshi ya halaka, Gimbiya Hasima ta qwala qara mai tsanani
qarfi saboda razana, saboda tasha ganin da irin wannan sihirin
ya hallaka wasu daga cikin masoyanta, zuhairu ya ji hucin
tahowar dutsen daga samansa ya yi tsalle ya kauce dutsen ya
faxi a wajen ya kama da wuta qasar wajen ta qone qurmus ta
yi baqi.
Bahalu ya fusata da ganin zuhairu bai halaka ba, ya sake
yin wani siddabaru cikin alqaluman tsafinsa, ya sari qasa da
takobin dake hannunsa nan take qasar ta riqa darewa tana
ruftawa da duk abinda yake kanta ta nufo zuhairu yake za ta
rufta da shi ya halaka zuhairu ya sake gocewa qasar bata rufta
da shi ba. Matsafi Bahalu ya sake yin wani qaraji dake tare da
aikin sihiri, iska mai tsananin qarfi tare da baqar guguwar nan
suka sake turnuqe wajen, Bahalu ya biyo ta cikin baqar
guguwar ya taso kan zuhairu zai halakashi, idan ya yi qaraji sai
21
BAKAR GUGUWA
ka ga feshin wuta yana zuba daga cikin guguwar saboda aikin
sihiri.
Gimbiya Hasima ta sake qara wata razananniyar qara
saboda firgici don ta sha ganin a gabanta ya halaka wasu daga
cikin wanda suka ce suna qaunarta da irin wannan aikin sihirin.
Kafin baqar guguwar ta isa kan zuhairu sai ya yi kabbara da
maxaukakiyar murya mai qarfi, tare da ambaton sunayen
ubangiji yana mai tasbihi gareshi dan yin tawassali da neman
kariya daga gareshi akan wannan aikin sihiri. Guguwar tana
qarasowa gareshi ya kai sara cikinta da dukkanin qarfinsa cikin
sa’a ya samu matsafi Bahalu a hannun kurtun sihirin dake
hannunsa ya faxi qasa ya fashe. Bahalu ya yi wata
razananniyar qara mai qarfi saboda azaba, guguwar da ta
tunkaro zuhairu ta koma baya ta vace, sannan wajen ya washe
zuhairu ya duba bai ga matsafi Bahalu ba ya shiga nemansa
cikin taka tsantsan amma bai sake ganin ya bayyana gareshi ba.
Bayan wani lokaci sai ya ji maganar matsafi Bahalu
yana cewa da shi cikin kakkausar murya “Azaba ta tabbata
gare ka ya kai wannan jarumin dake nufin tozarci ga girman
matsayina. Na yi rantsuwa da taurari tare da qarfin sihiri da
tsafi sai na halakaka da kisa mafi qasqanci da azaba mai
tsanani sabida abinda ka aikata gareni” zuhairu yace da shi.
“Banu razanarwa ko ban tsoro ga wanda ya zama
gajiyayye ma’abocin rauni da rashin tasiri, kaicon wanda yake
gudun ceton rai cikin tsoro da firgici akan abin da ya sha
alwashin ganin bayansa, alhalin abinda ka dogara da shi ya
kasa baka nasara, idan kana inkarin abinda na ambata ka sake
bayyana a gareni na rantse da wanda raina ke hannunsa sai na
22
BAKAR GUGUWA
halakaka da shafe ruhinka daga doron qasa, kamar yadda ka
halaka waxanda ka samu nasara akansu kake alfahari da hakan.
Matsafi Bahalu ya bayyana cikin fushi amma nesa da
inda zuhairu yake jini yana zuba a inda kaifin takobin sa ya
sareshi sannan kurtun sihirin da yake hannunsa ya fashe ya
dubi zuhairu yace da shi.
“Zai zama abin kaico gareni idan na bar wannan waje
ba tare dana hallaka ba, sai dai ya zama dole gareni na koma ga
bagirena don sake yin shiri a kanka, sababin fashewar kurtun
sihiri da yake hannuna amma ina mai sake yin rantsuwa da duk
abinda nake yin rantsuwa da shi, halaka za ta tabbata gare ka a
duk sanda na sake bayyana gareka, sababin abinda ka aikata a
kaina” Yana gama faxar wannan maganar sai suka ga ya vace,
sannan baqar guguwar nan da ya bayyana ta cikinta ta sake
turnuqewa ta yi tsiri sama, ta nausa ta nufi inda ta fito har ta
vace, duhun daya rufe wajen ya washe komai ya koma yadda
yake.
Da zuhairu yaga matsafi Bahalu ya tafi sai ya yi ajiyar
zuciya irin na jarumta sannan ya maida takobinsa ya juya
wajen Gimbiya Hasima da sauran kuyanginta suke tsaye suna
kallon abinda ya faru tsakaninsu da matsafi Bahalu, suna haxa
ido da ita sai ta fashe da kuka sannan ta soma yi masa magana
cikin wata tattausar murya mai ban tausayi tace masa “Wannan
shi ne abin da yake damuna a rayuwata ta duniya, tun daga
ranar da wannan matsafin yace yana qaunata na rasa sukuni da
farin ciki har ya zuwa yau, babu shakka duk abinda ya faxa
haka yake wannan matsafin ya halaka jama’a da dama saboda
ni tun daga ‘ya ‘yan sarakuna da manyan attajirai da suka
gabata suna neman aurena har ta kai a yanzu babu wani namiji
23
BAKAR GUGUWA
da ya isa kusantar inda nake bare ya yi min magana matuqar ba
mahaifina ba, har sai wannan shu’umin matsafin ya halakashi,
wannan ne yasa ban yi maka magana ba bare godiya a sanda ka
tava taimakona a farkon haxuwata da kai don jaka ina roqonka
ka nisanta kanka da kusantar inda nake matuqar ba kana so
wannan matsafin ya halakaka ba kamar yadda ya halaka wasu
mutane a baya”.
Zuhairu yace da ita “Ka da ki zama mai raunin zuciya
da zai saka imaninki ya raunana, ki sani cewa tsafi da sihiri
shirka ne wadda ba ta tasiri akan gaskiya, wato addinin
musulunci kuma Allah yana tare da duk wanda ya dogara da
shi zai kuma kareshi daga sharri ma’abota tsafi da sihiri komai
tasirin tsafi sa gareshi na dogara garesa kasancewar shi mai
rinjaye ne akan duk wani aikin sihiri na samu labarin abinda
yake faruwa gareki game da wannan shu’umin matsafin
wannan shi ne dalilin da ya kawoni gareki har na ambata ina
qaunarki cikin yarda Allah sai na rabaki da wannan matsafin
na kuvutar da ke daga halin da kike ciki”.
Gimbiya Hasima ta sake cewa da shi “Ka yi haquri ya
kai wannan bawan Allah, ba na so ka halaka a kaina kamar
yadda wasu da dama suka hallaka saboda ni” Zuhairu yace da
ita “Idan ya samu nasara hallaka wasu mazajen saboda ke a
baya Allah ne ya qaddara faruwar hakan a kansu kuma wannan
ba yana nufin cewa ya fi qarfin hukuncin ubangiji ba, cikin
yarda Allah ni zan zama sanadiyyar halakarsa matuqar bai rabu
da ke ba. Daga kaina ba zai sake halaka wani ba”.
Gimbiya Hasima ta yi shiru ba ta sake yin musu akan
maganarsa ba, bayan wani lokaci ta xago kanta tace da shi
24
BAKAR GUGUWA
“Yaya sunanka kuma ina labarin garinku da abinda yake
kawoka wannan wajen?”
Zuhairu yace “Sunana Zuhairu bin Safwan kuma na kan
zo wannan wajen ne daga birnin samaras dake qarqashin
masarautar mahaifinki” Nan ya sanar da ita dukkanin labarinsa
sannan suka yi sallama, ta kama dokinta ta hau sauran
kuyanginta suma suka kama nasu dawakan suka hau suka yi
masa sallama suka kama hanyar komawa birnin Bahazum sai
da suka yi nisa sannan shima ya kama dokinsa ya hau ya nufi
hanyar komawa gida.
**
Da isar Gimbiya Hasima gida ta sauka daga kan dokinta
ba ta tsaya a ko ina ba sai cikin xakin mahaifinta ta shiga cikin
matuqar murna da farin ciki ta sameshi a zaune cikin halin
damuwa, saboda baqin cikin da ‘yarsa take ciki. Da shigowarta
sarki shaiban ya ganta cikin murna da farin ciki abinda ya daxe
rabon da ya ga ‘yarsa Gimbiya Hasima a cikin irin wannan
yanayi tun daga sanda matsafi Bahalu ya ambata yana qaunarta
ya miqe cikin sauri yana mai matuqar mamakin tare da
tambayarta abinda ya sanyata wannan farin ciki.
Gimbiya Hasima tace da shi “Ya kyautu gareni na yi
godiya ga ubangiji Allah buwayi a bisa taimakon da rahamarsa
da ya saukar gareni” Ta kwashe labarin abinda ya faru gareta
tsakanin matsafi Bahalu da jarumi zuhairu a bakin lambun da
take zuwa ta sanar da mahaifinta.
Ta ci gaba da cewa “Ya samu nasara akansa har sai da
matsafi Bahalu ya gudu da kansa dan neman tsira,ya kuma
xauki alqawarin taimakona da raba tsakanina da wannan
shu’umin matsafin cikin yarda Allah” Sarki shaiban ya yi
25
BAKAR GUGUWA
matuqar mamaki da al’ajabi na jin wannan labari tare da yabon
jarumta da bajinta jarumi zuhairu tare da farin cikin jin cewar
ya xauki alqawarin zai taimakawa ‘yarsa Gimbiya Hasima ya
rabata da wannan shu’umin matsafi ya xaga hannunsa ya yiwa
Allah godiya sannan ya dubi Gimbiya Hasima yace da ita.
“Idan kin koma bakin wannan lambun da kike zuwa ki
ka haxu da wannan jarumin ki ce masa ya zo birnin Bahazum
ni sarki shaiban ina son ganinsa” Gimbiya Hasima ta amsa
masa da cewa za ta sanar da zuhairu abinda ua umarceta
sannan ta tashi ta koma cikin gida wajen mahaifiyarta.
**
Shi kuwa zuhairu da ya koma gida bai sanar da kowa
abinda ya faru tsakaninsa da Gimbiya Hasima ba ya ci gaba da
harkokinsa kamar yadda ya saba.
Washe gari da yamma ya sake yin shiri ya tafi bakin
wannan lambu kamar yadda ya saba, yana zuwa ya sauka daga
kan dokinsa ya xaureshi sannan ya koma inda ya saba zama ya
zauna. Bai daxe da zama ba sai ya hangi Gimbiya Hasima tafe
ta nufo inda yake ya cika da mamaki ganinta ita kaxai ba tare
da kuyanginta ba kamar yadda ta saba wani abu da ya qara
bashi mamaki shi ne bai ganta akan doki ba, kuma ya san ba
zai yiwu ta taho daga birninsu zuwa bakin wannan lambun da
qafarta ba.
Zuhairu ya ci gaba da dubanta har ta qaraso inda yake
tana mai yi masa murmushi sai dai ya sake yin mamaki da ya
ga bata yi masa sallama ba, kamar yadda yake a shari’ar
musulunci ga duk wanda ya zo ga xan uwansa musulmi sai ya
ji ta ci gaba da yi masa magana da cewa “Zuciyata na cike da
farin ciki sake ganinka masoyina, marhabin da zuwanka abin
26
BAKAR GUGUWA
begena cewa dai ni na kasance mai ni’imtuwa da qaunarka a
raina tamkar buguwar numfashi ga dukkan mai rai” Duk da
zuhairu ya ji murya tare da ganin surar mai yi masa magana
tamkar ta Gimbiya Hasima amma sai ya ji yana kokonton
tabbatar da cewar ita ce ya ci gaba da dubanta bai yi magana ba,
zuciyarsa tana shakka ace Gimbiya Hasima ce ya ji a jikinsa
cewa akwai yaudara a cikin lamarin don haka ya yi
takatsantsan.
Ta sake matsowa gareshi tana mai yi masa magana
cikin tattausar murya da cewa “Ya ya na ga ka yi shiru ba ka yi
magana ba, kuma ka qi sakin jikinka da ni kamar kana cikin
wani hali na damuwa”.Ta kai hannu zata tava jikinsa a sannnan
ne ya ji zoben da yake hannunsa ya yi motsi. Alamar wani
ma’abocin sihiri ne ya kusanceshi cikin sauri ya miqe daga
inda yake zaune ya zare takobinsa da take xaure a xamararsa
ya dubeta yace da ita. Duk da jin murya da ganin sura irin ta
Gimbiya Hasima ban yi imani da cewar ke ce Gimbiya Hasima
ta gaskiya ba, don haka ki sanar da ni wace ce ke kuma daga
wane jinsi ki ka kasance, idan ba haka ba kuma na halakaki dan
na ga akwai aikin sihiri irin na ma’abota shirka da vata a cikin
lamarinki”.
Matar nan dake tsaye a gabansa cikin surar Gimbiya
Hasima ta dubeshi ta bushe da dariya sannan lokaci guda sai ta
rikixa daga wannan surar ta koma surarta ta asali wato
Buniyatu Hajir qanwar matsafi Bahalu dake hallaka duk wanda
yace yana qaunar Gimbiya Hasima ta sake dubansa tace da shi
“Lallai ka yi zurfi cikin begen Gimbiya Hasima yadda har ka
ke iya gane cewa ba ita bace koda an suffantu da irin surarta da
ni kake bege kamar yadda kake begenta a zuciyarka babu
27
BAKAR GUGUWA
shakka da na yi farin cikin da babu wata halitta da ta tava yin
kamarsa a duniya. Zai kyautu gareka ka cire qaunarta daga
zuciyarka dan ita ‘yar sarki ce mafi girman daraja daga ‘ya
‘yan sarakunan duniya ba za ta auri wanda ba xan sarki
kamarta ba.
Zuhairu yace da ita “Ba zan so ki ba ba zan aminta da
maganarki ba, kuma babu shiriya tsakanina da duk wani
mutum ma’abocin tsafi da sihiri a duk inda yake ina mai sake
jaddada nasiha gareki ki gaggauta tuba daga halin da ki ke ciki
dan samun rahama idan ba haka ba kuma ki nisanta da inda
nake ko kuma na salwantar da kaifin takobina”.
Buniyatu ta sake yin dariya sannan ta ce da shi “Mai ya
haddasa irin wannan gaba da qiyayya tsakanina da kai
masoyina? Me Gimbiya Hasima tafi ni da kake matuqar
qaunarta har ka kasa amincewa ka so ni kamar yadda ka ke
sonta” Zuhairu ya ce da ita “Shirka tsafi da sihiri sune suka
haddasa gaba da qiyayya tsakanina da ke. Kuma ba zan tava
aminta da ke ba cikin wannan hali da ki ke ciki har abada, ita
kuma Gimbiya Hasima ta fi ki daraja ta addini da hasken
musulunci. Ta fi ki nasaba ta xaukaka da daraja, sannan ke
najasace a bar qi kasancewar kina halin vata da tavewa kuma
za ki zama mafi munin halin vata da tavewa kuma za ki zama
mafi munin makoma idan ki ka mutu cikin halin da ki ke ciki a
yanzu”
Buniya ta fusata da jin maganar da ya faxa ta ce da shi
“Haqiqa ka zama mai muzanci da tozarci matsayina akan
wadda ka ke bege na rantse da girman daraja abin da na gada
na sihirin tsafi da sihirin mahaifina ba don na yi alqawarin
aurenka ba, kuma ba na so ka shiga halin damuwa har ka
28
BAKAR GUGUWA
halaka da sai na xauke Gimbiya Hasima na hallakar da ita
yadda ba za ka sake ganinta ba har abada. To amma ka sani na
yi alqawarin aurenka ta kowane irin hali, kuma ko ba ka
amince ba sai ka zamo miji a gareni har qarshen rayuwarka, ba
za ka auri Gimbiya Hasima ba, ka yi saurare da zuwan abin da
zai faru gareka nan gaba a duk sanda na sake dawowa muka
haxu”.
Tana gama faxar maganar ta vace a fusace cikin
alqaluman sihirinta ba tare da ta saurari abinda zuhairu zai sake
cewa ba da zuhairu ya ga Buniyatu ta tafi sai ya maida
takobinsa sannan ya koma wajen da yake zaune ya zauna yana
tunanin abinda ta ce cikin kalamanta. Bayan tafiyar Buniyatu
ba da daxewa ba, sai ga Gimbiya Hasima tare da kuyanginta
sun iso bakin wannan lambu da zuwansu ba su shiga ciki
lambun ba kamar yadda suka saba sai zuhairu ya ga sun
tunkaro inda yake zaune, suna zuwa Gimbiya Hasima da kanta
ta yi masa sallama zuhairu ya amsa mata sannan tace da shi.
“Na zo gareka ne domin na sanar da kai saqon
mahaifina sarki shaiban ya ce na shaida maka ka zo yana son
ganinka a bisa ga taimakon da ka yi min” Zuhairu ya xan yi
shiru kamar yana tunani sannan ya ce da Gimbiya Hasima
“To” Ya tashi ya je ya kama dokinsa ya hau suka juya baki
xaya suka kama hanyar komawa birnin Bahazu suna tafe suna
hira har suka isa qofar shiga birnin.
Tun daga bakin qofa masu tsaron qofar suka fara duban
zuhairu cikin mamaki da al’ajabin ganinsa tare da Gimbiya
Hasima ba tare da ya hallaka ba kamar yadda suke da
masaniyar cewa duk wani namiji da ya kusanci inda take sai
wannan matsafin ya halaka shi matuqar ba mahaifinta ba. Da
29
BAKAR GUGUWA
suka shiga cikin birni duk inda suka wuce sai jama’ar gari su bi
zuhairu da kallo saboda ganin sa tare da Gimbiya Hasima suna
masu mamaki da ganin wannan al’amarin shi kuma zuhairu bai
damu da abinda yake faruwa ba, suka ci gaba da tafiya har suka
isa fadar sarki shaiban. Bayan sun isa fada Gimbiya da sauran
kuyanginta suka shiga ciki ta je ta sanar da mahaifinta sarki
shaiban zuwan zuhairu ta yi masa iso. Sarki ya bada umarnin
zuhairu ya shiga aka je aka shigo da shi har cikin fadarsa. Tun
da aka shigo da zuhairu cikin fadar sarki shaiban ya dubeshi sai
ya sake cika da matuqar mamaki saboda ganin shi ne jarumin
da ya yi mafarki da shi mahayin doki da ya yaqi matsafi
Bahalu ya halakashi a cikin mafarkinsa, gashi yanzu ya ganshi
a zahiri kuma shi ne wanda ya xauki alqawarin taimaka wa
‘yarsa. Zuhairu ya kai gaisuwa gaban sarki shaiban, sarki ya
amsa masa aka yi masa ishara da wajen zama, ya zauna suka
kaxaita daga shi sai sarki a fadar sannan sarki shaiban yace da
shi.
“Labari ya isheni game da taimakon da ka yiwa ‘yarta
Gimbiya Hasima, tare da alqawarin da ka yi na kuvutar da ita
daga halin da ta ke ciki shi ya sa na umarceta cewa idan ta
koma inda ku ka haxu da ita ta sanar da kai cewar ina son
ganinka. Ya kamata na sake yin godiya ga ubangijina bisa
baiwa da ni’imar da yake saukarwa akan bayin sa, don kafin
faruwar wannan lamari na yi mafarki da zuwan wani jarumi
mahayi doki da ya zo ya halaka wannan shu’umin matsafi ya
kuvutar da ‘yata daga halin da take ciki, sannan a yanzu da aka
shigo da kai fadata sai na ga cewa babu shakka kaine jarumin
da na yi mafarki da shi ya halaka wannan matsafi, don haka
30
BAKAR GUGUWA
nake mai kyakkyawan zato na samun nasara mafarkina ya
zama gaskiya.
Ba za mu zama masu yawaitar mamaki akan abinda ya
faru ba don buwaya ubangiji da ikonsa ta wuce haka, sai dai
mu yawaita godiya gareshi da addu’ar neman nasara, kuma na
yi maka alqawarin cewa matuqar ka rava Gimbiya Hasima da
wannan shu’umin matsafin da ya sanya rayuwarta cikin qunci,
to kuwa zan baka aurenta tunda itama tana qaunarka, wannan
shi ne dalilin da ya sa na ce ta sanar da kai ina son ganinka
Allah ya yi maka albarka”. Zuhairu ya yi matuqar farin ciki da
jin wannan bayani na sarki shaiban saboda qaunar da yake
yiwa Gimbiya Hasima ya yi masa godiya cikin girmamawa tare
da tabbatar masa da alqawarin da ya xauka na taimakawa
Gimbiya Hasima akan sha’anin matsafi Bahalu.
Daga nan suka yi sallama da sarki shaiban zuhairu ya
tashi ya fita daga fada ya koma wajen su Gimbiya Hasima ya
sanar da ita abinda ya faru tsakaninsa da mahaifinta Gimbiya
Hasima ta yi matuqar murna da farin ciki, sannan ta sa aka kai
zuhairu wani xaki na hutawa, abin