cikinsa a sanda matsafi
Bahalu ya bayyana. Sannan kuma sun sake ganin fitowar baqar
guguwar daga cikin kogon dutsen ta tashi sama. Daga nan sai
suka ji wannan tsawa mai tsananin qarfi da ruggugi na
fashewar dutsen har sai da suka razana suka ja baya, saboda jin
wannan qarar, sannan sai suka ga dutsen da zuhairu ya shiga
cikinsa ya dagargaje ya fashe.
Hankalin Buniyatu da na sauran jaruman ya yi matuqar
tashi, suka razana matuqa da ganin fashewar dutsen da zuhairu
yake ciki, Buniyatu ta tashi cikin kixima da ruxani ta nufi
wajen da dutsen yake, amma hucin wutar da ya gauraye wajen
ya bugi jikinta tsananin zafi ya sa ta kasa qarasawa inda wutar
take. Dole ta juyo ta dawo da baya, ta fashe da kuka dan razana
da tunanin zuhairu ya hallaka. Suma sauran jaruman da suke
105
BAKAR GUGUWA
tare da ita jikinsu ya yi sanyi, saboda ganin abinda ya faru babu
wanda bai yi zaton zuhairu ya hallaka ba daga cikinsu.
Suna tsaye cikin wannan hali na fargaba da jimami sai
suka hangi zuhairu ya keto ta cikin duhun hayaqin da ya
lulluve wajen. Sai dai ga alama ya yi matuqar jigata saboda
ganin yadda yake tafiya a galabaice. Nan take fargabarsu ta
koma farin ciki suka yiwa Allah godiya da ya sa zuhairu bai
hallaka ba, wasu daga cikin jaruman suka tafi gare shi suka
taro shi, suka qaraso da shi inda suke tsaye suna jiransa. Suka
kai shi gindin wata inuwa mai sanyi, suka zaunar da shi dan ya
samu nutsuwa ya huta.
Bayan zuhairu ya huta, ya shaida musu ya samu nasarar
abinda ya shigar da shi kogon dutsen ya basu labarin abinda ya
faru tsakaninsu da boka Afrahu har ya mallaka masa mukullin
da zai buxe waxannan qofofi da kuma bayyanar matsafi
Bahalu ya hallaka Boka Afrahu, da abinda ya faru tsakaninsa
ya yi nufin hallaka shi, su Buniyatu da sauran jaruman da suke
tare da shi suka yi farin cikin samun nasara tare da yin godiya
ga Allah da ya kuvutar da zuhairu daga mugun nufin matsafi
Bahalu bai hallaka ba.
Da yake yamma ta qarato rana ta kusa faxuwa sai suka
samu waje suka yada zango dan su kwana anan kafin gari ya
waye su ci gaba da tafiya.
**
Da gari ya waye su zuhairu suka yi sallar asubahi, suka
yi addu’ar sannan suka tashi suka kama hanya, suka ci gaba da
tafiya kafin rana ta xaga sama sosai suka isa lardin Ashtar da
shigarsu cikin lardin suka ji yanayin wajen ya sauya gaba xaya
dajin ya yi duhu wani farin hayaqi ya gauraye ko ina, iska mai
106
BAKAR GUGUWA
tsananin zafi dake busar da maqoshi tana busawa daga ko ina
suna qara shiga cikin lardin zafin da suke ji na daxa qaruwa.
Haka suka wanzu suna tafiya har rana ta kusa faxuwa
suka yada zango a lokacin zuhairu ya basu shawarar yadda za
su bi wajen yaqar waxannan sadaukan. Jaruman suka amince
da shawarar da zuhairu ya kawo akan yadda za su yaqi baradan
da ke bayan tsauni. Sannan masu harbi da kibiya da masu
majaujawa suka je suke voya a cikin duhun itatuwa kamar
yadda zuhairu ya umarce su. Su kuma su zuhairu,Buniyatu da
sauran jarumai masu faxa da mashi da takubba suka tafi suka
tunkari inda rundunar baradan suke.
Da zagayawarsu bayan wannan tsauni sai suka hangi
dandazon baradan nan sun jeru sahu-sahu, sun yi sujjada gaban
wani gunki da ke kusa da tsaunin. Wasu kuma daga cikinsu
suna tsaye dan lura da duk abinda zai tunkaro wannan waje
daga kowanne vangare da ganin su zuhairu sun tunkaro inda
suke sai xaya daga cikin baradan nan ya daka musu tsawa da
maxaukakiyar murya yace da su.
“Kai waxannan al’umma fanxararru, hallaka ta tabbata
a gareku bisa ga shigowar ku lardin Ashtar da zuwan ku
wannan waje da sanin ku ko kuma bisa ga rashin sani na
kuskure. Haqiqa makoma ta munana gareku cikin qasqanci da
zama ababan shayar da jinin ku ga abin bautarmu dan
girmamawa”
Zuhairu ya maida masa da raddi da cewa “Kaicon mai
ambato da abinda yake ambatawa cikin zantukansa marasa
tasiri, ka sani cewa ba ka da ikon tabbatar da hallaka akan mu
har sai wanda ya halicce mu ya tabbatar da hakan a garemu.
Kuma mun yi imani da shi tare da neman taimakonsa don mu
107
BAKAR GUGUWA
karya rundunar mushirikai ma’abota bautawa gumaka wanin
Allah ba Allah da ya halice su ba. Don haka ina mai yin ishara
a gare ku da cewa; hallaka ce ta gabata gare ku da kawo
qarshen shirka da baxala da kuke aikatawa a bayan qasa”.
Mai maganar nan na farko ya fusata da jin abinda
zuhairu ya ambata ya sake yin magana cikin tsawa yace da shi
“Kai dattijo gajiyaye ma’abocin rauni da gazawa ka bari
matasa masu sauran jini a jikinsu su yi magana ba kai dattijo ba
wanda ba shi da tasiri aikata komai na jarumta. Kuma na rantse
da girman daraja gunki da nake bauta a gare shi sai na hallaka
ka don na tabbatar da girmansa da kuke qasqantarwa” Ya fidda
wata irin baqar takobi daga xamararsa ya tasama zuhairu a
fusace da nufin hallaka shi.
Shi ma zuhairu ya fidda tasa takobin ya tare shi suka yi
haxuwa irin ta karon battar qarfe, tare da kaiwa juna sara, irin
na hallaka abokin karawa. Kaifin takobbinsu ya haxu a sararin
samaniya da qarfi barden nan ya ji tamkar sun haxa qaifin
takobi da matashin jarumi sadauki, savanin dattajo mai raunin
da tarin shekaru da yake kallon zuhairu, suka rabu babu wanda
ya samu wani. Suka sake zaburowa sukai sara ga juna zuairu
ya goce kaifin takobin barden ya wuce, kafin ya juyo ya sanya
tasa takobin cikin gwanintar sara da zafin nama ya sare kan
barden ya yi tsalle sama gangar jikin ta faxi qasa daga nan tasa
ta qare bai ko shura ba.
Da ganin haka sai ragowar baradan da ke tare da shi
suka yi qaraji da kururuwa mai qarfi suna ambatan wasu
kalamai da su zuhairu ba sa jin abinda suke cewa. Nan take
sauran baradan da ke cikin halin yin sujjada gaban gunki suka
xago cikin sauri, sannan suka riqa zare makamansu suna
108
BAKAR GUGUWA
tasowa kan su zuhairu da sauran jarumai da suke tare da shi,
suka ja daga cikin shirin artabu da waxannan baradan duk da
cewa idan suka farmusu wani ma ba zai ga koda gawarwakin
su zuhairu ba, saboda tsananin yawansu.
Kafin su isa gare su sauran jarumai da suke tare da su
zuhairu suka soma sakar musu ruwan kibau da jifa da
majaujawa, daga cikin duhun itatuwan da suke voye. Baradan
nan suka riqa zuba qasa matattu tamkar yayyafi. Duk wanda ya
zaburo kan su zuhairu sai ka ga ya faxi qasa matacce ba tare da
san abinda ya hallaka shi ba. Sai dai masu harbi da kibiyar da
jifa da majaujawa suka ci qarfin rundunar baradan, sannan su
zuhairu da sauran jaruman da suke tare da shi suka farma
rundunar baradan da sara. A ka yi arangama da qazamar
haxuwa. Nan take waje ya yamutse, qura ta turnuqe ta tokare
sararin samaniya. Qarar haxuwar takubba ta cika wajen,
kururuwar mazaje ta yawaita. Zuhairu na kai sara cikin baradan
yana halaka su yana qara dannawa cikinsu. Duk inda ya sa
gaba a tsakanin baradan sai dai ka ga wajen ya zame masa
hanyar wucewa. Haka kuma komai yawan baradan da suka
taso kansa sai ya qarar da su gaba xaya, da kaifin takobinsa.
Haka ya yi ta keta dandazon baradan nan har sai da ya isa inda
wannan gunki da suke bauta a gare shi yake, ya xaga takobinsa
ya yi kabbara ya sari kan gunki da dukkanin qarfinsa, ya raba
shi da gangar jikinsa.
Da sare kan gunki sai suka ji wata irin qara mai
tsananin qarfi ta gauraye wajen, gangar jikin gunki ta kama da
wuta. Tsaunin da ke kusa da su ya soma girgiza yana
tsatstsagewa. Da ganin haka sai baradan da ke bauta ga wannan
gunki suka firgita, hankalinsu ya tashi suka gigita, tsaunin da
109
BAKAR GUGUWA
suke samun abinci da abin sha daga gare shi ya tarwatse ya
fashe. Nan take suka soma watsar da makaman da yake
hannunsu suna fantsama cikin daji a firgice. Su zuhairu da
sauran masu harbi da kibiya da jifa da majaujawa suka ci gaba
da hallaka su suna yi musu kisan qare dangi, har sai da suka
ragargaza rundunar baradan suka tarwatsa su, da yawa daga
cikin baradan sun hallaka. Wasu kuma suka fantsama cikin daji
suka arce a firgice dan su tsira daga hallaka da guguwar ajali
da ta turnuqe a tsakanin sannaninsu.
Bayan su zuhairu sun gama da baradan da suka rage ba
su samu damar arcewa aga wajen ba. Suka qarar da su baki
xaya, sauran jaruman da suka voye a cikin duhun itatuwa suka
taho suka haxu da su zuhairu. Suka dubi baradan da suka
hallaka da irin yawansu suka yi godiya ga Allah da ya ba su
nasara akan wannan rundunar mushirikai, suka ga bayansu don
su yi imani da cewa ba qarfi da dabarunsu ce ta sa suka samu
nasara akan su ba, illa taimako daga Allah.
Bayan sun nutsu qurar yaqi ta lafa, sai suka hangi wani
kogi a kusa da inda suke tsaye, Ruwa yana gudana a cikin
kogin garai-garai fari tas da shi. Da yake su zuhairu da sauran
jaruman da suke tare da shi, suna tare da qishir ruwa ga kuma
gajiya ta artabu da gumurzu da suka yi da waxannan barada.
Don haka suka tunkari wannan kogin da nufin zuwa gare shi su
sha ruwa.suna isa inda kogin yake suka fara xiban ruwan za su
sha. Buniyatu da ke tare da su da ta ga abinda suke shirin
aikatawa ta yi musu magana cikin tsawatarwa ta ce da su.
“Kada wanda ya sake ya sha wannan ruwa daga cikin
ku, saboda musifa dake tare da shi” Jaruman nan suka dakata
110
BAKAR GUGUWA
gabarin shan ruwan suna masu saurarenta da jin abinda ta
ambata gare su, Buniyatu ta ci gaba da cewa.
“Babu shakka duk wanda ya sha wannan ruwa daga
cikin ku to kuwa zai hallaka saboda akwai guba irin ta aikin
sihiri a cikinsa. Su kan su baradan da ke zaune a bakin wannan
tsaunin ma’abota tsaro ga fadar matsafi Bahalu ba sa shan
wannan ruwan kogi sukan sha ruwa ne da yake zubowa daga
saman wannan tsauni da yake kusa da su, sai dai idan wani
daga cikin su ya yi laifi akan yi masa azaba da wannan ruwa a
ba shi ya sha don ya hallaka.
Da suka ji wannan bayani na Buniyatu sai suka haqura
da shan ruwa. Suka tashi suka bar bakin kogin, suka xauki
makamansu da sauran kayayyakin su,suka ci gaba da tafiya
duk da tsananin qishirwa da take tare da su, suna masu neman
inda za su samu ruwan da za su sha. Kafin su isa sansanin
baradan ma’abota tsaron da ke gaba.
**
Al’amarin matsafi Bahalu kuwa bayan da ya bar zuhairu
a cikin kogon dutsen Boka Afrahu a sanda kogon dutsen yake
shirin fashewa ya tarwatse. Ya koma fadarsa cikin yaqinin
cewa zuhairu ya halaka a cikin kogon dutsen. Don ya yi imani
cewa babu yadda za’a yi ya kuvuta ya fita daga cikin kogon
dutsen ba tare da ya hallaka ba. Kuma bai sake komawa takan
jaruman da ke tafe tare da zuhairu ba, don ya san ba su da
tasirin aikata komai akansa, kuma ya san za su hallaka ne a
cikin wannan daji saboda ba su da damar shigowa lardin
Ashtar ko kuma su koma inda suka fito, don haka ya maida
hankalinsa ga sauraren haxewar taurarin nan na aikin sihiri da
111
BAKAR GUGUWA
za su tabbatar da mallakar Gimbiya Hasima a gare shi, ya samu
damar kusantar ta.
Bayan kwanaki uku yana zaune a fadarsa, sai ya ga
fadar ta yi duhu, duhun da ke bayyanar da isowar saqo a gare
shi cikin alqaluman sihirinsa. Ya ji an yi ambato a gare shi da
wata firgitacciyar murya mai nuna gajiyawa. Muryar mai
maganar tana raurawa aka ce da shi.
“DARUL UKUB ta karye, sansanin ma’abota tsaro na
farko ga wannan fada mai daraja, wasu jama’a da ba a san
maqasudin abinda ya kawo su ba, ko kuma aka haqiqance
qarfin tasirin abin bautarsu, sun farmaki sansanin cikin wata
sa’a daga cikin sa’o’in da mazauna sansanin suke gudanar da
ibadarsu. An samu tsaiko da tagaiyara baradan ma’abota tsaro
da ke zaune a wannan sansani. Wanda hakan ya jawo
mummunan yanayi na salwantar rayukan baradan cikin
qasqanci. Da yawa daga cikin su sun hallaka, gunkin da suke
bauta a gare shi ya kama da wuta ya qone qurmus. Tsaunin da
suke samun abinci daga gare shi ya tarwatse ya fashe, hakan
tasa sauran baradan suka razana suka fantsama cikin daji akan
samu nasara akan su aka karya sansanin su Darul Uqub ta faxi”.
Da jin wannan saqon sai ran matsafi Bahalu ya vaci,
zuciyarsa ta harzuqa ya fusata da fushi mara musaltuwa ya
tashi cikin sauri ya tafi ga kaskon bincikensa na alqaluman
sihiri don neman sani ga wanda suka aikata wannan al’amari
akan sansanin baradansa.
Bayan ya zana qasa ya share da yin sauran siddabarunsa
cikin alqaluman sihiri. Bayanai suka bayyana gare shi cewa,
zuhairu da ya bari a cikin kogon dutsen boka Afrahu bai
hallaka ba. Kuma shi da sauran jaruman da suke tafe tare da shi
112
BAKAR GUGUWA
ne suka shigo lardin Ashtar suka farmaki sansanin ma’abota
tsaro na farko, suka samu nasara akan su suka karya Darul
Uqub. Kuma yanzu haka suna kan hanyarsu ta zuwa sansani na
biyu don kai hari akansa. Ya yi matuqar mamaki da ganin
yadda suka samu nasara akan wannan sansani duk da tsananin
yawan baradan da ke cikinsa. Wanda ya dogara a gare su don
bada kariya da kiyayewa daga masu kawo hari akan fadarsa.
Hankalin matsafi Bahalu ya tashi zuciyarsa ta tunzura,
ya tashi cikin sauri dan tafiya ga sauran sansanin ma’abota
tsaro guda biyu da suke rage, don ya sanar da su abinda ya faru
ga sansani na farko, ya kuma qara karsashi a gare su akan su
qara tsaurara tsaro da kiyayewa, su kuma hallaka duk jama’ar
da suka ga sun tunkaro fadarsa ba tare da neman sanin ko su
wanene ba.
Da isarsa sansanin ma’abota tsaro na farko Darul maut
ya yi shela da maxaukakiyar murya mai matuqa qarfi da
hauhawa. Ta bakin gunki da suke bauta a gare shi cikin
alqaluman sihirinsa. Baradan da suke cikin wannan sansani
suka yi saurare ga abinda muryar take ambatawa. Bayan sun
gama jin wannan shela gaba ki xaya suka faxi gaban wannna
gunki suka yi sujjada a gare shi don girmamawa. Sannan suka
tashi cikin sauri suka himmatu ga aikata abinda aka umarce su
da aikatawa, suka qara tsaurara tsaro da kariya ga wannnan
sansani na su. Shugaba daga cikinsu ya qara musu karsashi na
qarfin zuciya, don tunkarar duk abinda ya kusanci wannan
sansani na su suga qarshensa su hallaka shi.
Daga nan matsafi Bahalu ya wuce ya zuwa sansani na
biyu, wato Darul musiba. Ya yi shela makamanciyat wadda ya
yi a sansani na farko. Cikin murya mai hauhuawa ta bakin
113
BAKAR GUGUWA
gunki da suke bautawa su ma waxannan baradan suka shiga
shiri kamar yadda sansani barada na farko suka yi. Matsafi
Bahalu bai baro waxannan sansanin barada guda biyu da suke
bada kariya akan fadarsa da kuma yin shirin tunkarar duk
wanda ya ce zai farmaki sansanonin baradan su ga bayansa,
sannan ya koma fadarsa ya zauna cikin yin imani da cewa
abinda ya aikata zai zama kariya gare shi akan duk wanda ya
ke son zuwa fadarsa dan yin yaqi da shi.
**
Su kuwa su zuhairu da sauran jaruman da suka rage tafe
tare da su, bayan da suka bar wajen da suka yaqi sansanin na
farko suka ci gaba da tafiya a cikin wannan daji suna masu
neman inda za su samu ruwan da za su sha. Suka yi tafiya ta
tsayin yini guda ba su samu inda ruwa yake ba, qishirwa ta
tsananta gare su ga zafi da xumamar yanayi na daxa qaruwa
don haka suka yi matuqar jigata da yawansu suka galabaita. Ba
su samu inda ruwa yake ba sai da rana ta kusa faxuwa, sannan
suka riski bakin wata qorama a tsakanin wasu kwazazzabai,
ruwa yana gudanawa a cikinta, suka yi matuqar farin ciki da
ganin wannan ruwa suka isa ga qoramar su ka sha, suka yi
hani’an sanna suka yi alwala su ka yi sallah magariba. Suka
xebi wanda za su yi guzuri da shi idan sun ci gaba da tafiya.
Da yake dare ya yi ga kuma gajiya sai suka yada zango
a bakin wannan qorama dan su kwana kafin gari ya waye su ci
gaba da tafiya zuwa sansani na gaba.
Da gari ya waye suka tashi suka yi sallah tare da addu’a
ta neman samun nasara, sannan suka kama hanya suka ci gaba
da tafiya ba su isa inda sansani na biyu yake ba sai da kusan
faxuwar rana. Tun daga nesa suka hangi qaton tsaunin nan na
114
BAKAR GUGUWA
biyu inda sansanin baradan yake a bayansa, a jikin tsaunin an
yi rubutu kamar haka.
“Wannan shi ne DARUL MUSUBA, sansanin ma’abota
tsaro da bada kariya ga fadar DARUL SABAR na biyu hallaka
ta tabbata ga wanda ya kusanci wannan sansani bisa ga rashin
sani ko kuma don nuna tijara da jin kai”.
Da suka isa inda wannan tsauni yake sai suka dakata
suka sauka a bayanhsa bayan sun huta sun samu nutsuwa sai
zuhairu ya tashi ya tafi don ya leqa bayan wannan tsauni a
voye, ya ga yadda jama’ar da ke cikin sansanin suke saboda su
san ta inda ya dace su farmake su don samun nasara akan su
cikin salon yaqi.
Da zuhairu ya zagaya inda zai iya hangen sansanin
baradan, sai ya voya cikin duhun itatuwa yadda ba za su iya
ganinsa ba. Ya hangi baradan cikin shirin yaqi ba kamar yadda
suka tadda sansani na farko cikin shagaltuwa da bautar gunki
ba, an zagaye wajen da tsaro yadda babu wanda zai iya keta
wajen ya shiga ba tare da sun gan shi ba. Wasu daga cikin
baradan suna kaiwa da komowa a kewayen sansanin xauke da
miyagun makamai. Suna duba da binciken duk abinda ba su
yarda da shi ba, don bada kariya da tsaurara tsaro da kiyayewa.
Zuhairu ya qare musu kallo tare da wassafa yadda za su
kai hari akan wannan sansani, don samun nasara akan baradan.
Daga nan ya tashi ya koma bayan tsaunin inda sauran abokan
tafiyarsa suke. Yana isa gare su ya kwashe labarin duk abinda
ya gani ya sanar da su, sannan ya qara da cewa.
“Haqiqa suna da labarin karyewar runduna ta farko da
hallaar sansanin baradan da ke cikin ta. Don haka suka kasance
cikin tsaurara tsaro da kiyayyewa kada abinda ya faru da
115
BAKAR GUGUWA
sansani na farko ya faru da su. Saboda haka ba za mu tunkare
su kai tsaye ba, don yin yaqi da su saboda suna xauke da
manya makamai a tare da su, za mu yi amfani da hikimar yaqi
ta voye. Za mu farmake su cikin wannan dare kafin gari ya
waye mu qarar da su cikin yarda Allah.
Yadda zamu samu nasara aikata hakan kuwa shi ne, za
mu tafi cikin duhun itatuwan da ke kusa da sansanin gaba
xayan mu mu vuya, kwararrun masu harbi da kibiya da jifa da
majaujawa za su yi ta kai hari akan baradan suna hallaka su
kamar yadda muka yi a sansani na farko. Ni kuma zan bi duhun
dare na shiga cikin sansanin na je na sare kan wannan gunki da
suke bauta a gare shi, idan na samu nasara aikata haka tsaunin
da suke zaune kusa da shi zai fashe ya tarwatse kamar yadda
tsauni na farko ya yi idan hakan ta faru baradan za su razana
zuciyarsu ta karaya da ganin abin bautarsu ya hallaka. Za su
tarwatse su fantsama cikin daji mu kuma sai mu yi amfani da
wannan damar mu ci gaba da saransy muna hallaka su har mu
ga qarshen su, mu karya sansanin na su kamar yadda muka
karya sansani na farko”.
Da zuhairu ya gama yi musu wannan bayani sai suka
tashi suka yi shiri. Bayan sun yi sallah magariba da isha’i suka
tafi can cikin duhun itatuwa da ke kusa da sansanin suka voye.
Can daga nesa suka hangi baradan nan sun kunna wasu
manyan fitilu na itace masu matuqar haske. Haskensu ya
haskake da’irar wajen baki xaya tamkar rana zuhairu ya umarci
masu jifa da majaujawa su fara jifa kan manya fitilun su kashe
su. Jaruman nan suka aikata abinda ya umarce su nan take
dukkanin fitilun suka mutu duhu mai tsanani ya gauraye wajen.
116
BAKAR GUGUWA
Baradan da ke tsaron wajen suka ta so cikin sauri don
sake kunna fitilun zuhairu ya sake bada umarnin akai farmaki
akan su. Masu harbi da kibiya suka soma sakar musu ruwan
kibau. Wanda kibiyar ta fara samu ya yi qaraji da kururuwa
mai tsananin qarfi saboda shigar kibiyar cikin kwayar idanunsa
na hagu. Ya faxi qasa yana wannan qaraji saboda azaba. Kafin
ransa ya fita, sauran baradan suka tafi gare shi don kai masa
xauki su ga abinda ya faru gareshi, kafin su kai kan shi wasu
zafafan kibiyoyn suka keto duhun dare suka fantsama a
tsakaninsu suka hallaka su.
Wasu baradan suka sake tasowa masu jifa da majaujawa
suka farmake su suka hallaka su. Da ganin haka sai sansanin
baradan gaba xaya suka tunkaro wannan waje don yaqar
abinda yake hallaka ‘yan uwansu, suka taso cikin qaraji da
kururuwa irin ta fusatuwa. Jarumai da suke tare da su zuhairu
suka ci gaba da sakar musu ruwan kibau da jifa da majaujawa
suna hallaka su. Nan take waejen ya hargitse qura ta turnuqe ta
qara wanzar da duhu cikin duhun dare zuhairu ya fito daga
inda yake lave ya shiga cikin sansanin baradan ya hau su da
sara, waje ya sake rincavewa,yanayi ya tsananta ga wannan
barada suka shiga halin kixima da ruxani saboda rashin sanin
taqamaimai abinda yake hallaka su cikin daren. Su da kansu
suka riqa kai sara ga kawunansu suna hallaka junansu cikin
duhun dare saboda firgici da ruxewa kafin wani lokaci baradan
nan sun yi raga-raga da junansu suka karya rundunarsu da
kansu.
Zuhairu ya ci gaba da keta tsakiyarsu yana kai sara a
tsakaninsu dama da hagu, cikin tsananin jarumta da qarfin
zuciya, yana hallaka su da haka har ya isa inda wannan gunki
117
BAKAR GUGUWA
da suke bautawa yake. Yana zuwa wajen ya xaga takobinsa
tare da kabbara cikin maxaukakiyar murya mai qarfi ya sari
wuyan gunkin da dukkanin qarfinsa kaifin takobinsa ya sare
kan gunkin ya faxi qasa.
Da sare kan wannan gunki sai suka ji wata irin qara mai
tsananin qarfi da ban firgici ta gauraye wajen tsaunin da ke
bayan gunkin shi ma ya yi qara ya fashe ya tarwatse, qasa ta ci
gaba da girgiza da raurawa mai qarfi kamar za ta tsage jama’ar
dake wajen su nutse a cikinta su hallaka, gangar jikin gunkin ta
kama da wuta, hasken wutar da haske ko’ina baradan suka ga
abinda yake faruwa a tsakaninsu.
Da ganin gunkin da suke bautawa ya kama da wuta,
sannan sansanin da suke samun abinci daga gare shi ya fashe
ya tarwatse, sai baradan nan suka sake firgita da razana da
abinda yake faruwa, zuciyarsu ta karaya suka ga tamkar ranar
hallakace da azaba mai tsanani za ta wanzu a gare su cikin
wannan dare. Nan take suka zubar da makaman da ke
hannunsu cikin tsaro, suka fantsama cikin dajin a firgice don su
tsira daga hallaka.
Su zuhairu da sauran jarumai da ke tare da shi suka tare
su suka ci gaba da hallaka su kafin su kai ga arcewa. Suka
hallaka da yawa daga cikin su sai ‘yan qalilan daga cikin su ne
suka samu nasarar arcewa suka shiga cikin daji ba su hallaka
ba.
Da su zuhairu suka ga sun karya rundunar baradan sai
suka yi matuqar farin ciki da samun nasara akan sansani na
biyu, tare da yin godiya ga Allah abisa wannan nasara da suka
samu. Daga nan suka koma inda suka fara sauka da farko don
su huce gajiya su kwana anan kafin gari ya waye su ci gaba da
118
BAKAR GUGUWA
tafiya ya zuwa sansani na uku, kuma na qarshe. Wanda daga
shi sai fadar Darul sabar inda matsafi Bahalu yake zaune.
**
Can kuma a Darul sabar fadar matsafi Bahalu a cikin
wannan dare mummunan labari ya isa gare shi na karyewar
sansani na biyu na ma’abota tsaro da bada kariya ga fadarsa.
Ya gari da idanunsa cikin alqaluman sihiri, yadda sansanin
baradan suka tarwatse suka bazama cikin daji a firgice. Dan su
tsira daga hallaka da musiba da ta afka musu cikin sulusin dare
wadda ba su san mafarin ta ba, da yawa daga cikin baradan sun
hallaka. Gunkin da suke bautawa a gare shi ya kama da wuta
ya qone qurmus. Tsaunin da baradan suke samun abinci da
abin sha daga gare shi wanda alqaluman sihirinsa suke tare da
shi don tabbatar da kafuwar sansanin shi ma ya fashe ya
tarwatse.
An samu matuqar damuwa da vacin rai mara musaltuwa
tattare da matsafi Bahalu game da abinda yake faruwa na
karyewar sansanonin baradan sa ma’abota tsaro ga fadarsa da
yadda sua zama marasa tasirin bada kariya a gare shi kamar
yadda ya ta’allaqa dogaronsa gare su, sai dai wannan bai sa
zuciyarsa ta sake karaya ba, ko kuma ya zama izina a gare shi
da cewa hallaka na qara kusantar shi cikin kowacce sa’a idan
har su zuhairu da sauran jaruman da suke tare da shi suka samu
nasarar shigowa fadarsa suka iso gare shi. Don ya yarda da
kansa da kuma alqaluman sihiri da ya mallaka, kuma bayanai
cikin bincikensa ba su tabbatar masa da cewa hallakarsa tana
tare da xaya daga cikin waxannan jama’a ba, sannan ya yi
imani da cewa shi mai samun nasara ne akan su, da ma duk
119
BAKAR GUGUWA
wanda yake yin jayayya da shi ko kuma zai tunkari fadarsa da
nufin yaqi da shi a faxin duniya.
Haka ya kasance cikin wannan yaqini da ke zuciyarsa
saboda tsananin shirka da vata irin na ma’abota aikin sihiri da
tsafi. Allah ka tsare mu da wannan al’amari, Ameen.
Can kuwa a birnin BAHAZUM sarki shaiban ya sanya
malamai suna ta addu’a don neman samun nasara ga su zuhairu
akan wannan shu’umin matsafi su kuvutar da ‘yarsa Gimbiya
Hasima daga hannunsa. A kullum aka yi saukar Alqur’ani mai
girma kamar